Breaking News

Furar Danko 52

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

 


 

 

 

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗

 

 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣2️⃣

 

 

……Shirye-shiryen biki kam ya kankama ta kowanne ɓangare. Yayinda shima Abba ya goce batun tada mutane da ga gidan su Ammah a gyarama Smart. Yana ganin hakan zai zama su kuma an cuta musu. Gara dai kawai a kama masa haya na shekara biyu idan zai samu kafin aga abinda ALLAH zaiyi kuma. Ana cikin wannan lissafi sai ga Coach ɗin su Abdull-Hameed yazo da batun Smart ya amsa gidansa da ke anguwar sharaɗa ya zauna har sanda ALLAH zai hore masa nasa. A cewarsa wannan itace tasa gudummawar. Da farko dai Smart ƙin yarda yay, sai dai ya kafe akan zai biya kuɗin hayar gidan, sai da Coach ya nuna masa ɓacin ransa akai sosai harda faɗin ashe shine keta haukansa Smart ɗin bai ɗaukesa matsayin Yaya kamar yanda shi yake masa kallon ƙaninsa Ahmad ba, yay fushi zai tafiyarsa sai da ƙyar Smart ya bashi haƙuri ya tsaya suka tattauna. Da ga ƙarshe dai Abba ya ce an amshi gidan sukai godiya da sanyama Coach ɗin albarka dan ya jima yana ɗawainiya da Smart. Duk wani matakin nasara akan ball shine riƙe da hannun Smart ɗin. Dan tunda ya ga iya ƙwallo na Smart a wani wasan sada zumunta na makaranta da sukai sannan Smart na ss1 ya jashi jikinsa, tun ma suna ɗar-ɗar har suka saki jiki da juna ganin kowanne nada zuciya mai ƙyau. Kusan family ɗin su Ahmad sun san Smart sosai, haka suma family ɗin Smart sun san waye Ahmad da Abdull-Hameed a rayuwar Smart. Babu hanyar da Umma batabi na son ganin ta rabasu ba amma hakan ya gagareta shiyyasa ta tsani Coach matuƙa. Akwai lokacin da har sharri tai masu wai Coach kodai yana ɗabi’ar banza da Smart ne. Sai da Abba ya nuna mata asalin haukarsa a lokacin dan har saki ɗaya yay mata sannan ta dawo hankalinta tana bada haƙuri, da ga nan bata sake maimaitawa ba kuwa.

Smart yaje ya ga gida tare da Ahmad. Gidane madaidaici zaman mace ɗaya flat. Bedrooms uku biyu manya ɗaya ƙarami kowanne da toilet sai falo babba tare da dining, sai kitchen da store. Harabar gidan zai iya cin mota biyu zuwa uku. Ga flowers an zagaye ko’ina da suka ƙara ƙawatashi. Sabon fenti da gyare-gyare duk an masa, dan ana dawowa da ga ɗaurin auren Smart Coach ɗin ya nema masu aikin gidan aka fara. Dama ƴan hayane suka fita kusan watanni huɗu kenan kasancewar ALLAH ya hore musu suma sun gina nasu, shi kuma sai bai sake saka kowa ba a ciki ya ɗan fara masa gyara sai kuma ya watsar ya rufesa kawai. Sai da idanun Smart ya ciko da ƙwalla, dan a rayuwa yakan rasa mizai ma Coach ya iya kwatanta alkairan da yay masa ne koma yake a kan masa, ya jima yana ɗawainiya da shi kashi-kashi da shi kansa bai san adadi ba.

Bayan sun dawo suma su Aunty Bilkisu sukaje suka gano, Abba kuma da Ammah sai washe gari ya kaisu suma. Su Umma dai basu san hidimar da ake ba, summa koma gefe sun zuba ido suga wai yaya wasan zai ƙare ne. Dan ta aiwatar da ƴan abubuwan da malam Na-zuru ya bata yanzu jiran ranar tarewar amarya kawai take ta samu kayan da aka kawota da su da wanda Smart zai saka shima. Alhmdllh lefe ma ya haɗu tsaf, dan bayan ƙoƙarin su Hawwah suma dangin Ammah sun taka rawar gani, dama su mutanene masu haɗin kai matuƙa. Gashi kuma yanzu ne Ammah zata aurar da ɗa namiji kuma shi kaɗai tilo gareta. Hankalin su Umma da ya ɗan fara tashi ganin gudunmawar da keta shigowa mai jijjiga zukata da ga ƴan uwa da abokan arziƙi, dan ko kuɗi Smart ya samesu ba laifi. Ana saura kwanaki uku ya amsa kiran su Uncle Yousuf, dan rabonsa da gidan fa tun kafin a ɗaura aurensa da gimbiya. Aiki bai sake zuwa ba, dan itama dai Lulun Uncle Yousuf ya dakatar da ita fitar bisa wayon Aunty Saliha da ta ɗakko mai mata gyara tun daga Sudan da Marocco. Da farko tayi butsutsun nata na bata so Uncle Yousuf ya zauna ya tsarata tsaf a kwali dole tabi. Suma dai shirye-shirye suke na bikin ƴar gata, musamman ma Uncle Yousuf da Baba da Mommy da Aunty Saliha. Ya samu tarba ta muntunawa ga Mommy matsayin suriki garesu a yanzu. Duk da dama dai ita kam bata taɓa wulaƙantashi ba. Shima ya gaishesu cikin mutuntawa da girmamawa kamar yanda ya saba. Da ga haka suka fara tattauna abinda ya tarasu. Shiru yay yana sauraren Daddy da ke masa bayani akan takardun hannunsa. Ɗaya na gida da ya bashi halak malam ƙaton gaske anan cikin anguwar hotoro G.R.A ɗin upstairs ma, sai key na mota da takardunta itama sabuwa fil a ledarta, da zunzurutun kuɗi har naira miliyan ashirin, ya kuma zaɓi duk aikin da yake so ya nema masa. Tunda Daddy ya fara murmushi kawai Smart yake yi amma baice komai ba. Shima dai Uncle Yousuf da Mommy basu ce komai ba dama.

A hankali Smart ya girgiza ma Daddy da ke miƙo masa takardun da key ɗin motar kai. Cikin tausasa harshe da girmamawa ya ce, “Daddy kayi haƙuri bazan amsa komai da ga gareku ba ni. Na auri Mawaddat ne domin ALLAH da bautarsa. Na kuma muku alƙawarin riƙeta in sha ALLAHU da abinda ALLAH ya azurtani da shi, bazaku taɓa dana sani da ni ba. A yanzu haka inada inda zan ajiyeta, batun neman aiki kuma insha ALLAH shima zan nema abinyi da kaina, hakan zai fi ƙaramin himma da sanin muhimmancin abinda na samu ɗin. Idan nayi ba dai-dai ba a gafarceni dan ALLAH”.

Tsittt falon yay tamkar ruwa ya cinye kowa. Bakaji komai sai sautin ƙarar ac da ke aiki. Murmushi sosai Mommy da Uncle Yousuf keyi ƙasa-ƙasa. Yayinda Daddy yay wani sansarakwai da shi yana kallon Smart cike da mamaki da al’ajab. Kaba mutum irin wannan dukiyar amma ya nuna maka bai buƙata, matashin saurayi kuma da ayanzu yake fafutukar gina rayuwarsa. Da ƙyar ya iya jan numfashi har sannan idanun nasa dai akan Smart. Ya ce, “Aliyu ban baka wannan abubuwan ba dan wataran ka maido min da madadinsu. Na baka ne saboda kaima yanzu matsayin ɗa kake amsawa a garemu, fatanmu kawai ka riƙe mana Mawaddat cikin aminci da amana”.

“In sha ALLAHU Daddy zan cika alkawarin riƙeta, koba komai nima inada ƴan uwa mata, bazan so na tsinci rayuwarsu cikin aƙubar zaman aure ba. Zanyi iya ƙoƙarina kamar yanda MANZON ALLAH (S. A.W) ya koyar da mu murayu a gidajen auren mu”.

Magana Daddy ya ƙara yunƙurowa zai yi cikin ɗan jin haushi-haushi, amma sai Uncle Yousuf yay saurin taresa yana girgiza masa kai da faɗin, “Shike nan Aliyu mun gode da wannan karamcin naka. Dama mu ai hakan muke son ji da ga gareka. Zamu cigaba da muku fatan alkairi dana zama lafiya. ALLAH ya baku ikon sauke hakkin juna. Ga waɗan nan katunan Baba ya ce a baka. Sai dai yace a faɗa maka kayi haƙuri baiyi shawara da kai ba wajen haɗa wannan dinner, yaso yin hakan sai uziri mai girma ya taso masa dan yanzu haka ma yana Abuja. Muma a madadinsa muna sake neman afuwarka da roƙon kayi haƙuri ya haɗa dinner ɗin ne sakamakon yanda ɗaurin auren ya kasance ga kuma mutane da yawa ya cancanci suzo”.

Ɗan murmushi kawai Smart yayi, duk da harga ALLAH shi a tsarinsa babu batun waɗan nan bidi’oin, amma yana jin nauyin Baba da Uncle Yousuf ɗin. Dan haka ya amsa katunan yace ba komai abin ƴan awoyine ai. Da ga haka yay musu sallama ya wuce da sanar musu baƙi na zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Daddy dai bai tanka ba, hasalima ransa a ɓace yake. Taya zai haifi yarinya, ya raineta tsawon shekara ashirin da huɗu. Rana ɗaya tak wani ya nuna masa iko akan al’amuranta. Idan bai amshi waɗan nan abubuwan daya bashi ba taya zai riƙe masa yarinya da daraja kamarr yanda ya raini abarsa. Sosai Mommy ta fahimci yanda Daddy ke cika da batsewa, dan haka ta miƙe tana cema Uncle Yousuf bari taje tai waya da su Hajiya Aysha da su Aunty Saliha suzo a tsara abinda za’a tarbi baƙin da Smart ɗin ya ce zasu zo gobe. Cikin murmushi da barkwanci Uncle Yousuf ya ce, “Umm bafa sabun ba zamu aurar da ƴar farko a gida”. Dariya ta fita tanayi. Shima yana tasa. Tana gama ficewa Daddy ya miƙe a zafafe.

“Kai Yousuf bazai yiwu ba. Shiyyasa tun farko nace maka yaron nan zai iya bamu matsala dan na fahimci gadararre ne shi mai girman kai. Taya zan bashi abinda zai inganta rayuwarsa da ma ta duk zuri’arsa darajar ƴata zata shiga cikinsu amma ya nunamin shi yafi ƙarfin hakan bayan baida komai. To gaskiya ayi komai a rubuce wata ɗayan daka ambata ya sakamin yarinya ta kawai……” Haka ya cigaba da zazzaga masifa ko haɗiyar yawu bayayi. Shi dai Uncle Yousuf na zaune kawai yana kallonsa har yayi ya gama. Baice komai ba, sai ma ya tashi tsam ya fice a falon yay tafiyarsa ya bar Daddy da sakin baki yana kallonsa………✍️

 

(Uncle You kaima fa ɗan manni ne wlhy🤣).

 

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

VIP🔥💯

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments