Breaking News

Furar Danko 31

 

 

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

 

 


 

 

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗

 

 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣1️⃣

 

 

 

………“Mtsoww! Kaifa baka da aiki sai gantali, a ina kuma kake haka irin wannan lokacin?”.

“Kai mai maganar a ina kake? Kujimin sa ido. Kodan kaje Kano kai ka koma ɗan

gargajiya”.

Ƙaramin tsaki Mm atik yay da faɗin, “Ɗan iska banda time ɗinka. Nifa magana mai muhimmanci na kira muyi, ka ɗan fita gefe Please nasan kana nan nane da cingam gal ɗin nan taka”.

“Naji, na matsa ɗan shiga sharo, ina saurarenka”.

Ɗan tsaki MM Atik yayi, dan harga ALLAH ya tsani budurwar abokin nasa da tabi ta kanainayesa ta hanashi rawar gaban hantsi. Cikin ture batunta ya ce, “Akan yarinyar nan ce dana faɗa maka. Plan ɗin mu na jiya fa ya rushe bata shiga tarkon ba”.

“Whart! Wai kana nufin ka aiwatar?”.

“Eh mana yau ɗin nan ma, amma sai…..” ya zayyane masa komai da ya faru. Da ga can Arman yay ƴar dariya da faɗin, “Wai driver? To ko dai shima yana hutawar ne?”.

“Mtoww bana jin hakan gaskiya. Dan randa na fara haɗuwa da ita na gansa. Yanda ta yarfashi ma sai ya baka tausayi. Kawai dai irin mutanen nan ne masu shegen shishshigin tsiya. Nidai yanzu manta bani mafita”.

“Ni dai mafita ɗaya na hango maka nasan kai kuma baka buƙatarta”.

“Waccece? Please tell me!”.

“Aure!”.

“Mtsoww auren ƙaniya. Nima ina tunanin haka, sai dai banda shiri gaskiya na zama da mace yanzu, ban san takura kai ma ka sani….”

“Ka tsaya nakai ƙarshe mana”.

“Oh sorry ina jinka”.

“Abinda nake nufi bawai auren nata zakai ba. Tunda ka riga ka ƙwallafa ranka ka zama cingam boy kuma ita bazata samu ta sauƙi ba kawai kasa su Dad gaba aje maka neman aurenta…..”

“Baka da hankali! Dad fa? Kasan waye Dad kuwa?!”.

“Calm dawn mana my man. Lamarin fa duk lissafine. Yanda Dad keda alfarma na tabbatar sun san juna da babanta tunda kace itama ƴar manya ce. So da zarar magana ta shiga kai kuma sai kaita jan ra’ayinta harka samu cikar burinka. Daga haka mu ƙirƙirar mata laifin da shi Dad ɗin da kansa zai ce bazaka aurenta ba”.

“Woow! Woow woow my dear wannan salon yayi kuma zai ƙayatar. Sannan ita kanta zan firgita lissafinta tasan ba irinmu ake ja a ƙasa ba. A safiyar yau ɗin nan zan zauna da Dad, nasan zai matuƙar ɗaukar abin da muhimmanci tunda dama burinsa kenan shi da Mom. Kai dai ALLAH ya barka da cingom gal taita ƙarar maka da ruwan kai bye”. Ya yanke wayar yana wani jin matuƙar farin ciki tamkar ya samu Lulu ƙamshi ɗin ya gama ne.

 

Ni ko na ce, “Hummm!”

 

 

★★★

 

Kamar yanda Alh. Baita da Hon. Nakowa suka girgiza da jin Mawaddat ɗiya ce ga Alhaji Isma’il Jiƙamshi haka shima Hon. Misau yay matuƙar girgiza da batun. Dan abune da ko’a lissafin hasashe basu taɓa kawowa ransu ba. A take suka zauna teburin shawara. Dan kuwa tabbas wata dama ce a yanzu tazo hannunsu akan Alhaji Isma’il Jiƙamshin. Kuma lokaci ne na ɗaukar fansa da zai goge tarihin baya labarin yazo da salon alƙalamin da sune zasu zama masu rubuta shi.

Tsaf suka kammala tsara komai a yanda suke buƙata. Fatansu kawai nasara da kuma sake sabon bincike dan ƙara riƙe hujjoji masu ƙarfi musamman akan Alhaji Sufi Garko da suka yanke shawarar tunkara a farko. Dan tabbas babban ɗaurin huhun goro suka shirya yima uban da ƴar gaba ɗaya dan su kasance gaba ɗaya a tafin hannunsu. Basu sa wasa ba tun a ranar suka nema appointment ɗin ganawa da babban ɗan kasuwar, kuma ƙusa a ɓangaren siyasar arewacin kasar musamman ma Kanon ta dabo Alhaji Sufi Ado Garko. Tsoho da kuɗi kenan abokin tafiyar yara, manyan kuwa baba suke kiransa dan ya kere ya kuma zarce koda a tsaransa. An tabbatar musu yaje Umrah sai dai nan da kwanaki biyu idan ya dawo washe gari su shigo. Sun samu wannan damar ne dalilin shaƙama babban yaronsa kuɗaɗe masu kauri, sai kuma mulki da Hon. Nakowa da Hon. Misau ke riƙe da shi wannan ma babban makami ne…..

 

★★★….

 

Ga Alhaji Sulaiman Sufi Garko ma ya gama shiryawa tsaf domin tunkarar mahaifin nasa game da auren Tajuddeen da Mawaddat. Dan a wannan karon ya ɗau aniyar koda yardarta, ko babu sai wanan auren ya ƙullun. Dan ya gama tanadar kalaman da zai tsara mahaifin nasa da su tsaf komai ya tafi dai-dai. Tajuddeen ya samu cikar burin shima ya samu nashi…..

 

★★★….

 

A ɓangaren Lulu ƙamshi da bata san mi suke ba gaba ɗaya hankalinta na kan case ɗin yarinya da akaima fyaɗe ne. Dan anata neman mijin matar amma an rasashi wai ya gudu yabar gari tun a randa yay abun. Wannan takaicin ne ya taru yay mata yawa ta tada hankalin su Sha’aibu ɗan sanda dama na duk wanda ke mata aiki idan irin wannan case ɗin ya taso. Hatta Daddy bata barsa ya huta ba. Ga takaicin Smart yaƙi dawowa aiki itako ta gaji da tuƙi dan sunata zirga-zirga. Shiko Uncle Yousuf ne yace ya zauna gida ya huta har sai jikinsa yay masa ƙarfi. A washe garin kwana na biyu da take saka ran dawowar Grandpa ɗinta da ga umra duk da tarin ayyukanta haka tai wancakali da su ta shiga tawagar ƴan tarbarsa a airport dan ya kwana biyu baya Nigeria, saboda daga uk ganin doctor ɗinsa ya wuce Saudiya Umrah. Tana kewarsa dan tana matuƙar so da ƙaunar kakan nata daya haifi mahaifiyarta da bata sani ba sai a hoto. Shi takema kallon uwa ga shi kuma shine kaɗai ya rage mata a kakanninta dama. Shima kuma a karan kansa yana nuna mata tsagwaron soyayya kasancewar ta ɗiya ga Mawaddat dinsa da ya rasa dan ita kaɗai ya taɓa rasawa a cikin ƴaƴansa shiyyasa yake matuƙar tausayin Lulu.

Ƙarfe kusan sha biyu jirginsu ya sauka. Duk da hango ƴan uwanta jikokin Alh. Sufi Garko da tai su Tajuddeen da sukazo tarbarsa suma ƙin fitowa tai tana daga motar har sai da taji ance jirgin da ya taso da ga Saudiyan ya sauka sannan ta fita. Sanye take cikin gawn ta material mai taushi da santsi da sukai matuƙar mata ƙyau da fidda mata ƙyaƙyƙyawar surarta kamar wata ƴar tsanar roba. Ɗaurin kanta da Amrah (Hussaina) tai mata yayi ƙyau ya kuma rufe mata gashi, sai ta gaba kaɗan da aka zamashi ake iya ganinsa baƙi siɗik a kwance, Kasancewar a ɗaure yake da ribbon sai yay tilluwa a cikin ɗankwalin da aka rufesa da shi ruf. Siririn mayafi kalar material ɗin ta ɗora a kafaɗa babu zancen yafawa. Sai dogon takalmi kamar koyaushe duk da kuwa ita ɗin doguwa ce amma bacan ba tsaka tsaki. Ƙaramar handbag ɗin hanunta ta sake gyarawa da gilashin idonta da ya sake ƙawata kwalliyar tata duk da kuwa a fuskarta babu ko ɗigon kwalliya bayan hoda dan itafa bata kwalliya, sai lips glose data saka a lips ɗinta kaɗan. Yanda take taku kamar wata tarwaɗa da sautin da takalmanta ke badawa ga ƙamshin turarenta data bulbula ya sata janyo hankulan mutane gareta musamman na kusa da ita. Sosai numfashin Tajuddeen ya dinga kaikawo a ƙirji har ta ƙaraso garesu. Ya haɗiye busashen yawun da ya kasa wuce masa a maƙoshi yana ɗan sakin murmushi. Ɗauke kanta tai kamar bata gansa ba, sai ma yatsu biyu data ɗaga musu a taƙaice tare da faɗin, “Hy girls and boys”. Duk wanda yasan Lulu a family ɗin yasan ba kanwar lasa bace, ba kuma wani take ragawa ba. Duk da mafi yawansu sunada labarin tushen asalin arzikin mahaifin nata da ga kakansune wani bai isa furtawa ba tai masa wankin babban bargo ita babu ruwanta. Yanda tai musu gaisuwar cike da raini ya zafi wasu musamman ma matan amma babu wanda ya nuna, to ita bama ta tsaya sauraren amsawar tasu ba tuni tai gaba, dan a dai-dai nan Alhaji Sufi Garko ke fitowa da ga jirgi gefensa p.a ɗinsa ne da shima zai iya kai sa’annin su Daddy. Lallai ya tsufa kam, damma harka irin ta masu hannu da shuni mai wahalar sha’ani. Amma irin wannan tsoho ai kamata yay ace yana zaune gida jikoki zagaye da shi yana hutawa kawai. Cike da ɗoki da farin cikin murmushi mai bayyana haƙora da ke da tsada a fuskar Lulu dan kafin ka gansa ka yara ta nufi kakan nata ta rungume. Shima tashi fuskar ƙawace da murmushin ya tarbi abarsa yana mai farin ciki da jin kewarta har cikin ransa. Sai da ta gama nata farin cikin sannan sauran yaran suma suka matso garesa su Tajuddeen. Suma ya nuna jin daɗin ganinsu dan yana son ƴan jikokin nasa da a yanzu duk suka zama manya samari da ƴammata har ma da masu aure, dan su Lulu kusan sune ƙanana ma duk da dai suma akwai waɗanda suka girma. Da ga haka aka ɗunguma zuwa gida, inda Lulu ta tubure motarta zai shiga dole kuma akai hakan dan kowa yasan rigimarta original ce. Yanzu kam a hankali take tuƙin dan Alhaji Sufi yayi gargaɗi. Daga shi sai ita ne a motar, dan haka taketa masa hira shiko yan biye mata. Tausayinta yake ji fiye da kowa a cikin zuri’arsa saboda maraicinta, ga kuma ƙaunar da yakema mahaifiyarta itama ya shafeta. A gidan ma koda suka iso sai suka samu ƴaƴansa maza da mata da ke cike da gidan duk dai akan dawowar tasa. A duk sanda akai irin wannan taron da wahala kaga Lulu batai kuka ba koda a ɓoye ne saboda jin buƙatar mahaifiyarta itama. Yanzu ɗin ma da ƙyar take iya danne hawayenta, tama ƙi shiga gidan, tana ganin ƴaƴansa sun janyesa ta zame jikinta ta gudu. Tuƙi take tana hawaye da jin kewa mai tsanani, tasan Mommy uwa ce a gareta, amma da gaske tana buƙatar ɗumin mahaifiyarta koda sau ɗaya ne inda ace hakan zai yuwu, sai dai tasan har gaban abada bazai yiwun ba kuma. Gefen titi ta gangara a hankali ta kashe motar ma baki ɗaya ta lafe cikin kujerar idanunta lumshe tai shiru, so take tai kuka amma tana ƙoƙarin hana kanta hakan. Bata cika son shan komai da rana ba musamman a lokacin aiki, sai dai a yanzu babu abinda tafi buƙata kamar tasha ɗin. Duk yanda taso hana kanta taji shan kawai take buƙata. Cikin rawar jiki ta jawo handbag ɗinta, faudanta ta zaro tare da buɗeta acan ƙasa ta ciro wata takarda da’aka naɗa kamar ƙullin magani. Tana warwareta sai ga ƙwayoyi a ciki. Gaba ɗaya kusan fin biyar duk da ƙananu ne sosai ta afa batare da neman ruwa ba ta haɗe abinta tana wani sauke ajiyar zuciya. (Kamar wadda ta haɗu da uwar tata da take nema😔🤦. Ya rabbi ka shiryemu ka shirya mana zuri’a ka rabamu da mummunar ƙaddara😭🙏)………..✍️

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

VIP🔥💯

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments