Breaking News

Gidan Aunty Book 1 Page 51-52

BOOK 1📕

Page 51_52💖

Zaro idanuwanta tayi waje tana kallansa da mugun mamaki akan fuskarta, kokarin tashi take akansa amma ya ki bata damar Hakan bata Ankara ba sai ji tayi ya mirginata ta koma kasan sa , motsi ta somayi da bakinta ,kokarin magana take amma ta kasa sai


kallan kofa da take , bin jikinta yake da kallo ganin wari irin kyau da ta kara yi masa , fuskarta ta ciro sai glowing yake ,tunda yake a rayuwarsa zai iya rantsewa bai taba tsayawa ya rike ko hannun mace ba , shi kansa mamakin irin kallan da yake mata yake ,kamar wani magnet haka ya kura wa fuskarta kallo, babu abunda ya fu birgeshi kamar yanda lips dinta suke faman rawa, ga kwayar idanuwanta da suka kara haske da sheki, hannunta d’aya ta daga zata turesa yayi saurin rike hannun sai yanxu idanunsa suka kai kan zanan dake hannunta, kokarin kwace hannun take ya kara rikewa,bin hannun yake da kallo kamar yau yata ba ganin hannun nata , a hankali ya dago da kallan su zuwa gare ta “ wanene yayi miki wannan abun”,bata gane me yake nufi ba shiyasa ta dan kallesa , kunshin dake hannunta ya nuna mata da ido, dan kawar da Kai tayi kafun ta furta “watace”, bece mata komai ba sai hannun da ya kara bi da kallo, bude tafin hannunta yayi guda d’aya tare da yi wa hannun kiss, saurin fusge hannunta tayi jin bakon lamari na ziyartarta tun daga kan dan yatsun kafarta,hannun kallanta yayi ganin ta hade ran ta ,tana bude hannun, kara rike hannnun yayi tare da zuba mata lumsassun idanuwansa,”Are you still angry” ya furta mata,bata bashi amsava sai ma cewa da tayi “ ni ka saukar mun ajiki”,bata kammala zancan nata ba ya kara kusan tota sosai, hakan da yayi kuwa shi yabawa damar bathrub dinta kara budewa,breast dinta daya gama shan gyara sosai suka kara girma,kallan ta yayi kafun ya mayar da kallansa kan breast din a karo na biyu, hannu daya yasaka ya fincike bathrub din, baki ta bude da niyar yin ihun ya hade bakinsu waje daya, wani irin kiss yake mata me wuyar fassara,sumbatarta kawai yake idanuwansa a kulle, hannunsa daya yakai kan breast din, jin laushin su kadai yakara zautar dashi, duka hannayensa biyu yasaka ya damki breast din nata,matsasu kawai yake da hannayensa biyu, fisge bakinta da ya fara yayi tayi tana kuka kasa kasa jin yanda bakinta da breast dinta ke zafi, saukar bakinshi akan breast dinta ne yasata sakin wani ajiyar zuciya me karfi, rintse idanuwanta da suka fara canza launi tayi, sakonsa sosai yake ziyartarta, kasa kasa ya somayi da hannunsa har ya dora akan mararta, zaro ido waje tahee tayi wani irin tsoro da fargaba na ziyartarta,ganin yana kokarin cire mata pant din jikinta ne yasata sakin kuka , a mugun rude ta fara basa hakuri” dan Allah yaya king kayi hakuri bazan sake ba,dan Allah”, be kulataba sai hannunsa da yake kokarin do rawa a kasan Marar ta ,cikin sauri ta riko hannunsa , tana langwabar da Kai , cikin muryar da bata san ta iya ba ta soma bashi hakuri”Dan Allah dady”, kallanta yayi jin dadyn data kara ambata,muryarsa a shake ya furta “meyasa” wani kukan takaicine ya kamata , tsoran ta ma kada wani yashigo dakin ya samesu a haka” ni banaso “ ta karasa da niyar sakin kuka, hannunsa ya dora abaki alamun ta yi mishi shiru, shirun kuwa tayi masa tana fiki fiki da idanuwanta,”ni inaso” ya bata amsa ,waro idanuwanta tahee tayi jin amsarsa,”Dan Allah kayi hakuri , mahma zata iya shigowa ko dada dan Allah kabar dakin nan”, jinjina mata kai yayi,”sune bakyaso su ganki, toh bari na baki ajiyar baby inyaso sai su gani da kyau”, fashewa kawai tayi da kuka ganin ta rasa abun cewa ma,dariyar da take kokarin fitowa ya hadiye tare da daure fuskarsa , girgiza masa kai tashiga yi kamar wata yarinya ,”dan Allah “ tsoro duk ya bayyana a fuskarta sai faman hada gumi take “ ba fushi kike da dadyn ba, shiyasa zan miki abunda zaki dena fushin”, girgiza Kai tashiga yi tunkan ya karasa zancansa “na dena fushi da kai Allah”, girgiza mata kai yayi “nan yardaba “ bata bari ya kai karshen zan can saba tace “Allah da gaske nake”, karamun dan ya tsansa ya mika mata friends, burun ta kawai ya bar dakin shiyasa tayi sauri sarke karamun dan yatsan, gajeran murmushi ya saki” mun zama friends tunda kin amince and duk abunda friend yake ayi dole ayi kinyarda “ nan cikin sauri ta gyada masa kai”na yadda “, kallanta kawai yayi batare da cewa komai ba “ba tafiya zakayi ba” tayi sauri fada tana dauka bathrub dinta, girgiza mata kai yayi “ah ah anan zan kwana” kamar wacce zata saki kuka ta furta kayi hakuri dan Allah mahma zata iya shigowa,”ok bari na kira ta sai na fada mata ba sai tazo ba kina wajena”ya karasa yana daukar wayar tasa, da wani irin mugun sauri takamo gabansa batasan lokacin da ta fincike wayar hannunsa ba, zaro idanuwansa yayi da mamaki kafun ya hade ransa lokaci d’aya ,tana ganin yanda ya hade ransa take a wajan wasu hawaye suka fara sakkomata, cikin yar rawar da hannunta ya soma ta miko masa wayar”kayi hakuri dan Allah”, be amsa mata ba sai zama da ya gyara, wani saban kukan ta fashe masa dashi” dan Allah kayi hakuri dady”, be ce mata komai sai hannunsa d’aya daya mika mata atunaninta wayar zai karba sai taga ya rike hannunta tare da kaishi saitin bakinsa ya sumbata” I like it so much “ ya fada tare da kara kai bakinsa kan hannunta da yasha maroon din kunshi ya sunbata.motsin da ta Jine yasata saurin hade hannayenta biyu “dan Allah dady ?gashinan mahma zata shigo ,please badan niba “da mamaki ya kalleta,lalle bata san wanene shi ba sunan kawai take ji, kara gyara zama sa yayi, ita kuma gabaki d’aya ta rude mikewa yayi tare da zuwa inda take Daidai lokacin da ake taba kofar dakin, da wani irin sauri ta janyosa bayan kofar tare da dora hannunta guda daya kan kirjinsa,he can’t believe it wai shi ne abayan kofa yau , bece mata komai ba sai hannunsa da ya saka cikin aljihu yana kallan ikon Allah. Basma ce ta bude kofar tana kallan tahee dake jikin kofar itama ,kokarin shigo dakin take amma tahee taki bata wannan damar, sakin baki tayi tana kallan yanda ta koma ko wata babbar albarka ,yar dariya basma ta saki duk da azuciyarta ba haka bane,”Lalle baki da hankali,da kika tsaya akai miki wannan abun da ko kyau be miki ba”, kallan tara saura kwata tahee tayi mata sam ta manta king na bayan kofa” ko ina da ja da kyan da nayi, ta karasa zancanta tana dan juyawa, karki damu wanda akayiwa dan shi ya yaba ya biya tukwuici kinga nana bukatar yabawar wasu “ta karasa zancan tana turo kofar ta tare da barin basma da sunan tsaye,sai alokacin idanuwanta suka sauka kansa , gira d’aya y dage mata da sauri kuwa ta juya masa baya wani kunya na kamata Allah yasa be jita ba, murmushi ya kasaki kadan da ko a la’b ‘bansa be fito wa ,cikin kunnnata ya rada “ na yaba amma ban bada tukuicin ba ai “ ya kara zancanta tare da daukar wani Siririn box me shegen walwali, ita dai har yanxu bata san meke faruwa ba dan taki yarda takallesa, wani dan siririn chain ya ciro a ciki meshegen walwali da daukar ido yasa mata a tsintsiyar hannunta , jikin chain din wani dan karamin adone da rubutu a cikinsa. “Ga tukwuicina”, ya karasa zan cansa da yi mata peck a kumatu,kasa motsi tayi saida taji karar rufe kofa alamar ya futa, wani irin ajiyar zuciya ta sauke fatanta Allah yasa karya hadu da kowa a hanya , chain din hannunta ta kura wa ido ganin yanda take ta faman walwali a hannunta har yanxu , sumbatar hannun tayi tana sakin murmushi ita kadai ,wani irin son king ne ke kara shiga zuciya da bargon ta , a wani ban garan kuma ta na tausayin kanta ne sanin cewa baya santa, kwallar da ta tarar mata ta goge , shaf shaf ta shirya jikinta cikin kayan bacci tare da kwantawa,bata dade ba bacci yau keta me cike da mafarkai daban daban.

✨✨✨✨✨

WASHE GARI

Tunda ta tashi sallar asuba da wani irin tsoro da firgici ta tashi, ita kadai sai faman kuka take, jikinta har ya fara daukar zafin zazzzabi, tana idar da sallanta amzy ta shigo dakin cikin sallama bayan ta kuma mahma ce ko wannansu d’auke da tray a hannunsa, cikin sanyin jiki da kunyar da ya kamata ta gaishesu,gabaki d’aya amsa mata sukai cikin farin ciki ,trays din hannunsu suka ajje mata ,mahma na mikewa ta kalli amzy” amzy ga yata nan ki tabbatar kinyi abunda ya dace”, Insha Allahu cewar amzy tana sakin murmushi, fita mahma tayi ta barsu itama amzy abincin da aka kawo wa tahee tasata ci da kyar shima din tsakura tayi, bayan ta kammala cin abincin da kusan mintuna talatin amzy ta miko mata babban tray din gabanta, kaza ce a ciki jikinta duk Kantu sai wasu kayan fruit da wani abu da bansan ko menene ba ta sata sa ciki, kamar zatayi kuka kuwa hka ta zauna tana ci jikin ta duk ba dadi yau , da kyar ta cinyesu, tana kammala ci amzy ta sata yin wani wanka bayan Wanda tayi da turaruka da ya fi na baya kamshi,tana fitowa amzy ta shafe mata jikinta da wani abu sai glowing fatar jikinta keyi, bayan sun kammala ne amzy ta kara zaunar da ita , darasin yanda ake kula da miji ta fara mata da yadda zata kankaro wa kanta mutunci, sosai take mata darasi akan zaman aure da hakuri da juna, ta karasa zancanta dacewa “da yawa matan hausawa sun kasa ganewa , zama da miji bawai kawai auratayya da za kudunga yi bane aure, akwai kyauta tawa, akwia biyayya, akwia tsafta, uwa uba iri girki, kafin kiyi masa magana ki tabbata me dadi ce zata fito daga bakinki, idan kinga ransa yana abace kisaka kissarki ta mace ki shawo hankalinsa tare da kwantar masa da hankali, idan wani abun farin ciki ya samesa ki nuna masa kin fisa farinciki, idan na bakin ciki ne ma ki nuna masa rashin jin dadi, ki zama me kula da tsabtar ki da tsaftar mijinki, dan kina da yar aiki ba hakan ne ze baki dama ba kice bari ta wanke wa me gidan ki abu ba,komai dukiya da nasabarki ki kyautatawa mijinki, dan boxer din nan idan nacire dauka ki wanke masa cikin farin ciki( da yawa mutane abunda basa ganewa wanke wa miji boxer da singlet ba kazanta bace kamar yadda wasu ke dauka,wallahi ba karamun so , mutunci da kima yake karawa mace wayan mujinta ba, shiyasa hausawa ke cewa yare asirce miji suke yi kuma da yawa daga ciki ba haka bane tsantsan kulawa da mijine kawai,masu Shan maganin mata kuma ku kiyayi kanku wallahi ba kowana magani ne ake sha ba,idan kika yawaita shan maganin mata Wallahi duk ranar da baki shaba mijinki sai ya jiki wani irin, idan kinasan gyara kanki ina kika bar fruit masu daraja, ina kika bar dabino,kwakwa, da madara,abubuwa da ban daban , idan matsincin ne ki yawaita yin Tsarki da ruwan dumi wallahi ke da kanki zaki ji canji a jikinki, ina kukabar kanunfari!? Shima akwia abubuwa da mana da zakiyi wajan gyara jikin ki da abubuwa nagartattu basai kinje kin bata kanki ba ,please mata mu kula please yar kisisinar nan da rankwada da shagwaba a dungayi , dan honey 😂, darling dinnan please , karki yarda waidan kina da ‘ya’ya kice kin dena , da kun shiga daki maida kanki kamar yar baby😂, kar inji ana baban sani ko baban haruna, yan gidan aunty daku nake ,MAMAN SUDAIS kija musu kunne)sosai amzy ta cire kunya ta koyar da ita abubuwa da yawa, tsabar kunya kasa dago dakanta tahee tayi , ita kadai sai kuka take, amzy bata kulataba sai data bata kalubalan rayuwa, aure dan hakuri ne ,zomu zauna zo mu saba ba kullum ne ake kasancewa cikin farinciki ba. Ba ita ta kyaletaba sai wajan 2, bayan ta bata damar tayi sallah sannan aka kara sa mata wasu turarukan da zatayi Wanka dasu,TAHEE har yanxu bata dena kukan ba,tayi sallah tare da yin Wanka , wani Saban kukane ya kara zuwar mata , oummanta da taheer dinta duk sai da tayi musu addua sosai,uku daidai amzy tashigo dakin dauke da wata trolley me dan girma, wani brown din atanface me shegen kyau ba wani tarkacene a ciki ba simple dinki akayi amma sosai fadin yanda ya hadu bata lokaci ne, stone din jikin kayan sai faman walwali suke takalmi da da pose duk saida ta fito mata dashi da mayafinta, shiryawa tahee tayi cikin kayan bakaramun kyau sukai mata a jiki ba kamar a jikinta aka dinka su,sai da ta bari akai kiran sallar la’asar sannan tayi mata simple makeup mata hanayina, “fatabarakallahu ahsanin khalikin, Allah yayi halitta awajan nan ,sai da na furta Masha Allah, Masha Allah , Masha Allah, Iya kyau da haduwa ta hadu, tayi kyaun da yafi Akirata da zinariya , daya tamkar dubu ko makiyi ya ganta sai ya kara kallanta balantana masoyinta,abun hannun da king yasa mata sai faman kyalkyali yake , stones din jikin kayan ma sai ya kara kawata kwalliyarta, daura mata dan kwalin amzy tayi amma ta boye mata gashin kanta sai wanda suka kwanta a gangan goshinta, farar kyakkyawar fuskarta sosai ya fito cikin daurin bakinta sai faman sheki yake, takalmin da amzy ta dakko mata me dan tsini ne kadan,hatta da bracelets din daka saka mata masu walwaline,sai pose din data mika mata tana yafa mata mayafi, ita kanta amzy tana shiryata tana sakin murmushi me kayatarwa tabbas kyan da ake cewa akwai kyau tabbas akwai kyaun ,waje ta samu ta zaunar da ita akan gadon ka fun ta fita daga dakin, Daidai inda ta zauna din taji dan tudu a wajan , tana dubawa wayarsa ta jiya ta gani a wajan da Sauri ta saka ta cikin pose din gudun kar wani ya shigo dakin,amzy ce ta dawo dauke da kayan daukar hoto sosai ta ke dauka tahee ,zaman da tayi akan gadon sai ya kara kayata wajan kasantuwar bedsheet din gadon me design din brown ne , suna cikin saukar hoton mahma ta shigo ita da small mom, gabaki d’aya sakin baki sukai suna kallan ikon Allah,In banda tubarkalla Masha Allah babu abunda bakinsu ke furtawa, gabaki dayan su sun kasa kwakkwaran motsi, mahma ce tayi karfin furta “tubarkalla Masha Allah “ a fili, “daughter wannan kyan naki ya wuce akira ki da kyakkyawa sai dai shugaban kyawawa , har na rasa tsakanin keda mijin naki wanene ya fi kyau,”a maimakon su fito da amarya kamar yanda akace sai suka tsaya koda ta , gabaki dayan su photograper suka zama sai faman daukan ta hoto suke , saura kadan ta fashe da kuka, tun snap din da amzy tayi Mata tasaka a status dinta , cikin mintuna da basu fi goma ba sama da mutane dari sai da sukai mata magana harda Wanda basa kulata , HIS QUEEN shine kadai abunda ta rubuta a jiki amma zonaga comment, zata kara posting mahma ta hana ta sabida tasan in king yagani baruwanshi zaiyi maganintane, da sauri kuwa ta cire tana sakin dariya ko ba komai kusan mutane ashirin sun yi booking dinta acikin mintuna da be wuce goma ba, tabbas zuwan ta gidan alkairi ne,mikar da amarya suka tare da gyara mata mayafin kanta, abun hannunta ne ya sauka a kan hannun tahee , zaro idanuwa waje tayi tana sakin dariya “ Diamond heart love “, ta furta kasan zuciyarta, iya hasashenta ta kasa hasasho a dadin kudin sa Sabida yanda yake walwali zai tabbatar maka da asalin zallan diamond akayi shi. Har za’a sanar da fitowar amarya mahma ta hana acewarta angone zai fara ganin kwalliyar, gabaki d’aya fita sukai akabar small mom gudun kar Wanda ya shigo dakin, mahma kuwa kai tsaye part din king ta nufa, bin falon na shigayi da kallo dan gabaki d’aya an canza komai na cikin falon komai nacikin falon sabone, kallan sha’aban dake cikin shigar manyan kaya fara kaldasu tayi,”yana ina “ ta furta , fusgar da iskar bakinsa yayi” mahma tun dazu nake kiransa amma yaki jina yayi wuce warsa sama wai bacci zaiyi”, mahma batace komai ba sai wayar ta da ta dauka cikin dan baci bacin rai take kokarin dialing din number din sa, wani irin sahirtaccen kamshin turaransane ya daki hancinta, da sauri ta daga idanuwanta tana binsa da kallo, gabaki dayansu daga ita har sha’aban sakin baki sukai suna binsa da kallon kurulla, yayi bala’in kyaun da baki bazai iya kiyas ta kyan da yayi ba, sanye yake cikin wasu hadaddan ubansun shadda, light brown meshegen kyau da tsada kallo daya zaka mata kasan ba karamun kudi aka kashe mata ba, dinkin zamani ne ajikin rigar hatta babbar rigar dake jikinsa, kafarsa sanye take cikin wani half qucci dark brown kafarsa fara suwal sosai ta bayyana a cikin takalmin, fararan hannunsa ma sanye yake cikin diamond wuce me shegen tsada da zoben sa , dayan hannun kuma wasu siraran abun hannun diamond a jiki, dayan kusan kullum yana hannunsa Wanda ya fi kyallin cikine kawai yafi daukar idona, fuskarshi babu ko digon murmushi kawai amma ba kadan ta fito da zallan kyansa na larabawa ba, pink lips dinsa sosai ya turo ga gashinn idanuwansa da suka kara fito da fararan idanuwansa,hatta gashin kansa gyaran da ya sha nadaban ne sabida yanda hular kansa ta fito da adon gashinsa, a hankali yake taka stairs din sai ji yayi ana snapping dinsa , dago idan da zaiyi ba sha’aban kadai ba hatta mahma snapping dinsa take, tunda aka haifeshi zata iya rantsewa bata taba ganin kyawun da ta hango awajan saba kamar yau, dukda kasancewar sa kyakkyawa ne shi na karshen karshen, dan hararan sha’aban yayi yana kara tsuke fuskarsa kafun ya kalli mahma dake faman sakin murmushi”son na kasa ganewa da kai da ita wanene yafi wani haduwa,kamar hadin baki ,Anya bazan fara kishi ba “ ta karasa cikin Zolaya, dan kauna kansa yayi batare da yace komai ba, wani shegiyar dariyar iskanci sha’aban ya saka da har saida mahma da kai masa duka, hanyar fita king ya nufa kallansa mahma tayi ina zuwa,batare da ya kalleta ba ya furta “ office”, da sauri ta kallesa “office, wasa kake ko , dan wallahi yau duk wani miskilancin ka bazan dauka ba , yanxu maza ka wuce kai muke jira ka fito da amarya, nan da mintuna biyar nakeso a fito da ita inva haka ba ran kowa sai ya baci”ta karasa da nuna sha’aban “Kai ma wuce ka tafi wajan taron “ da sauri kuwa ya wuce yana dariyar dramarta da king, ganin tana kokarin juyawa yasashi riko hannunta, harara ta sakar masa zata wuce ya rungumeta “ am sorry, I will do everything to make you happy” wani murmushi ne ya subuce mata raba jikin ta tayi da nasa tana shafa gefan fuskarsa “ please kazo in not less than 5 minutes dan Allah “ lumshe mata ido yayi alamar toh, ta gane me yake nufi shiyasa ta juya ta far part din, amaimakon ya biyo bayansu sai ya shiga wani dakin da tahee ta taba zama dashima komai na ciki sai da aka canza masa, dan wani bottom ya danna da komai ganin ka bazaka san dashi ba, yana dannawa kuma wardrobe din wajan ta rabe biyu yana shiga ya kulle taci , ta wajan kuma wai ta dawo yanda take kamar babu wani makamancin abu a wajan, tafiya yayi me dan tazara kadan kafun ya iso wasu kofofi a wajn, kofar biyun karshe ya nufa, yana bude kofar abun mamaki sai gashi a part din dada, a bun frame din dake wajan ya taba take awajan kofar ta kulle ya dawo ainahin jikin bangon,yana dan jin hayaniyar mutanan gidan kadan kadan, dan tafiya yayi kadan batare da kowa ya gansa ba , kofar dakin da take ya kalla kusan second biyu kafun ya murda ya shiga dakin da sallama, sallamar sa daddadan kamshin sane ya ziyarceta da sauri ta daga manyan idanuwanta, take a wajan ya sauka cikin nasa idanuwan dake binta da wani irin kallon dashi kadai yasan ma’anarsu, yanda ya jingida da jikin bangon dakin ta kalla , itama a wannan karan ta kasa dauke kallanta daga garesa, cikin takun kasaita ya nufota da tun lokacin da ta kallesa bugawa zuciyarta ya tsananta, gefen inda take ya zauna tare da dora kanta akan kafadunsa” cikin rada rada ya furta fatabarakallahu ahsanin khalikin”,daga nan be kara cewa komai ba sai sauraran zuciyoyin su da suke yi na tsawan mintuna biyar itama tana lafe kwance kan kafadunsa, knocking kofar akai saudaya kafun suji saukar muryar Mahma” zaku iya fitowa yanxu” tana kammala zancanta , suka farajin takun takalmin ta alamar ta bar wajan, kusan mintuna biyu kafun ya mike tare da ita a cikinsa yana nufar kofar fita da ita da sauri ta kwace jikinta tana zaro masa ido , idanun cike da kalla harda dan turo karamin bakinta,kallan bakin yayi kafin ya kalleta “bakin nan da kike yawan turo Munsu xanyi maganinki and in baki dena ba yanxu ba gobe ba zan karbesu kamar yanda kika so” ai damugun sauri ta mayar da lips dinta tana sunkuyar da kanta, be kara bata damar magana ba ya janyota ajikinsa tare da tura dakin, sai da ya kara janyo gelenta kadan ya tabbatar ya rufe mata ciki kafun su karaso kofar da kowa ke zaune anzuba mata ido ana jiran fitowarsu, gefensu wasu matane guda hudu ko wanne da damin fulawa a hannunsa,suna jin alamun taba kofa aka kashe gabaki daya light din wajan sai ta wajan kofa da aka bari masu walwali,ana bude kofar zo kuga yadda zuciyoyin mutane ya dunga tsunkewa take a wajan aka fara musu watsin flowers masu kyau kafun wutar wajan ta dawo gabaki d’aya , gabaki d’aya mutanan wajan zuba musu ido sukai ga wata irin dum waka dake tashi kadan dan ,kowa ya rasa abun cewa basma da ke kokarin dago kai sai gashi tayi saurin maida kanta , amrah ma bakadan ba tayi nadamar zuwa wajan har idanuwanta suka sauka akansa, yanda ya rike ta sai ka dauka wayanda suka dade da shiga gogin soyayya bakaramun matching sukai ba , me daukar hoto sai faman taukansu yake , yanda take faman kashe idone alamun hasken ya mata yawa be san lokacin daya kwantar da Kanta kan kirjinsa ba ,gabaki d’aya mutanan falon kara sakin baki sukai suna kallan ikon Allah , Kai tsaye wajan dada suka nufa , tana ganinsu ta saki kuka me taba rai”oh ni yasu , Allah nagode maka adduar tsawan ran da nadungayi yau ta cika burina ya cika naganin Auran tahanuni, tunda Allah ya dauke ran mahmuda, Allah ka basu zaman lapiya me dorewa” ta karasa zancanta tana goge hawayanta, wani dan madaidaicin box dada ta dakko tare da daurawa tahee a tafukan hannunta”wannan kyauta ce na baki sabida yanda kike sani farin ciki tahura ta karki ji komai duk lokacin da ya bata miki rai ki sanar dani zanyi maganinsa” kuka tahee ta fashe dashi me rasa zuciya ko magana ta kasa yi,a hankali sautin kukanta ke tashi kadan kadan, daga wajan dada wajan ummey aka nufa dake share hawayan farinciki yau Allah ya nuna mata bikin d’anta da take mararin gani har cikin zuciyarta , itama nasihar tayi musu kafun ta bawa tahee kyautar diamonds set tundaga kan sarka , dan kunne , zobe da abun hannu bayanshi kuma ta bata kyautar manyan Lamborghini sababbin yayi gudu biyu ,guda gabaki d’aya aka saka afalon dukda dayawa mutanan wajan ba haka suka soba , da aka zo kan ammey kuwa kuka ta fashe dashi daya taba ran kowa ga tahee da take kuka kasa kasa itama , da kyar aka samu tayi shiru itama nasiha tayi musu kafun tayi musu kyautar diamond itama da babban mall dinta dake Lagos, kowa yaji dadin yanda ta hadasu musamman yanda ta raini king amatsayin d’anta tun yana karami,gabaki d’aya iyayan falon kowa kyautar da daga gold sai kyautar motoci da company da take samu , wannan abu shi ya kara bakatawa amrah da basma rai kowa yana ganin da ace babu tahee da shine zai samu wannan kyautar. Part din abeey aka suka nufa mahma na take musu baya, yanda ya gansu ba karamun farinciki yasa shiba daya kasa boyuwa akan fuskarsa, shima sosai yayi musu nasiha ne ratsa jiki akan zaman aure, yana kammala yi musu kuma ya basu kyaututttuka masu girman gaske , d’aya daga cikin jirgin NAHYAN sukutum ya mallakawa tahee,wani saban kuka tahee tasaka masu, kama hannunta mahma tayi batare da ta bari tace komai ba ta nufa da ita dakin da su ummey suke ciki daga ummey sea small mom, anyi anyi da ammey tazo taki zuwa acewarta sune iyayanta ai, sosai suka zaunar da ita sukai mata nasiha me ratsa jijiyoyin jiki da tsoka ko wannansu saida ya rungumeta tare da lallashinta kafun abar mahma ita kadai sai amzy da aka kara kira , wani wanka suka sata ta sake yi kafun su shirya ta cikin Wani Dan ubansun lace meshegen kyau red colour , shigarta ta ynxu harta taka wanda aka yi mata dazu kyau da haduwa, wani abu amzy ta bata Tasha kafun akara kyarata, suna kama gyarata kuwa aka dakko wata lapaya red itama aka nada mata a jiki( oh oh oh ni miss lee, ni kaina saida kyawun ta ya tafi dani).

A bangaran king kuwa Suna fita abeey ya rungumeshi , yana sauke a jiyar zuciya ba “addua ta daya kullum naga auranka tun bayan rasuwar Mohammad, amma Allah baiyi ba sai yanxu , na rokeka ba danni badan na isa da kai ba , ka kula da maraicin yarinyar nan , tana bukatar kulawa ta musamman ko dan irin kaddarar rayuwar da ta fuskanci kanta a ciki, idan kamun hakan ka gama yi mun komai arayuwata, Allah yayi maka albarka yanda ka faranta mun Allah ya baka masu faranta maka kaima “, lumshe idanuwansa king yayi yanajin kalaman mahaifinsa har cikin zuciyarsa,har yanxu yana tuna kalaman nan” akhie , idan Allah yasa ban ga auranka ba inaso ka zama da happiness man , ranar auranka,duk matar da aka zaba maka ka karbeta hannu biyu kasota kamar yanda kake san mu”, kara lumshe idanuwansa yayi tuno Wannan kalaman daka wajan mutumin da har yau bazai taba mantawa dashi ba, besan lokacin da bakinsa ya furta “I promise you , I will always be what you wanted me to be”, kara rungumeshi abeey yayi tsam a jikinsa kafun ya raba jikinsu, dan Allah abeey king yayi “abeey ni baka bani kyautar jirgin ba ‘ai”, dan bugunshi abeey yayi “ Wanda kake dasu ya isheka, maza tashi kabar mun daki”, wani gajeran murmushi king ya saki da ya fito da zallan kyawun da Allah yayi masa ,ban taba ganin wanda ko be yi murmushi ba yana kyau balantana ya gwada koda motsa lips dinsa ne, sallama yayi wa abeey kafun ya bar part din, koda suka hadu da sha’aban sai faman tsiya yake masa, saida ya dawo masa asalin king dinsa kafin ya kyalesa.

✨✨✨✨

Karfe 8:20 pm mahma da small mom suka dauki tahee zuwa dakinta na aure bayan nasihohin da jan hankalin da akai mata,kasa mikewa tahee tayi daga zaunan da take sai faman kukar da take Durza da ya haifar mata da zazzabi, mikar da ita small mom tayi kafun su nufi motar da aka bude musu, ba ayarda kowa ya bisuba,suna zuwa Daidai part din akasa tahee ta fitowa da kafar dama bakin ta dauke da bismilla,har suka shigo part din komai sai sun sa tayi bismilla cike da addua suka shiga part din, basu tsaya a falo ba suka hau step da ita, wani door suka bude Babban falo ne meshegen kyau a wajan, shima basu tsaya a wajan ba kai tsaye daya daga cikin bedrooms din aka kaita, ba bata lokaci su mahma suka sata yin wani saban wanka, tare da shirya ta, saida suka zo tafiya ne tasakar musu wani saban kukan , jikinta sai faman rawa yake sabida zazzabin da ya kamata,da kyar suka samu sukayi mata dabara suka gudu. Ganin saura ita kai yasa ta kara fashewa da wani saban kukan.

Kallan yanda take faman kuka yayi kafun ya karaso cikin dakin bakinsa dauke da sallama , kan gadon ya karasa tare da dagowa, jin an dagata yasa tayi saurin bude idanuwanta , kallan Wanda ya dagatan tayi kafun ta kara sunkuyar da kan nata tana fashewa da wani saban kukan, rungumeta yayi a jikinsa yana sauraran yanda take kukan,bayanta ya dan shafa kafun ya furta “it’s ok don’t cry”, a tsaye ya cigaba da shafa bayanta har saida ta daina kukan ta dawo ajiyar zuciya .

Zaunar da ita yayi akan gadon kafin ya fita daga dakin ba dade wa ya dawo hannunsa dauke da karamun tray,farfesun kayan cikin dake cikin plate din ya mika mata , girgiza masa kai tayi alamun bata jin yuwa, shima dan girgiza mata kan yayi ganin tana kokarin yi masa musu yasa ya hade ransa , da sauri ta fara shan farfesun,daman yunwa take ji , be kyaleta ba saida Tasha fresh milk din da ya zuba mata, tana kammalawa ya bata magunguna Tasha , tana turo bakinta tashanye magun gunan,”we’re friends ai yanxu ko”, dan kanta ta daga masa kadan har yanxu taki yarda ta kallesa”ok since we’re friends , ai zaki te makamun ko” yanxu ma kanta daga masa, murmushin iya kan labba ya saki kafun ya mike “je kiyi alwala, turo masa bakinta tayi kafun ta furta “ni nayi salla” Nima nayi ai , ya bata amsa ganin zata kara magana ya katseta “banasan musu go and do what I asked you “
Tana shiga toilet ya ciro mata hijab shima ya fita , futowarta daga toilet din ta tarar da hijab din da ya fito mata dashi, sawa tayi Daidai lokacin da yashigo dakin,sallah ya ja su raka ‘a biyu , ya dade yana addua kafun ya dora tafukan hannunsa akanta yana addua, duk tanbayar da yayi mata game da addininta sosai take bashi amsa, suna kammala adduar ta kara turo bakinta, kallanta yayi kafun ya furta “na fita ko” da sauri ta daga masa kai, be ce mata komai ba kuwa yace mata saida safe ,kafun ya bar dakin. Wani ajiyar zuciya ta sauke , wardrobe ta bude ganin babu kayanta aciki sai wata karamar trolley , tana bude wasu kayan bacci ne a ciki dakyar ta iya daukan guda daya a ciki ta saka , tana sakawa ita kansa saida taji kunyar kayan da sauri ta haye kan gadon tana lulluba sabida sanyin da ya ratsa mata sassan jiki, da Kyar bacci barawo ya saceta tanayi tana farkawa gudun karya shigo dakin kafun bacci ya nauyi ya dauke ta sosai.

Karfe 2am ya shigo dakin ganin ta takure waje daya ne yashi karasawa gaban kan,a gefenta ya kwanta a hankali gudun kar ta tashi daga baccin da take yi kamar a takure, goshinta ya taba yaji har yanxu zafin jikin ta be sauka ba, janyota yayi gabaki dayanta ya dora akan kirjinsa, wani ajiyar zuciya ta sauke me karfi da yasashi kallanta kadan, kara rungumeshi taji ajikinta kamar wacce akace za’a kwace mata shi, lullube jikinsu yayi da bargon yana jin yanda zafin jikinta ke ratsa sa,kallan innocent face dinta dake bacci cikin kwanciyar hankali yayi kafun ya furta “ stubborn girl na kusa yin maganinki “, yana kara rungumeta a jikinsa, ba dadewa shima bacci ya daukesa, baccin da zai iya cewa tun tsawan wasu shekarun baya beyi baccin da begaji dayinsaba kamar na yau.

Kiran sallar asuba na farko ne ya farkar dashi, a hankali ya fara mutsu mutsu da idanuwansa kafun ya bude su gabaki d’aya akan kyakkyawar fuskarta ,zubawa fuskar idanuwansa yayi Kafun ya gyara mata kwanciyarta yana barin dakin. Kusan mintuna 30 da fitarsa itama ta soma mutsu mutsu kafun ta bude idanuwan gabaki d’aya, adduar tashi daga bacci tayi a bayyane ganin babu kowa a dakin yasa ta sakin ajiyar zuciya , Wanka tayi cikin simple doguwar Riga kafun ta tayar da sallar asuba , tana idarwa karatun alkurani ta yi , ta dauki kusan good 2 hours tana karatun har saida gari ya fara haske tukunna.

Turo kofar dakin da akaine yasa ta Mayar da kallanta bakin kofar, zuba masa ido tayi ganin shirgarsa ta yau sak balarabensa , jallabiya ce a jikinsa white colour sai abun nadin larabawa red colour , harya karaso wajan bata sani ba sabida yanda ta zuba masa ido , sai da ya hura mata iska kadan kafun ta sauke ajiyar zuciya, cikin kunya ta sunkuyar da kanta,kafun ta furta “ina kwana”, ba amsa mata ba sai kallanta da yayi, kara maimaita gaisuwar tata tayi ,ynxu ma be kulata ba , sun kuyar da Kai tayi kasa ya daga da kanta, bakinsu ya hade waje d’aya kusan mintuna daya kafun ya zare bakinsa “ bakyajin magana kenan ko”girgiza masa kai tayi alamun Aah , waje ya samu ya zauna , dan turo masa bakinta tayi kadan “ina kwana “, har yanxu be amsa gaisuwar tata va, sai ma a wayarsa da ya dauka , tunowa da wacce take hannunta yasa taje ta dakko ta , binta da ido kawai yayi kafun ya dauke kansa, cikin girmamawa ta miko masa wayar be amsa ba sannan be kalletaba,”ga Wanka “ ta furta a sanyaye, kallanta yayi “Menene nawa “ wayanka ta basa amsa ,”it’s your” ya furta , da wani irin shock ta kallesa, batasan lokacin data rungumeshi ba,hannu d’aya yasaka ya tallabota gudun karta fadi” dady dagaske ta wace”, gira kawai ya dage mata,kara rungumeshi tayi lokaci d’aya wani kukan ya kara wace mata, dagasken gasken yanxu kukan take me taba zuciya , very tight king ya rungumeta a kunne ya rada mata “it’s ok” kafun ya dago da ita , kallan yanda hawayen suke zuba afuskarta yayi kafun ya harareta kadan”so kuke su mahma suzo suce miki na miki wani abun kenan ko”, girgixa masa kai tayi tana goge hawayan nata “nagode sosai Allah ya kara budi”ya ji dadin adduar da tayi masa sosai cikin zuciyarsa ya amsa da amin, a fili kuwa dan tabile baki yayi “we’re friends ai no need” jinjina masa kai tayi zata mike yakara gyara mata zama akan cinyarsa,yanda ake anfani da yawar ya nuna mata komai already daman anyi settling komai na cikin wayar, murmushin fuskarta kasa boyuwa yayi sosai ta nuna jin dadinta,ganin karfe takwas ta kallesa “dady me kake so kaci” Kai tsaye ya bata amsa da “you”,wara idanuwanta tayi “toh ni taya za a da fani” bece mata komai ba yakama hannunta suka fito falon sai ynxu ta ke kallan yanda komai na dakin yake a canje,janta yayi har wajan dining ganin abunci ajjjere ne tayi serving dinsa tare da kunun aya, kince yayi saida tasa hannu ta fara basa a baki, duk loma d’aya in yayi baya sakamar mata hannun sai ya tsotseshi,abun har kunya ya fara bata, sai da tayi feeding dinshi kafun shima yasoma bata dan dole take karba,suna kammala ci falo suka zauna tana zaune kan cinyarsa kallan gashin kansa take so take ta taba amma ta kasa, kamar yasan me take tunanin ya dauki hannun nata guda daya ya dora a saman kansa,murmushi ta saki tana kara tura hannayenta cikin gashin kansa me tsananin taushi da laushi, suna zaune ahakan sukaji an turo kofar da dan karfi, zaro idanuwa tayi waje tana kokarin sauka amma ya kara riketa ajikinsa sosai yana bin amrah da tashigo masa part kai tsaye da wani rin birkitaccen kallo daya firgitata, hatta karamin ture din hannunta saida ya fadi kasa tsabar firgita.

💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖

Mss Lee 💖
💖💖GIDAN AUNTY💖💖
( a heart touching love story)

Story & written
By
Mss Lee 💖

💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖

PAID BOOK

MAI BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YA TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581.

No comments