Breaking News

Kurkukun Kaddara 24-25

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*


_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E24-25

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

Uncel abdallah ne Ya shigo Falon, Hannun shi ruƙe da key ɗin motarshi, Suit ne ajikin shi, Miƙe wa Hajiya adama tayi fuskarta asake tace “Welcome back dear, I heard the sound of cars Coming in ko munyi baƙi ne”? sai da ya samu wuri ya zauna tukunna ya kalle ta fuskarshi ɗauke da murmushi yace”Ni ne baƙon ae, fatan na same ki lafiya, Yau naga walwala atattare dake, Ga shi kin ɗau wanka kinyi kyau abunki,”

Ta6e baki ta yi “Ae tun da kayi mun albishir game da komawarmu gida, Nake ta sakin fara’a ni kaɗai abuna, Yanzu haka ma da kaganni a zaune, Ina duba kayayyakin da zan siyane na tsaraba da zanyiwa mutanan gida,” takai ƙarshen maganar tare da kama hanyar zuwa kitchen tace”Bari na kawo maka Ruwa mai sanyi kasha”

“Da kanki Hajiyata? Ina mai aikin gidan take ne”? A sukwane ta Juyo tana bin shi da kallon bansan rainin wayau,

“Oh kamanta irin Korar da kayi ma Ajumma daga gidan nan, Saboda laifin da ba nata ba, ƴar baiwar Allah, dama burinka kaga ina shiga kitchen da girmana, ae yanzu hankalin ka ya kwanta, Hajiya adama ta zama kukun mijinta” Dariya Uncle abdalla Yayi”Matar nan kina sani nishaɗi, Abun alfahari ne mace ta girka ma mijinta abinci da hannunta yaci ya sanya mata albarka, Ta samu lada, Ni ae naga Cigaba sosai, da na kori wannan tsohuwar matar, Tun barinta gidan, kika daina shan Soju, gashi yanzu kin samu natsuwa kin dawo Hajiya adamar dana sani,”

Hararar wasa ta jefa mashi daga inda take a tsaye” korar ajumma da kayi ba shi ne yasa na daina shaye shaye ba, Da naso zan fita inje in siyo da kaina ne, Allah ne yayi silar shiryuwata, dama ba halina bane, tsautsayine da ƙaddara, da kuma damuwar da na shiga na rashin mutun uku masu mahimmanci acikin rayuwata……….” muryarta a karye takai ƙarshen maganar, da sauri tajuya ta shige Cikin kitchen,

Jingina bayan shi Yayi a jikin Sofa ɗin da yake zaune, Har ga Allah Shi kanshi yana acikin matsanaciyar damuwa na rashin ya’yan shi da ya yi, Yaji raɗaɗi sosai, sai dai ba yadda zai yi, daure wa kawai ya ke yi, A duk lokacin daya tuna rashin Da yayi, Na ɗan uwansa, Kuma yayansa Malam zahiru, da mahafiyarsu deeja, Sai ya dinga Jin kanshi tamkar marayan da baida mafaɗi aduniya, Dama wake gaya mashi gaskiya idan yay badai dai ba? malam zahiru ne, tun yana yaro shi yake zaunar dashi yayi mashi nasiha game da rayuwar duniyar nan, kalmar da yafi faɗa mashi itace “ABDALLAH KAJI TSORON ALLAH, ‘ tuna wannan yasa shi kai hannu ya dafe goshinsa, Idanuwanshi suka Cicciko tab da kwalla, haƙika yaji mutuwarsu, Hatta yahana su Mahaifiyar Tajuddeen, Yaji mutuwarta sosai, Mutanan kirkiki, Mutane masu ƙima da daraja,

Ajiyar zuciya ya sauke, tare da lumshe idanuwanshi, Bakomai yake tunawa ba face Tajudeen lokacin da zai raba shi da iyayenshi, Suna kuka yana kuka saboda basu son rabuwa da juna, Suna matuƙar ƙaunar ɗansu, Amma saboda son zuciya yabi ta ƙarfi da yaji don yana da arziƙi, ya ba mahaifiyarsu Cin hanci, aka damƙa mashi yaro, tun da yake bai ta6a danasanin raba tajudeen da iyayenshi ba, Sai bayan rasuwarsu, tsawon shekaru basu yi tozali da dansu ba, har sun koma ga mahaliccin su, Shi ma kuma ɗan nasu An neme shi ƙasa ko sama babu shi, Wannan wata irin ƙaddarar rayuwace? Yanzu idan Allah yasa aka ga su tajudden Taya zai Iya Sanar dashi game da mutuwar Iyayenshi!!? innallahi wa’inna ilaihirraji’un…………

Tun ɗazu Hajiya adama ta fito daga cikin kitchen, hannunta ruƙe da plate mai ɗauke da glass cup na ruwa mai sanyi tare da snacks, ta jima a tsaye tana kallon Mijinta nata da ya yi zurfin Cikin tunani, Hawaye ta gani kwance a cikin idanuwanshi, Da alamun damuwa attare da shi ba kamar yadda ya shigo mata ba, A saman C table ta ɗaura plate ɗin dake hannunta,

Kwala mashi kira Tayi A firgice yakai idanuwanshi akanta yana kallonta

“wai lafiya dear, Ina ta kiran sunanka Amma hankalinka sam baya atare dakai, Meya faru ne? Yanzu fa nabarka fuskarka asake, amma kuma na dawo na taras dakai cikin damuwa” tayi maganar tare da kai hannu ta ɗauki Cup ɗin ruwan ta miƙa mashi,

Hannu yasa ya kar6a, tare da kaishi saitin bakinshi yana sha, Zama hajiya adama tayi tana fuskantar shi, Jira take yi ya gama sha yayi mata bayanin dalilin shiga damuwarshi,

A hankali ya sauke Cup ɗin saman table, ya zura hannu Cikin trouser pocket ɗinshi ya zaro hanky ya goge fuskarshi, sai da ya daidaita natsuwar shi tukunna ya kalle ta, gaba ɗaya hankalinta na akanshi, sam baison ya faɗa mata dalilin shiga damuwar tashi, don yasan halitta, Yanzu ta kama yi mashi kuka, shiyasa ko zancen su Taj bai cika son yi mata ba, Rauni ne da ita,

Gudun kada ta ƙara tambayar shi meke damunshi, yasa shi yin saurin canza zancen ta hanyar cewa”Yawwa, Yanzu wani shirye shirye yakamata muyi na komawa Ƙasar mu? Naji kince zaki yi siyayyar kayan tsaraba da zaki yi ma mutanan gida,”

Jinjina kai Hajiya adama tayi tare da cewa”eh, idan ya rage kamar saura 4 weeks Mu tafi, Inaso zamuje Shopping mall atare, Akwai kayayyakin da nake so Na Siyawa ƙanne na, kasan su mayun kallon korean drama ne, suna san suturarsu ba ƙaramin burgesu yake yi ba, inaso na siya masu, hada Jikana zan siyawa kayan wasan yara, da kayansu na al’ada suna burgeni, ita Fatima ma hada cewa in yi masu tsarabar abincinsu, In banda shiririyata, zan dai siya masu chocolates ɗinsu kalar wanda bamu dasu a gida, ” magana take yi mashi amma hankalin shi gaba ɗaya baya akanta, har saida Tace”Kai fa? Me zaka yi tsaraba da shi
Murmushin yaƙe ya yi mata, muryarshi a karye yace”Wa nake da shi da zanyi ma tsaraba? Dama ƴa’ƴana ne, yanzu kuma babu su, amma duk da haka zan siyawa Angel kalar suturarsu, a ƙiyashin da nayi yanzu takai 15years a duniya, Zan yi mata siyayya sosai in ajiye mata, hada bags and shoes da teddys, komai ma zan siya mata, duk ranar da Allah ya bayyanar dasu, sai in damƙa mata abunta,’ yakai ƙarshen maganar, tare da duƙar da kanshi ƙasa, Shi kanshi baisan yayi waɗannan Zantuttukan ba, Saboda su ne aranshi shiyasa yayi maganar, Shessheƙar Kukan Hajiya adama yajiyo acikin kunnanshi, Kafin ya ɗago da kanshi tuni ta miƙe da sauri ta wuce zuwa bedroom ɗinsu, Binta yayi da kallo har saida ta 6ace ma ganinshi,

Girgiza kai kawai yayi, kafin ya miƙe ya nufi ɗakin, Don ya samu yayi wanka Ya canza kayan jikinshi,

*Back To Prison🥺*

Mutsu mutsun farkawa daga bacci ta ke yi, eye lashes ɗinta sun manne ma juna, daƙyar ta samu ta ware idanuwanta basu sauka akan kowa ba, sai akan fine face ɗin Danish dake ta sharar bacci, kasalalliyar ajiyar zuciya ta sauke a yayin da take kallon shi cikin natsuwa, kamar wani baby ya naɗe Jikinshi cikin bargo, fuskarshi kaɗai ce awaje, tun daga kan yadda yake fitar da numfashin shi, zaka shaida yana acikin kwanciyar hankali, baƙaramin daɗi taji ba, tana fatan Allah ya yaye mashi lalurar dake damunshi,

Almost 15 mins tana kallon shimfiɗarshi, kafin ta yunƙura ta miƙe zaune ta jingina bayanta a jikin bango, gadajensu batool tabi da kallo, Tayi mamakin ganin basu farka ba, Kamar wasu matattu sai sharar bacci suke yi, kowa ya kudundune jikinshi cikin bargo, sunyi matuƙar burgeta sai ta dinga jin inama ace Acikin Gidan Mahaifinta suke ba’a Cikin Gidan Kurkukun ba, da sun more rayuwarsu, tasan cewa Danginta zasu kar6esu hannu bibbiyu, musamman aunty aneelerh, da hajiya adama suna son yara sosai, taci alwashin idan Allah ya bata Ikon musuluntar dasu, Zata nema masu hanyar da zasu gudu daga Cikin Gidan kurkukun ƙaddara, Sai dai babban abunda take yi ma fargaba shine, Taya za’ae Su fita daga Cikin kurkukun da ransu da lafiyarsu? Idan Allah yasa sun samu ƙopar fita kenan, Bayan wannan abunda take matuƙar jimawa Anya kuwa GIDAN KURKUKUN ƘADDARA A cikin ƙasar Nigeria yake!? idan har ba’a Nigeria yake to kuwa dai suna acikin tsaka mai wuya! Fatanta Allah yasa ba awani ƙurmin dajin ginin yake ba, Don kuwa akan hanyar guduwa ma wata dabbatar na iya kai masu hari ta Cinye Naman Jikinsu…….”

Tana Cikin yin wannan Zancen Zucin nata, Karaf idanuwanta suka sauka akan danish dake ƙoƙarin faɗowa daga saman gadonshi, Cikin magagin bacci, A hanzarce ta duro daga saman gadonta tayi gaggawar tarbe shi, ƙiris Ya rage ya tiƙo ƙasa, ba don Allah yasa tayi saurin zuwa ba, da kanshi yayi mugun buguwa,

Nannaɗeshi tayi tare da turashi saman gadon, Ya koma yadda yake, Ajiyar zuciya ta sauke yayin da take kallonshi, Soft red lips ɗinsa ta gani suna motsi, alamar yana sambatu, miƙewa tayi ta hau saman gadon, ta duƙar da kanta saitin la66ansa, ta natsu tana sauraron me yake cewa,

_the sounds is soothing me, I can’t stop listening to ur voice, pls keep reading it in my ears, am really enjoying it_

Murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, jin sambatun da danish yake yi, duk akan Karatun kur’anin da tayi mashi jiya ne, ta fahimci cewa ba ƙaramin daɗi yaji ba, shiyasa ma har yake sambatu acikin Baccinsa,

Whispering tayi mashi acikin ear ɗin nashi tace”Kana so In koya maka”? sam batayi tunanin zai amsa bata, sai ji tayi yace”yeah,” da sauri ta kalle fuskarshi, Abun mamaki Bacci yake yi bai farka ba, amma yana magana, ƙumshe dariya tayi kafin ta ƙara cewa”Dame zaka biya ni idan na koya maka”? Tayi tambayar Tana sauraron amsar da zai bata,

Cikin muryar bacci yace”I ave nothing to pay you, but I can promise you myself if you want” Cikin nishaɗi angel take dariya, A maganar da yayi mata idan har zata fassarata a matsayinta na wadda tayi rayuwa awajen kurkuku, Tamkar kalaman soyayya ne, Amma shi awurin shi bakomai bane, ya faɗi mata hakan ne saboda baida abunda zai iya biyanta da shi, idan ba kan nashi ba,

“does that mean you will be my slave? If I give you an order, will you follow?”
Amsa mata yayi”yeah” koda wankin Uniform ɗina ne? Tayi tambayar tana kallon fuskarshi, idanuwanshi na arufe gam, wannan karan bai bata amsar tambayarta ba, da alama ya kuma yin nisa Cikin baccin sa,

Ruƙo bargon shi ta yi tare da ƙara janshi ta rufe mashi har zuwa saman fuskarshi, Tana ƙoƙarin saukowa daga saman gadon danish, Ta ji yo motsin buɗe ƙopa, da alama giants ne suka ƙaraso, Yau Abinci ya riga masu Cin shi, ƙarasowa,

Ƙarasa saukowa tayi daga kan gadon nashi, ta tsaya a tsaye tana Jiran su ƙarasa shigowa Ciki, Takun tafiyarsu ta soma jiyowa, kafin su bayyana su ukun nan hannayensu a ruƙe da wooden trays, mai ɗauke da kayan Kalacinsu,

Akan idonta suka wuce zuwa saman dining carpet ɗinsu, Kowa ya sauke Farantin dake a hannunshi, Ja da baya su kayi atare suka ƙame kamar yadda suka saba, tunani ta shiga yi Kowanene acikinsu Ya damƙeta aranar nan har yayi wurgi da ita, bazata ta6a manta azabar da tasha ba, Ta tsani giants a rayuwarta, ko son ganinsu bata yi, Saboda basu da Imani, Ga ƙarfi kamar na dawakai, ta jima tana kokwanto akansu Anya kuwa Cikakkun mutanene? Kodai half jins ne?

Ta yi zurfi Acikin tunaninta, taji motsinsu, Ras taji gabanta ya faɗi ganin suna tattara kayan abincin da suka ajiye masu, aruɗe tace” ina zaku tafi da abincin mu? Bayan bamu Ci ba” babu alamun suna sauraronta,

“Magana fa nake Yi maku, idan saboda suna yin bacci ne yanzu zan tashe su, pls kada ku tafi” ko waiwaye wannan basuyi mata ba, Tana ji tana gani suka haura saman bene da abincin suka fuce daga Cikin ɗakin, Tana Jiyo sautin garkame ƙopa da su kayi,

“Ya salam” ta ambaci hakan tare da dafe kanta, muryar batool ce ta katse ta da cewa”Angel lafiya naji kina sambatu ke kaɗai”? Da sauri angel ta juya baya tana kallon batool dake kwance saman gadonta, farkawarta kenan daga bacci,

“Giants ne, Sun kawo abinci kuma sun tafi dashi bansan meyasa ba”?

Waro ido waje batool tayi fuskarta da alamun tashin hankali tace”mun shiga uku! Shikenan yau mun rasa abincin da zamu ci, angel meyasa baki tada mu daga bacci ba lokacin da suka zo”? Fuskarta a hargitse tayi maganar,

“Ina fa kokarin in tada ku daga bacci, sai naga suna tattara kayan abincin, kuma har roƙonsu nayi su tsaya amma basu saurare ni ba…..” tunkan takai ƙarshen maganarta, suka soma Jin shessheƙar kukan Parveen, gaba ɗaya suka kai idanuwansu akanta, zaune take saman gadonta, ta wage baki tana ta kuka, Jin cewa Giants sun zo sun tafi da abincinsu,

Sautin Kukan Parveen ne ya farkar da sauran Ƴan uwan nasu, Hanna tana hamma tace”wai meke faruwa ne? Me akayi ma Parveen take kuka”

Javed yace”Yanzu haka rigimartace kawai, duk tabi ta tashi mutane daga bacci, saboda tsabar jarabarta,

Hannu danish ya sanya tare da zame bargon da ke lullu6e a jikin shi, idanuwanshi sun ƙanƙance daƙyar yake iya ware su, saboda baccin bai ishe shi ba,

Haris dake faman yin miƙa yace”kun yi shiru baku bamu amsa ba, Meyasa take kuka”?

Batool ce ta bashi amsa da cewa”Saboda giants sun kawo abinci, Angel bata samu damar tada mu daga bacci ba, har suka tafi da kayan abincin shine take ma kuka”

saboda tsabar tashin hankali Har suna haɗa baki wurin cewa”What? giants sunxo sun tafi da abincin mu”? Amatuƙar ruɗe kowannasu yake faman baza ido,

Dafe kai javed yayi”ae shikenan mun rasa abinci yau, Mu da ganinsu kuma sai gobe, kafin lokacin mun gama jigata,”

Yana rufe baki Rubina tace”Wlh bazan iya jurewa ba, da matsiyaciyar yunwa na farka yau….” mubeen yace”ae ba ke kaɗai ba, Cikina har wani kukan yunwa yake yi” yayi maganar yana shafa stomach ɗinshi,

“Yanzu ya zamu yi kenan”? Naufal ne yayi tambayar yana kallonsu,

Azeeza tace”Mu ci hakuri kawai, Idan munji ƙishi musha ruwa sai mu kwanta muyita bacci har gobe tayi, Harara Hibba ta jefa mata daga inda take zaune saman gadonta”Wannan fa ba abun wasa bane azeeza, magana ake ta babu abincin da zamuci yau, ” azeeza tace”idan bamuyi haƙuri ba, to ya zamuyi” tayi maganar tana watsa hannayenta,

Da buɗar bakin deeja sai cewa tayi”bakowa bane ya jamana xama da yunwa ba face angel, meyasa da suka zo baki tashe mu daga bacci ba? Saboda tsabar mugunta,’

Shiru angel tayi don bazata biye mata su yi cece kuce ba, tun da ita halinta ne bata gajiya da shiga sabgar mutane,

“Kodai naje na faɗa ma tsohuwa, ta taimaka tayi magana, su giants su dawo mana da abincin mu,” fuska amarairaice parveen tayi maganar, tagama shan kukan nata, taga babu mai lallashinta ta haƙura don kanta,

“Koda kinje babu abunda tsohuwa zata iya yi mana, kema kinsani” yasmin ce tayi maganar, fuskarta a hade, shi dai danish yayi lamo saman gadonshi yana bin bakunansu da kallo, sam baison hayaniyar da suke yi, don ba yadda ya iya ne daya dakatarsu,

Bakowa Angel tafi jima tausayi ba, Sai danish sanin cewa Jiya baici abincin shi ba, ya basu suka cinye, yanzu ga shi sun rasa abincin yau, dole yafi kowa jin yunwa bawan Allah,

Yau fa ba kanta, Duk jikinsu yayi laushi, Ko toilet babu wanda ya shiga don yin wanka ko wanke fuska, damuwarsu Yunwar da zasu kwasa yau, an sanyasu yin azumin dole batare da sunyi niya ba,

Saukowa haris yayi daga saman gadonshi, Ya wuce gadon danish, daga ƙasa ya zuƙunna tare da ruƙo hannun danish acikin nashi, idonsu cikin na juna, yace”ɗan uwana, ya jikin naka”? Cikin sanyin murya ya amsa mashi da cewa”da sauƙi sosai,” murmushin haris yayi”Am glad to hear that, Nayi kewarka sosai na tsawon kwana biyar din nan, saina ji kamar na rasa wani sashe na jikina ne” wannan maganar ta haris ba ƙaramin faranta mashi rai tayi ba, shi kanshi ya shaida irin ƙaunar da haris ke yi mashi aduk duniya bai da tamkar shi,

“Haris, nima nayi missing ɗinku sosai, har bazan iya misaltawa ba………” dakatawa ya ɗanyi da yin maganar, ya juya bayan shi yana kallonsu batool,

“Can i talk to u”? Danish ne yayi tambayar yana kallon kowannnsu, Jin haka yasa suka sauko daga saman beds ɗinsu, suka Nufi gadon danish, a kewaye da gadon suka tsaya curko cirko suna yi mashi Yaji ki, ƙasa ƙasa da murya yake amsa masu, yayin da idanuwanshi ke akan fuskar angel dake a tsaye can nesa da su, Batool ce ta lura da kallon angel da yake yi, ta fahimci yana son itama tazo ne, amma tasan bazai iya kiranta ba, hakan yasa ita ta kira ta da kanta tace”Ki zo mana, danish yana son yin magana damu” tafiya ta soma yi xuwa bakin gadonshi ta tsaya a gefensu tare da goya hannayenta saman kirjinta,

Calmly yaci gaba da cewa”dama inaso nayi maku godiya ne, bisa irin nuna kulawarku agare ni, kun damu dani sosai, nasan kunyi missing ɗina na tsawon 5 days da bana acikin ku, nima kuma duk da bana atare daku kuna araina, i luv u so much guys……” tun da ya soma magana suka natsu suna sauraronshi, Yaushe rabon da suji danish yayi magana mai tsayi irin wannan har sun manta, lallai jiki yayi sauƙi suka ayyana hakan acikin ransu,

still bai janye idanuwanshi daga kan fuskar angel ba, itama shi ɗin take kallo, So yake yayi mata godiya amma ya kasa, ita kanta angel ɗin ta lura da hakan amma saita basar, Jira take taga idan zaiyi mata magana,

Muryar javed ce ta janyo hankalinta wurin kallonshi” Angel Amadadin danish, muna matuƙar yi maki godiya, bamu ta6a tsammanin zaki iya taimakon shi ba, a lokacin da kika nemi alfarmar mu baki dama, Sai gashi kin bamu mamaki, Ta silarki danish ya fara wartsakewa, tabbas ke ɗin alkhairi ce agare mu, Kuma yakamata Gaba ɗayanmu mu fahimci cewa angel masoyiyarmu ce ba maƙiyiyar mu ba” ya ɗan dakata da yin maganar yana kallon fuskokin sauran ƴan uwan nashi, kafin yaci gaba da cewa”Idan har muka yi ma angel biyayya zamu koyi abubuwa da dama awurinta wanda bamu Iya ba, zata wayar mana da kanmu, kuma zata ɗaura mu akan hanyar dai dai, Amma fa shawara ce nake bamu muyi tunani,” yakai ƙarshen maganar yana jira yaji amsar da zasu ba shi,

Deeja ce tace”Amma ae tsohuwa tace mana kada mu yarda da ita, mu daina sakewa da ita, zata gur6ata mana tarbiyarmu ne, kuma tana yi mana ƙarya nidai gaskiya bazan yarda da angel ba, ” tayi maganar tana maƙe kafaɗarta, maimakon angel taji haushin maganar deeja, Saima ta saki murmushi saboda ta lura hada quruciya ke ɗawainiya da ita,

“maganar da Javed ya faɗa gaskiya ne, Angel masoyiyarmu ce, kuma komai take yi mana tana ƙoƙarine don taga mun dawo akan hanyar dai dai, Ina roƙon duk wani dake ƙyararta acikinmu ya ajiye makaman yaƙin shi, yazo mu rungumi juna, faɗa ba namu bane,” a tsanake batool takai karshen maganarta,

“Silar angel, danish ya samu sauƙi, bashi kaɗai ba, Tun jiya da angel ta raira mana waƙar nan mai daɗi da sanyaya zuciya, gaba ɗaya jikin kowannanmu yayi sanyi,……” dariya angel tayi jin abunda azeeza tace,

“Ba waƙa bace, Karatun al’qur’ni ne mai girma, ” cike da mamaki suka maimaita kalmar”Karatun al’qur’ani mai girma” Hanna tace”menene ma’anar hakan? Ko zaki iya fahimtar damu”? Tayi maganar a ƙagare da son Jin amsar da angel zata basu,

Ƙoƙarin buɗe baki tayi da niyar ta ba Hanna amsar tambayarta, Sai dai kafin tayi yunƙurin yin hakan, Suka Jiyo Motsin buɗe ƙopar ɗakin tsohuwa, Nan fa hankalinsu gaba ɗaya ya koma akan ƙopar ɗakin,

Fitowa tayi daga Cikin ɗakin tana dogara sanda, Fuskarnan a tur6une babu walwala acikinta, da sauri Su hanna suka Nufe ta, Cikin girmamawa suka gaishe da ita, babu yabo babu fallasa ta amsa masu,

Parveen tace”tsohuwa Yunwa muke ji, Giants sun kawo mana abinci, A lokacin bamu farka daga bacci ba, har suka tafi da shi”

Jinjina kai tsohuwa ta ɗanyi tana bin fuskokinsu da kallo, Su kansu sun lura da canjin dake atattare da ita, kamar wani abu na damunta, Hanna tace”tsohuwa Baki da lafiya ne? Naga kamar bakya Acikin walwala,” sai lokacin tsohuwa ta buɗe baki tace” kunyi kuskure da ku ka bari giants suka juya da abincin nan, ai kunsan basa wasa da lokaci, meyasa baku farka daga bacci ba har suka tafi? Bayan kunsan cewa Ba dawowa zasuyi ba, idan har suka tafi dashi”!

Muryar Parveen tamkar zata fashe da kuka tace”yanzu shikenan bazamu samu abinci ba yau”? Idanuwanta suka cicciko da ƙwalla,

angel dake acan tsaye ruƙe da qugu, ta tunkari inda suke, agaban tsohuwa ta tsaya tare dacewa”Irin ƙaunar da kike masu kenan? ashe uwa zata Iya barin ƴa’ƴanta da yunwa? Alhalin ita tacika cikinta ta ƙoshi! Waye bai kuskure rayuwa? Yin bacci ya zama laifi kenan? Inbanda rashin lissafi taya mutumin dake bacci zai zama mai laifi? Meyasa su giants ɗin da suka zo basu ajiye mana farantan abincin ba, su sai su tafi idan yaso aduk lokacin da muka farka sai mu ci, Amma saboda tsabar zalunci shine suka tattara kayan abincin suka tafi dashi, Anya kuwa tsohuwa? Cike da tuhuma takai ƙarshen maganar tana kallon fuskar tsohuwa, ta tsareta da waɗannan Jagwalallun idanuwan nata,

Daƙyar ta iya buɗe baki tace”Haka dokar Aikin Giants suke! Lokaci gare su, basa wasa da aikinsu, idan suka kawo abinci suka ga babu wanda yazo yaci zasu kwashe ne su tafi dashi,” wannan itace amsar da tsohuwa taba angel,

Mamaki akan fuskar angel tace”Wannan wata irin dokace mara kan gado mara tsari? Wannan ae horo da yunwa ne! Abincin ma da sau ɗaya ake bamu shi a rana, mun ƙoshi bamu koshi ba wannan ba damuwarku bace, Shine kuma harda wata dokar in an kawo abinci bamu hallara ba, za’a juya dashi? Me hakan ke nufi? Wai mu me kuka ɗauke mu dabbobi ko me? A harzuƙe angel tayi maganar,

Wata irin gigitacciyar tsawa Batool ta daka ma angel, gaba ɗaya saida kowa ya razana hatta danish dake a kishingiɗe saman gadonshi saida ya firgita ya nemi zaucewa,

A matuƙar ruɗe Angel ke kallon batool, ta ɗaure fuska tamkar ba ita ba, Cikin fushi ta soma magana
“Yakamata ki kiyaye harshenki aduk lokacin da zakiyi magana da tsohuwa, don me zaki dinga yi mata magana a gadarance? Babu tausasa harshe? Idan ma kina son shiga tsakaninmu da ita ne, Inaso ki sani bazaki ta6a yin nasara ba, ita ɗin uwace agare mu kuma bazata ta6a iya cutar damu ba……” ba angel ba, hatta su haris sai da suka sha Jinin jikinsu, Jin yadda Batool ke magana a faɗace abunda bata ta6a yi ba,

Muryar angel adisashe tace”Batool! Yau keda kanki kike Yi mini tsawa! Saboda kawai ina son ƙwato maku haƙƙinku da aka tauye…..” kafin takai ƙarshen maganarta, Javed ya dakatar da angel ta hanyar ɗaga mata hannunshi”Is enough! Kawai kiyi mana shiru, Kina so ne, Ki shiga tsakaninmu da ita, babu ruwanki da rayuwarmu, Ki barmu a yadda kika ganmu, haka muka saba rayuwa, bin dokar kurkuku wajibi ne agare mu prisoners” wani irin shu’umin murmushi tsohuwa ta shiga saki Nan da nan walwalar fuskarta ta dawo Jin yadda Suke Goyan bayanta, ashe har yanzu Hayaƙin sihirinta na aiki yadda ya dace, ta ambaci hakan acikin zuciyarta,

Tuni idanuwan angel sun Ciko tab da kwalla, tsabar baƙin Ciki Ya hana ta ƙara cewa komai, Juyawa tayi a fusace ta koma saman gadonta, Ta zauna tare da ruƙo pillow ta rungume a kirjinta,

Kallonsu tsohuwa tayi da alamun farin Ciki akan fuskarta tace”Ku cigaba da yi mun biyayya ƴa’ƴana, albarka zata tabbata akanku, ” muryar parveen a ƙule tace”Abincin fa”?

Tsohuwa ta bata amsa da cewa”Ku jira ni, Ina zuwa” ta ambaci hakan tare da juyawa ta shige Cikin ɗakinta, baka iya hangen komai ko ka leƙa sai duhu,

Badajimawa, Sai ga tsohuwa ta fito hannunta ɗaya a ruƙe da Kwandon kayan marmari, Miƙa ma Su tayi” Ku je kusha, Kafin zuwa gobe zaku samu abinci” Hannunsu har kerma yake yi wurin kar6ar Kwandon daga hannunta,’ Juyawa tayi tana dogara sanda ta koma Cikin ɗakinta, tare da jan kopa ta datse,

Ita dai angel sam bata yarda da kayan marmarin da tsohuwa ta basu ba, Cike fa da kwando, manyan apples ne tare da damin ayaba,” a kalla kowa zai samu apples uku, da Ayaba Uku, Batool ce ta rarraba masu kayan marmarin kowa ya kar6a yana sha, koda ta miƙa ma angel hannu tasa takar6a amma bata sha ba, A ƙarƙashin pillow ɗinta ta 6oye su, tana jira taga idan sun kammala sha batare da wani abu ya faru dasu ba, itama sai tasha, Har batool sai da tayi mata magana akan bazata sha ba, tace mata ba yanzu zata sha ba, Sai zuwa anjima,

Tun da suka kammala Cin apples ɗinnan da ayaba, wani irin matsiyacin bacci ne yazo masu, lamarin ya ɗaurewa angel kai, Ganin su kwakkwance A ƙasa suna bacci, kamar waɗanda suka Sha kayan maye, Juyawa tayi da sauri tana kallon gadon danish, cike da fargabar kada ace shima baccin ya ɗauke shi, idonshi biyu ta same shi, ya kwantar da kanshi saman pillow, babu alamun bacci attare dashi, Su biyu suka rage idonsu biyu,

Tabbas tafara zargin Kayan marmarin da tsohuwa ta basu ne ya sanya su yin bacci, da yake ita da danish basu sha ba, shiyasa bacci bai ɗauke su ba, ko meyasa tayi masu haka? Kodan kada su ji yunwa ne”?

“Meyasa ba zaka sha ba”? Tayi tambayar tana kallon danish, ganin ya ajiye nashi apples ɗin a gefenshi,

Cikin sanyin murya ya amsa mata da cewa”bana ra’ayi, zuwa anjima xansha” ya ƙarasa maganar, tare da miƙewa zaune, ya zuro da dogayen ƙafafuwanshi ƙasan gadon kafin ya yunƙura ya miƙe tsaye, Har yanzu jikin nashi babu ƙwari, shiyasa tun ɗazu ya gaza saukowa daga saman gadon,

Daƙyar yake ɗaga ƙafar yana tafiya, Ji take kamar taje ta taimaka mashi sai dai batasan tana kusanta kanta dashi,

Tafiya yake yi yana waiwayon su Haris dake baje a ƙasa suna sharar bacci, sam bai kawo komai aranshi ba, Shigewa Ƙopar toilet ɗinsu yayi, Sai da ya 6ace ma ganinta tukunna ta ɗauke idonta daga kanshi, Cike da fargabar kada ya raunata kanshi, tun da ba ƙoshin lafiya gare shi ba,

Tsawon lokaci da shigarshi cikin toilet ɗin, ta Lumshe idanuwanta tare da kishingiɗawa, da niyar ta ɗan runtsa itama, Takun tafiyar mutun tajiyo acikin kunnata, tana buɗe ido ta fasa wata irin gigitaciyar ƙara tare da sanya hannu ta rufe idanuwanta, Jikinta na kerma, A matuƙar ruɗe Ya koma Cikin 6angaren toilet ɗin nasu, Ya la6e abakin ƙopa yana leƙen ta,

Abunda ya faru Lokacin data buɗe ido, Karaf idanuwanta suka sauka akan Surar danish, Ya fito naked babu sutura ajikinshi, Wannan ne yasa tayi matuƙar firgita, Jikinta ya hau kerma, dole ta ruɗe saboda halittar dake gare shi, Dogone sosai komai Na jikinshi ba ƙarami bane, shi kuma tsawar da tayi ne yasa shi gigicewa ya juya aruɗe ya koma sashen toilet ɗin, Yana leƙenta,

Ƙanƙame jikinta tayi ta gaza motsawa, tayi matuƙar tsorata, ranta ya 6aci sosai batare data buɗe idanuwanta ba, taci gaba da surfa mashi masifa ta inda take shiga bata nan take fita ba, sai da ta gaji da zazzaga mashi masifa tukunna ta yi shiru tana faman huci har lokacin bata buɗe idanuwanta ba,

Jin yayi shiru bai ce mata komai ba, yasa ta sassauta muryarta tare da cewa”Go back, I don’t wanna see you naked, if you need something, you should ask me to give it to you”

a ƙule tayi maganar, don ba ƙaramin haushin sa taji ba, ƙato da shi zai fito babu kaya ajikinshi, yanzu da ace idonsu Batool biyu ba bacci suke yi ba, duk haka zasu ganshi, tarasa gane wani irin mutunne shi, duk da tana yi mashi uziri na halin da yake Ciki na rashin lafiyar da take tunanin ɗaura mashi ita akayi, shiyasa ya zama wani sauna dashi,

Kasa kunne tayi sosai don ta samu damar jin me yake ce mata, magana yake yi mata akan ta miƙo mashi bargonshi, yana so zai lullu6e jikinshi,

Sai lokacin ta fahimci cewa, Ya wanke kayanshi, dama haka suke Yi idan suka wanke kayansu, sai su sanya bargo su lullu6e jikinsu, maimakon tunkafin ya shiga cikin toilet ɗin ya tafi da bargon shine bai tsaya ya ɗauka ba, yanzu gashi yasata kallon haramun, ta ambaci hakan acikin zuciyarta,

“wait, I will hand it to you ka koma toilet” amsa mata yayi da toh, bayan wasu daƙiƙai, ta ɗan zame tafin hannunta daga kan fuskarta, ta saci kallon Hanyar toilet ɗin, Ganin babu shi yasa ta yi saurin saukowa daga saman gadonta, takai hannu saman nashi gadon ta ɗauko bargonshi, Ta nufi bakin door ɗin farko ta tsaya tare da ɗaga murya tace”Ga bargon” zuro mata da hannun shi yayi, maimakon ta miƙa mashi bargon saita tsaya tana kallon kyawawan yatsun hannunshi, sai kace bana ɗan bil’adama ba, saboda tsabar kyau, matsalarsu ɗaya basu yanke akaifa, yadda kasan hannun shaiɗanu, Ƙumba zaƙo zaƙo,

“Bring me am waiting” figigit tayi jin muryarshi, harya gaji da miƙa hannu, da sauri ta damƙa mashi bargon, ya kar6a,

Abakin ƙofar ta tsaya tana jiran ya kammala sanya bargon ya fito itama ta samu ta shiga wankan,

Tana Cikin tsawuwar nan, Taji takun tafiyarshi, bin ƙopar tayi da kallo, Fitowa yayi, Jikinshi ɗaure da bargon daya sanya, har zuwa chest ɗinshi,

Bata bari sun haɗa ido ba, Ya wuce ya nufi gefen gadonshi Ya zauna, tare da jingina bayanshi a jikin bango,

Tunani tayi kodai itama ta wanke kayanta ne ? Domin kuwa tajima bata wanke su ba, har tsami suke Yi mata,

Komawa tayi ta dauko bargonta dake yashe saman gadonta, da sauri ta nufi toilet ta shige, tsawon lokaci tana aciki, sai da ta kammala wanke kayan ta ta shanyasu, bayan tayi wanka ta ɗaura bargon a ƙirjinta, A bakin ƙofar fitowa daga sashen makewayin nasu ta la6e tana satar kallon danish, Sam bata so ya ganta in zata wuce,

Ganin ya lumshe idanuwanshi ne, yasa ta yi tunanin yin sauri ta wuce, Cikin sanɗa take tafiya, har ta samu takai bakin gadonta ta haye ta kwanta, yinin ranar su biyu suka yi shi, ita da danish, lokacin da kayansu suka bushe ita taje ta dauko masu uniform ɗinsu, ganin ya fara bacci yasa tayi saurin warware bargon dake ajikinta, ta xura uniform ɗinta, sai daga bisani taje bakin gadon danish ta tada shi daga bacci, ta miƙa mashi nashi unifom ɗin yasa hannu ya kar6a,

Ta juya ta koma gadonta, ta zauna daga gefe, idonta akansu batool dake ta sharar bacci, koda taga yana kokarin zame bargonsa don ya zura kayanshi da sauri ta kifa kanta saman pillow, ba ita ta ɗago ba har saida ya kammala sanya kayan ajikin shi, tukunna ta ɗago da kanta,

Abu kamar wasa har dare yayi su batool basu farka daga bacci ba, Hankalin angel yaƙi kwanciya shi kanshi danish jikin shi duk yayi sanyi, har sauko yayi daga saman gadonshi yaje ya duƙa agabansu yana tatta6a su, wannan wani irin dogon bacci ne da mutun zai kwashe yini guda tun safe har dare? Anya kuwa tsohuwa abunda tayi ta kyauta masu? Sai kace wasu matattu,

*Domin neman ƙarin bayani 08103884440 ko 08169856268 Text on whatsapp only banda phone calls, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, Ga wanda ya shirya yin payment, zai iya yi mini magana, a ƙarshen wannan watan free pages zasu ƙare na Takun farko, zamu nutsa Cikin labari, tun acikin week din nan kowa ya ɗaura ɗamara🤣🤣*

share fisabilillah👌

No comments