Breaking News

Duk karfin Izzata Book 1 Page 21

Episode 21*

💖الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر💖

 

Kalmar shahada kawai hiyana take tagama saddakarwa mutuwa zatayi “kamar daga sama taji an damki kafarta ɗaya,wani dogon numfashi taja tare da sauke nauyayyar aji


yar zuchiya” gaba ɗaya kayan jikinta ya zame ya dawo wuyar’ta daga ita sai ɗan karamin wandon da iya chinya ya tsaya mata ko bra bata saba tula tulan boobs nata awaje “da sauri, DON ya kawar da kan’sa kefe,yana faɗin mikomin hannunki yafaɗa yana ɗaure fuska, hiyana kuwa kayan jikinta ya rufe mata fuska bata ganin’sa hannu kawai ta ɗaga masa ” dogon tsaki yaja san nan ya kama hannu nata ya saki kafarta,ta juya suna fiskantar Juna amma idon ta a lumshe “a hankali ta buɗe ido karaf idonta ya sauka chikin nashi, da sauri ta kawar da idon’ta daga kallansa ” Ke taka karfe ki hauro yafaɗa yana kara ɗaure fuska ” dan Allah yaya prince kayi hakuri wlh bazan iya takawa’ba tayi maganar kamar zatayi kuka ” shiru yayi yana tunani wai meyasa ma naka matane, meyasa ban barta, tafaɗa ba wlh badan yanzu idan nasake’ta ta faɗa tamutu nina yi kisan kae ba da sai na saketa, yayi nisa chikin tunani yaji hannunta na zamewa daga chikin nasa,zata faɗa kasa, da sauri yajawota da karfi tafaɗa kan faffaɗar kirjin’sa” hiyana duk tunanin’ta sakin ta yayi tsabar tsorata datayi sai da numfashin’ta ya ɗauke “jin jikinta ya saƙi ne yasashi kallan fuskar’ta hannu yasa ya ɗago haɓar’ta da’alama ta sume “dogon tsaki yaja yana turnuƙe fuska ya saɓeta a kafaɗar sa yajuya chikin ɗakin da ita a saman sofa ya kwantar da ita ya juya yanufi wajen mirrow
Mayukan sa masu kamshi da tsada ya shafa ya feshe jikin sa da perfumes masu kamshi da tsada a nitse ya gyara gashin kan sa sai sheki da kyalli gashin keyi, gashi dark black ga tsansi, a hankali yake takawa kamar baisan taka kasan yanufi dressing room almost 30mnt yayi a chiki san nan yafito chikin suite baki sosai kayan suka masa kyau asalin kirar kijin’sa na jarumin namiji ya bayya half cover baki yasa a kafarsa ga wata ɗankareriyar agogon daimon a hannun sa sai kyalli yake yana ɗaukr ido ya sake fesa,Dubai perfume a jikinsa yadawo gaban drawer ya ɗau wayar’sa yanufi waje, a hankali yake takawa kamar baisan tafiya dakaga fuskar nan tashi kasan yana chikin bachin rae

A bangaren diyana kuwa da sallama ta shigo palon Aryan baya palo Kai tsaye tawuce betroom nashi, sallama tayi a bakin kofa bata jira ya amsaba,tashiga tsaye yake a gaban mirrow, yagama shiri yana fesa turare, dressing iri ɗaya da DON sukayi,jin anshigo ɗakin’ne yasashi ɗago kai ya kalle’ta tachikin mirrow, “asukwane ya juyo domin ya tabbatar wa da idon itace ko aljana che sosai yake kallan ta “itama shi take kallo dan yau baƙaramin kyau yayi ba ” ina kwana yaya Aryan tafaɗa tana kawar da kanta daga kallan sa “kasa amsa gaisuwar nata yayi ya zuba mata ido yakasa ɗaukewa “Abba yace wae kazo da sauri tana gama faɗin haka ta juya daniyar tafiya,”da kyar ya iya buɗe bakinsa yace inazakije kuma “juyowa tayi a hankali fada zan koma tafaɗa tana turo baki,”ok to jira muje yana gama faɗin hakan ya ɗauki wayar sa,ya nufota “a tare suka jera kamar wasu taurari, kyau iya kyau “kayan nan sun miki kyau sosa, yafaɗa yana kokarin jan kofar palon “Yaya Aryan to tunda sunmin kyau kamin hoto dan Allah ta karisa maganar a shagwaɓe “to tsaya namiki guda biyu da wuri kinga Abba na jiran mu,”to hutona wajen guda 15 ya ɗauke’ta batare daya sani ba,”har sai da tace Yaya Aryan baka gama bane,” nagama amma matso nan na mana mu biyu “da sauri ta matso kusa dashi,ya juyo da wayar yamusu selfie kala 5 san nan yace,to muje “to ae baka nunamin hoton ba a shagwaɓe tayi maganar tana turo baki “mika mata wayar yayi yana faɗin,to muje muna tafiya kina kalla har mu iso, “to tace tare da fara tafiya

Da Sallama suka shiga fada,gaba ɗaya kallo yadawo kansu,” a sukwane Khalid ya ɗago yana kallan su kama yajuyo yana kallan Yusuf yayi da shima Yusuf ɗin kallo Khalid ɗin yake,” Abba naganin su atare ba faɗa ba ɓachin rae a fuskar Aryan sae ma annashuwa daya gani a tattare da Aryan ɗin gawani ɗan murnushi da Aryan ɗin keyi yakai kallansa,kan diyana dake gefensa sun gera kafaɗa rike take da wayan Aryan tanata sakin murnushi”wani daɗi Abba yaji ya lulluɓe sa baima san lokachin daya fara sakin murmushi ba,chikin ransa yana faɗin alhamdulillah alhamdulillah, Allah na goɗema saura Safras kuma ya Allah ka kar’katomin da hankalin sa shima yadawo mutun
“kasa kasa Umar yace wa haidar wai haidar ba wayar,yaya Aryan bane a hannun yarin yar nan,”shine mana haidar yaba shi amsa yana taɓebaki,”Aunty amarya kuwa kamar zata mutu dan bakin chiki tayi kwafa a zuchiyar’ta tana faɗin wlh,nakusa kawo karshen ku,”Ammi da Ummi kuwa ko ajikin su

“jerowa Aryan da diyana sukayi kamar wasu taurari,sae taku suke a nitse diyana na kallan waya Aryan kuwa ya ɗaure fuska yana kallan kasa sai da suka iso tsakiyar fada, Aryan ya juya yanufi wajen zaman su ” da sauri diyana tace yaya Aryan wayan,kafa ta tambaya tana kallan’sa “baga ɗaya jamar wajen ido kawai suka zuba musu “Aryan baiyi magana ba har sai daya kae wajen zaman’l su ya zauna kusa da Khalid san nan ya ɗago ya dubeta kije da wayar idan kingama kallan hoton sai ki kawomin,”mamakine yakama gaba ɗaya family Abba musan man Aiman Aunty mardiya Aunty salma Umar haidar Ammi dakuma Ummi,
“Abba da Khalid da Yusuf kuma sae murmushi suke,”Aunty farida kam tafi kowa murna da hakan, “Aunty amarya na sanyin magana tana tsoran Abba gakuma taron jama’a kar aji kunya,Amma tachi al’washin yin maganin abun ” Aunty Maryam kuwa kamar,zata mutu take ji dan bakin chiki,”kusa da Aunty farida diyana taje ta zauna tana faɗin Aunty farida ki kalla tayi maganar tana nunawa Aunty farida wayar Aryan,dake hannun’ta “ansar wayar Aunty farida tayi tafara kallan hotu nan, mamakine ya bayyana a kam face ɗin ta a hankali ta ɗago kae tana kallan inda Aryan ke zaune,”shima ita yake kallo, suna haɗa ido yama alama da ta kashe masa wayar kar tabari kowa yaga hotan, Jinjina kai kawai Aunty farida alamar to san nan ta kashe wayar ta sa chikin jakarta,”ta chiro wayar ta tamikawa diyana “da sauri diyana ta amsa tana murmushi tafara buga game ” tunani Abba yashigayi ba hiyana ba DON anya lfy kuwa buɗe baki yayi zaiyi nagana sae ga DON yashigo shi kaɗai “taku yake irin na jaruman maza gaba ɗaya Jamaar wajen,sai kallansa suka dan yahaɗu sosai mazama burge’su yake bare mata, kusa da Aryan yaje ya zauna ” gyaran murya Abba yayi ya dubi DON yafara magana Safras ina hiyana take ” shiru DON yayi yana ɗan tunani wacece kuma hiyana,kodai wan nan yarinyar da aka aiko takirani ” Abba ne ya katse masa tunani dachewa wai ba kai nake tambaya ba “da sauri yace tana ɗaki Abba yafaɗa yana turnuƙe fuska “gaba ɗaya idon kowa yadawo kansa “to meyasa kabarta a ɗakin Abba ya tambaya yana karewa DON kallo ” akule yace suma tayi Abba zan zuba mata ruwa kuma na manta Fahad yaje ya’zuba mata ruwa yayi maganar yana nuna Fahad da hannu ” a ruɗe Ammi tace me kamata tsorata kayi koh ” ka daure fuska yayi yana faɗin tazo zata faɗine na riketa ta tsorata da yawane shiyasa ta suma, ya karisa maganar kamar zae fasa ihu dan haushi,a ransa yana chewa wlh badan iyayena,ke min wan nan tambayarba da bazanyi maganaba haba dan Allah ayita sa mutun magana, “Ammi zata sake magana,Abba ya ɗaga hannu alamar tayi shiru “mikewa Fahad yayi daniyar yaje ya zubawa hiyana ruwa “Abba yace kae Fahad dawo kayi zaman ka shi daya razana ta tasume shi zae farfaɗo da ita idan an gama taro sae kaje ka zuba mata ruwan yakarisa maganar yana nuna DON “wani kululun bakin chikine,ya tokarewa DON makoshi a ransa yake wae shin meyasa na tai’maki yarinyar nan ne, meyasa ban barta ta faɗi ta mutu kowa ya huta’ba wlh na tsani yarinyar jifa yadda Abba yake wani magana sae…bae karisa tunanin ba yajiyo muryan Abba na magana, gaba ɗaya fada tayi tsit kowa ya zubawa Abba ido yana jiran yaji wanene sarki

Ina mai farin chikin sanar da al’umma a yau ni Abubakar Khalid saraki zan sauka daga kujerar mulki na miƙawa ɗaya daga chikin ƴa’ƴana “asukwane DON Aryan Aiman Yusuf Fahad suka ɗago suna kallan Abba ido chikin ido suna jiran suji su nan wa zai kira gaba ɗayan su kirjin su sae dukan uku uku yake dukkan su kowa na adduar Allah yasa bashi,bane “Aunty amaraya kuwa sae murmushi take dan tasan abun dasuka kulla” Abba kuwa sake gyara murya yayi hankalinsa kwan che yachigaba da magana,a chikin ƴa’ƴan nawa bakowa bane face Ahmad “dam dam gaban Aunty amarya ya buga ” DON da bai taɓa murmushi ba a rayuwar sa,yau sae daya saki wani cool murmushi “wani nauyayyar ajiyar zuchiya Aryan da Yusuf suka sauke a tare “Aiman kam har da faɗin alhlillah ” nan take zufa yafara ketowa Aunty amarya”Aunty farida kuwa sai alhamllh munyi nasara take faɗi ” zubur Ahmad yamiƙe zai yi magana, Abba ya watsa masa harara, bashi yakoma ya zauna “Abba yachi gaba dacewa ” kubani hankalin ku ban gama magana ba ae,shiru sukayi suka saƙe nitsuwa yanzu ba sae anjima ba waziri kutashi ku naɗa Ahmad a matsayin sabon sarki,Abba nagama faɗin hakan yamiƙe nanfa jama’a suka fara hira masu murna sunayi masu,blach stomach sunayi, “jama’a suka fara turu ruwa wajen gaisawa dasu DON, “a kafara shigo da abin chiye chiye da shaye shaye

“sauri sauri gudu gudu Aunty amarya ta bar fada tanufi chikin gida ɓangaren ta tawuce tana shiga ɗaki tafashe da kuka mara sauti ta ɗaukoh wayar ta tana kuka tafara kiran layin sadiya,”bugu ɗaya sadiya ta ɗaga “chikin kuka Aunty amarya tafara magana sadiya mun shiga uku aikin gagarabadau baiyiba sadiya ba Aryan ko Aiman a kabawa sarautaba, Ahmad akabawa “dan Allah hajiya hajara kiyi shiru kidai na kukan nan,mubi komai a sannu,dan anbawa Ahmad sa rauta sae akache maki bazamu iyasawa a chan zashi bane,chewar hajj sadiya” Aunty amarya ta goge hawayen ta tana faɗin to dan Allah sadiya kikoma wajensa gobe inkinje ki tuna masa da batun aikin yaran nan kinji,dan suma yanzu sun fara wuche gona da iri a gidan nan,bakiga yadda samarin gidan nan suka fara shisshige musu bane har da Safras fa wai yanzuma ɗayar yarinyar tana ɗakin’sa ga shigiyar ɗayar kuma ta makalewa Aryan harda bata wayar sa gashi uban su shi ya ɗaure musu gindi yahana kowa magana a kan yaran takarisa maganar chikin ɓachin rai “kai, kai, abun har yakai haka to wlh dole mutsaya muyi maganin karki damu ae wan nan ni aka taba ba keba dan Safras na zulaihat che dole gobe zan tafi Enugu idan ma gagarabadau bazae iya aikin ba zan tsallaka niger dan ayi mana sha yanzu magani yanzu ” to shike nan sadiya badamuwa bari naturo miki kuɗi yanzu batare data kira amsar Hajj sadiya ta katse kiran ta zauna a bakin gado tachi gaba da kukanta

Sai misalin karfe 1:30 a kagama taro jama’a suka fara watse’wa

diyana kuwa sae chin chocolate suke itada Zahra da amrat “lamrat kuwa tana zaune kusa da yaya Yusuf suna hira kamar wasu kawaye,hiyana kam har yanzu bata farfaɗo ba tana ɗakin DON
Diyana ta ɗaukoh wani carton na chocolate zata buɗe karaf idon ta ya sauka chikin na Aryan dake zaune kusa da Aunty farida suna hira, wani mugun kallo ya wurga mata da sauri ta ajiye chocolate ɗin tana turo baki ” diyana lfy kika ajiye chocolate ɗin ki buɗe mana musha mana chewar Zahra “ni Aunty Zahra bana sha sai dai ku kusha tafaɗa tana kunbura kumatu “Aryan daga inda yake zaune bai san san da yayi murnushi ba dan yadda tayi maganar ”
Daga bayansu sukaji a na faɗin, meyasa bazakisha ba yammata da sauri suka juya dan suga wanene wani hadadɗeb saurayine kyakkyawa mai chikar sura “lfy malam Zahra ta tambaya tana kallan face nashi “zama yayi a ɗaya daga chikin kujerun wajen yana faɗin lfy wajen sister ki nazo” wace sister nawa daga chiki Zahra ta tambaya “gata nan yayi maganar yana nuna diyana da hannu “ɗago fiska diyana tayi zatayi magana caraf suka haɗa ido da Aryan, ” da mamaki diyana ke lallan yadda ya chanza lokachi guda ta shiga tunani wae Bayanzu naga yaya Aryan na ɗan murnushi ba to me aka masa kuma naga idon sa sun sauya sunyi jaa gashi yawani ɗaure fuska”Zahra che ta katse mata tunanin datake dachewa diyana ana miki magana “firgigit tayi tare da sake kallo inda Aryan yake sae taga bashi a wajen dawo da kallonta tayi kan saurayin,dake zaune gabanta “kallon shi tayi from head to toe a gatsale tace waye kai “ajiyar zuchiya ya sauƙe san nan yafara magana nidae sunana walid ni ɗane ga sarkin zaria,kuma maganar gaskiya son ki nake kuma so irin na aure ba wasaba ” wani dariya diyana tayi kafin tace ni kake so amma dai baka da hankali koh to ni matar soja che sojan ma mai manya manyan bindigu “da sauri walid yamike yana faɗin kiyi hakuri wlh ni bansan ke matar aure bace “baki diyana ta taɓe tana mamakin kowaye yafa ɗa masa ni matar aure che daga chewa ni matar soja che to ae ban auri sojan ba tukun nan tayi nisa chikin tunani taji, Zahra na faɗin tashi muje chikin gd muyi wanka muyi sallah “Aunty Zahra wae har yanzu hiyana bata dawoba diyana ta tambaya tana kwaɓe fuska “eh bata dawo ba amma kar ki damu bakiji yaya prince yace tana ɗakin saba “mikewa diyana tayi jiki ba kwari suka nufi chikin gd

Misalin karfe 8 na dare gaba ɗaya family Abba sun haɗu a table ɗin chin abinch har da DON,”Abba yayi gyaran murya yafara magana,ina hiyana take ne yayi tambayar yana kallan Ammi”da mamaki Ammi tace kae badai tun safe yarinyar nan tana sume ba takarisa maganar tana watsawa DON harara “miƙewa DON yayi da sauri dan bai san Abba yafara faɗa yanufi hanyar fita dan shi wlh kwata kwata ya manta da yarinyar,yau kwata kwata bai koma ɗakiba tun daya fita, da sauri yanufi betroom nashi kamar yadda ya kwantar da ita da safe haka ya sameta “dogon tsaki yaja, yajuya yakoma palo ya ɗauko ruwan Faro mai sanyi a freij ya dawo betroom ɗin a gaban gadon ya tsaya,ta buɗe bakin robar ruwan gaba ɗaya ya duddule mata a fuska,”a razane tamike zaune tana ihu,”wani tsawa ya daka mata shoothup, “shiri tayi ta ɗago ido a hankali tana kallansa jikinta sai kerma yake “kawar da kansa gefe yayi yana faɗin tashi kifita min a ɗaki tun ban babballaki ba “da sauri ta miƙe danufin tatafi amma ina wani jirine ya kwashe ta tafaɗi kasa kanta ya bugu da jikin gadon, wani marayan kara tasake dan yinwar datake ji bazai bari tayi kara sosai ba “a fusace DON yace ke me haka kitashi kifita a ɗakin nan nace “chikin kuka da dashewar murya tace dan Allah yaya prince ka taimakeni wlh bazan iya tashiba jiri nake ji ga… Bata karisa maganar ba sakamakon wani mugun kallan daya wurga mata chikin tsawa yace wlh idan baki fita a ɗakin nan ba sai na ballaki “da kyar ta miƙe tana dafa bango tana tafiya, kamar zata mutu ga yinwa ga sarawar da kanta ke mata wasu siraran hawayen bakin chiki da azabar chiwon kae ke bin kunchinta ta kyar ta fito tanufi ɓangaren Ammi “shikuwa DON kwanchiyar’sa yayi a kan katafaren gadon’sa

Abba yaga shiru shiru ba DON ba hiyana sae yace ke diyana tashi kije ki kiramin Safras “da sauri Aryan yace bari na kirasa Abba, batare daya jira amsar Abba ba yayi waje da sauri,”itakuma diyana takoma ta zauna jim kaɗan sai ga Aryan da DON sun shigo a jere tun basu zauna ba Abba yafara tambayar ina hiyana “tatafi ɗakin’su DON yabasa amsa yana ɗaure fuska “da sauri Ammi ta miƙe ta ɗauki plate ta zubawa hiyana abinchi da kanta ta fice daga palon ” Abba yayi gyaran murya yafara magana kubani hankalin ku, kai Safras da kae da Aryan da Khalid da Yusuf wan nan ba shawara bane umarnine gobe inasan kuraka Aisha dasu diyana kauye “a sukwane DON ya ɗago zaiyi magana ganin babu wasa a fuskar Abba ne yasa yayi shiru “nima zanje Abba chewar Aunty farida “aa my daughter bani zaki tambaya ba ae mijinki zaki tam baya,” to shike nan Abba zan tambaye’sa
shiru palon yayi sae karan spoon kawae kakeji “Mikewa DON yayi rae a ɓache ya fita palon”miƙewa Aryan ma yayi yabi bayan sa har yakai bakin kofa sae kuma yajuyo yana kallan diyana ke kikawo min coffee da wuri yana gama faɗin hakan yayi waje da sauri “da ɗai ɗai suka watse kowa yanufi ɓangaren’sa

Da sauri diyana tayi wanka ta shirya chikin wandon jeans blue da yar t-shirt fari, light make up tayi tasa lipsgloss a ɗan jaramin bakin nan nata ga kitso guda biyu a gaban goshi yakai har kan chikinta tasa turaren da Aunty farida ta bata tanufi shoe rack ta ɗauko high heel fari “hiyana na kwanche kan gado tana ta binta ta ido duk a galabaice take, Zahra kuwa tana palo suna hira dasu yaya Khalid da amrat da lamrat,” hiyana na tafi diyana tafaɗa tana kokarin fita da sauri “diyana bakisa ɗan kwali bafa chewar hiyana tayi maganar kamar zatayi kuka dan yadda kanta ke sara mata,”aa hiyana kyale ɗan kwalin nan zafi nakeji bata jira amsar hiyana ba tayi waje “a palo tasamu Zahra yaya Khalid yaya Yusuf lamrat da amrat sae hira suƙe ” har kasa ta duƙa ta gaida su Yusuf ” “khalid yace wow my sister irin wan nan kwalliya haka ina zakije “hannu diyana tasa tarufe fuskar’ta ta mike tana faɗin zanje na kae wa yaya Aryan coffee ne “kallon Yusuf khalid yayi suka haɗa ido suna ɗan murmushi Yusuf yajuyo ya kalleta yace to yi sauri kije kinji sister “bata jira ya karisa maganar ba tayi waje,dan daman yaya Aryan yace tayi sauri takawo mar gashi ta ɓata lokachi wajen wanka da kwalliya “kichin tanufa a gurguje ta haɗa masa coffee ɗin,ta ɗauka tanufi ɓangaren’sa

Da sallama a bakin ta tashiga palon zaune yake saman sofa yana latsa waya karisa shigowa palon tayi gaban sa tazo da ɗuƙa a nitse tace yaya Aryan ga coffee ɗin,”shiru yayi tamkar baiji me take faɗe ba, yachi gaba da latsa wayar sa shiru shiru almost 10 mnt “a shagwaɓe takuma chewa yaya Aryan pls ka ansa mana wlh nagaji “tam kar bai’san da mutun awajen ba ko motsi bai yi ba wayar sa kawae yake latsawa shiru shiru almost 15 mnt again”a hankali tamiƙe tanufi ɗan karamin table ɗin dake tsakiyar palon ta ajiye coffee ɗin takama hanyar fita daga palon “ke zo nan yayi maganar chikin tsawa wadda yasa sai da ta tsorata “da sauri ta juyo tana kallan sa fuskar nan tasa kamar bai san menen dariya ba ga idon sa sun jaa, wani tsoran sane ya dira mata a rae da,gudu gaske ta juya zatayi waje amma sae dae ta’manta high heel tasa “a zafafe yamiƙe taku ɗaya ya ɗamko gashin kanta ta baya”kware baki tayi zatayi ihu yasa hannu ya rufe mata baƙi,a fusace yake faɗin kimin shiru ko na ɓabballaki a chikin ɗakin nan ” shiru tayi tana zare ido”sakin ta yayi yana kallan face nata chikin tsawa “yace me yahaɗaki da wan chan yaro “wani yaro kuma tafaɗa tana zare ido” nikiƙe tambaya wani yaro, dawaye kukayi hira ɗazun a fada “baya baya ta farayi yana binta har suka kure bango “bazaki bani Amsa ba sai na ɓallaki yayi maganar chikin tsawa “muryana na rawa tafara magana,wlh yaya Aryan,ban san shiba shine kawai yazo yace yana so na kuma ni nafaɗa masa ni matar sojane “ido kawai ya zuba mata yana kallan yadda lips nata ke motsi,wani irin sabon yanayi yake ji yana ratsa jini da kowanni jijiya na jikin sa har izuwa zuchiyar sa “yatsa ɗaya ya ɗora a kan lips nata yana faɗin shiiiiiii alamar tayi shiru dan inta chigaba da magana zata iya zautar dashi “ɗago ido tayi tana kallan sa shima ita yake kallo, da kyar ya iya buɗe baki muryan sa har sarke wa yake “wae bana hanaki yin kwalliyar dare ba yayi maganar tare da chire yatsar sa daga kan lips nata “murya na rawa tafara magana kayi, kayi,kayi,hakuri ba…. chikin sauri yasake ɗora yatsan sa a kan lips nata yana girgiza kai ” ido kawai ya zuba mata yana kallon ta a hankali ta ɗago idon ta itama tana kallan sa matso da fuskar sa yayi dab danata har suna iya jiyo nunfashin Juna “zaro ido waje diyana tayi tana..✍️✍️

Sorry masu karatu sai mun haɗu gobe

*💫STAR LADY💫*

 

*DUK ƘARFIN IZZATA*

_💖Story And Written💖_
⬇️
*Star Lady*

*

 

No comments