Breaking News

Furar Danko 53

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

 


 

 

 

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗

 

 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣3️⃣

 

 

 

…….A ɓangaren Smart sosai abinda ya farun ya dinga cimasa rai. Amma haka ya danne bai sanarma kowa ba yama kashe wayarsa dan kar wani tsakanin su Daddy yace zai sake kiransa akan batun. Bayan ya koma gida ya shiga ciki gaida Ammah su Hawwah suka buɗe masa lefe ya gani. Set guda na akwati mai biyar, sai ƙwara biyu daban da Abba ya saya da kaya a ciki suma matsayin kayan sa rana. Kaya kam sunyi sai dai maƙiyi, ga shi kuma duk manyan atamfofi da lasses hakama shaddoji da dogayen riguna dai-dai ƙarfin mai rufin asiri dai. Sosai Aunty Bilkisu da Hawwah suka taka rawar gani, dama sunyi alƙawarin duk randa ɗan uwan nasu tilo ɗaya ya tashi yin aure sai sun nuna bajintar da zata girgiza jama’ar gidan nasu kowa ya tabbatar da shi ɗan gata ne. Aiko sun girgiza ɗin, dan ko gidan su ya girgiza matuƙa da ganin wannan lefe da ba’a taɓa tunanin gani ba, sai su Umma suka shiga yada habaicin wai sai dai in iyayen yarinyar ne suka haɗa lefen, da ga Ammah har ƴaƴanta babu wanda yay ko tari har sukaci suka tsire. Gyalillan ciki kaf ya kwashe yabar guda uku, da mamaki su Aunty Bilkisu ke kallonsa, duk da ya lura da hakan baice komai ba ya dubi Maryam ya ce, “Bani saƙon dana baki ajiya”. Tashi tai tana murmushi ta shiga bedroom ɗinsu. Babu jimawa ta dawo da leda babba ta miƙa masa. Amsa yay ya miƙama aunty Bilkisu da faɗin, “Ku saka waɗan nan a kayan, wannan kubarta har sai tazo na bata da kaina. Aunty Bilkisu zatayi magana Ammah ta katseta da faɗin, “Kumasa yanda yake so ɗin kawai tunda baku san dalilinsa ba”. Su masu biyayyane ga umarnin mahaifiyarsu, dan haka babu wanda ya sake magana aka loda hijjabai da suka sha guga har guda goma ciff cikin akwati….

 

Washe gari alhamis aka kai lefe, ba wani gayya akai ba. Umma ne da Aunty Amarya, sai Aunty Bilkisu da Inna Mariya. Da wata gwaggon su mai suna Jamila. Sai matan maƙwaftansu su biyu. Ahmad ne ya kaisu da motarsa, sunko samu tarba irin wadda basuyi zato ba. Dan su Mommy da su Aunty Saliha sun nuna karamci mai ban mamaki. Ga gida cike masha ALLAH iyalan gidan Baba suma sun zazzo. Sosai suma kansu su Mommyn sukasha mamakin wannan lefe, dan gaskiya basuyi zato ko tsammani ba. Abu a cikin kwana shida haka. Kai da mamaki. Ga kaya babu na kushewa sai san barka. Harda kuɗin ɗinki, sai dai basu amshi kuɗin ɗinkin ba dai. Su Umma fa sun girgiza matuƙa, dan ganin gidan su Lulun ya ƙara tayar musu da hankali da sake tabbatarwa eh lallai Smart ya shiga inda akafi ƙarfinsa, dan yanda mutanen keda wannan irin dukiya sai dai idan asiri ne yay tasiri, yo inba asiri ba ƴar data tashi a wannan gidan ce zata auri ɗan talakawa kamar Smart. Ammah dai tasan tsiyar data yi ɗan nata ya auri yarinyar nan. Duk wannan abu dake faruwa amarya bata sani ba, tana gidan Aunty Saliha data turketa ana mata gyaran jiki na fitar hankali. Dan ta ƙara wani irin fresh da ita, damuwarta ɗaya kayan shaye-shayen ta da bata samu. Dan a jiya har kuka tayi ita kaɗai a bayi saboda buƙatar son sha da takeyi amma babu dama. Tsoffin nan da aka kawo mata sunbi sun tare ko’ina basa barinta ko motsin kirki. Gasu da ihu da tace zata musu gardama suke rufeta da kwakwazo dole take zama suyi yanda suke so da ita. Sai dai ita kanta tasan ta canja. Dan fatan ta ko daga nesa ka hangota kasan ta ƙara karɓar sunnonin gyara. Ga wani almurin ƙamshi mai ratsa zuciyar mai shaƙa. Ita kanta ƙamshin ne ma ke tafiya da imanin ta shiyyasa wani lokacin take ragama tsoffin ta haƙura su zauna.

Bayan wucewar ƴan kawo lefe da aka cika da sha tara ta arziƙi suma su Aunty Saliha suka nufi gidan da za’a kai Mawaddat ɗin domin raka Company da Uncle Yousuf ya bama kwangilar shirya mata kaya. Su kansu gidan ya birgesu yanda yake cif-cif abinsa. Duk da nasu ya ninka shi sau biyar girma da ƙyau, shima wannan ɗin nada nashi kalar sirrin ƙyau ɗin da yanayin shiga rai. Bayan Company sun kammala aune-aunensu su Aunty Saliha suka dawo gida suka barsu suyi aikinsu. Dan gidajen biyu sun fara cika da ƴan uwa na jiƙamshi da abokan arziki musamman na tsohuwan anguwar da su ka rayu tun suna ƙanana kasancewar mutanen da da zuminci ga shi kuma Aunty Saliha ma ƴar canne. Anan gidan su Smart ma dai an dawo da labari mai daɗi na tarbar da suka samu da karramawa. Yayinda Umma keta faman haɗiyar zuciya, data samu abokin gulma kuwa tace “Anya yarin nan ba asiri yay ma mutanen ba kuwa? To wannan haba rawa har ina. Ga mutane a jiƙe cikin kogin dukiya amma sunama waɗan nan ɗan abinda muka kai haba rawa haka”. Wasu idan tace musu hakan sukan kulata, wasu ko su gwaleta. Wannan kai lefe ya sake yayata sanin ƴar wa Smart ya aura a anguwar, dan dannan fa masu hassada da masu taya murna aka kafa teburan kace nace kowa na faɗar albarkacin bakinsa. Oho shi baima san sunai ba. Yana can yana nashi ƙoƙarin na ganin walimar da suma suka shirya anan gidan a gobe idan ALLAH ya kai mu juma’a ta tafi dai-dai. Ga kuma can gidan da Company ke saka kaya dole suka raba hankalinsu biyu shi da Ahmad da wasu tsirarun abokansa da basa fushi da shi duk yanda yake sharesu a baya. Harda Sa’ad mijin Hawwah.

Zuwa washe gari suma fa nan gidan ya cika da dangi, musamman ma dangin Ammah kai harma dana Abban da kuma nasu aunty Amarya, ga ƴaƴan gidan duka dai duk sun hallara ƙwai da kwarkwata. Duk da wasunsu aikinsu tsogumi ne da kushe kamar yanda iyayensu keyi. Bayan an sakko massalacin juma’a aka fara walima da aka gayyato manyan malamai da zasu kwarara wa’azi. Abin mamaki sai ga gayyara Alhaji Sufi Ado Garko a wajen da na Uncle Yousuf da wasu a cikin mata ƴan biki. daddy dai baizo ba, Mommy ma saboda baƙi doke ta haƙura, sai Aunty Saliha ce ta jagoranci matan da akazo da su sai yazam kamar an raba Mommy nacan ita tana nan. Sosai suma gidan su Smart ɗin suka maida alkairi da alkairi, dan sun musu tarba ta mutuntawa duk da ba’asan da zuwansu ba. Amarya dai banda ita, tana can ana mata ƙunshi bayan Uncle Yousuf ya mata filla-filla da masifa yau dan da taƙi yarda ayi, tun yana lallashinta yaga taƙi saurarensa sai ma sake tuburewa take akan itafa babu inda zataje ya sashi yau buɗe mata wuta irin wanda bata taɓa gani daga garesa ba, dan har rantsuwar marinta yay idan bata shiga hankalinta ba. Ga wayoyinta dama ya ƙwace kusan kwana uku kenan. Dole dai ta haƙura ana can ana yarara mata wani lalle na nunama sa’a da tsara. Sosai walima tai matuƙar ƙayatarwa. Ango yasha ƙyau cikin dakakkiyar shadda sai kaiƙo take. Tana ɗaya daga cikin ɗinkunan da Abba yay masa har kala biyar domin fitar biki, sai kuma ga Ahmad da nasa kayan mamakin a safiyar yau da ƙaton akwati guda da ɗinkakkun kaya masu ƙyau har kala ashirin shima matsayin tasa gudummawar. Har ƙwalla Smart yayi a ɓoye na godiya ga UBANGIJI da ya rufa asirinsa. Dan baiyi zato ko tsammanin haka ba shikam. Walima ta matuƙar ƙayatarwa ga armashi data ƙara dalilin zuwan dattijon ƙwarai Alhaji Sufi Ado Garko da tawagarsa ta ƴan siyasa har da gwamna da yazo daga baya shi. Aifa sai gashi ƴan jarida sunyi caa anata ɗaukar rahotanni, labaran daran juma’ar nan sai gashi ya zo harda wannan taron walima darajar zuwan su Gwamna wajen. Ranar fa anguwar fagge kamar zata fashe (Kar wani ɗan fagge naji yayi magana😏🥱😂). Duk da babu inda abincin da aka tanada yajema mutane kasancewar abin ya zarce yanda aka tsarashi mutane basu damu ba. Ko’a tv kaga kanka ai ka more🤣 (Su Smart an auri ƴar gidan madara an samu promotion 😜). Tarofa yayi taro fiye da zato, dan da ƙyar aka tashi bayan sallar magrib. Dauriya kawai ango yake da ambaton addu’oi a cikin ransa dan gabansa haka kawai yake ta faɗuwa. Ga ciwon kai ƙasa-ƙasa dake nuƙurƙusarsa. Haka dai yayta dauriya bawan ALLAH dan manyan mutanen nan sai da Uncle Ameen ya kama hannunsa ya kaisa gaban kowanne suka gaisa. Da yawansu sun yaba da nutsuwar yaron, har wasun su najin sha’awar yin koyi da wannan al’amarin aure da a yanzu al’ummar mu suka daina. Da wahala kaga ɗan masu kuɗi ma ya aure mace ƴar talaka balle wannan ace namiji ne ɗan talaka ya auri ƴar masu kuɗi, kuɗin ma irin na gidan Alhaji Sufi Ado Garko da Alhaji Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Lallai wannan abun ayi koyine gaskiya dan sun kafa tarihi matuƙa. Washe gari asabar biki ya koma gidan su Amarya Mawaddatan’warahmah Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. ALLAH sarki Uncle Yousuf, yau dai kam duk sai jikinsa kuma yay sanyi, dan haka tun da safe yasa aka kira masa Mawaddat ya lallasheta sosai da mata nasihar ta nutsu dan ALLAH ayi komai yanda wani bazai fahimci akwai wata a ƙasa ba. Ayi a gama cikin farin ciki. Yanda taga yanata lallaɓata da nuna damuwarsa sosai, ga dangin mahaifiyarta tako ina kowa na tattalinta da janta a jiki musamman auntyn ta matar Uncle Khamil Aunty Naja’atu ta Abuja da tasu tazo ɗaya daman. Ga ƴan uwanta su Amrah nane da ita, su twins kansu yau har murmushi sukai mata da tsokanarta da amarya suna faɗa mata har sun fara kewarta duk sai ta karaya harda kukanta. Gefe kuma rashin samun kayan shaye-shayen ta na samunta, ya kumayi matuƙar tasirin sake sanyaya mata yanayi yau ba masifa ba ko maganar kirki ma bata iyayi. Ga mafarkin mamarta da tayi a daren jiya shima ya tsaya mata a rai. Duk sai komai ya haɗu ya tankwarata a yanda su Uncle Yousuf basuyi zato ba. Mai kwalliya ta musamman aunty Naja’atu tazo mata tun daga Abuja, kuma daga Lagos ma aka ɗakkota. Ga Mommy ta mata akwati guda na kayan fitar biki masu tsadar gaske. Dai-dai da gold Mawaddat an saya mata na nunama tsara ne, karku manta itace za’a fara aurarwa a jiƙamshi family bayan auren Daddy da na Uncle Yousuf…….✍️

 

 

 

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

VIP🔥💯

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments