Breaking News

Furar Danko 69

 

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

 

 

 


 

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗

 

 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣9️⃣

 

 

 

……..Cikin sa’a kuma ya gane muryar Daddy. Amma sai ya danne bai nuna ba, cikin dai nutsuwarsa ya ce, “Assalamu alaikum”.

“Da sallamar nake da buƙata da ita zan maka ai. Miye dalilinka na hana Mawaddat fita office ka kuma kulleta?”.

Shiru Smart yayi kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya furzar da numfashi kaɗan yana gyara kwanciyarsa. Sake tausasa muryarsa yay fiye da ɗazun ya ce, “Kayi haƙuri Daddy sallama wajibi ne ga musulmi, haka ma amsata ga wanda akaimawa. Kai ya kamata ka tunatar da ni hakan a matsayinka na mahaifi. Dan haka kayi haƙuri ka amsa min sallamata kafin muyi maganar da kake son. Assalamu’alaikum!”.

A cinkushe Daddyn ya amsa masa, Smart ya ɗan girgiza kansa sannan ya tashi zaune sosai. Cikin sake tsantsan da kai na girmamawa ya ce, “Daddy ina kwana”. Bai amsa masa ba nan kam. Shima sai bai damuba ya ɗora da faɗin, “Zan sake baka haƙuri a karo na biyu Daddy, dan ALLAH karka saka baki a wannan zancen dan a yanzu Mawaddat tana ƙarƙashin na ne. Inada damar zartar mata da hukunci akan abinda ya dace da kuma banbance mata wanda bai dace ba. Kai mana fatan alkairi kawai shi mukafi buƙata da sanya albarkar ku, na riga na gama yanke hukunci akan hakan babu kuma tunanin canjawa a tattare dani amin afuwa. Na Barka lafiya”. Daga haka ya yanke wayar tare da kasheta gaba ɗaya ya koma yay kwanciyarsa ransa fal mamakin halin surukin nasa.

Ƙaramin hauka ne ya kusan samun Daddy da ga can jin Smart ya yanke wayar bayan ya gama datsa masa zafafan magana kamar yanda zuciyarsa ta fassara masa. Ƙoƙarin sake kira yayi amma sai wayar switch up. Kaɗan ya rage ya maka wayar da ƙasa. Amma sai ya fasa ya maida akalar kiran kan Uncle Yousuf. Suna zaune shi da yara da akaima shirin makaranta suna breakfast kiran Daddyn ya samesa. Bai kawo komai a ransa ba ya ɗaga, sai dai kiran sunansa da Daddy yay a tsawace ya sashi rumtse idonsa. Sai kuma ya miƙe yabar daining ɗin ya nufi bedroom ɗinsa. Cikin tausasawa ya ce, “Yaya lafiya dai kuwa?”.

“Yousuf yanzun nan ka kira ɗan iskan yaron can ka faɗa masa ya sakar min yarinya tunda ba ubansa ya haifa min ita ba, har ni yake da bakin gayama Mawaddat ta koma ƙarƙashin ikonsa ya kuma yanke hukunci a kanta bazai canja ba kamar shine ya haifa min ita.”

“Ya Salam. Yaya Please calm down dan ALLAH muyi magana mana. Wlhy sam ban fahimci mi kake son faɗa min ba. Mi Aliyun yay maka ne?”.

“Miye ma bai mun ba, babu abinda ya manta na rashin kunya bai faɗa min ba. Shiyyasa tun farko na faɗa maka yaron nan ɗan zafin kai ne zai iya bamu matsa ta duk inda bamuyi zato ba. To gashi ya fara, ya kulle gida ya hanata fita aiki, ta masa magana ya ce sai next week babu inda zataje, ta kirani nai kiransa nai masa magana amma ya daddatsamin magana son ransa tsabar shi ya cika cikakken ɗan iska.”

Girgiza kai Uncle Yousuf yayi, kafin ya ce, “Dan ALLAH kayi haƙuri ka kwantar da hankalinka, ka dai san mi ɓacin rai ke haifar maka a yanzu. Zan kira shi na masa magana sai naji dalilinsa. Sai dai ma yaya banda abunka ai bai kamata ka biye mata kai kiransa ba, karfa ka manta yau kwana biyu kawai da tarewarsu, ai bai dace ba ta fita aiki sai mutane suyi magana kadai san yanda al’amarin yake yanzu mutane sun bar damuwa da al’amarin su sun koma hango na wasu”.

“Yousuf bana buƙatar jin komai, sannan ni babu ruwana da wasu mutane ko abinda zasu faɗa, farin cikin yarinyata kawai na sani. Shi wanene da zai tauyeta bayan da aikinta ya ganta, sannan waya faɗa masa shi ɗin har ma yanada wani ƙarfin iko a hannunsa a kanta da zaima mutane wani gadara koda ace auren nasu mai muhimmanci ne. Wannan shine na guda tun farko amma ka kasa fahimtata, shiyyasa kuma nace ayi komai a rubuce amma nan ma ka wani kakkaresa gashi nan tun kan aje ko ina ya fara nuna halinsa, a haka kwanakin da kace ɗin zai cika yay abinda ake so? an faɗa masa akan ƴata zai nuna gargajiyancinsa ne”.

“Naji duk na ɗauka kayi haƙuri zanyi magana da shi yanzun.” daga haka Uncle Yousuf ya yanke wayar batare da ya jira cewar Daddy ɗin ba. Hannunsa ya kai ya dafe kansa, sai kuma ya girgiza a hankali ya ɗago yana murmushi mai sanyi. A fili ya furta, “Yaya yaya kenan, kai da gaske jiran cikar lokacin kake kenan? Humm aiki ya sameka. Aliyun dama shine ai dai-dai da kai game da lamarin Mawaddat duka kai da itan. Ashe babu daɗi lokacin da ka dakatar da Aunty Kareema fita aiki a dalilin Marigayiya, duk da hakan ya mata ciwo kuma ta haƙura iyakarta kuka ta share hawayenta, ashe ita daga sama ta faɗo? Kai gashi hana fitar kwanaki kawai da akai ma taka ɗiyar ya zafafaka har haka. ALLAH na gode maka da ka kaini da rai da lafiyar ganin irin wannan ranar, shiyyasa akace yanzu ma tun a duniya ake fara hisabi basai an mutu ba. Muje zuwa yanzu aka fara wasan ai. Mai ƙarfi sai yaci kofin”. Ya ƙara sakin murmushi. Ƙoƙarin kiran Smart yayi sai ya samu wayar switch up. Ya sake sakin murmushi da faɗin, “Kaga mazan ƙwarai”. Da ga haka ya miƙe ya fito abinsa. Ya samu yara har sun wuce, sai Aunty Saliha da ke zaune tana tsumayen fitowarsa dan ya sakata a ruɗani.

“Abban Ra’is lafiya dai ko?”.

Ajiyar zuciya ya saki yana kaiwa zaune, ta turo masa kunun data sake zuba masa dan wanda ya bari ya huce. Sai da yasha kusan sau uku sannan ya dubeta. “Yaushe zakuje gidan Mawaddat ɗinne?”.

“Sai zuwa anjima kaɗan dan muje mu dawo da wuri ko”.

“Inaga ku kuyi zamanku, su Hussain suje sukai mata, motocin ta kuma a barsu ba yanzu ba.”

“Amma wani abu ya faru ne?”.

“Zai dai faru Saliha…….” nan ya zayyane mata komai daya faru. Cikin damuwa ta ce, “Amma Yaya da bai kirashi ba ai. Dan Aliyun ya fishi gaskiya, yaza’ai amaryar da aka kai gidan miji shekaran jiya kuma a ganta a office yau dole zai iya zama abin magana. Inda waɗan nan ƙananun matsalolin zai dinga sawa iyaye na neman sakin ƴaƴansu ai da kowama ya zama babu aure kenan. Ni sai nake ganin kamar maganar Aunty Kareema zata iya zama gaskiya….”

“Hummm ku mata kullum tunaninku iri ɗaya ne, miyasa komai a rayuwa idan yazo mana a yanayin da ba haka muke tunanin ganinsa ba sai mu dinga ɗaukarsa asiri. Nasan asiri yana ɗaya daga cikin abinda al’ummar mu suke kallon babbar mafita ga al’amuransu a halin yanzu, sai dai bai kamata muna tsuke dukkanin zukatanmu waje guda ba akan kowanne bigire muyi masa kallon asirin. Amma dai bari nai miki wata tambaya, shin ku minene dalilinku na kallon al’amarin Yaya matsayin asiri?”.

Duk da maganganunsa na farko sun shigeta sai bata gaza wajen faɗa masa hujjojin da suke kallonba su. Ta ce, “Na yarda da zancenka nima, sai dai ka kalla wani abu Abban Ra’is. Kafin auren marigayiya kai da kanka ka bani labarin ba haka Yaya yake ba sam, sannan Yaya nada ilimin addini mai zurfi da yasan minene aure da ƙaddara. Amma kaga yanda idanunsa suke rufewa ta yanda idan wani aka faɗamawa da bai gani ba zai iya ma ƙaryatawa. Dolene muyi tunanin akwai sammu tattare da shi”.

Murmushi yay da cewa “Hummm! Saliha kenan. Duk ilimin mutum bakwa tunanin son zuciya zai iya sakashi ajiye ilimin gefe ya aikata abinda baida alaƙa dana masu ilimin. A al’amarin Yaya babu wani asiri, akwai ɓoyayyen al’amarin da yake ɓoyewa dai tun kafin auren Mawaddat ɗin, sai da ya auretanne ya fara fitowa, wanda tamkar ALLAH ya jarabcesa da sanya masa tsoron faruwar irinsa akan Mawaddat ne, ba komai ya kawo hakan ba kuma sai dan itace mafi soyuwa a ransa ko kuma ana masa barazana da ita, shiyyasa ma tun farko ya gagara yarda da kowa game da kula da al’amarin ta, a tunaninsa shi zai iya kareta akan komai, sai kuma akai rashin sa’a ƙaddarorinta ba’a fatar jiki suke ba ko mahallin zamanta balle yay tunanin kuɓutar da ita a yanda yaso da kuma ƙarfinsa da wayonsa. Dan haka kuma bar damuwa da al’amarin sa ana gab da zuwa gaɓar da zai fallasa kansa da kansa batare da ya sani ba. Yanzu Mawaddat itace mafi ƙololuwar abar tausayi, dan ina matuƙar jin tausayin rayuwar yarinyar a dalilin halin data tsinta kanta a ciki.”

Yanda ya ƙare maganar cikin matuƙar damuwa da ɓacin rai yasa Aunty Saliha tasowa ta dawo kusa da shi tare da dafa kafaɗarsa. “Kayi haƙuri Abban Ra’is, tabbas tausayin Mawaddat dolene ga duk wanda ya fahimci muhimmancin rayuwa. Sai dai namu addu’a ce a yanzu tsakaninmu da ita, mu kuma cigaba da bama Aliyu goyon baya akan abinda ya fara, dan a yau na sake gamsuwa da fahimtar hikimarka ta haɗa wannan auren. Inaga kuma lokaci yayi da shima zaka fara aiwatar da shirinka na taimakonsa da tun farko shine dalilin jawosa jikinka da kayi, dan namiji bazai yiwu ya rayu babu abinyi ba yakan ja masa ƙasƙanci tsakaninsa da mace, musamman irin Mawaddat da tunda ta tashi bata san minene babu ba”.

“Hakane kam, insha ALLAHU kuma a yanzu haka ina kan shirye-shirye ni da Hameed, dan kin san al’amarin nasa sai anbi ta bayan fage yazo a bazata tamkar yanda maganar auren nan tazo a bazata. Dan bayyanawa na nuna zaburar da mai ƙullin ne”.

“Tabbas hakane, ALLAH ya bada nasara yasa shima iyakar wahalar tasa ce tazo. Ku kuma da kuke ƙoƙarin ALLAH ya saka muku da alkairi ya hana bayanku kuka”.

“Amin ya rabbi. Bara na kirata idan naga da yiwuwar kuje ɗin to”.

“To ba damuwa”………✍️

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments