Breaking News

Kurkukun Kaddara 30-31

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*


_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E30-31

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

“Angel Still ba’a dawo dasu ba, Abincin da muka rage musu tun jiya ya riga da ya lalace, da mun sani mun cinye shi,” Hanna ce ta bata amsa, Azeeza tace”Yanzu shikenan baza adawo mana da su Parveenar mu ba? sun tafi kenan”? Muryarta a sanyaye tayi maganar, Hibba tace”Pls Azeeza stop sayin that bana jin daɗi, kuna karya mana zuciya, Tsohuwa fa tace za’a dawo dasu da zarar Sun samu lafiya,” Eve ce ta kalli Hibba da tayi maganar tace”Hib kin manta lokacin baya? Ƴan uwanmu da muke atare dasu? Wasu in an ɗauke su ba’a dawowa dasu sun tafi kenan”? Idon angel akansu tana sauraronsu, kwata kwata bata acikin natsuwarta, tana matuƙar jin tsoron ta yi mummunan mafarki, saboda Xaiyi wuya mafarkinta yaƙi xama gaskiya, kafin zuwanta gidan kurkukun ƙaddara saida tafara mafarkin kasancewa acikin shi kuma sai ga shi ta tabbata, ta tsinci kanta acikin shi,

“Yakamata mu daina wannan maganar, Muna ƙara tayar wa junan mu hankali, Idan muka kwantar da hankalin mu, za’a dawo dasu ne,” acewar Javed, yasmin tace”Yanzu me zamuyi toh? Ni nagaji da zama zugudum, ” fuskarta a yamutse Tayi maganar,

Azeeza tace”Muna da abunyi mana, Angel zata Wanke mana gashin kanmu, ta kuma gyara mana shi, ” tunkan takai karshen maganar, yasmin ta harare ta”Kefa matsalarki kenan, Sai ana magana ta hankali ki wani soko wa mutane Shiririta aciki,” zum6ura baki Azeeza Ta yi tare da murguɗawa mata shi tace”To me kike so Muyi? Wanka ko motsa Jiki? Ko kuma bacci? Ko giants xamu Jira su kawo mana abinci”?
Banza yasmin tayi da ita, Zama batool tayi a gefen gadon angel, ta ruƙo hannun angel acikin nata tace”Sister, na lura sam bakya acikin hayyacin ki, Ki faɗa mini, me kika gani acikin baccin ki wanda ya tsoratar dake”? Idanuwan angel cike tab da ƙwalla ta ɗago ta kalli fuskar batool, bazata Iya faɗa mata ainihin abunda ta gani acikin mafarkin ta ba, Saboda Bata son ta tayar mata da hankali, Kuma faɗin baida amfani, sannan ma babu kyau mutun yayi mummunan mafarki ya faɗi ma wasu,

Don haka tace mata”bakomai batool Just bana Jin daɗin Jikina ne,”

“Ko zakiyi wanka ne? May be kiji daɗin Jikin ki,” cikin sanyin murya tace”eh, xanyi, ” tana rufe baki Azeeza tace”Angel me zamuyi yau”? Murmushi angel ta ƙaƙalo, yayin da take kallonta tace”Little Kome kike so Shi za’ayi, ” ashagwa6e Azeeza ta bubbuga ƙafar tare da cewa”Ni kidaina ce mun little bana so,” gaba ɗaya su kayi dariya, Hanna tace”Ae gaskiya ta faɗi, kallarki fa? Wata ƴar ƙarama dake, Ko kafaɗarmu baki kai ba, banta6a ganin wadda bata cigaba ba acikinmu irin ki, Duk yawan abincin da kike Ci sam baki ƙara auki, ba ƙiba ba tsawo,” dariya suka saki gaba ɗayansu, Rai a6ace Azeeza Ta zuƙunna kasa tana yin kukan ƙarya, Angel tace”pls kudaina janta, Nima na faɗi ne kawai don ayi nishaɗi, amma azeeza ae itace babbarmu,” ta yi maganar tana ƙyaftawa musu ido, atare suka haɗa baki wurin cewa”hakane Azeeza itace babbarmu, muma wasa muke Yi mata, don kawai ayi raha ne” Sunsan azeeza da son girma, jin wannan maganar tasu yasa ta miƙe tana gumtse dariya abaki,

Angel tace mata”Me kike so Muyi yanzu?
“Ki wanke mana gashin kanmu, Kuma ki gyara mana, keda batool kamar yadda ku kayi mana ran nan kin tuna’? Zaro ido angel tayi”Azeeza Baki ga yadda na farka ba yau, sam babu natsuwa atare dani, Taya zamu Iya wanke maku wannan uban gashin kan naku, Kuma mu gyara shi,? Ta6e baki azeeza ta yi, Itafa in taso abu to ayi mata kawai, idan ba haka ba yini zatayi tana faman tur6une musu fuska duk da tana da yawan fara’a kamar Gonar auduga,
“Kada Ki damu sister azeeza, Koda angel bata samu damar tayani ba, Ni xan gyara maku gashin kanku, Mu barta ta huta, tun da bata Jin daɗi, Kuxo muje toilet,” Batool ce ta yi maganar, Ta juya ta nufi toilet suka bi bayanta,

Bayan tafiyarsu Cikin toilet, Angel ta sauke ajiyar zuciya, tare da jingina bayanta Jikin bango, Gefe ta juyar da kanta tana kallon Gadon danish, kamar dai kullum yana a kudundune Cikin bargo, Haris da mubeen da Javed hada naufal duk basu farka daga Bacci ba, sakamon daren da su kayi jiya batare da sun runtsa ba, Suna Xaman Jiran adawo musu ƴan uwansu,

Saƙe saƙe ta shiga Yi acikin zuciyarta, game da wasu tambayoyi da suka cunkushe mata kwakwalwarta, sun hanata sakat, idan ta takura kanta akan tunaninsu Har wani matsanancin ciwon kai take ji, tabbas tana son Yin magana da tsohuwa duk da tasan zaiyi wuya tsohuwa ta amsa mata tambayoyinta, amma zata jaraba tunkararta, Yau ɗin nan,

A6angaren su Batool, sai da tabi kowannan su ɗaya bayan ɗaya ta wanke musu sumar kawunansu, Baƙaramar wahala tasha ba, domin kuwa Dukansu tsayin gashinsu Ya zarce midback ɗinsu, Ga uban yawa dake gare shi, bayan ta kammala wanke musu gashin, Sai da kowannan su Yayi wanka, Kafin suka dawo Cikin ɗakin, Kamar yarda suka bar angel zaune saman gadonta haka suka sameta, ganin sun fito daga wankan Yasa itama ta miƙe domin zuwa yin wankan, Shigarta da ƴan mintuna ta fito, A lokacin Danish dasu Mubeen duk sun farka daga bacci, saukowa su ka yi daga saman gadajen su, Atare suka Nufi Toilet domin suma suyi wankan ko sunji daɗin Jikin su.

A zaune ta samu batool gefen gado ta ruƙe Comb, Zata Gyara musu gashin kansu, hakanan taji tana sha’awar Tayi musu Kitson kalaba Guda Biyu akansu don ta Iyata, Kallon batool tayi tare da cewa”Ki bari In yi musu kitson Kalaba, Nasan ba’ata6a Yi maku ba, Yau zan jaraba mu gani idan zan iya” Cike da Jin daɗi Batool ta mika mata Comb ɗin, Tasa hannu ta kar6a, tare da samun wuri gefen gadon batul ta xauna, Ta ɗago ta kalli su Azeeza dake ta murna za’a gyara musu gashi tace Su zazzauna a ƙasa, zata fara gyarawa azeeza nata idan ta kammala mata zata Kira ta gaba da zata yi mawa,

A ƙasan gadon azeeza ta zauna tsakankanin ƙafafuwan angel, Hannu angel ta sanya tare da Ruƙo sumar kan Azeeza, Launin gashin kanta Dark blonde, mostly Turawa ne suke da irin wannan gashin kan, sharce sumar kan angel tayi, Kafin Ta raba gashin zuwa gida Biyu, a tsanake Ta soma yi mata kalaba, Tunkafin ta kammala su Hanna sai santin kalabar suke yi, duk sun ƙagara a kammala Yima azeeza suma ayi musu, Guda Biyu tayi mata shima daƙyar ta samu Tayi su saboda santsin gashin Ga tsayi da yawa, Tun da aka kammala Yima azeeza kitson, ta miƙe ta koma gefe tana ruƙe wutsiyoyin kalabar da hannayenta, Sai tsalle Take yi Wutsiyoyin kalabar suna yin sama da ƙasa, ita fa yau ta samu abun wasa,

Ɗaya Bayan ɗaya saida angel tayi musu kitson kalaba guda Biyu, Koda akazo kan Batool sai cewa tayi ta gaji bazata Iya ba, bakomai yasa tace haka ba face Fargabar Ta yadda zata Iya kama Gashin batool, Baƙar wahala zata Ci saboda yawan dake gare shi gashi kamar roba kuma Curly irin nata, a dole batool ta haƙura badan taso ba,

Danish Basu Jima da fitowa daga wanka ba, Giants suka zo Kawo musu abinci, Kamar Jiya haka Yau ma suka ɗibarwa Su Parveen Abincin acikin kwandonsu, Da niyar idan Allah yasa Aka dawo dasu Yau sai su basu su ci, gudun kada adawo dasu Da yunwa,

Bayan sun Kammala Cin abincin, Giants suka tattara Farantan suka Fuce daga Cikin ɗakin,

Duk sun damu da rashin ƴan uwansu, hakan yasa suka kasa samun natsuwa especially angel, Zarya ta soma Yi acikin aɗakin, idan takai ƙarshen bango saita dawo ta sake zagayowa, Har saida ƙafafuwanta suka soma Yi mata raɗadi tukunna ta dakata da yin zirga zirgar, Ta nufi gadonta da niyar ta huta, gefen gadon ta zauna Zugudum, Zuciyarta acike fal da tunanin duniya, wuraren marece su ka Jiyo alamun motsin buɗe ƙopar ɗakin tsohuwa, Bayin Allah da gudu suka duro daga saman gadajensu, Jikinsu na 6ari suka ƙarasa ƙopar ɗakin nata suna jira ta fito,

Sandar hannunta ce ta fara leƙowa, Kafin ta zuro kai ta fito waje, Jikinta sanye da jan doguwar rigar nan ta gado,

Kusan atare suka haɗa baki Wurin gaishe da ita, Ta amsa masu fuskarta asake, Sai faman mamular baki take Yi kamar me cin goro, fuskarnan a jagwale saboda tsabar tsufa ta koma kamar aljana, hurhura ta ko’ina,

“Tsohuwa Ya jikinsu Deeja? Tun jiya muke ta tsammanin jiran dawowarsu amma shiru ba’a dawo mana dasu ba, Munyi kewarsu sosai, Bacci ma daƙyar muka Yi shi, Ko abinci bama Jin daɗin Cin shi saboda rashin ƴan uwanmu” yasmin ce tayi maganar cikin nuna damuwarta,

Mubeen Yace”tun daga Lokacin da aka ɗaukesu har zuwa Yau, kullum Cikin zullumi muke,” Angel dai ta tsareta da ido kamar yarda itama tsohuwar idonta ke akan angel, Kowa da abunda yake saƙawa aranshi,

“Kinyi shiru baki bamu amsa ba? Yaushe za’a dawo mana da ƴan uwanmu? Idan mensturation ne Yanzu ya isa ace jikinsu Yayi sauƙi,” Fuska aɗaure angel ta yi mata maganar,

Jinjina kai tsohuwa Tayi, Sai da ta mula tasha Iska Tukunna tace”Ƴan uwanku suna acikin koshin Lafiya, Bazan Iya sanar daku lokacin da za’a dawo dasu ba, Saboda bani da masaniya, amma nasan bazasu wuce Cikin week ɗin nan ba,” A ƙagare Azeeza tace”Dagaske Su parveen Sun Ji sauƙi? Kuma Suna tambayar mu? Suma sunyi kewarmu”? Murmushi tsohuwa ta sakar mata tare da cewa”Eh mana, sun damu daku sosai, Kuma suna tambayarku, da zarar Sun ƙarasa Jin sauƙi za’a dawo maku da su” wani irin murmushin farin Ciki ne Ya bayyana akan fuskokinsu, In ka cire mutun Huɗu Batool Angel da javed sam babu walwala akan fuskokinsu, Baka iya tantance awani yanayi suke ciki, da alama suna kokwanton kalaman Tsohuwa, sun dai yi shiru ne kawai,

“Just for today, Ki kaimu inda suke domin muyi musu Ya jiki, Tunda Kince Suma sun Yi kewar mu, hakan zai rage musu damuwa” angel ce tayi maganar

Girgiza kai tsohuwa Tayi tare da cewa”Ba’a bada iznin ɗaya daga Cikin ku, Yaje inda suke ba, Idan Ku ka yi hakuri zasu dawo ne” batare da angel ta yi mata musu ba tace”Shikenan zamu zuba ido mu gani idan za’a dawo mana dasu”

Kallon su Batool angel tayi tare da cewa”Ku koma kuje ku zauna, inaso zanyi magana da tsohuwa” Jin wannan maganar yasa tsohuwa tayi saurin kallon angel fuskarta da alamun mamaki,

Juyawa su batool suka Yi atare suka tafi izuwa saman gadajensu, duk wannan abun dake faruwa danish Yana a kwance saman shimfiɗarshi, ko sarki bazai nuna mashi Jin daɗin gado ba, Ya cancanci da akirashi da MAJI DAƊIN GADO,

“Ƴar nan ina sauraron ki, wata Irin magana ce ki ke son Yi dani kuma? Yau ke da kanki”? tsohuwace tayi maganar, fuskarta akwa6e,

cikin sanyin murya angel tace”Inaso mu shiga daga Cikin ɗakin ki, Muyi magana” zaro ido waje tsohuwa tayi jin abunda angel tace, Can kuma saita yamutsa fuska tace”Ba dole sai mun shiga daga Ciki ba, Kome Ki ke son tattaunawa dani, Kiyi mini magana anan ya wadatar”

“Meyasa baki son in shiga ɗakin ki”? Ko akwai wani abu da bakya son in gani ne? Da tuhuma angel tayi mata maganar, girgiza kai tsohuwa ta yi tare da cewa”Babu abunda nake 6oyewa kawai dai bana bada iznin A shiga ɗakina, idan magana zakiyi dani to mu yi ta anan, babu wanda zai ji mu,”

Ta6e baki angel ta ɗanyi still idanuwanta akan tsohuwa tace”yau tsawon shekarata Biyu agidan kurkukun ƙaddara, Ban ta6a ganin wani ya shiga Cikin ɗakin ki ba, Bansan me kike 6oye mana ba, Amatsayinki na uwa agare su, meyasa baki bari muna leƙawa cikin ɗakin ki? Kuma bakya zama acikin mu domin Yin fira, Ko hakan ya sa6awa dokar prison ne”?

Bazawarin murmushi tsohuwa tasaki kafin ta Juya Tana dogara sanda tace da angel”Ki shigo daga Ciki,” tsananin mamaki ne Ya kama angel, Jin ta amince mata akan ta shiga Cikin ɗakin nata,

Sai da angel ta fara juyawa ta kalli su batool, ganin hankalinsu gaba ɗaya baya akansu Yasa ta bi bayan tsohuwa, Kafin ta shiga ɗakin tsohuwa Sai da takaranta addu’o’in neman tsari, sannan ta zura ƙafarta Cikin ɗakin, bakinta ɗauke da sallama,

A tsakiyar ɗakin Angel Ta tsaya tana bin Ɗakin tsohuwa da kallo, Abun mamaki abun al’ajabi, Bakomai bane aciki face Shufke sufken fulawowi,Ta ko’ina tamkar ɗan garde, Sai wasu tsoffin Kujeru guda Biyu suna fuskantar Juna, tsakiyarsu table ne mai ɗauke da Tea pot, da ƙananun Kofina guda Biyu, bayansu babu wani abu na furniture, Gado ko katifa,

Bayan ta kammala Kallon Cikin ɗakin na tsohuwa, Ta wurga idanuwanta kan tsohuwa dake yunƙurin zama saman ɗaya daga Cikin kujerun guda biyu dake fuskantar juna,

Muryarta angel ce ta katse mata hanzarinta da cewa”ina kayan ɗakin suke? Naga babu gado ko katifa? A ina kike kwana”?

Wata irin mahaukaciyar dariya tsohuwa tasaki, Mai matuƙar sautin gaske, Angel tuni tasha jinin jikinta, Muryar tsohuwa ashaƙe tace”Ƴar nan Badai Iya tambaya ba, Dama ganin kwakwaf kika zo Yi mini acikin ɗakin nawa? Keda kika ce Magana zamuyi ae kamata Yayi ki zo ki zauna ga kujera har ma da shayinmu na tsoffi in zuba maki musha don muji daɗin tattaunawa” Takai ƙarshen maganar tana nunawa angel kujerar da hannunta,

Jikinta tamkar na wadda aka zarewa Laka haka Taci gaba da tafiya Ta nufi kujerun Ta shiga Ciki ta zauna, tana Bin tsohuwa da kallon Ban yarda dake ba,

Ƙarasa xama saman kujerar tsohuwa Tayi, a yayin da suke fuskantar Juna ita da angel, Ido cikin ido suke Kallon juna,

“Ina sauraronki wata magana ce kikeson tattaunawa dani”? Ta yi tambayar a ƙagare da son ji,

Angel da ƙarfin hali tace”Tambayoyi ne nake son Yi maki, Ina fata zaki amsa mani” Wani irin kallo tsohuwa ta jefa mata, da mitsi mitsin idanuwanta,

Cigaba da magana angel tayi”Badan Hali na ba, Alfarmace nake nema awurinki, duk da nasan zaiyi wuya ki amsa mini tambayoyina, bansani ba ko yin hakan ya sa6awa dokar Prison”

Gajeren murmushi tsohuwa ta saki, kafin tace”A dokar gidan kurkukun ƙaddara, Ba’a ba mu damar Yin magana da prisoner ba dangane da abunda ya shafi Kurkukun, Yin hakan babban laifina wanda hukuncinsa mutuwa ne……….” aruɗe angel ta ɗan zaro ido tana kallonta, Tsohuwa tace”Kinga kuwa babu ta yadda za’ai In iya amsa maki tambayoyinki kodan saboda in tsira da raina”

Angel tace”Amma ae babu mai ganin mu, Daga Ni sai ke ne acikin ɗakin nan, Babu wanda zai san anyi” Cikin sigar wayau angel ta yi maganar, hakan ba ƙaramin dariya yaba tsohuwa ba, ganin ƙaramar yarinya na neman raina mata hankali, su da suka ga jiya suka yau

“Mu sha Tea mana, ” tayi maganar tare da kai hannu ta ɗauki tea pot, tana tsirara musu ruwan tea Acikin Cups,

“Ko kin zuba bazan Sha ba,” acewar angel, kallonta tsohuwa tayi”saboda me”?
“Ban yarda da duk wani abu da zai fito daga gare ki ba,”
“Amma meyasa ƴar nan”?

“Saboda Ina kokwanto Akan shayin da da zaki bani, Shekaran Jiya da kika ba su batool apples Sunyi bacci Na tsawon yini guda batare da sun farka ba, Har safiya tayi, ina da tabbacin cewa silar apples ɗin da kika basu ne, Shiyasa nake tsoron in sha tea ɗin nan, wata’ƙil kinsa Poison aciki,”

Fuskar tsohuwa ɗauke da murmushi tace”Da ace naso kashe ki da tuni na aiwatar da hakan, kada ki manta kina acikin ɗakina ke kaɗai, Koda sandar hannu zan Iya cutar dake, ƴan uwanki kuma dana bawa Apples Taimakonsu Nayi saboda bani da ikon da zansa Giants su dawo masu da abinci, Shiyasa na baku Apples ɗinmu na gidan kurkukun ƙaddara, Domin kuyi bacci Har gobe Ta yi saurin zagayowa ko kun samu Ku ci abinci” dariya angel ta ɗanyi Tare da cewa”Hakan Yayi kyau, yanzu dai tun da bakyaso In tambayeki agame da kurkukun ƙaddara, Inaso Nayi maki tambaya biyu bata Cikin kurkukun bace….”tsohuwa tace “ina sauraronki”

“Gidan Kurkukun ƙaddara A Cikin Nigeria Yake? Sa’an nan kince Mutum baya ta6a kasance Acikin kurkukun nan dole sai in na Jininsa ne Ya sadaukar da shi, Abunda da nake so In sani, Na jinin naka daya sadaukar dakai Kamar wa kenan”?

“Kin manta abunda na faɗa maki kenan? kiyi mini ko wace irin tambaya amma kada Ki tambayeni game da gidan kurkukun nan…..” tunkan takai karshen maganar angel ta katse ta da cewa”Amma ae ba’a Cikin kurkukun Nayi maki tambayar ba, Kawai ni inaso insan a wace nahiya Yake, Sannan Na jininka da zai Iya sadaukar dakai Kamar wa kenan”?

Tsohuwa bata amsa mata tambayarta ba, sai da ta fara miƙa hannu ta ɗauki kofin da ta zuba shayi acikin shi, takai bakinta tana kur6arshi kusan sau uku, Angel dai ta zuba mata ido, bayan ta Ajiye kofin saman table ɗin, Tana faman mulmula baki tace”Shayin da daɗi, Ki jaraba sha mana” girgiza kai angel tayi”Na ƙoshi, ni dai kawai ki amsa mini tambayata” dariya tsohuwa tayi”Ban ta6a ganin yarinya mai wayau da kaifin basira ba irin naki, Gaskiya Iyayenki Sun Iya haihuwa gaki Kyakkyawa Kamar ke kika ƙera Kyanki,..” ɗaure fuska angel tayi ganin tsohuwa Na ƙoƙarin Kaucewa Tambayarta, ta hanyar canza wani zancen,

Rai a6ace tace”ba wannan na tambayeki ba, Ki bani amsar tambayarta,”

Jinjina kai tsohuwa Ta yi idonta acikin na angel tace”idan na baki amsar tambayarki, Ni kuma me xaki bani? Kinsan ance gwammanti bata aikin banza” kallon rainin wayau angel tayi mata”Amma ae kinsan bani da abunda zan Iya biyanki da shi ko?, Ni dai kawai ki amsa mini tambayata”

Tea pot tsohuwa Ta ɗauka ta ƙara tsirara ruwan tea ɗin acikin cup ɗin gabanta, kafin ta ajiye pot ɗin ta ɗauki kofin takai baki tana sha” Sai da ta kur6e shi duka ta sauke kofin saman table, Tukunna tace”Tambaya ta farko, Gidan kurkukun ƙaddara Ni kaina bansan awace Nahiya yake ba, Abunda na sani shi ne ba’a Cikin kowace ƙasa Yake ba, mashin ko mota bazasu Iya kawo ki cikin kurkukun nan ba”

aruɗe angel ke kallonta, sai da takai karshen maganarta angel tace”Amma Ni lokacin da za’a kawo ni acikin mota aka ɗauko Ni, idan har zan Iya tunawa” dariya tsohuwa Ta saki,

“iya saninki kenan, A mota aka Cafko ki, Amma Bayan nan bazaki Iya tuna Ta Cikin ina aka ƙaraso dake nan ba,” shiru angel ta yi Zuciyarta cike da was wasin maganar tsohuwa, Gani take kamar ƙarya take Yi mata,

Muryar tsohuwa ce ta katse mata Zancen nata da cewa”Tambaya ta biyu, Na jinin ka da zai Iya sadaukar dakai, Mafi rinjayen sadaukarwa Iyayene waɗanda suka Yi silar zuwan ka duniya sune suke sacrificing ɗin ɗansu, Uwa Ko Uba, Bayansu Kuma sai Cikin Blood relatives ɗinka, Domin kuwa Bare bazai ta6a Iya sadaukar dakai ba”

A matuƙar kiɗime angel ke kallon tsohuwa, Muryarta har rawa take yi wurin furta”Iyayen mutun? uwa ko Uba? Anya kuwa zan Iya yarda da maganarki? Duk irin ƙaunar dake a tsakanin Iyaye da ɗansu Zasu Iya sadaukar dashi zuwa ga wannan ƙuntatacciyar rayuwar? To Meyasa zasu Yi hakan?

Fuskar tsohuwa ɗauke da murmushi tace”Kina mamaki ne?, dama nasan zaiyi wuya ki yarda da magana ta, Yanzu dai Ina sauraronki, Idan akwai tambayar da kike da ita, Ki faɗa mini kafin in tafi”

Angel dai ta jinjina maganar tsohuwa abun Ya tsaya mata arai, ya cunkushe kwakwalwarta, Daƙyar ta iya buɗe baki tace”Tambaya Ta ƙarshe da nake so Inyi maki, Mu prisoners dake rayuwa a gidan Kurkukun ƙaddara, Jinsi ɗaya ne? Dukanmu ƴan nigeria ne? Naga da yawan mu kamar fararen fata ne,

Tsohuwa tace”meyasa Ki kece haka”?

Angel tace”saboda Sam babu kamanceceniyar Jinsin baƙar fata atare da mafi rinjayenmu, Misali Kamar danish da Parveen da Javed Sun fi kama da ƴan ƴankin Asia, Azeeza Kuma kamanninta sak da European, Ita kuma batool tafi kama da Jinsin Larabawa, idan muka koma 6angaren Hanna da Hibba, sun fi kama da buzaye Ƴan ƙasar niger…..” ɗaya bayan ɗaya saida angel ta korawa tsohuwa Bayani adangane da Jinsin da kowannan su take hasashen yana kama da shi, takai ƙarshen maganar, a ƙagare da son jin amsar da tsohuwa zata bata,

“Lokacin da kina atare da Iyayenki, Mutane da wani jinsi suke kwatantaki”? Tsohuwace ta jefa mata tambayar yayin da take sakin murmushi,

Yatsina fuska angel ta yi tare da cewa”Sun fi tsammanin Ni balarabiyace wasu kuma baturiya, amma asalin mahaifiyata half cast ce, auntyna ce ta faɗa mini cewa kakata mace balarabiyar ƙasar egypt ce”

Tsohuwa tace”Kinyi kyan kai, Wannan tambayar da kikayi mini, Kina da amsarta ahannunki, ina fata zaki tashi ki tafi Cikin ƴan uwanki tunda na amsa miki tambayoyinki,” maƙe kafaɗa Angel tayi alamar bazata tafi ba

“Korata kike Yi daga ɗakin ki? Tsohuwa tace”a’a kawai dai Akwai inda nake son xuwa ne” Mamaki akan fuskar angel tace”ta ina xaki bi ki fita daga Cikin ɗakin nan naki bayan naga babu ƙopa, Koda yake ba abun mamaki bane, ae naga kafin ma in shigo Ciki, Kincanzawa ɗakin suffarshi duk don kada In yi maki leƙen asiri” tuntsirewa tsohuwa tayi da dariya, Itama angel ɗin dariyar tayi, sai da suka kammala shan dariyarsu kamar wasu ta6a66u, bayan sun tsagaita da yin dariyar angel tace

“Na jima inaso in tambayeki, Ya akai kika san Tarihin rayuwata? Kinsan komai dangane dani, Bayan haka kuma inaso insan asalin sunanki, Daga kin amsa mini waɗan nan tambayoyin xan Tashi intafi Cikin ƴan uwana”

Tsohuwa bata amsa tambayar ba, har sai da ta ɗauki tea pot ta ƙara zuba ruwan shayi a kofi ta kur6a sau biyu, Sannan ta ajiye kofin ta soma magana atsanake,

“Amsar tambaya ta farko, Duk yaron da aka sadaukar agidan kurkukun ƙaddara, Muna bibiyar rayuwarshi ne tun Yana acikin Cikin mahaifiyarshi, Har zuwa lokacin da zata haife shi, zamuyita bibiyar rayuwarshi da zarar yakai shekarun da muƙe buƙatarsa To babu makawa xamu ɗauke shi ne….”

“hakan na nufin tun ina jaririya kuna atare dani? Kenan kune kuke sanyani duk wani mugunta da nake Yiwa daddyna”? Da ruɗu akan fuskarta tayi tambayar, tsohuwa tace”A’a, bamu bane, baƙin aljanine dake atare da mahaifiyarki, Yana matuƙar sonta, Kuma yana da zafin kishi, shine maƙasudin rashin jituwar Iyayenki, Ya tsani Mahaifinki tajudden yaso ya tarwatsa shi, Amma hakan ya faskara saboda Daddnyki mutunne maison yin ibada, bai wasa da azkhar, kuma yana yawan yin sadaka, sannan babbar kariyar dake atare dashi, Yana Yin nafilfilin tsakar dare, A lokacin da benazir ta haifeki, Baƙin Aljani Ya fita daga jikinta ya koma a jikin ki, domin ɗaukar fansa akan mahaifinki, yayi amfani dake wurin ƙuntata mishi, Amma A yanzu Baƙin Aljanin baya atare dake,

Angel fa ta shiga ruɗu, duk da tana kokwanton maganar tsohuwa, Bakasafai Take yarda da zantuttukan ta ba saboda sanin Cewa Ita ɗin Babbar maƙaryaciya ce,

“Kin tambayi sunana, Zaki iya kirana Da TAMIRA Shine Asalin sunana,” Tsohuwa Na kai ƙarshen maganarta, Ta yunƙura ta miƙe daga saman Kujerarar, Da sandar hannunta ta nuna ma angel hanyar fita daga ɗakin, batare da musu ba, Angel ta miƙe ta nufi hanyar fita daga Cikin ɗakin Har takai bakin ƙopat fita, Muryar tsohuwa ta dakatar da ita,

“Shawarar Da nake so Na baki, Kada ki kuskura kice zaki Sanya naci akan sai kin gano ainihin ma’anar Kurkukun ƙaddara, domin kuwa daga ranar da kikasan ma’anarshi, Bazaki sake runtsawa ba, Kuma ba zaki sake Jin daɗin abinci ba, duk wani kingin jin daɗi da ya yi saura acikin rayuwarki, Zaki rasa shi ne! Wani irin mummunan faɗuwar gaba angel taji, Har saida ta dafe kinjinta saboda bugun da zuciyarta tayi mai sautin gaske,

Tsohuwa taci gaba da cewa”Ƴan uwanki suna farin Cikin kasancewarki acikinsu, Saboda Kin kawo musu canji acikin rayuwarsu, Ina fata zaki mayar da hankali wurin faranta musu rai, Amma fa kinsan da sanin duk ranar da kika Binciko ma’anar The destined prison, daga ranar daga ke har su, Zaku fuskanci matsanancin tashin hankali, Kuma daga wannan Lokacin bazaku ƙara Yin tozali da TSOHUWA TAMIRA ba, Zaku yi ta yin gwagwarmayar rayuwa ne atsakaninku, na gargaɗe ki ne saboda Ina sane da duk wani ƙudurinki nasan bin kwakkwafin Gidan kurkukun ƙaddara, Shiyasa na sanar dake irin matsalar da zaki jefa kanki da kuma ƴan uwanki” angel na ƙoƙarin Waiwayowa baya ta kalli tsohuwa taji an ingizata waje, Ƙopar ɗakin ta rufe,

Kamar an jehota ta faɗo ƙasa, Cikin ɗakinsu, har kanta saida Ya bugu,

Tun daga wannan Ranar Angel tashiga ruɗani, Kalaman tsohuwa sunyi matuƙar ɗaure mata kai, Tarasa Ina zata tsoma ranta taji daɗi, Kowa Saida Ya lura da canzawar da tayi, Sam tadaina shiga cikinsu, Gani take kamar Dukansu mutuwa zasuyi shiyasa take janye jikinta gudun kada sabon Yayi yawa ta yadda zata rasa kanta idan ta rasa wani acikinsu, Su batool duk sunyi tsammanin rashinsu Parveen Ne yasa ta canza ta shiga damuwa, Kullum cikin Lallashinta suke yi, Akan tayi haƙuri su koma kamar yadda suka ada, Daƙyar suka samu angel ta koma Yi musu wasa da dariya, Harma tana koya musu wasu wasanni donsu farantawa junansu,

Akwana a tashi Yau tsawon Sati Biyu kenan, Ba’a dawo musu da ƴan uwansu ba Har sun fidda rai da sake ganinsu, tun suna tambayar tsohuwa har sun gaji sun daina, kowa ya zubawa sarautar Allah Ido👀

Yau Tun da Suka tashi daga bacci suke ta jiran a kawo musu abincinsu suci amma shiru giants basu zo ba, Tun safe Har marece, Jikinsu duk Ya yi laushi, azeeza tuni ta fara Yi musu kukan yunwa, Lokacin da dare Ya ratsa hasken ɗakin Yayi duhu, Nan fa suka ƙara shiga tashin hankali ganin zasu kwana basu Ci abinci ba, la66ansu duk sun bushe, Ruwa kaɗai suke tasha tun safe, Cikinsu harya ɗaure, wasu daga Cikinsu hada amanshi su ka yi,

a ƙarshe suka haƙura Da abincin, Kowa Ya hau saman gadonshi ya kwanta, Cikin sa’a bacci ya ɗauke su, Ganin sun nutsa acikin baccin su yasa angel ta sanya hannu ta yaye bargon data lullu6e fuskarta da shi, Saukowa ta yi daga saman gadonta, Sumar kanta duk ta cukurkuɗe kamar ƴar mahaukaciya saboda rashin gyara, Cikin duhu take tafiya tana laluban hanya, Fitila taje ta ɗauko ta kunnata, Tana haske Saitin gadajensu Hannah, ganin babu mai motsi acikinsu Yasa tayi sauri Cikin sanɗa ta nufi sashen toilet ɗinsu, har yanzu bata haƙura da Ƙudirinta ba, Nason fasa gilashin nan, Alwashi ne ta ɗaukarwa kanta Koda zata rasa ranta saita Ga uban me ake aikatawa acikin gidan kurkukun, Duk da tana Jin fargaba akan irin gargaɗin da tsohuwa tayi mata, don a lokacin harta fara tunanin ajiye makaman yaƙinta, amma daga baya sai ta dinga jin tamkar ana tunzurata akan taje taci gaba da jaraba fasa gilashin zata Ci nasara, Zuciya da saƙe saƙe, gani take kamar idan ta fasa gilashin ta dira ta cikin tagar, zata samu damar zuwa wurinsu deeja ne, Harma ta dawo dasu Cikin ɗakin, Da yake sune damuwarta,

Tana shiga Cikin toilet ɗin, Taja ƙopa ta garƙameta da jamlock, A ƙasa ta sauke fitilar, ta ɗaga hannayenta Sama tana roƙon Allah Ya bata Ikon Fasa Glass ɗin a karo na karshe don daga yau ta sanyawa ranta cewa idan har bata fasa shi ba, ta gama zuwa tana shan wahala, zata haƙura ne,

Bayan ta kammala yin addu’ar, Da ƙwarin gwiwarta ta kai hannu ta rarumi bokitin ƙarfen, Sai da taja da baya ta watsa dagudu ta buga tsalle ta daki glass ɗin Da iya ƙarfinta na karshe, Amma wani abun takaici ko tsagewa Baiyi ba, kamar dai kullum haka taci gaba da bugun glass ɗin da bokitin amma Yaƙi nuna alamar ana bugunsa, saboda tsabar zufar dake tsastsafo mata ajikinta Tamkar wadda aka tsamo daga Cikin teku, Idanuwanta sun rune saboda wahala, Hannunta sai zogi yake yi mata, ga wani irin fitsari daya Matseta, da sauri ta jefar da bokitin gefe ɗaya ya gangara ƙasa, Tasanya hannu ta kwale wandon jikinta, Zuƙunnawa tayi a bakin magudaji tana fitsari, sai da ta kammala taje gaban fanfo tayi tsaki, tana kokarin miƙewa kwatam ta hango mutumin jingine da bango, Ya goya hannayen shi saman ƙirjinshi, Tun kafin ma ta ƙarasa juyawa ta gane kowanene, Sakamakon doguwar sumar kanshi data hango,

Muryarshi ce ta ratsa kunnuwanta,

“Can I give u a hand”? ras taji gabanta ya faɗi, azuciyarta tace”Danishi! Nashiga uku, kada ace ya ga abunda nake ƙoƙarin Yi, wayyo Allah na” rai a6ace ta ƙarasa juyowa tana fuskantar 6angaren da yake atsaye ya jingina bayan shi jikin bango, Rai a6ace ta nuna shi da yatsa”Wannan wani irin shashanci ne danish? Why zaka dinga faɗo mini Cikin toilet? yanzu da ace na tu6e kaya ina wanka ko ina wani uzirin Shikenan ka gane mini tsiraci na, Wlh bazan ƙyale ka ba” A fusace ta nufi bokitin data jefar ƙasa tasa hannu ta ɗaukeshi Ta daddage ta wurga mashi bokitin, Da sauri danish ya sanya hannayen shi biyu ya cafke bokitin a hannunshi, ɗagowa yayi da lumsassun idanuwanshi ya ɗaurasu akan fuskantar,

“Raunata ni kike so Ki yi? A ƙule tace”kashe ka zanyi ” Cikin sanyin murya yace”Am really sorry, na kar6i laifina, kada ranki ya 6aci, daga yau bazan sake ba faɗo maki cikin toilet ba,” yakai ƙarshen maganar a yayin da ya ajiye bokitin ƙasa, ya ɗago idonshi Yana kallon Tagar da angel ke ƙoƙarin fasawa,

Zaro idanuwanta ta yi ganin yana kallon glass window ɗin da alama yaga abunda take Yi, muryarta na kerma tace”Nasan kaga abunda nake kokarin yi, So nake in fasa gilashin tagar nan, Saboda Ina da matsalar kwakwalwa, Tun lokacin da ina agidan daddyna kafin zuwana kurkukun nan, Na fasa gilassai bila adadin saboda Ni idan nayi tozali da gilas tsoro Yake bani, kuma hakan yana jaza mini matsala, Likita ma yace Idan ina yawan zama inda ke akwai glass zan Iya mutuwa” angel sarkin wayau, idanuwanta cike tab da kwalla takai karshen maganar, hada marairaice mishi fuska don Yaji tausayinta, ya kuma yarda da maganarta,

Danish bai kawo komai aranshi ba, har cikin zuciyarshi ya yarda da kalamanta, matsawa yayi kusa da ita, Ya sanya hannayenshi biyu ya tallabo fuskarta, Idanuwan su acikin na juna, Cikin sigar lallashi yace”Am sorry angel, don’t cry pls, da kin faɗa mini tuntuni da na jima da sauke miki gilashin,” ta6e baki tayi tare da cewa”Ae bazaka Iya ba, ko Ni nasha gwada cirewa amma na kasa, kullum saina sha wahalar,” ta fadi hakanne don tasan Cewa danish bazai Iya ba, ita kanta da take da ƙarfi ta jaraba ta kasa balle shi da yake sai a hankali ba ƙoshin lafiya ba,

“xan jaraba in gani idan zan iya,” yakai karshen maganar yana tattara hannun rigarshi, da sauri angel ta ɗauko mashi bokitin ta miƙa mashi, bakinta ƙumshe da dariya So take yasha wahala kamar yarda ta sha, Shima Yaji ajikinshi,

Girgiza mata kai yayi”bana buƙatar yin amfani da bucket, I will use my hands” dariyar rainin wayau angel tayi mashi”wlh bazaka Iya ba, Da hannu fa ka ce, haba dai, kai dai ka kar6i Bokitin inga iya ƙarfin ka,” Bai saurareta ba, Ya tunkari Glass window din, Da yake Allah yayi shi da tsawo, Yafi angel tsayi ba sai yasha Wahalar yin tsalle ba kamar yarda take yi, Agaban tagar ya tsaya yana kallonta,

Angel ta ruƙe qugu, Tana jiran ganin Ikon Allah, Fuskarta ɗauke da dariyar mugunta,

hannayen shi biyu ya sanya yana shafa Jikin glass ɗin da ya yi uwar ƙura, ƙasan glass ɗin Ya ruƙo da yatsunshi, Ƙura ido angel tayi ganin glass ɗin kamar ya fara motsi, Gabanta ne ya faɗi ganin Danish ya daddage Ya 6a66ako glass ɗin tun daga tushen shi can cikin ginin dutsen da aka zura shi, Haka ya zaƙulo shi gaba ɗaya ya curo faskeken glass ɗin, Tashin hankalin da ba’a sama shi date,

Kanta Ya gama ɗaurewa, Ta zazzaro idanuwanta waje, kwayar idon kamar zata faɗo ƙasa saboda tsabar mamaki, Gaba daya tabi ta ruɗe ta rikice, Tarasa bakin magana sai bin shi da ido take yi kamar wadda aka dasa ma Aya,

A ƙasa Ya jingine glass ɗin Jikin bango, Ya ɗago yana kakka6e tafin Hannayenshi da ƙura ta buɗe su, A wani slow Ya juya bayan shi Yana kallon angel dake atsaye Ko motsi bata Yi, Ta ƙame kamar abun bautar ƙasar india wato kirishna,

Cikin sanyin mirya ya ambaci sunanta”Angel”? Shiru bata amsa mashi ba, domin kuwa sam bata acikin hayyacinta, matsawa yayi kusa da ita, Ya sanya hannayenshi biyu ya dafa kafaɗunta,

“Meke faru ne? Maimakon inga farin Ciki akan fuskarki, Ko baki ji daɗi bane? Na sauke maki glass ɗin, daga yanzu kin daina shan wahalar bugun shi da bokiti” shi kaɗai yake ta maganarshi, kwata kwata bata a hayyacinta, hura mata iska Yayi asaman fuskarta da bakinshi, Amma ƴar tahalikar nan ko ƙyata idonta bata yi ba, Janyota yayi zuwa jikinshi Ya kwantar da kanta saman chest ɗinshi, Ya sanya hannunshi abayanta yana shafa sumar kanta, kafin ya matso da lips ɗinshi saitin kunnanta yayi mata raɗa”angel, faɗa mini meya faru? Ko kina so in kawar da glass ɗin daga Cikin toilet ɗin gaba ɗaya, yadda bazaki sake ganin shi ba? Jin taƙi yi mishi magana, ya raba jikin shi daga nata, Ya nufi gaban fanfo Ya kunna ruwa ya ɗebo a tafin hannunshi, Ya dawo inda take atsaye kamar gunki, Ya watsa mata ruwan saman fuskarta, Nan take Taja dogon numfashi, har wani zabura tayi ganin shi agabanta, a ruɗe ta wurga idanuwanta kan tagar, Tayi tsammanin ko mafarki take Yi, amma sai taga akasin Hakan dagaske dai Danish Ya cire Glass ɗin tagar da take ta shan wahalar son fasa shi, Tsawon kwanaki, Lamarin Yayi matuƙar ɗaure mata kai, yadda har ya iya 6a66ako shi tun daga tushen shi ya zaro shi, Wanda Tayi imanin Babu wani mahaluƙin da zai Iyayin wannan aikin hakanan siddan ragadan batare da Akwai wani shiri atare da shi ba, Tsohon ginine fa kuma na dutse, A yanayin fuskarta baka iya gane halin da take Ciki, Ta yi farin Ciki da cire glass din da Danish Yayi ko kuwa batayi ba? Tabbas tayi fari ciki mara misaltuwa sai dai mamaki Ya hana ta nuna wannan farin Ciki, Ayanzu ta ƙara zargin cewa danish Ba shi kaɗai bane, Kuma ba wani ke sarrafa shi ba, tunda da ace wani ke sarrafa shi da baza a bari Ya cire glass ɗin nan ba, ganin irin kallon da take Yi mashi ne yasa shi ruƙo hannunta acikin nashi yace”Angel baki bani amsa ba, kina so in kawar da glass ɗin daga Cikin toilet din”? kamar wata sakarya haka take binshi da ido, sai da ya sake maimaita maganar tukunna ta iya bashi amsa da cewa”Inaso ka maida shi yadda ka ciro shi, Kaga duk lokacin dana shigo cikin toilet ɗin sai in zaro shi in kawar dashi wani wurin yadda bazai iya yin affecting ɗina ba” amsa mata yayi da toh, Ya juyawa ya nufi inda ya ajiye glass ɗin Ya ruƙo shi ya shiga kiciniyar mayar dashi, Bayan Ya kammala Ya juyo yana kallonta a lokacin Ta juya baya tare da ranƙwafawa Ta ruƙo hannun fitilar da tazo da ita, ɗagowa tayi suka haɗa ido da shi, Daƙyar ta ƙaƙaro murmushi tasakar mishi, muryarta na rawa tace

“Nagode sosai danish, you’re so kind, ka damu dani kuma kana bani kulawa, miƙa mashi hannunta tayi”Zo mu koma ɗaki mu kwanta, Dare yayi sosai,” ƙarasawa danish yayi inda take atsaye ya zura hannunshi acikin nata, ta ruƙe sosai tana faɗin”pls keep it under wraps, saboda bana so kowa Yasan cewa Mun cire glass ɗin nan kaga tsohuwa za ta yi mana faɗa idan taji awurin wani, koba haka ba” ɗaga mata kai yayi alamar eh, tare da cewa”I will zip my lips, daga ni sai ke,” Cike da jin daɗi tace”Mu biyu kaɗai muka sani, Idan naji maganar awurin wani To kaine, duk da nasan bazaka faɗa ma kowa ba,” Ba ƙaramin daɗi danish yaji ba ganin yadda take ta fara’a saboda Ya cire mata gilashin dake Sanya mata jin tsoro, yayin da ita kuma angel ɗin Shine abun tsoro awurinta, don kuwa ga dukkan alamu Akwai wani abun al’ajabi attare dashi,

Kusan atare suka duro da ƙafafuwansu Cikin ɗakin nasu, Adai dai Lokacin kunnuwansu suka soma Jiyo musu motsin buɗe ƙopar ɗakinsu, Mamaki ƙarara akan fuskarsu suka kai idanuwansu saitin benan dake a ɗakin, daga saman matattakalar benan suka Fara kallon ƙafafuwan Mutun Uku dake saukowa, masu sanye da jajayen Uniform, daga bayansu Kuma Giants ne Hannayensu a ruƙe Da Kayan abinci……shin su wanene?

*Domin neman ƙarin bayani 08103884440 ko 08169856268 Text on whatsapp only banda phone calls, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, Ga wanda ya shirya yin payment, zai iya yi mini magana, Cikin next month Takun farko zai ƙare in sha Allah, zamu nutsa Cikin labari*

share fisabilillah❤👌

No comments