Breaking News

Furar Danko 75

 

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗

 


 

 

𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

 

 

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣5️⃣

 

 

 

 

……..Washe gari bayan ya dawo motsa jikin safe da yake fita yace ta shirya zasu fita, da mamaki ta dubi agogo da faɗin, “Da sassafen nan? Ko 8 fa batai ba”.

Shima agogon ya kalla sai kuma ya dubeta. “Ina ganin kafin mu kammala shiryawan tara ma zata iyayi, dan inada abune mai muhimmanci shiyyasa nake son mu fita da wuri”.

“Wai ina to zamuje?”.

“Idan mun fita ai zaki gani, ke dai ki shirya”. Ya faɗa yana ficewa, kitchen ya nufa ya sake ɗaukar ruwa ya sha sannan ya nufi bedroom ɗinsa ya cire kayan motsa jikin dake jikinsa ya faɗa wanka. Itama a ɓangaren Lulun wankan ta tashi ta shiga, dan dama dai tana duba karatun da ya ƙara mata ne kafin fitarsa training. Harga ALLAH tana jin daɗi da farin cikin karatun da sukeyi na addini, abinda kuma ke sake zaburar da ita akan hakan watarana akan wani case an gayyaceta hira a gidan wani tv tare da wani lawyer da basa shiri sam saboda duk karon da tai da shi a shari’a sai ta kaisa ƙasa. A cikin hirar kawai ɗan jaridar sai ya sakko wata magana data shafi addini, amma sai ta kasa amsa masa dan bata sani ba, sai shi lawyer ɗin ya amsa da karsashi da son nuna isa har yana mata shaguɓe akan bata da ilimin addini. Abin ya mata ciwo, tun a lokacin kuma tayi ƙudirin fara neman ilimin sai dai bata san tayaya zatai hakan ba, sannan bata da shaƙuwa da wani a ƴan uwanta da zata iya kawo zancen ta yanda za’a fahimceta, na biyu rashin barin abu a rai da take da shi ya sata tattara abin ta ajiye gefe ta cigaba da sabgoginta. To bayan fara karatun nan da Smart ke koya matan sai ta fara fahimtar abubuwa da dama, sannan tana jin wani nutsuwa da jinta daban da dacan duk da bawani nisa sukai ba can sosai, dan ma dai ƙwaƙwalwarta mai saurin ɗaukar abu ta taimaka mata matuƙa. Kamar yanda ya faɗa sun kai kusan ƙarfe taran, dan sanda ya fito bayan ya shirya koda yaga kayan data saka kai tsaye yace mata ta sakesu. Taso masa gardama amma sai yace tayi haƙuri gidansu fa zai kaita ta gaida su Ammah kuma can zata yini sai dare. A take yaga farin cikinta ya bayyana, dan ita dai tunda Asma’u suka bata labarin yanda Ammah ke sonta da bibiyar abinda take yi sai take jin ɗokantuwa da sake ganin Ammah ɗin duk da a waccan zaman na kwana ɗaya da aka kaita gidansu bazata ƙarar da fuskar kowa ba. Kanta tsaye ta ce, “To dan ALLAH zoka tayani zaɓen wanda zasuyi”.

Idanu kawai ya zuba mata sai kuma ya saki murmushi zuciyarsa na ayyana masa abubuwa da dama. Baiyi zaton zata nuna ɗokin sake zuwa gidansu ba tunda ta kwana a ciki taga yanda yake. Ya fahimci gane wacece ita kai tsaye abunne mai wahalar gaske, dan idan ya gama haddace nan ya buɗe mata sabon shafi sai yaga nan ɗin ma dai akwai abubuwan ban mamaki a cikinsa fiye dana baya daya baro.

 

Da kansa ya zaɓa mata kayan kamar yanda ta buƙata. Atamfa mai ƙyau da akaima ɗinkin zani da riga, sai hijjab. Anan ne ta ɓata fuska da ɗauke hijjab ɗin gefe ta ajiye ta ɗauka gyale. Zaiyi magana ta marairaice fuska. Shiru yay baice mata komai ba ganin gyalen nada girma. Sai kuma wajen ɗaura zani ma wata sabuwa. Dan Lulu bata iya ba, da tayi-tayi taga ta kasa saita shiga ƙwala masa kira dan sanda zata saka kayan catai sai dai ya fita, shi kuma baiyi musu ba ya fita ya tsaya a ƙofa. Kiran nasa da tai ya sakashi dawowa. Cikin ɓata fuska ta ce, “A canja wasu gaskiya”.

“Saboda mi”.

“Toni na iya ɗaura zani ne”.

Dariya taso ƙwace masa amma ya danne. Ya ƙarasa shigowa ciki yana faɗin, “Kin yarda na ɗaura miki?”.

Shiru tai kamar mai tunani, sai kuma ta ɗan hararesa da faɗin, “To wlhy ka rufe idonka, dan inka kallan ban yafe ba”.

“Oh hakama zaki ce daga taimako?”.

Baki taɗan murguɗa batace komai ba. Shi kuma sai yay murmushi kawai da ƙarasowa inda taken dan bai son ya biye mata Coach nacan na jiransa. Da taimakonsa ta ɗaura zanin duk da anata masa masifar ya rufe ido kuma karya taɓa mata jiki, duk da yana da abubuwan faɗa baice komai ba shi dai. Ɗaurin ɗan kwali ma bata iya ba. Cikin dafe kai ya ce, “Naga takaina, na auri bahaushiya a zahiri amma bata da banbanci da turawa ni Aliyun Ammah”.

Harara ta zuba masa ta figi handbag ɗin ta da mayafi ta fice. Sai wata leda da bai san ko minene a ciki ba hartayi gaba ta dawo ta ɗauki kayarta. Bayanta yabi yana dariya da faɗin, “8-6 kenan”.

Sai da ta hararesa ta ce, “Kama isa. Wlhy 7-6 na sani”.

“K matsalata da ke rinto, garama ki yarda kinyi game over”.

“Never give up wlhy, mai sama da hundred ne yay wining”.

Ta amsa masa nan ma tana hararsa. Ita ta fara fita, shi kuma ya kashe kayan wutar dan an haɗa musu tv yanzu ya kullo ƙofar ya fito. A jikin motarta ya ganta tsaye, sai ya ɗauke kansa ya nufi gate. “Ina kuma zaka je?”. Ta faɗa tana kafesa da idanun ta. Kansa tsaye ya bata amsa batare da ya juyo ba. “Zan sama mana Napep mana”.

Da mamaki ta ce, “Napep kuma? Ita kuma wannan motar fa? Ni malam bana son ƙauyanci kazo mu wuce danni kam bana hawa Napep. Bamma taɓaba”.

“Sai ki fara da ga yau”.

Ya amsa mata yana yin gaba. Tana nan tsaye mamaki da jinjina girman kansa na cimata zuciya, dan ita abinda ta fassara kawai kenan a al’amarin nasa sai gashi ya dawo, baice da ita komai ba ya ɗauka handbag ɗinta da ledar nan ya dubeta da faɗin, “Muje”.

“Aliyu!”.

Ta faɗa cikin kaiwa ƙarshen mamakinsa. Amma sai ya ɗaga mata hannu da nuna ƙofa alamar suje. “Sai dai ka tafi kai ɗaya dan gaskiya bazan shiga Napep ba, kaje zan sameka acan”.

Wani ɗan lumshe idanunsa yay na gundura da maganar a taƙaice ya ce, “Zan ɗauke ki har ƙofar gidan ba ruwana. Dan na faɗa miki ana jirana ko”.

Yanda yay magana a dake babu alamar wasa ya sake sata tsira masa ido. Sai kuma shawarar da zuciyarta ta bata na ta bishin koba komai yau ta ɗan fita tasha iska ya sata ture komai gefe tai gaba yabi bayanta yana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya. Lulu naji na gani a karo na farko na tarihin rayuwarta ta shiga Napep. Sai kuma taji hakan ya sakata a farin ciki batare da tayi zato ba, ga wata iska mai daɗi na rsatsaka tako ina. Sannan kai-kawon mutane da yanda kowa ke sha’aninsa musamman masu tallar abubuwa akan titi yay matuƙar ɗaukar hankalinta da sakata jin tausayinsu. A karon farko zuciyarta ta bata talaka na wahala akan taro da kwabo a ƙasar nan. Wani ɗan yaro da ke tallar papcorn ta yafito da hannu sanda suke tsayawa cikin wani gajeren holdup. Bazai wuce shekara goma sha huɗu ba.

“Hajiya guggurun na nawa kike so?”.

Yaron ya faɗa yana ƙoƙarin yago ledan guggurun a jikin ƴan uwansa. Dakatar da shi tai da faɗin, “No ba shi nake so ba. Miya hanaka zuwa makaranta kake nan kan titi?”.

Ɗan jim yaron yay kamar bazaiyi magana ba, sai kuma ya kalleta ya sake kallon Smart da ke kallonsu kawai batare da ya tanka ba. Muryarsa da alamar damuwa ya ce, “An koroni ne dan Abbana bai biya ba tunda na gama aji uku wai baida kuɗi.”

Idanu ta zaro na mamaki. Sai kuma ta ce, “Kaga yanzu a titi muke ina ne gidanku?”.

“A kwana uku muke”.

Handbag ɗinta ta ɗauka ta ciro jota da pen ta miƙa masa. “Kaga samun Number wayan mamanka anan idan ka sani”.

“Sai dai na yayata, Umman mu wayanta ya faɗa ruwa”.

“Idan ba damuwa sakamun ta yayar taka”. Da murna sauri-sauri yaron ya saka dan an sakesu. Ya miƙa mata. Amsa tai da miƙa masa 2k tana murmushi. Da ga haka suka wuce. Mai Napep da ke kallon komai yay ƴar dariya da faɗin, “Hajjaju idan irin waɗan nan yaran kikace zakiyita amsar lambarsu dan basuje makaranta ba aiko zaki amshi sama da miliyan goma a garin nan. Bayan ƴan gari akwai ƴan cirani kamarsa-kamarsa ba adadi. Su dama sauƙi tunda suna neman na kansu ai, wasu kamarsun rashin karatun kesa abokan banza jan ra’ayinsu su faɗa ƙwacen waya da tare yaran da aka aika a lungu su amshe kuɗin. Ko kiga sun faɗa harkar shaye-shaye yara ƙanana kaga yaro na zuƙar maka tabar wiwi ƴan iskan banza iyayensu sun haifa mana bala’i”.

Wani irin harbawa zuciyar Lulu tai akan zancensa na ƙarshe. Sai taji bakinta yayi nauyi tama gagara cewa komai, sai ɗagowa da tai ta ɗan dubi Smart da yay kicin-kicin da fuska yanzu kam yana ma mai napep ɗin wani shegen kallo. Aiko sai taji mai Napep yay tsitt yana ɗan satar kallon Smart ɗin ta mirror. Har suka iso fagge zantukan na mata juya-juya a zuciya da kartar mata rai. Ba komai ya kawo hakan ba gareta sai tuna itama fa ta fara shaye-shaye ne tana da shekara goma sha uku a duniya. Har ƙofar gida aka kaisu, anguwar da mutane sosai kasancewar Lahadi ne wasu basa fita, ganin yanda akai musu caa da idanu yana biyan mai Napep ɗin yaja hanunta suka shige ciki. Sun samu yaran duk suna nan, basu kai ga wucewa islamiyya ba gidan caka-kai caka-kai. Sai shigowarsa ta sa mafi yawan yaran yin shiru, masu aiki suka maida hankalinsu ga aikin da sukeyi. Asma’u ce dake shanyar kayan Ammah da suke wankewa ita da Maryam ta taho da gudu tana faɗin, “Aunty Oyoyo Oyoyo. Sassanyan murmushi Lulu ta saki ta riƙo hannun Asma’u da ta noƙe gab da zata iso saboda hararar da Smart yay mata ta fasa rungume Lulu da tai niyya, hararsa tai da jawo Asma’un jikjnta dan sarai taga hararar da yayma yarinyar. Maryam ma tasowa tai da fara’arta tana musu sannu da zuwa tare da amsar kayan hanun Yayan nata. Sai suma sauran yaran dake a tsakar gidan duk suka shima musu sannu da zuwa da gaishesu. Suna ganin sun shige falon Ammah kowa ya nufi kaima uwarsa rahoto dan duk suna cikin ɗakunansu aunty Amarya ce kawai a wajen Abba dan yau itace da shi. Sun sami Ammah na sallar walha, sai Nasreen da ke kuka mamanta ta daketa, yayinda ita kuma Hawwahn ke ƙoƙarin saka turaren wuta a rushin da ta ɗibo………✍️

 

 

 

 

 

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

 

*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*

 

FURAR DANKO

Billyn Abdul

 

-ZAFIN KAI

Mamuhgee

 

-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma

 

-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo

 

Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400

 

Pay at👇

 

1487616276

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇

 

09032345899

 

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070

 

 

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

 

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

 

Zafafa🫶🔥

 

 

 

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments