Breaking News

Kurkukun Kaddara 36-37

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*


_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E36-37

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

Haƙiƙa maganar tsohuwa ta yi matuƙar ta6a zuciyoyinsu, Jin cewa Iyayen su suna can suna sharholiyarsu sun manta da suna da wasu ƴa’ƴa da su ka sadaukar, Wai ashe dama su ba Marayu bane marasa Iyaye! ? Jikin su ya yi mugun sanyi, kamar waɗanda aka zarewa laka, ita dama angel ta san da wannan shiyasa ta ƙudiri aniyar idan har Allah yasa tayi nasarar fita daga Cikin kurkukun, Kaitsaye zata fara neman Azzalumin da ya yi sacrificing ɗinta acikin danginta, don a halin yanzu kowa suspect ne awurinta, Mahaifinta da aunty aneelerh kaɗai ta cire aciki, Amma sauran dangin nata da wanda ta sani dama wanda bata sani ba, Kaf ɗinsu she’s suspecting them,

ɗakin nasu ya yi shiru babu mai magana saboda ruɗanin da tsohuwa ta jefa su aciki, Kowa da abunda yake saƙawa aran shi, kuma har lokacin suna atsaitsaye kewaye da deeja, babu wanda Ya motsa, danish Yana a gefe ɗaya ya goya hannayenshi saman ƙirjinshi,

Lokaci ɗaya kamar an zungure su gaba ɗaya suka ɗago da idanuwansu suna kallon saman benan Jin motsin buɗe ƙopa, Hankalin deeja yabi ya tashi haiƙam Jikinta ya soma kerma ta ƙanƙame Jikin haris tana kuka tana faɗin kada su bari atafi da ita, duk ta cukuikuye mashi rigarshi, Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,

“Pls kada wanda yayi yunƙurin dakatar dasu, am warning u,” danish ne ya gargaɗe su,

Babu wanda Ya kalli inda yake sai dai duk sun sare zuciyoyin su sun karaya,

Takun tafiyar giant ne Ya ja hankalinsu zuwa ga kallon staircase ɗin dayake saukowa, Shi ɗaya yazo musu wani gabjejen ƙato dashi a bubbuɗe yake tafiya, Ganin Yana tunkarosu gadan gadan Yasa duk suka watse saboda tsoratar da suka Yi, batool taja hannun azeeza duk suka ja gefe, Ya rage daga angel sai haris daya fusata Yana jiran shi ya ƙaraso, da sauri danish ya sanya hannyenshi biyu ya ruƙo wuyan rigar haris dana angel da ƙarfi Ya janyesu gefe ɗaya batare daya saki wuyan rigarsu ba, duk yadda suka so su kwace daga ruƙon da yayi musu sun kasa, Angel hada yakushin shi tadinga yi da hannayenta amma ko ajikinshi,

Giant ɗin na ƙarasowa Ya sanya hannayenshi biyu ya ɗauki deeja saman kafaɗarshi tana ta kuka baiwar Allah, a haka Ya juya da ita ya fuce daga Cikin ɗakin, suna ganin an tafi da ita, su ka fashe da kuka kamar ransu zai fita,

Kamar Jira take Giant ɗin Ya fita, Danish na sakin wuyar rigarta, Awani fusace Ta juya ta fuskance shi ta ware yatsun hannayenta biyar cuf, ta wanke shi da zazzafan mari ji kake tasss, Har saida kanshi yayi gefe ɗaya,

Ranta amatuƙar 6ace tace”Banza daƙiƙa, ban ta6a sanin kai wawa bane dolo sai yau, Kana ji kana gani za’a tafi da ita baka iya ta6uka komai ba, don me zaka hana mu taimakonta? Ta yi maganar tana ciccije le6enta, ɗagowa yayi da fuskarshi, tafin hannunshi dafe da inda ta mara, wurin yayi ja saboda hasken fatarshi ga sahun dogayen yatsun hannunta nan ruɗu ruɗu asaman fatar, wani irin raunataccen kallo yake binta dashi batare daya furta komai ba, Sauran ƴan uwan nasu duk suna a tsaye cirko cirko suna kallonsu, Haris dai baice komai ba, duk da baiji daɗin marin da angel ta yi ma danish ba, Sai dai shi kanshi yaji haushin yadda danish yaƙi nuna fusatarshi akan tafiyar da aka yi da deeja,

“Angel meyasa kika mare shi? Kalli yadda kika raunata mashi fuska! shi fa bashi da laifi, yana ƙoƙarine Ya dakatar da ku gudun kada ku jefa rayuwarku cikin hatsari, saboda Lafiyarku yayi hakan, taya zamu Iya ja da giants? Kin manta irin wurgin da su ka yi damu lokacin da muka yi yunƙurin hana atafi dasu Hannah”? Juyawa angel tayi tare da kallon batool da ke magana, nuna danish tayi ta yatsan hannunta tace”batool kina supporting ɗinshi? duk irin halin ko in kulan da ya nuna akan deeja? Kowa ya nuna tausaya agareta ganin irin halin da take ciki tana kuka tana roƙonmu akan kada mu bari atafi da ita, Amma wannan Kwankon ashanan Koda naje na faɗa mishi Ba abunda yace saima ya share ni kamar wata ƴar iska, ni shi ne abunda yafi ƙona mini rai” azafafe ta ƙarasa maganar tana jifarshi da harara, duk ya sha jinin jikin shi,

Muryar azeeza kamar zata fashe da kuka tace”Ni dai dan Allah kowa yayi haƙuri, tun da an riga an tafi da deejan mu, Muje mu kwanta dare yayi sosai,” harara haris ya wurga ma azeeza duk da bata iya ganinshi yace”Baki da ƙafa ne? Ki wuce kije ki kwanta ko wani ya ruƙe ki ne”? Da alama dai duk sun fusata,

Jikin danish a sanyaye Ya juya ya nufi azeeza ya ruƙo hannunta yaja ta har zuwa saman gadonta ta hau ta kwanta ya sanya mata bargo ya lullu6e mata Jikinta, kafin Ya koma Saman gadonshi Ya kwanta idanuwanshi na fuskarta ceilling, Angel itace mutun ta farko da ta ta6a bugunshi, karo na biyu kenan tana ta6a lafiyar jikin shi, abun ya tsaya mashi arai,

Ɗaya bayan ɗaya suka nufi gadajensu kowa Ya haye ya kwanta, Ya rage saura angel ita kaɗai a tsaye, tsabar baƙin Ciki Ya hana taje ta kwanta, saboda mugun haushin danish da take ji, ga zarginshi da take Yi, gani take kamar shi ɗin secret Giant ne acikinsu,

Sai da ta bari Kowa Yayi bacci, Ta haura saman gadonta ta janyo pillow ta ɗaura kanta akai, Yau ta juya ma danish baya, ada kullum Juna suke fuskanta idan zasu yi bacci,

Sam ta kasa runtsawa tunanin deeja ya hanata sakat, tarasa ina zata tsoma ranta taji daɗi,

Muryar danish ce ta ratsa kunnata,

“Angel” Ya kira sunanta, Yana daga kwance saman gadonshi, tana ji tayi banza ta ƙyale shi, ya kasa bacci saboda fushin da take yi da shi, Sake kiran sunanta ya yi”Angel” kusan sau Biyar amma bata amsa ma shi ba, miƙewa yayi tare da saukowa daga saman bed ɗinshi, Ya matsa daga gefen gadonta ya zauna, hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba, duk da bata waigo ta kalle shi ba amma taji alamar yana akusa da ita,

Cool voice dinshi ce ta kara ratsa kunnanta, “Am really sorry, I don’t mean to hurt u, just bana son Su cutar da ku ne that’s the reason why na hana ku abunda ku ke ƙoƙarin yi, Giants sunfi ƙarfin ku, ba zaku iya ja dasu ba…..”kamar an katse shi ya dakata da yin maganar yana kallon gefen fuskarta, pillow yaga ta sanya saman kanta ta toshe kunnanta, don ma yasan ba sauraronshi take yi ba, duk sai yaji ba daɗi, Gaba ɗaya ya rasa sukuni, shi dai bai ƙaunar yaga wani na fushi da shi, ko zafin marin da ta yi mashi ɗazu baiji ba, da ace wani ne tayi ma marin nan ko bai rama ba sai ya fusa ta,

“Angel pls talk to me. i realized my mistake, and I regret it, ba zan sake ba” shiru bata tanka mashi ba, ” wannan karan muryarshi tayi zaƙi da sanyi kamar zaiyi kuka, Miƙa hannunshi yayi tare da ruƙo doguwar sumar kanta, aikuwa a fusace ta sanya hannunta da ƙarfi ta ka6e mashi hannunshi,’ batare da ta yi magana ba,

Still baiyi fushi ba ya kuma cewa”Angel if you don’t talk to me, I won’t sleep, I will spend the whole night here” babu wasa a fuskarshi yayi maganar,

Ji take gaba ɗaya ya takura mata, zaman shi agefen gadonta kamar saman kanta take jin shi, Tasan halin shi Ba cikakken hankali ne dashi ba, Yana iya aiwatar da abunda ya fada, Tuna wannan yasa ta miƙe xaune har ya fara sauke ajiyar zuciya atunaninshi ta yafe mashi ne, ashe masifa ta tashi ta zazzage mashi,

Cakumar wuyan rigarshi tayi da hannayenta biyu, ta zazzare mashi manyan gray eyes ɗinta Ta jijjiga wuyan rigar tashi, Saboda masu bayyaci yasa ta sassauta muryarta,

“Wai menene alaƙata dakai ne? Ka addabi rayuwata ka hanani sakat, kai nifa bansan ganin wannan mummunar fuskar taka, na tsani ragon namiji irin ka, pls na roƙe ka ka tashi kabar gefen gadona ko na samu inyi bacci” Takai karshen maganar tare da ture shi gefe, ko motsi baiyi ba, kallonta kawai yake yi da lumsassun idanuwanshi,

A hasale tace”idan har bazaka sauko daga saman gadon ba, Ni zan tashi in baka wuri,” ganin tana ƙoƙarin saukowa daga saman gadon yasa shi yin saurin damƙar hannunta, wani irin mugun kallo ta jefa mashi”sakar mini hannu na,” ba musu ya saki hannun. ta sauko daga saman gadon, Ta dauƙi bargonta da pillow, Ta juya ta nufi tsakiyar ɗakinsu Ta shimfiɗa bargon ta jefa pillown saman shi, Ta haye ta kwanta, duk yana a zaune gefen gadonta yana kallonta,

Lumshe idanuwanta ta yi da niyar bacci ya ɗauketa, kamar daga sama taji an sanya hannu an ɗauketa da ita da bargon da pillown duka ya tattare su ya ɗaga sama Ya nufi gadonta, Yana zuwa ya jefe ta saman gadonta, aɗan tsorace ta ware idanuwanta tare da wurgasu kan fuskarshi Yana atsaye ya kafe ta da ido, Tsabar mamaki ya hana ta furta komai, kamar walƙiya haka Yaje ya daukota,

Cikin nuna jin takaici tace”Nashiga uku! Wai ina ruwanka dani ne? idan na kwana a ƙasa matsalarka ce ko tawa”? Ya bata amsa da cewa”tamu” guntun tsoki taja, bata ƙara furta mashi komai ba, tana jin motsin shi abayanta, haukanshi na matuƙar ɗaure mata kai, Lokacin da bacci yayi awon gaba da ita, A zaune ya fara gyangyaɗi, A ƙarshe da baccin yafi ƙarfinshi a bayanta ya kwanta saman gadonta, lallai ya taro march,

*ANEELAH*

Wuraren ƙarfe 12 na safe, Tana a ƙudundune Cikin bargonta, Tun bayan sallar asuba data kwanta bacci bata farka ba, wani irin nauyin bacci ne ya ɗauketa, Hada ƙarin maganin muran da tasha a daren Jiya,

Baby junaid ne ya shigo cikin ɗakin yana azaune Cikin motar shi ta wasan yara, Da hannu Yake juya streering wheel ɗin motar, Ba ƙaramin kyau yayi ba, jump suit ne a jikinshi launinsu ɗaya da ƴar motar wasan shi, Army green, da alama ba ƙaramin daɗin motar yake ji ba, daga ya juya steering saita tafi da gudu, agaban gadon Mommynshi Ya tsaya, tare da kai hannu ya danna wani maddani A jikin motar, nan take motar ta soma yin Jiniya, Afirgice aneelerh Ta farka tare da yaye bargon data lullu6a dashi hannunta dafe da ƙirjinta, jallabiya ce a jikinta, Muryarta na kerma take ambaton” Innallahi wa’inna ilaihirraji’un”

tayi matuƙar tsorata, Duk a tunanin ta ƴan sanda ne suka zo gidan ashe motar wasan junaid ce, Fuskarta a yamutse take kallon shi, ya wage baki yana dariya fararen hakoranshi tar dasu, Dimples ɗinshi biyu sun lotsa sosai, a fusace ta miƙa hannu ta ɗauki pillow ta wurga mashi saman fuskarshi, nan take ya kwa6e fuska zai yi kuka,

Cikin nuna 6acin ranta ta soma Yi mashi magana”Karka kuskura kace zaka yi mini kuka stupid, Wlh nayi regretting dana fidda kuɗina na siya maka motar nan ashe kaina abun zai ƙare!, bazaiyiyu ba ka hanani kwanciyar hankali, zan 6a66alla motar In jefata cikin bola kowa ya huta” Jin wannan maganar yasa shi ƙara sautin kukan nashi, Ganin tana yunƙurin saukowa daga saman gadon yasa jin tsoro, gudun kada ta 6alla mashi motarshi kamar yadda tace, aikuwa da sauri yaja streering Ya juya motar da gudu yajata ya nufu ƙopa, Murmushi ta saki tana bin bayanshi da kallo, aranta tace”Allah kaɗai yasan irin ƙalin sharrin da zaije yayi mini a wurin mami, yau nifa na shiga uku, Wata’ƙil ma yaja a hanani Yin breakfast, ” takai karshen maganar tare da saukowa daga saman gadon takai hannu ta ɗauko filon data jefa mashi a ƙasa ta wurgo shi saman gadon, miƙa tayi tare da yin hamma ta wuce toilet, after some minutes ta fito tana tafiya a slow ta nufi gaban mirror ta zauna, wata irin yunwa take ji kamar taci ƴan hanjin cikinta, wayarta ta ɗauka dake ajiye gaban mirror, ta danna power hasken screen ɗin ya kawo, hoton angel ne a matsayin wallpaper ɗinta, ta yi mata hoton ne saman gado tana bacci ta saki baki, Tana matuƙar son angel, Tayi missing ɗinta sosai, duk rana ta Allah idan tafarka daga bacci ta ɗauki wayarta saita sumbaci hoton, Yanzu ma kiss ta manna mashi, aranta tace”I really missed u angel, kamar in yi hauka, Allah ya kare mini ke aduk inda kike, Inaji araina cewa Kina araye kuma kina tunani na, I luv u so much” tuni hawaye sun Cika idonta,

Tana yunƙurin miƙewa daga saman mirror chair ɗin, Sai ga Ana Mai aikin gidansu ta faɗo Cikin ɗakin tana Haki hannunta ruƙe da wayarta, Jikinta sanye da Riga da skirt, Sun matseta, Hankalin aneelerh ba ƙaramin tashi yae ba, Ta cikin mirror ta hangota, da sauri ta ƙarasa Juyawa Baya tana kallonta tace”Ana lafiyarki kuwa? Babu neman excuse kin faɗo mini ɗaki? Kamar wadda tasha ƙwaya”? Tayi maganar tana tunkararta, Duƙar dakai ƙasa ana tayi Muryarta na ɗan rawa tace”Am sorry madam, Wani abune na gani daya bani mamaki, shi ne nazo in nuna maki,”

Matsawa aneelerh tayi kusa da ita, Tare da miƙa hannu ta kar6i wayar Ana, tana ɗaura idanuwanta kan screen ɗin, Ras taji gabanta ya faɗi waro ido waje tayi tana kallonta, mamaki ƙarara akan fuskarta tace”Abun mamaki! ana a ina kika samu hoton nan? Kuma daga gani sabuwar ɗauka ce!” murmushi ana ta ɗan saki kafin tace”Yanzun nan Na ganshi A instagram, shafin twins Na Family ɗin Obinna, Zayn da zaid pravin Obinna, Su ne su ka yi posting ɗin a page ɗinsu na insta, madam i was shocked da naga pic ɗin nan nace ashe matar nan tana araye da ranta da lafiyarta! ” jinjina kai aneelerh tayi da alama tayi matuƙar girgiza tace”Wonders shall neva end” kallon Ana tayi tare da cewa”Ki jira ni ina zuwa, dole mami taga hoton nan, amma dai matar nan ta bani mamaki matuƙa” Jiki na rawa aneeleh ta fuce daga Cikin ɗakin, gudu gudu sauri sauri ta nufi bedroom ɗin mami, bayan tafiyarta ana ta fito ta tsaya a falo tana jiran dawowarta,

Aneelerh Na yunƙurin yin sallama a ƙopar ɗakin Mami, sai ga mamin ta fito Jikinta sanye da riga da zani na atampa, Ƙiris Ya rage su bangaji juna ita da aneelerh, Sakin baki mami tayi tana kallonta,

Da sauri aneelerh tace”Am sorry mami, a ruɗe nake ne, wani abun mamaki ne Ana ta gwada mini acikin wayarta, Shi ne na kawo maki kema ki gani” tana inda inda tayi maganar, tare da miƙa ma mami wayar hannunta, tasa hannu ta kar6a, koda mami ta kalli hoton saita ruƙe ha6arta da hannu ɗaya, ta ɗan zaro ido da mamaki akan fuskarta tace”Kai! Wa nake gani kamar BENAZIR”! aneelerh tace”Mami itace, Kalli dakyau ki gani, ba’a jima da yin posting ɗin ba, ” Mami tasha ruwan mamaki, Sai ƙarewa hoton kallo take yi, dagaske ɗin dai benazir ce, Daga gani hoton batasan an yi mata shi ba, tana a tsaye, hannunta ɗaya ta dafa murfin danƙareriyar motarta, tsadaddiyar gaske, jikinta na sanye da business suit black colour sunbi shape ɗinta sun zauna mata cuf cuf, kamar don ita aka ƙera kayan, hips ɗinta sun fito sosai, hannunta ruƙe da wayarta ƙirar i phone 15 pro, kanta babu hula ko ɗan kwali, Zallar gashin kanta ne daya sha gyara Har midback dinta, idanuwanta na manne da glass, idan ka ganta a hoton ba zaka ta6a yarda cewa ta ta6a aure ba, Ko tana da ƴa, saboda tsabar haɗuwarta, Jikinta Badai kyau ba, agogon diamond ɗin dake sanye a hannunta, a ƙalla Price ɗinta yakai 100m,

Kallon Juna mami da aneelerh su ka yi kowa Fuskarshi ɗauke da al’ajabi, mami tace”Abun mamaki baya ta6a ƙarewa, Wai dama ƴar nan tana nan da ranta da lafiyarta? Hankalinta kwance tsawon shekara da shekaru bata ta6a waiwayar ƴarta da mijinta ba, Anya kuwa benazir ce aneelerh? Kodai watace me kama da ita? to ae abunne da ɗaure kai wlh, ‘

Murmushin takaici aneelerh ta saki tare da cewa”wlh mami itace! Babu shakka benazir ce, ae ina ganin hoton ko doubting ban yi ba, na shaida itace, Kinsan dama ita tun fil’azal wayayyiyar macace akwai son gayu, Kuma tafi sha’awar rayuwar ƴanci, ” mami tace”Haka fa take, Oh Ni ƴarsu, duniya da abun tsoro take, Anya kuwa Benazir tasan ciwon kanta”? aneelerh tace”Ina fa, ae babu alama, Yanzu haka ko Iyayenta basu da masaniya akan inda take rayuwa, Duk da Naga kamar Ƙasar waje ne, idan kika ƙura ido a jikin Ginin dake a bayan hoton an rubuta Rbc (Royal bank of canada) dake acikin toronto, Kuma ga dukkan alamu mami hoton bada saninta aka ɗauke shi ba, don da ace ta sani da bata bari an ɗauke shi ba, kodan kada asirinta ya tonu agane inda take, tun da ko Iyayenta basu son awace nahiya take zaune ba suma nemanta suke Yi ruwa ajallo,”

Mami tace”Nama rasa me xance, kawai dai Allah ya shiryeta in me shiryuwace, amma dai wannan rayuwar da ta ɗaukarwa kanta bamai 6ullewa bace, Wlh zata yi danasanin mara amfani, kwata kwata benazir bata yi wayau ba, Allah kanta tayi mawa, Ace da ranka da lafiyarka, Ka gudu kabar Jinjira acikin kwamin wanka, da mijinka batare da ka waiwaye su ba almost 4 years, Saboda shafewar basira da rashin hankali, tana can tana yawon biɗiɗi,” takarasa maganar tare da jan dogon tsoki Ranta ya 6aci ta miƙe ma aneelerh wayar”kar6i nan nagaji da ganin kayan takaici,” kar6ar wayar aneelerh Tayi, Har ta juya zata Bar ƙopar ɗakin mami sai kuma ta ɗan dawo baya tace”mami Baby junaid fa”?

“Yana aciki kwance saman gado yana bacci, Yazo yana kuka ya faɗa min wai kin ce zaki 6alla mashi mota, Daƙyar na samu na lallashe ya daina kuka ya kwanta,” dariya aneelerh tasaki tare da cewa”Ya takura mun ne mami, ina tsaka da yin bacci na ya daddage ya danna jiniyar motar, baki ga yarda na zabura ba, Ni nayi tunanin ƴan sanda ne suka zo ashe shine” Dariya mami tayi tana girgiza kai tace”Allah ya shirya min jikana, ” aneelerh ta amsa da amin, kafin Ta juya ta nufi falo, Agaban dining ta hango ana tana jera kayan breakfast ɗinsu, Ƙarasawa tayi inda take atsaye ta miƙa mata wayar tare da yi mata godiya, don ba ƙaramin daɗi taji ba, atlease tasan benazir tana araye, Idan Allah yasa suna da tsawaicin kwana wata rana Allah zai haɗa su ne, ta wani 6angaren kuma Abun ya tsaya mata acikin zuciyarta, Irin yadda taga benazir a hoton hankalinta kwance babu wata damuwa akan fuskarta,

Yinin ranar da tunanin benazir tayi shi, Da rana ne Abie Ya dawo daga wurin aikinshi, Yazo musu da babban albishir Na ƙara mashi matsayi da akayi zasu koma Abuja da zama, mami tayi farin ciki, aneelerh kuwa sam bataso haka ba, Ita fa duk wani abu da zai rabata da jos ba son shi take Yi ba, gani take kamar idan ta ɗaga ƙafa tabar garin shikenan ba zata ƙara ganin mutanan nan ukun da ta rasa ba, waɗanda a koda yaushe take Addu’ar Allah ya Bayyanar mata dasu, babu yarda ta iya yanzu dole tabi iyayenta don bata son rabuwa dasu, tafi so duk Inda zasu je ƙafarta ƙafarsu,

*Back To prison*

Ƙwaƙƙwaran Juyi angel tayi da niyar ta gyara kwanciyarta, sai ji tayi an tokare bayanta, A matuƙar ruɗe ta juyo tana kallonshi, waro ido waje tayi ganin danish saman gadonta, Aikuwa rai a6ace ta sanya ƙafarta da ƙarfi ta ture shi gaba ɗaya ya gangara ƙasa Kanshi Ya bugu sosai har saida yafirta”ash!!” saboda zafin da ya ji, Zazzaga mashi masifa ta soma Yi ta inda ta shiga bata nan take fita ba, sautin muryarta ya karaɗe Kunnuwan masu bacci ɗaya bayan ɗaya su batool suka dinga farkawa Suna tambayar lafiya me ya faru?

Nuna danish ta yi da yatsan Hannunta tace”wlh kaɗan ka gani, Idan har baka fita sabgata ba, Ina mace kana namiji Ka kwana a gadona, Salon kawai kaja mini zunibi,” Tun da ta fara Yi mashi faɗa, bai motsa daga kwancen da yake a ƙasa ba, ya dafe gefen goshin shi da hannu, Yaji zafin buguwar da kanshi yayi,

Saukowa su batool su Ka yi daga saman beds ɗinsu, fuskokinsu duk A yamutse idanuwansu sun kumbura sakamakon kukan da suka sha Jiya da za’a tafi da deeja,

Abakin gadon angel suka tsaya suna kallonsu ita da danish, Ta rufe ido sai faɗa take mashi hada pillow ta jefe mashi saman fuska, Ya rasa ina zai tsoma ranshi yaji daɗi, shouting ɗin da take yi mashi ba ƙaramin gigita shi yake yi, daurewa kawai yake yi,

“Pls angel, Ki yi haƙuri Ki ƙyale shi hakanan, kodan saboda lallurarshi ta rashin son hayaniya zai iya rikicewa, Hanna ce tayi maganar, angel ta watsa hannu tare da cewa”Idan ya tashi ya haukace ƙarewa ma, wlh ko ajikina, tun farko saida naja mashi kunne akan ya ni santa kanshi dani amma yaƙiya, saboda head fish ne dashi”

Girgiza kai batool ta ɗanyi idonta akan angel tace”Sister badan halina ba, Pls Ki bar maganar nan, Ki barshi yaji da kanshi, Nasan kina fushi dashi ne saboda abunda ya faru jiya, Ki yi haƙuri ki manta komai, kuma ki daina fushi dashi saboda Baya ƙaunar yaga ana share shi, Yana shiga damuwa” daƙyar batool takarasa maganar ganin irin kallon da angel ke jefa mata,

Gyaɗa kai tayi tare da jinjina kai tace”Shikenan zan ƙyale shi amma babu ruwanshi dani! Ni kawai bana son Yana kallona ko Yana yi mini magana, ” Tana kammala maganar ta sauko daga saman gadonta ta bi ta gefensu Ta shige toilet,

Zuƙunnawa batool tayi agaban Danish Ta ruƙo hannunshi acikin nata, Ba ƙaramin tausayin shi taji ba, ganin sahun marin da angel tayi mashi asaman fuskarshi har yau bai disashe ba,

Cikin sanyin murya tace”Am sorry danish, Kamar yarda tace ka ƙyale ta, to ka rabu da ita har zuwa time da zata huce, if not zata cigaba da Ƙyararka ne, Nasan zata dawo da kanta ne ta nemi yi maka magana,” sai lokacin ya samu ya miƙe zaune, ya jingina bayanshi jikin bango, ɗaya bayan ɗaya ya shiga binsu azeeza dake atsaye da kallo, matan ne gaba ɗayansu, Sai daga bisani Haris da su naufal Suka Sauko daga saman gadajensu, A inda yake zaune suka tsaya cirko cirko suna kallon shi,

“Kuma fushi ku ke yi da ni? Kamar yadda take fushi dani”? Yayi masu tambayar idonshi akansu, atare suka haɗa baki wurin cewa a’a, Kallon haris yayi tunkafin yayi mashi magana haris yai saurin cewa”am not angry with u, kaima ka sani bazan iya fushi dakai ba, just banji daɗin abunda ya faru ba jiya, amma komai ya riga daya wuce” jinjina kai danish yayi kafin ya kuma cewa”komi nake yi ina yi ne saboda ku, amma nasan zaiyi wuya ku fahimci hakan, sai nan gaba”

Naufal yace”Pls danish, mu komai ya wuce awurinmu, abunda ya faru ya riga daya faru ba wanda ya isa ya dawo dashi baya, so pls mu manta kawai, baida amfani tuna baya,” Danish yace”idan ku kun fahimce ni, ita taƙi ta fahimce ni, tun daren jiya nake bata hakuri amma taƙi ta saurare ni,” sai lokacin suka gane inda damuwarshi ta dosa, dama shi haka yake sam baya son wani yana fushi dashi tun fil azal, gaba ɗaya yake rasa sukuni,

“Danish kada ka damu kanka, In dai angel ce Zata kula ka, Ae bata iya fushi ba, tana da saurin hawa da kuma saurin sauka,” acewar javed,

Ta6e baki yai tare da cewa”Its okey, ngde da kulawarku agare ni, ” daga haka Ya miƙe jiki ba ƙwari Ya Nufi toilet, domin yin wanka,

Kafin Giants su kawo musu Breakfast ɗinsu, Sai da kowannan su Ya yi wanka, Basu jima da hallara A cikin ɗakin nasu ba, Sai ga Giants ɗin sun shigo ɗauke da kayan abincinsu, bayan sun ajiye musu saman dining carpet, duk suka zazzauna kewaye da farantan, Yau farfesun naman kaza aka kawo musu da zafinshi hada tiriri Yaji kayan ƙamshi, ga kuma dambun nama da aka haɗo musu dashi, sai Kayan marmari kamar kullum da kuma soft drinks, Abun na ɗaurewa angel kai, ganin irin badagon da ake yi da nama agidan kurkukun, sam bata yarda da irin wannan Lafiyayyar cimar da ake kawo musu ba, kullum basu da abinci sai nama kala kala! Na kaza na shanu na rago, wani naman ma batasan na wace dabbar bane, tana yawan tambayar kanta ko su wanene ke girka abincin kurkukun daga gani ƙwararru ne a 6angaren catering, sun iya sarrafa abinci, wani naman saboda tsabar dahuwar shi kana jefa shi abaki tunkafin ka taune da haƙori zai dagargaje da kanshi, ita dai fargabarta kada ace abincin da ake basu su naci, da ransu za’a fanshe, duk in zuciyarta ta saƙa mata hakan sai taji gabanta ya faɗi rasss! Don kuwa ko gwamnati bata aikin banza, balle kuma mutanan da Ba Allah ne aransu ba, Sunsan dalilin dayasa suke basu lafiyayyan abinci wata’ƙil kodan suna amfani dasu ne, Allah wa’alamu

kafin su fara Shan farfesun saida ta tunasar dasu akan su yi bismilla, Kullum ne sai ta tuna musu, hatta haris yau da tace su yi bismillah sai da yayi duk da bai musulunta ba, danish ne kawai baiyi ba, Ta lura dashi duk wani abu daya ƙunshi sunan Allah aciki bai furta shi, hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yake yi ba, Har suka kammala cin abinci, da zarar sun haɗa ido dashi sai ta dinga jefa mashi harara, duk yabi ya tsargu ya hana zuciyarshi sakat, farfesun ma ba’a cikin kwanciyar hankali yasha shi ba,

Bayan sun kammala Cin abincin, Giants suka tattara farantan Suka fuce daga Cikin ɗakin,

Ganin suna yunkurin zuwa saman gado su kwanta ne, yasa angel ta dakatar dasu, tace su motsa jikinsu, Idan sun kammala su watsa ruwa ajikinsu, Sannan Sun kwanta su huta, babu musu suka amsa mata da toh, banda danish da haris, tuni sun haye saman gadajensu, Shi haris damuwar rashin deeja ne yasa shi ƙin ta6uka komai, tunanin abunda ya faru daren jiya kafin atafi da ita ya tsaya mashi arai, Yaji tausayinta sosai, su kansu sauran ƴan uwan nasu sun damu da deeja, Ba yadda zasu yi ne shiyasa suka barma Allah komai,

A tsakiyar ɗakin suka Jera layi suna yin exercise, kamar wasan ƴar tseral haka suka dinga zubawa da gudu idan suka kai ƙarshen bango sai su dawo su sake komawa, Sai da suka tara uwar zufa ajikinsu tukunna kowa Ya nufi toilet domin watsa ruwa, Bayan sun fito ne, parveen ta matsa ma angel akan tayi mata irin kalabar da tayi ma su azeeza, Dama tun ranar da ta ganta ta kwallafa rai akan tana so itama, kafin marece yayi angel tayi ma parveen kalaba biyu akanta, ba ita kaɗai ba hada rubina tayi mawa, Bayan ta kammala musu kitson, Kowa Ya koma saman gadonshi ya zauna, Fira suka soma yi atsakaninsu acikin firar ne, suka tambaye ta, wai da tace musu wata rana zasu fita idan suka fita ina zasu je? Su da basu san komai na wajen kurkuku ba, murmushi tayi tare da cewa su kwantar da hankalinsu, Gaba ɗayansu zasu yi rayuwa agidan daddynta, Tace daddyna yana da gida, kuma gidanmu ɗaki Shida ne, Akwai palour ɗaya, dani da azeeza da batool zamu ware ɗaki ɗaya, Parveen da deeja da hanna zasu ware nasu ɗakin ɗaya, sai Eve da hibba da rubina suma zasu ɗauki ɗaya, nawa kenan? Suka ce mata Uku, tace toh, sauran ɗakunan guda uku, Javed da Naufal tare da Mubeen zasu ɗauki ɗaya, sai Haris shi da wancan Maji daɗin gadon suma zasu ɗauki ɗaki ɗaya,” da ta ambaci maji daɗin gado hada harara ta wurga ma danish, ya lumshe idanuwanshi tamkar baiji me tace ba,

Azeeza tace”Saura ɗaki ɗaya ya rage, wa za’a bamawa” angel tace”Na daddyna ne idan Allah yasa yana araye, ko ince daddynmu” gaba ɗaya suka saki murmushin farin ciki, parveen tace”amma kina ganin daddynki zai so mu,” angel tace sosai ma, In ma daddyn nawa baya araye, zamu zauna wurin auntyna adama ne, Ko gidansu aunty aneelerh na, zasu ɗauki nauyin duk wani abu da zamu buƙata, Cin mu shan mu da suturarmu, kuma zamu yi rayuwar ƴanci, Zamu je inda muke so, Muje shan ice cream, muje cinema kallo, hada shopping mall zamu dinga zuwa kowa ya za6i abunda yake so, ” parveen na murmushi tace”Zamu dinga samun abinci akai akai”? Dariya angel tayi tare da cewa”Sau uku arana, za’a bamu breakfast, lunch and dinner, Idan ma kinga dama tsakar dare kika farga da yunwa zaki Iya zuwa kitchen ki girka abunda ranki yayi maki, ” Gaba ɗaya suka sanya ihu suna murna jin tace zasu Iya girki da kansu, Ga kuma abinci available, A lokacin jikin angel yayi mugun sanyi, ganin yadda suke ta farin Ciki, gani take kamar bazasu rayu ba, balle aje ga maganar fita daga Cikin wannan Kurman kurkukun ƙaddarar,

Batool tace”wlh angel baki ji irin daɗin da naji ba, sai naji dama ace yau mu fita daga kurkukun nan, muje gidanku, kinga shikenan mun rabu da giants, bazasu ƙara zuwa su ɗauki wani acikin mu ba, balle har su cutar dashi,”

Azeeza tace”Nima na ƙosa inga ranar da zamu fita daga prison ɗin nan, wlh Ina so inyi rayuwa irin wadda ki kayi tare da daddynki, ae kince mana zai so mu, muma zai maida mu kamar ya’yanshi, zai dinga zuwa damu yawo yakaimu wuraren da kika bamu labari ko”? Angel tace”Eh, kuma koda ace babu daddyna, akwai sauran dangina duk zasu so ku, kuma zasu gatanta ku kamar ya’yansu ku,” acikin zuciyarta tace”sai dai fitar ce keda wuya, bansan ya zamuyi ba, gidan kurkukun nan yafi ƙarfi na, sai dai bai fi ƙarfin mahaliccin mu ba,

Har dare Yayi suna fira Gwanin ban sha’awa, ta faranta musu sosai, Bayin Allah sun ƙwallafa rai da son yin irin rayuwar da tayi, wato rayuwar ƴan ci, yanzu a shirye suke da zarar sun samu hanyar fita zasu bita ne, hmmmmmm

(da su kayi wannan firar sai suka tuna mini da wani labari dana ta6a tsarawa acikin zuciyata mai suna)

*ANYA ZAMU KAI LABARI❓*

*Amma fa bashi bane next novel dina ba, Acikin middle step na Kurkukun ƙaddara zan faɗi sunan next novel dina amma wannan karan babu wanda zai fahimta idan na rubuta😂 ɗan adam da buri, In sha Allah idan Allah yakai mu da rai da lafiya, rayuwa ba tabbas*

*Read pls👇*

akwai wani jawabi da nake so inyi dangane da littafin kurkukun ƙaddara, i know ba kowa keda jumuri ba, wasu suna ƙagara akan suga anzo wuri kaza, shiyasa nace kwara in faɗa maku da bakina kada mu wahalar da shari’a, zaku ga antsaya iya cikin kurkukun zancen gaskiya atsarin labarin ba’a ta6a kowani part a takun farko Iya rayuwar prison ce, Kaf din part one! Daga wannan page din, na yau baza a ƙara ta6o wani 6angare ba, Iya rayuwar kurkuku ce till d end of takun farko, Ina fata zaku Yi haƙuri da juriyar karanta part one din nan, duk da ayanzu mun hau kan tudu saura gangara ya rage mana, Amma fa Labarin nan wlh ba yabon kai ba, Zaku yi matuƙar mamakin irin Baiwar dake acikinshi, Labarin na musamman ne, Zan iya cewa ya zarce abban sojoji saboda baza ata6a haɗa kurkukun kaddara da abban sojoji ba, Sarƙaƙiyar dake aciki ma ba ɗaya bace, komai ya haɗa story ɗin, Ni kaina da nake rubuta labarin ina mamakin yarda Allah ya sanya min shi acikin raina, cos da farko naji fargabar in rubutashi saboda akwai bantausayi sosai aciki, ga duk mai hankali idan ya karanta labarin zai fahimci cewa yana faruwa dagaske! Tabbas akwai yaran da ake rabasu da daginsu aware su daga Cikin mutane akaisu can wata uwa duniya Cikin dajin Allah, Ana azabtar dasu harma akashe su, Yasha faruwa a ƙasarmu🥺 Idan ya kasance matsafa ne Wannan abun fa kamar true life story ne, Sau nawa ake sadaukar da Mutane zuwa gidan matsafa don Cimma wani buri na neman duniya? kowa yasha jin wannan labarin ba baƙon abu bane awurinmu, basai na tsaya yin dogon jawabi ba, Allah dai yasa mu dace duniya da lahira, Ubangiji Allah ya kare mu daga sharrin zuciya, sharrin mutun da sharrin shaiɗan, da kuma ruɗun duniya, Allah ya tsare ahlinmu da kuma sauran ƴan uwanmu musulmai, Ƴan uwanmu waɗanda ke a hannun ƴan ta’adda da masu garkuwa Allah Ya ku6utar dasu🥺🙏 Tunasarwa adunga sanyasu acikin addu’a, wlh suna cikin matsanancin tashin hankali, su kaɗai suka san halin da suke ciki, Mu dake anan bamusan komai ba, shiyasa ba lallai bane adinga tunawa dasu akai akai ba, wasu sai an ta6a nasu na jininsu tukunna suke Ji ajikinsu, Amma a zahirin gaskiya ga duk mutum mai cikakken imani idan yaji irin azabtarwar da ake yi musu, sai ya matse Kwalla kuma zai dage da sanyasu cikin addu’arshi ne koda baisan su ba, musulmi ɗan uwan musulmi ne👌

(Kaɗan daga Cikin abubuwan da zasu faru next week da zamu shiga👇 za’a dawo da deeja, angel zata dura ta tagar nan zata shiga Cikin kurkukun, dakwai yiyuwar a rasa rai, basai na kama suna ba, wa’adin aikin tsohuwa zai qare! Jini xai zo ma ɗaya daga Cikin waɗanda basu ta6a yi ba)

*Domin neman ƙarin bayani 08103884440 ko 08169856268 Text on whatsapp only banda phone calls, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, Ga wanda ya shirya yin payment, zai iya yi mini magana, a ƙarshen wannan watan free pages zasu ƙare na Takun farko, zamu nutsa Cikin labari*

share fisabilillah❤👌

No comments