Breaking News

Bakar Ayah 19

Page 🖤19🖤

 


 

A zaure mlm ya hadu da Bombee tashigo gidannasu,shikuma zai fita sallahr magriba.
Kallonta yayi na ɗan sakanni kana ya jijjiga kai,inda duka da faɗa suna yin aiki,da sunyiwa Bombee a ƴan watanninan,amma abinnata gaba gaba ma yakeyi kaman ana watsawa wuta fetur.
Shuru tayi taji mai zaice,saidai ga mamakin ta,waucewa yayi batareda yace mata komai ba,sauƙyƙyƙyiyar ajiyar zuciya tasaki,dan dama hakan takeso kada yayi mata maganar.
Kao tsaye ɗakinsi ta wuce tacire kayan jikinta,ta canza wasu daban,sallah tayi kafin tafito wajen cin abinci..
Ƙwanon nata abincin ta ɗauka a gaban Daneji wacce take zuba miya akan tuwon dawar da sukayi.
“Hmmm wai ke bana mijiba,amma saiki saka kai kifice daga gida sai magriba ki dawo,idan kika saka masa ciwon zuciya ya mutu ai saiki nemi wani uban koh?”
“Inna daga yau bazan sake fita da yamman ba,nagama fitan yamman dama yau”
“Ohh duk maganar da akayi baki dainaba saida kikaga dama tukunna,kenan bama bacin raina ne ba yanaki fitar,gama fitar kikayi?”
Shuru tayi bata amsawa innartata maganarta ba,inda wani ne dai da yanzu ya karbi amsa.
Cikin dare can misalin ƙarfe sha ɗayah Bombee ta tashi innayi wacce tayi nisa cikin Bombee.
“Ke dallah tashi ki rufe ƙofah ta ciki zan fita”
“Amma addah in baba yakamaki watarana kina fitar darennan fah,ko shiyasa kikace kin daina fitar yamma kin dawo ta dare?”
“Ina ruwanki toh,sauran naji ko wani zance mai kamada shi,saina babballaki a gidannan”
Gadon Bombee innayi ta kalla,inda ta haɗa tsummokara kaman itace akai a kwance,saboda ko baba zai iya leƙosu cikin dare.
Tashi tayi tabi bayan Bombee ta rufe ƙofar bayan ta fita.
Baƙaƙen kayane a jikin ta riga da wando sai hula,rufe idonta tayi kafin ta buɗe su a duhun gidannasu,ga gari yayi baƙiƙƙirin abinda da damuna.
Dan murmushi tayi ganin idonnata yamayar mata duhun zuwa haske,tarau take gani kaman safiya.
Kama katangar gefen ɗakinsu tayi ta ɗale kaman biri.
Kai tsaye gidan su bello ta nufah,nan kam bata tsaya bata ƙarfinta wajen hawa katanga ba,ta ƙofa tayi shigowarta,kasancewar ba ƙyaurene dasu ba,wani ɗan buhu kawai aka saka a bakin ƙofar gidan.
Tumaki suna kwance a tsaƙar gidan ta tsallekesu ta wuce ɗakin gaji.
Ƙyauren ta tura a hankali,tayi sa’a kuwa babu sakata,dan tsabar rashin tsoro duk barayin da ake fama dasu a garin amma ko sakata basu da ita a jikin gidansu.
Gaji ce a kwance ita malm idi akan gadon,ƙasansu kuma ƴaƴane guda uku anyi musu shimfiɗi suna bacci.
Babu abinda yake tashi a cikin ɗakin sai ƙarar gwartin gaji da kuma idi,ƙaremusu kallo Bombee tayi a duhun ɗakin,tareda yamutsa fuska tana toshe hanci,hamamin damuna da warin fitsari ya haɗu da ƙarnin jikinsu,da kuma warin bakinsu da miyar kuka yabada wani irin mummunan wari mai tada zuciya.
Kai barina gama abinda yakawoni nabar ɗakinan,irin wannan wari haka?”
Tsallaka wa tayi kansu tareda hawa kan ruwan cikin gaji,wacce take ɗaya bangaren akan gadon.
Cikin bacci gaji jin an hau ruwan cikinta tafara cewa.
“Kaifah mlm tsiyata dakai kenan,banda jaraba bakada aiki,yaushe ma kayine dazaka sake dawowa,so kake saika tsamamin jiki nakasa sana’ar gobe koh”
“Ba mlm ɗin bane buɗe i donki kiga waye”
Ihu gaji taso kurmawa lokacin data buɗe ido taga Bombee akan a zaune.
Kafin tace wani abu ta tura mata zanin data ɗauka a tsakar ɗakin.
Wuƙar Daneji ta zaro a kunkuminta ta mannawa gaji ita a wuyanta,wacce dama tun jiyan take kaifata,tayi kaifi sosai sai ƙyalli takeyi.
Wani yawun tashin hankali gaji ta haɗiye muƙutt tana zazzare ido.
“Tashi mijinki yanzu nan,sonake nayi muku kashedi kiji shima ya ji,kuma idan kikayi ihu saina girba miki wukar nan a wuyah,zanga dawane kan zaki dafa abincin siyarwar gobe”
“Dan Allah karki girbamin wannan wuƙar,ki bari tsaya yanxunnan na tasheshi,m…alllammm malam ka tashi”
“Uhn menene kike tashina ne,banace miki idan akayi ruwa bazani masallaci ba,ki bari da safe zanyi sallahr”
“Dallah ba sallah bace,in sallah ce ina ruwana dakai,kabarinmu ɗaya,sanda lawakiri yake tafkarka mai ya dameni,wannan rayuwata ce,katashi ka gani ni lusari kawai”
Idonsa ya buɗe yana rarraba ido,tareda lalumo fitila gefensa ya kunna.
Wani madoki ya ɗakko a gefensa tareda buge Bombee dashi saida ta faɗa ƙasan gadon.
sai a lokacinne gaji ta tashi ta zauna tana maida numfashi,.
“Ahh mlm ashe kai jarumine bansani ba,yaudai kayi abin kai,kullum ina cewa kadaina kawomin madoki ɗaki,ashe dai zayyi amfani”
“Me yarinyar nan take a ɗakinna da wannan dare haka”
“Ina zansani nikuma,yanda ka ganta nima haka na bude ido na ganta a kaina ta saka min wuƙa a wuyah”
“Wuƙa kuma mekika mata haka”
“Ina zan sani,inaga danna yiwa innarta kashedin zamukai ƙarane shiyasa,da Alama kasheni tazoyi”
Suna cikin maganar ne Bombee ta tashi ta tsayah tana jujjuya wuyah inda mlm idi ya ɗan sameta.
Hasketa yayi da fitilar hannunsa,take kuwa idonta yakama hasken fitilar,lokaci ɗaya shima yakoma tamkar fitilar dan haske.
Murmushi Bombee tayi jin yanda suke bada sautin mamakin abinda suka gani,amafani tayi da hakan ta wafce fitilar da take hannun mlm idin.
Maida hasken tayi kansu tana enjoying tsoron dayake kan fuskarsu,wanda yake sauƙar mata da nishadin a cikin ranta.
“Hhhhhhh daga kallon idona harkun razana dayawa haka,ohh dama duk gulmar da kuke yaɗawa akan idonnawa na mayune,bakuma gama saninsa ba.
Wani abun dazai ƙara baku mamakin shine,bakwa tunanin yaakayi na fito daga gidanmu da wannan duhun har nazo nan batareda fitila ba……saboda inagani a duhu tamkar rana.
Mai zai faru idan na kashe fitilar ni ina gani ku kuma bakwa gani,sannan kuma ga wuƙa a hannuna?”
Tana gama fadin hakan kuwa ta kashe fitilar ƙitt,duhu ya gwauraye ɗakin,wani irin ɗurar ruwa cikin gaji yayi,sai karkarwa take tana hada gumi.
“Hmm baban Zulaiha ka ajiye wannan itace takake saitawa,ohhh baka yarda dani ba danace ina kallonka,ko na fara faɗamaka a duk lokacin daka motsa,ko kuma idonka ya ƙifta?”
“Wannan ƴa kekuwa mutum ce?”
“Nima ban tabbatar ba tukunna,saidai ku kunriga kun yanke hukunci ai,cewa ni mayyace ina koh?”
“To ina wani abu kike,meyasa kika tsallake gidaje dayawa kika shigo mana nan,mai muka miki,sannan mai kike nema”
“Hhhhh abu daya kuka min sannan abu biyu nake nema.
Innar Zulaiha taje har gida taciwa innata mutunci,dan kawai narama abinda ɗanka bello yayimin,har tana cewa zatakai kotu.
Abinda nakeso shine ta fasa kaiwa ƙarar nan,sannan kuma babu ita babu gidanmu,idan su bello sukayimin abu kuwa babu mai hanani ramawa.
Wannan shine abinda nake nema,inkuma naga sabanin abinda na nema,zan dawo watarana,inna dawo kuwa duk ɗakinnan sai yankaku kuna bacci baku sani ba,kuma bazan bar shaidar ninayi ba,ko an kamani ma kukam kun tafi ai”
Ta karisa maganar tana dariyah.
“Munji hakan ma bazata faruba aniyarki tabiki,dan Allah kuma ki ƙyaleni nida ƴaƴana,yau na yarda ke wacece kam”
“Yarjejeniya ta ɗauru,ni barina tafi gida kar a gane bana nan”
Tana faɗin hakan ta fita daga ɗakin,hankalin ta kwance aikin ta ya kammala.

An dawo labari………

Tunda wanann abin yafaru babu yaran dayasake tsayawa a hanyar Bombee,komai ta fadawa yaro da sauri yake yi babu bata lokaci. A da itace ke shan azaba a wajen yara,amma yanzu tashi ɗaya ya juyah itake zaluntarsu,idan yayanka ya daketa tasake kamaka ta dakaka,haka za’ai tayi har sai kahana yayannaka da kanka,uwar ɗa ma idan taga abin yaƙi dole ta zubawa sarautar Allah ido.
A makaranta kuwa tana shiga aji zayyi tsit,lokacin da takejin yin magana haka zata saka su suna bata labari,idan bataga dama ba babu wanda ya isa ko motsin kirki yayi a ajin.
Ta daina jarrabawa,karatu kam da su jinga ba’a magana,bata komai saidai tazo ta zuba tantirancinta ta tafi gida.
Bata cikin prifect ɗin makarntar,amma hatta head boy saitaga dama yayi abu.
An sha kaita office ɗin head master za’a koreta. Haka zata ce idan aka koreta saita bunkawa office ɗinnasa wuta da daddare,haka dole suka rabu da ita,a samu a tama gama kowa ya huta.
Shiyasa maganin hakan kowa ya daina shiga harkarta,take cin karenta babu babbaka.
Shirye shiryen fara exam ɗin common akeyi a makarantar su,tun waccan shekarar tayi da ƴan ajinsu bata ciba,hakanne yasa mlm Ahmadu sakata akan tasake jarrabawar,yayi niyyar makarantar kwana zai kaita kowa ya huta,shima ya huta da karbar ƙararta,dan abin ƴar tasa yazama sai zubawa sarautar Allah ido. Suje can suyita mata horo kowa ya huta.

 

Forseen

……..”kee Bombee yanzu dan zabar baki ɗaukeni da daraja ba,ashe dana sakaki kije ki zana jarrabawar bakiyi ba,kika cemin kuma kinyi?”
“Danajene an gama shiyasa”
“Hmm to shikenan,ki rubuta ki ajiye,aure zan miki kawai na huta dake,tunda kinƙi karatu saiki tafi gidan miji?”
Ƴar dariyar tayi irin bata ɗauki maganar da ɗumi ba kafin tace.
“Aure kuma baba wai niɗin?”.

😁😁ya kukace toh mutanen bombee?😁😁

 

 

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK1_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

 

*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03

*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna

______________****_______________

 

No comments