Breaking News

Furar Danko 34

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

 

 

 

 

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗


 

 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣4️⃣

 

 

 

…….Idanu kawai Daddy ya zubama Mawaddat hawaye na kwaranya saman dattijuwar fuskarsa. Itako sai surutai take musu. Sai ta kalla Daddy tayi ta kalla Uncle Yousuf shima tayi. “Yaya kukan nan fa bashi da wata ma’ana, addu’a itace kawai. Sannan bazan gaji da faɗa makaba ka bada kaso mafi yawa akan shiga wannan yanayin nata. Sai dai kawai muyi ƙoƙarin gyara kuskuren a yanzu. Ga kuma wannan matsalar data kutso kai, duk da dai ni da za’a bi ta tawa da kawai a aura ma Tajuddeen ɗin tunda mun san dai yaron nan bashi da wani aibu a rayuwarsa…..”

“Yousuf matsalar ba daga Tajuddeen take ba da ga mahaifinsa ne. Nasan abinda baka sani ba akan sulaiman sani na haƙiƙa. Kamar yanda na faɗa maka tun a wancan karon Tajuddeen an kwaɗaita masa son Mawaddat ne kawai da manufa, sai dai shi yaron ya afka batare da sanin manufar mahaifin nasa ba, ko kuma dama yana son nata shiyyasa Sulaiman yay amfani da wannan damar wajen sake jan zuciyarsa da tunanin hakan zai bashi nasara akaina.”

“To amma yaya ai shine zai zauna da ita ba Mahaifinsa ba. Indai har mun tabbatar da yana son nata kamar haka banga aibun aura masa ita ba. Na sani ka sani Mawaddat bata kula kowa, ta ina shi mijin daka ambata gaban Baba zamu samar da shi? Dan kasan dai in har babu wannan mijin to dolene Mawaddat ta auri Tajuddeen tunda baba da dangin mahaifiyarta duka sun ɗauki abin da muhimmanci bakuma zasu taɓa bijirema umarnin mahaifinsu ba kamar yanda suka saba”.

“Duk nasan da wannan Yousuf. Kuma nima damuwata a yanzu shine ta yanda zamu samar da mijin koda ace na wucin gadi ne kafin ƙura ta lafa.”

“Wucin gadi kuma?”.

“Yes wucin gadi, dan ba zan taɓa yima yaranmu ko ɗaya auren dole ba. Auren ma da jini irin na Sulaiman mai shirye da manufofi masu yawa da sai anyi auren ne sun fara bayyana zaka fara dana sani kai kanka”.

Shiru kawai Uncle Yousuf yay yana kallonsa, shi kam gaba ɗaya ma a wannan gaɓar ya shiga ruɗani zai ce. Ya kasa fahimtar ainahin abinda ke tsakanin yayan nasa da yayan matarsa da a shekarun baya suka kasance shaƙiƙan abokai da ko ƙuda baya iya jin sirrinsu. Anya kuwa yayansa baya ɓoye masa wani babban al’amari da ya kamata ace ya sani…..

“Assalamu alaikum”. Sallamar Smart a ƙofar falon ta katse tunaninsa. Daddy ne ya amsa tare da bada izinin shigowa dan ya shaida muryar yaron. Akan Lulu da ke kwance a ƙasa barci na neman rinjayar idanunta tana kokawar hanashi ya fara sauke idanunsa. Kaudasu yay duk da sanye take da hijjab ɗin da ya saka mata har yanzun. A nutsensa ya gaishe da Daddy, tare da ajiye key ɗin motar hannunsa. “Sannu da ƙoƙari fa, ALLAH ya saka maka da alkairi kaji”. Daddy ya faɗa a karo na farko. Ɗan murmushi Smart yay cikin jinjina kai. “Babu damuwa ai Alhaji. Nima na gode. Bara na wuce gida”.

Godiya Daddyn ya sake masa, tare da zaro kuɗaɗe masu yawa da ga aljihunsa ya miƙa masa. Kallon kuɗin Smart yay da sake sakin murmushi mai ma’anoni da yawa sai kuma ya girgiza kansa. “A’a Alhaji nagode sosai. Amma bazan amsa ba, albashin da ake biyana ya wadatar dani ALLAH ya ƙara buɗi”. Mamaki matuƙa Daddy ya shiga, dan haka ya kalla Uncle Yousuf da tun shigowar Smart ɗin baice komai ba. Kafaɗa ya ɗage masa alamar haka yake. Ai Daddy kasa ƙara cewa komai ma yayi har Smart ya sake musu sallama ya fice abinsa…..

 

★★ *_8:25pm_* ★★

 

Ƙarfe takwas da kusan rabi na dare tawagar Hon. Babale Nakowa da su Alhaji Baita suka isa gidan Alhaji Sufi Ado Garko kamar yanda suka tsara. Ziyara ce ta bazata, dan haka Alh. Sufi yay mamakin zuwan nasu duk da kuwa su dukansu sun kasance yaransa ne ta fannoni daban-daban kafin yau. Sai dai duk da kasancewar wannan zuwa nasu ya kasance na bazatan hakan bai hana su sami tarba ta mutuntawa ba. Bayan sun gaisa da Alh. Sufi cikin girmamawa a matsayinsa na _God Father_ nasu sai kuma hira ta ɓalle mafi ƙarfi akan kasuwanci da siyasa. Sun ɗan taɓa hira kafin Hon. Misau ya fara bayani akan abinda ya kawosu.

“Ranka ya daɗe mufa zuwan nan namu kamar gaisuwa ce da roƙon iri. Munzo mu maka Barka da dawowa da kuma yaya jiki sai kuma babbar magana mai alaƙa da son ƙulla sabon zumincin da muka san kaima zakayi farin ciki da shi”.

Cikin mamaki da dattijantaka Baba yay murmushinsu na manya idonsa akan Alhaji Misau. “Jeka maganarka kai tsaye Ɗan kande! kasan ni a koda yaushe nafi buƙatar abu abuɗe fiye da rufa-rufa”.

“Hakane Baba”.

Cewar Hon.. Misau cikin murmushi da sake gyara zama. Sai da ya ƙara juya zancen a ransa ta yanda zai fito da armashi sannan ya cigaba da faɗin, “Akwai wata yarinya a cikin zuri’arka da Alhaji Haruna ya gani ya kuma ji ta kwanta masa matuƙa a rai saboda nutsuwarta da hankalinta. Da farko mun shirya tunkarar mahaifinta sai kuma mukai tunanin ai baba ma da babansa. Shiyyasa muka dakata har sai yau daka dawo mukazo da ɗumi-ɗumi dan a tabbatar bada wasa muke ba”.

Murmushin mai cike da jin daɗi Alhaji Sufi Garko ya saki tare da faɗin, “Kai kai Masha ALLAH. Masha ALLAH, naji daɗin hakan kuma zanayi matuƙar farin ciki saboda sani da naima Haruna a rayuwa da nagartarsa. Amma wace yarinya ce wanna haka?”.

Yanzu kama Hon. Baita ne ya nisa shima da murmushin shinshino nasara akan fuskarsa ya ce, “Baba sunanta Mawaddat. Ƴar wajen Alhaji Isma’il Jiƙamshi. Kaga a gareku ku jikace.”

“To to! Ko kaine dama yake faɗa mijin data fidda ɗin? Dan ɗazun dama muke magana akan ɗan wajen Sulaiman da aka taɓa son haɗa su sai abin bai yiwu ba da yake a lokacin ba matarsa bace.”

Kallon juna sukai kowanne zuciyarsa kamar zata ɓallo ƙirji ta fito, sai kuma suka haɗa baki wajen faɗin, “Aiko bazai wuce hakan ba kam”.

Duk da maganar ta ɗan yima Alhaji Sufi Garko gingirin a zuciya sai kuma hakan bai hanashi jin daɗi ba da nuna farin cikin sa. Dan haka babu wani kwalo-kwalo ko jan magana ya tabbatar musu suje gida insha ALLAHU zuwa gobe su dawo garesa da shirinsu bayan sallar azhar zasu samu amsa mai gamsarwa. Dan ya tabbatar musu duk da shi kaka ne ta ɓangaren mahaifiya yana da nasa ƙarfin ta wani fanin ma ubane shi ga mahaifin nata shima ai. Farin ciki iya farin ciki sun shiga, dan haka suka tafi da ƙwarin gwiwar samun nasara batare da sun sha wata wahala ba. Gefe ɗaya kuma suna dariyar muguntar kama Daddy a tafin hannunsa ta inda bai zato ba ko tsammani. Ko a mota hirar da suka dinga yi kenan cike da jin alfahari…..

 

★★ ……

 

Tun bayan wucewar Uncle Yousuf da ya maida Mawaddat ɗakinta batare da ko ɗaya a cikin ƙannenta ya ganta ba shima ya shige nasa ɗakin ya kulle kansa dan samun damar yin isasshen tunani. Ƙarar wayarsa ce ta katse masa dogon lissafin da zuciyarsa tai nisa a yi. Jawota yay cikin jan ƙaramin tsaki zai kashe yaci karo da sunan _Baba garko._ Tashi yay zaune sosai, sai dai bai ɗaga ba har sai da ta yanke shi yay kiransa. Dan haka dama yake masa. Cikin girmamawa ya gaida ogan nasa kuma surukinsa. Da kulawa Baba ya amsa. Ta re da faɗin, “Isma’il ko ka fara barci ne na tasheka amin afuwa. Na kasa haɗiye abin farin cikin nan ne shiyyasa na nemeka yanzu ɗin. Ashe baƙon da kake maganar ɗazun na gida ne…..”

“Baba baƙo kuma?”.

“Eh baƙo mana Isma’il. Mai auren Mawaddat mana. Dan yanzu nan suka wuce su sarakan zumuɗin ma sun kasa haƙuri har sun kawo kansu. Ko kuma ja’irar ƴar taka ce ta turosu ma dan kasanta da gaggawa”.

Sosai ƙirjin Daddy ke lugude. Duk da shi sam yama kasa fahimtar Baba ɗin yanda ya kamata. Kasa jurewa yay dai yace, “Baba kai min afuwa. Wlhy ban gane akan wa kake magana ba. Dan inada tabbacin Mawaddat bata turo kowa ba kasancewar ma ni bamu zauna magana ba dan na sameta kwance a gida ma kanta na ciwo tun bayan ɗakkoka airport”.

“Tofa wata sabuwa kenan? Su Alhaji Baita ne fa suka sameni a daren nan kan wai Hon. Haruna Dauda Nakowa na son Mawaddat har ma sun dai-daita kansu kaima kuma kasan maganar ma. A yanzu haka ma na basu damar dawowa a gobe idan ALLAH ya kaimu da shirins…..”

Cikin suɓutar baki Daddy ya furta, “What! Su Alh. Ɗan-kande Baita fa kace baba?”.

“Eh ƙwarai su ɗin fa na faɗa Isma’il. Shin akwai matsala ne?”.

Yawune ya nema sarƙe Daddy, da ƙyar ya iya figo glass cup ɗin ruwa dake a bed side drawer ya kwankwaɗa. “Baba ni wlhy bamma san akwai wata alaƙa tsakanin Mawaddat da su Alhaji Baita ba sam. Sannan kuma bana jin ita ɗince ma ta turosu. Dan yaron da take so ɗin wanine daban”.

“Ikon ALLAH to mi hakan ke nufi?”. Cewar baba. Daddy da takaici da damuwa suka lulluɓe a lokaci guda ya ce, “Baba wlhy ban san manufa ko dalilinsu nayin duk hakan ba. Danni nasan Mawaddat bata da wani alaƙa da su”.

“Uhhmm to kaga ina ganin mu ajiye maganar nan to. Amma ka tabbatar gobe idan ALLAH ya kaimu a  wajen taruwar meeting ɗin nan kazo min da Mawaddat, idan ma zai yiwu harda shi wanda take so ɗin”.

Godiya Daddy yay masa. Yayinda tuni yay jagaf da zufa. Kamar wanda ya fito a wanka. Gaba ɗaya lissafinsa ya rushe shi yanzu ma baya gane komai ma. Wayar ya ɗauka yay kiran Uncle Yousuf. Ba’a ɗaga ba sai da tai gab da tsinkewa. Ko sauraren tambayar da Uncle Yousuf ɗin ke masa bai yiba. Sai ma katsesa yay da faɗin, “Yousef akwai matsala. Tabbas akwai matsala. Amma ka jirani ina zuwa gidanka ɗin yanzu”.

“Haba-haba yaya da kanka. Inaga ka jirani kawai gani nan zuwa”.

“Karka damu Yousuf kai dai ka jirani kawai. Nan ɗin zaifi sirri ”.

Babu yanda Uncle Yousuf ya iya dole yabi umarnin nashi yay zaman jiransa. Mintinan da basu wace goma sha ba sai ga Daddy ya iso……….✍️

 

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

VIP🔥💯

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments