Breaking News

Kurkukun Kaddara 42-43

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*

_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E42-43


💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

“Sannu deeja ya jikin naki” ya yi maganar tare da buɗe murfin robar ruwan ya kwafa mata baki, Hannu bibbiyu tasa ta tallabe hannanyenshi dake a ruƙe da robar, saboda tsabar yadda take shan ruwa kana Iya jin sautin throat ɗinta kwat kwat! Har sai da yace mata tasha a hankali kada ta shaƙe, janye robar ta yi da hannunta alamar ta ƙoshi, Sai lokacin ta samu damar ƙare mashi kallo, su batool dake a zazzaune saman gadajensu suna yin fira, Ganin deeja ta farka yasa suka dawo bakin gadonta, wasu suka zauna wasu kuma suka tsaya atsaye, A hankali take binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, Ba ƙaramin daɗi taji ba, irin yadda suka nuna mata kulawa, sai dai a yayin da take kallonsu, wani irin tausayin kansu ne ya kamata, domin kuwa tasan ƙarshen su yana dab da zuwa, a yanzu bakowa tafi jimawa ba face waɗanda ba’a ta6a ɗauka acikinsu ba, musamman azeeza da tafi kowa rauni acikinsu, gata ƴar ƙarama duk da ba shekaru suka fita ba, amma babu alamun girma atattare da ita, saboda rashin tsawonta, idan suka miƙe tsaye ko kafaɗarsu bata kai ba, farat ɗaya ka kalleta sai ka yi hasashen shekararta Goma, saboda ƙarantar jikinta,

tana Cikin yin zancen zucin nan muryar batool ta katse ta da cewa”deeja me kike tunani muna ta yi maki magana tun ɗazu amma kin yi shiru baki ce komai ba, ina fata kina lapiya,” ajiyar zuciya ta ɗan sauke, still idonta na akan azeeza data zauna gefen gadonta ita dasu Yasmin, haɗa baki suka yi wurin yi mata ya jiki ta amsa musu da cewa”Alhamdulillah Jiki da sauƙi, Naji daɗi sosai da irin kulawar da kuka bani, Ina matuƙar alfahari da ku ƴan uwana nakaina” Murmushi suka saki gaba ɗayansu, ta mayar da idonta kan haris dake kallonta, ta lura da irin damuwar da ya yi akanta,

“Lokacin da aka tafi dani, haris ya iya Cin abinci kuwa”? da zolaya tayi maganar, gaba ɗaya suka yi dariya, yasmin tace”ae tunda aka ɗauke ki, ya gaza samun natsuwa, idan ya kwanta saman gadonshi idanuwanshi na fuskantar ceilling sai ya ɗauki tsawon lokaci bai tashi ba, wata’ƙil hoton fuskarki yake gani” Harara haris ya watsa ma yasmin da tayi maganar,

Kafin yace “Abunda ta faɗa ba ƙarya bane, Na damu dake sosai, Ko bacci nake yi sai nayi mafarkin ki, Bani kaɗai ba Kowa ya damu dake” duƙar dakai deeja ta yi hawaye suka cicciko idanuwanta, muryar azeeza ce ta ratsa kunnan ta”Sister deeja pls don’t cry, muna cikin farin cikin samun sauƙin ki, kada ki karya mana zuciyoyin mu,” azeeza na rufe baki, deeja ta karasa kifa kanta saman gwiwowin ƙafarta, sosai ta fashe da kuka, Sai faman lallashinta suke yi, ita bakomai ne yafi damunta ba, face tuna cewa wata rana fa dole wani ya mutu a cikin su, gashi sun shaƙu da juna, Allah kaɗai yasan raɗaɗin da zasu ji aranar da suka rasa wani acikin su,

Haris ne yace dasu”kubarta ta huta, kowa yaje yayi wanka, zan kula da ita” kasa tafiya suka yi har saida ya maimaita musu maganar tukunna suka miƙe, azeeza hada bubbuga ƙafarta tana faɗin”wai shi yacika takura, yana ganin kamar yafi kowa girma, shine zai wani kore su” murmushi haris ya saki batare da ya mayar mata da martanin ba, bayan sun bar bakin gadon deeja, suka nufi toilets domin yin wanka, hannunshi ɗaya ya ɗaura asaman bayan deeja yana ɗan bubbuga shi cikin sigar lallashi yake yi mata magana”its ok my lovely sis, kukan ya isa haka, ki daina pls kina ƙara ma kanki ciwo, kuma kina sanya mu cikin damuwa” Sai lokacin deeja ta ɗago da idanuwanta sunyi jawur da su, yadda kasan na mashayin giya, kallon shi kawai take yi kamar yarda shima yake kallonta, matsawa yaɗan yi dab da ita, ya sanya hannunshi ya ruƙo arm ɗinta tare da janyo da ita, ta kwanto saman kafaɗarshi, lallashinta yaci gaba da yi har saida ta daina yin kukan, Cikin sanyin murya tace”Danish baizo ya duba jiki na ba, naga fuskar kowa amma banda tashi, meyasa”? Girgiza kai haris ya ɗanyi dama saida ranshi ya bashi cewar saita yi magana akan danish, Yaji haushi da takaicin irin halin ko’in kulan da danish yake nuna musu, duk da yasan yana yi badan baya ƙaunarsu ba ne, Amma aduk lokacin da basu jin daɗi zaiyi wuya yaja su ajiki, har ƙwara Azeeza, itama ɗin ya lura don yana mata kallon ƙaramar halitta ne shiyasa yake damuwa da ita sosai, muryar deeja ce ta kuma katse shi”haris naji ka yi shiru? Ko dai danish bai yi farin ciki da dawowata ba ne?”da sauri yace”A’a, Ke ce baki ganshi ba, danish ya damu dake, ko adaren jiya da angel tazo tada mu daga bacci, hada shi muka shigo cikin toilet ɗin,” Deeja tace”Amma shi bai jani ajiki ba, kamar yadda kayi” runtse ido haris ya ɗanyi kafin ya buɗesu a hankali yace”ki yi haƙuri yanzu bacci yake yi, amma ina da tabbacin zuwa anjima idan ya farka zaizo da kanshi ya duba jikin ƴar uwarshi” ta6e baki ta ɗanyi tare da cewa”da kamar wuya” ruƙe hannunta haris yai acikin nashi yace”Akwai steak da muka ajiye maku tare da fruits in ɗauko maki ki ci” yayi mata maganar ne don ya kawar mata da zancen danish, ɗago da kanta ta ɗanyi daga saman kafaɗarshi tace”Anya zan iya ci, baki na babu daɗi, amma ina jin yunwa aciki na”

“Don’t worry ur self xan taimaka maki ki ci shi” yakai karshen maganar, tare da miƙewa daga saman gadonta, Ya juya ya nufi gadon batool dake gefen na Danish, yana kwance sai baccin shi yake sha hankali kwance, guntun tsoki haris yaja ji yake kamar yaje saman gadonshi ya shaƙon wuyanshi, Bayan ya ɗauko kwandon ƙarƙarshen gadon batool, Ya juya ya koma gefen gadon deeja, a tsakankaninsu ya ɗaura basket ɗin, Deeja sai kallon shi take yi don ba ƙaramin burgeta yake yi ba, saboda irin yarda yake nuna damuwarshi akanta,

“Angel ta yi bacci ne”? Yace”I don’t think so, Kinsan jiya ranta ya 6aci sosai, saboda tsohuwa tace bazata duba lafiyar jikin ki ba, har sai ta durƙusa agabanta ta roƙe ta, Inaga shiyasa ta lafe saman gado ta rufe ido, amma ba bacci take yi ba” juyawa deeja tayi tare da kallon gadon danish dana angel, duk suna kwance abunsu, kafin ta juyo da kanta tana fuskantar haris dake miƙo mata yankan Nama, buɗe baki tayi ya tura mata aciki, tasa hannu ta dafe tana Ci, sai da ta kammala taunewa tace”Haris, naji daɗin abunda angel tayi saboda Ni, farkon zuwanta prison din nan, Nayi tsammanin bata ƙaunata, duk da a lokacin Mune muka fara nuna mata ƙiyayya, Amma yanzu na gane kuskure na, domin kuwa angel tana matuƙar son mu sosai, kuma ita ɗin Alkhairi ce agare mu,” jinjina kai haris ya ɗanyi, tare da cewa”Nima na fahimci hakan, yanzu dai ki maida hankali ki ƙarasa cinye naman kisha fruit ɗin sai ki kwanta, ki ƙara hutawa” murmushi tasakar mashi, shima ya mayar mata da martani, A tsanake yaci gaba da bata Naman tana ci, bayan ta kammala tasha fruit ɗin ta kwanta saman mattress ɗin, Ya lullu6a mata bargo ajikinta, baisan ya zai ƙare dasu angel ba idan suka farka suna Jin yunwa, ganin deeja tana Ci yasa ya ƙara yankan nama Shida Cikin nasu Ya haɗa mata, kuma duka ta cinye shi, wanda ya rage acikin kwandon yanka shida ne na mutun ɗaya sai dai su raba uku uku ita da danish, Sai apple guda ɗaya, ayaba biyu, ɗauke basket ɗin yae daga saman gadon deeja, Yaje ya tura shi ƙarƙashin gadon batool, A lokacin duk sun fito daga wanka, ba ƙaramin daɗin jikinsu suka Ji ba, a tsakiyar ɗakin nasu suka hallara, Hannah ce ta shirya musu wasan da zasu Yi,

Angel dake kwance sautin hayaniyarsu duk ya cika mata kunnuwanta, pillow ta sanya saman kanta ta toshe kunnuwanta, Ƙasa ƙasa take jin hayaniyar ta ɗan ragu, wani irin baccine yayi awon gaba da ita batare da ta shirya yin shi ba, su batool sunsha wasansu, har sai da dare yayi hasken ɗakin ya ɗauke sannan kowa ya koma saman gadonshi ya kwanta,

Batare da sun kunna fitilun ɗakinsu ba, yayi duhu sosai, Har time ɗin bacci bai ɗauke su ba, fira suka soma yi a tsakaninsu kowa yana daga kwance saman gadon shi, Batool ce ta fara cewa”kun lura da angel duk yinin yau bata sauko daga saman gadonta ba” Haris yace”Kije ki tada ta mana” muryarta ƙasa ƙasa tace”So kake in jama kaina, ae tun ɗazu naso inje in lallashe ta, amma fargaba ta hana ni, kasan halinta, zata iya sauke fushinta akaina”Hanna tace”nima abunda ya hanani tunkararta kenan, kada in sha mari” Gaba ɗaya suka tuntsire da dariya, Javed yace”gaskiya banji daɗin abunda tsohuwa ta sanyata tayi ba, kawai don ba yadda zamuyi ne shiyasa muka tursasa mata akan ta durƙusa mata” Haris yace”nifa Haushin tsohuwa nake ji, don me zata ce dole sai angel ta durƙusa mata tukunna zata duba lafiyar deejan mu? Kenan koda ace mutuwa za ta yi bata iya duba ta ba, in har angel bata bi umarnin taba, sai dai tarasa ranta?Anya kuwa tsohuwa tana son mu? Eve tace”nima nafara kokwanto akanta, ae bata ƙaunar mu, shiyasa ran nan naƙi gaishe da ita,” eve na rufe baki hibba tace”kuma hada cewa wai angel ce babar mu, baku ji me tace ba ɗazu ba da muna a wurin toilets, ” waɗanda basu sani ba, suka tambayeta me tsohuwa tace, Nan hibba ta kwashe maganganun da su ka yi da ita, ta sanar musu, aikuwa sunsha dariya, batool tace”oh shiyasa naji tace aje akira babar mu tazo ta ɗauki ƴar ta, tsohuwa ta iya zolaya, gashi yau ta fusata mana Mamanmu,’ rubina tace”Abunda ta faɗa gaskiya ne, angel itace babar mu, saboda tafi kowa damuwa da mu, bazan ta6a manta irin wahalar da ku kasha ba, ita dake batool wurin yin jinyarmu lokacin da giants suka dawo damu, kun nuna mana ƙauna, muna matuƙar alfahari daku,’ azeeza tace”Da Batool da angel sune zasu zama iyayen mu idan muka fita daga Cikin prison ɗin nan, zasu bamu kyakkyawar kulawa” eve tace”Nifa ina tsoran ranar da zamu fita, mutanan dake awajen kurkukun nan zasu Iya su cutar damu, ko su kashe mu ma,” parveen tace”waya faɗa maki? Ba angel tace mana gidan daddynta zamu zauna ba, ina ruwan mu da wasu mutane, ae ba akansu zamu zauna ba, dangin angel ne zasu taimake mu”da ƙwarin gwiwa parveen tayi maganar, Haris dai sai dariya yake yi musu, jin irin wasiƙar jakin da suke saƙawa, wadda bazata ta6a zama gaskiya ba, azeeza tace”Na ƙosa Allah, zamu ji daɗin rayuwar mu, kowa zai sakata ya wala, muje inda muke so, ni dai kawai burina inga ga gidansu angel da kuma daddynta,”

“Amma fa ita kanta angel ɗin bata da tabbacin cewa daddyn nata yana araye koya mutu,” acewar Batool, azeeza tace”Ae ko baya araye akwai auntynta aneelerh, da mommynta adama tace duk danginta ne kuma zasu ɗaukin nauyin ɗawainiya damu” sai lokacin javed ya tsoma baki, muryarshi da alamun bacci yace”pls, surutun ya isa haka, kun takura mana, dare fa yayi sosai, yakamata kowa yaja baki yayi shiru ku kwanta ku yi bacci, kun zauna kuna ta tsara shirme da shiririta, kuda fita daga Cikin kurkukun nan sai dai ata mafarki, amma badai zahiri ba” a ƙule ya ƙarasa maganar, shi kanshi javed ɗin da yayi maganar ba ƙaramin buri yake dashi ba akan su fita, kawai dai baison suna ƙwallafa rai ne, tun da babu ƙopar da zasu Iya guduwa acikin kurkukun, tun da javed yai musu magana babu wanda ya kuma cewa wani abu, tuni bacci ya fara ɗaukarsu, mutun ɗaya ce bata runtsa ba, Jira take suyi nisa dayin bacci ko ta samu ta lalla6a taje ƙarƙashin gadon batool ta ɗauko Yankan naman da aka ajiye masu danish ta cinye, dama ta ƙware wurin iya satar ragowar abinci,

lokacin da parveen ta tabbatar da cewar sun nutsa Cikin baccin su, Cikin sanɗa ta sauko daga saman gadonta, duk da duhun dake akwai hakan bai hanata gano inda gadon batool ya ke ba, daga gefen gadon ta zaƙunna tare da zura hannu cikin ƙarƙashin gadon ta janyo kwandon, har wani lumshe idanuwanta take yi tana shaƙar ƙamshin naman, tana yunƙurin tsoma hannu da niyar ta ɗauki tsoka ɗaya, kwatsam taji an damƙi wuyan rigarta ta baya, A matuƙar tsorace ta wage baki zata fasa ƙara, yayi saurin sanya tafin hannunshi ya toshe mata baki, ta yadda bazata iya yin ihun ba, Saboda tsabar tsoratar da tayi har saida ƴan hanjin Cikinta suka kaɗa, Jikinta sai kerma yake yi, shegen tsoro ne da ita, duk a tunaninta ɗaya daga Cikin aljanun da tsohuwa ta basu labarin akwaisu agidan kurkukun ne yazo ya damƙeta, zazzaro idanuwanta tayi waje, jikinta ya ɗau zafi,

Cool voice ɗinshi ce ta ratsa kunnanta”its me, me kike yi agaban gadon batool? Ko kinzo ne ki sace mana steak ɗin mu da aka ajiye mana ne? wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke jin muryar danish, Ta harzuƙa sosai ashe shine ya firgitar da ita, tayi matuƙar yin mamakin taya akai ya iya ganinta Cikin duhu? Kuma har yasan cewa tazo satar naman da aka ajiye musu ne, bayan basu da masaniyar sun ajiye musu,

“Am talking to u, ki amsa mini, dama har yanzu baki daina bin abincin mutane kina satar musu ba”? Yawu ta haɗiya, tare da sanya hannayenta ta zame mashi hannunshi daya toshe mata baki dashi” ta juyo tana fuskantar inda yake atsaye, duhu ya hana ta ganshi dakyau,

Muryarta kamar zata fashe da kuka tace”Ae zuwa nayi inga idan ya lalace, in zubda, tunda naga tun ɗazu da safe aka ajiye maku amma baku ci ba” muryarshi asake yace”A cikin Cikin ki zaki zubda shi ko?” shiru tayi bata bashi amsa mishi ba,

“Maza ki wuce kije ki kwanta, tunkafin in yi wurgi dake” tana ƙunƙuni ta juya tana laluban hanya harta gano gadonta ta haye ta kwanta, zuciyarta duk ajagule, taso ace tacinye naman duka, ita uwar haɗama, kuma ba yunwa take ji ba,

Bayan tafiyar parveen, danish ya duƙa inda ta ajiye kwandon, yana ƙoƙarin ruƙe handle ɗin yaji an damƙi hannunshi, har sai da ya ɗan ji bugun zuciya, duk da bai iya gane wacece ba, amma yaji aikin shi cewa ANGEL ce, itama parveen ɗazu daya Canko sunanta, saboda yasan halinta ne, Ya farka yana Jin yunwa, ɗazu yaji haris yana cewa arage musu nasu naman shiyasa ya yi tunanin akwai saura, wannan dalilin ne yasa shi saukowa daga saman gadon shi, ya nufi gadon batool donya duba yaga idan an rage musu nasu, Yana tunkaro bakin gadon yaji motsin mutun, nan take ranshi ya bashi cewar itace, dama halinta ne,

Kusan atare zuciyoyinsu ke bugawa, gashi dai basu ganin juna dakyau, saboda duhun da ya mamaye idanuwansu, muryarshi na ɗan rawa ya ambaci sunanta”Angel” Muryarta a kausashe tace”Ni ce, sai me? Idan ma yankan naman nan kazo ka ɗauka sai dai ka haƙura kabar mini saboda nafi ka jin yunwa ” yadda tai maganar babu sassauci, dagaske yunwa take ji sosai, kamar ta cinye ƴan hanjin Cikinta, shima kuma yunwar yake ji, cikin sanyin murya yace”me zai hana mu ci atare, sai mu raba” kamar tana ganin shi tace”A’a, kawai dai ka haƙura kabar mini, saboda ba isata zaiyi ba”

“but why ɗazu baki ci ba? Da haris ya yi maki magana”? A harzuƙe tace”Saboda bana jin yunwa a lokacin yanzu kuma ina jinta, meyasa ma ka tambayeni? bata jira yabata amsa ba, ta kuma cewa”To kai meya hana ka cin naman ɗazu”? Tayi tambayar tana jiran jin amsarshi, sai da ya ɗanyi jim before yace”saboda ke, na damu da halin da kika shiga, naji kince ba zaki ci abinci ba, shiyasa nima naƙi ci, saboda bana so ki ji yunwar ke kaɗai,” sam bata ji ɗaɗin maganarshi ba, saima haushin shi data ƙara ji, muryarta ƙasa ƙasa tace”Nifa baka burgeni komai zaka Yi, ko son ganinka ma bana yi, wlh haushinka nake ji kamar in nannaushi fuskarka, ka 6ata mini rai sosai, Kana nuna ka damu dani wannan duk abanza ne, tun da baka iya nuna damuwarka akan deeja, da aka dawo da ita daren jiya, kowa yana tofa albarkacin bakinsa amma kai kaja baki kayi shiru amatsayinka na babba acikin mu, har haris ma yafi ka sanin yakamata,” Tana kai ƙarshen maganar, ta fusge kwandon daga hannunshi ta miƙe, cikin duhu ta nufi table dinsu ta ɗauko fitila ɗaya ta kunnata, A saman dining Carpet ta zauna, Ta ajiye kwandon agabanta, ita kuma fitilar ta ajiyeta a gefe, Zuciyarta duk ba daɗi, ita kanta bada son ranta take gaya mashi magana ba, daurewa kawai take yi,

Daga inda yake a zuƙunne bakin gadon batool yana hangenta, jikin shi yayi mugun yin sanyi, duk sai yaji ya rasa kuzarinshi, tamkar ya fashe da kuka haka yake ji, baya son angel tana yin fushi da shi, hatta faɗan da take yi mashi baya so, dan ba yadda zai da ita ne, kasa jurewa yai ya yunƙura ya miƙe ya nufi saman dining carpet ɗin, Yana ƙarasawa ya zauna tare da lanƙwashe ƙafafuwanshi Yayi zaman cin tuwo kamar yadda tayi, Ya kasance suna fuskantar juna ita dashi, Ko kallo bai ishe ta ba, bakinta acunkushe da yankar naman data tura sai tauna take yi, duk in suka haɗa ido saita jefa mashi harara, bawan Allah miyan sai tsinkewa yake yi,

yana so ya ɗauki naman yaci, sai dai ya kasa saboda gudun faɗan ta, Muryarshi arauna ce yace”pls angel, ki bari na ɗauka naci nima, koda fruit ɗinne, am serious yunwa nake ji” sai da ta kammala taunar naman dake abakinta tukunna tace”baka da ƙarfin da zaka ƙwata ne? Wai kai wani irin namiji ne? Mace kake marairaice ma fuska? duƙar da idanuwanshi ƙasa ya yi batare daya tanka mata ba, dogon tsoki taja, takai hannu ta ƙara ɗaukar yankan naman ta tura abaki tana ci, Sai da ya rage saura biyu, tace mashi”in kaga dama ka ɗauka kaci,” tayi maganar tana daukar fruits din ciki tana sha” muryarshi na rawa yace”bazan ci ba, saboda me zaki dinga yi mini faɗa? Nifa haka rayuwata take, ki ƙyale ni mana, bana jin daɗin yadda kike kushe ni,” Ranshi amatuƙar 6ace ya miƙe, Ya juya ya nufi gadonshi ya haye ya kwanta,

Sai bayan daya tafi, Jikinta yayi sanyi, daƙyar ta iya shan fruits ɗin, idanuwanta suka Cicciko tab kwalla, yunƙura ta yi tare da miƙewa ta ɗan ranƙwafa ta ɗauki fitilar ahannu ɗaya, yayin da ɗayan hannun kuma ta ruƙe handle na kwandon, wurin gadon shi ta nufa, daga gefe ta ajiye fitilar tare da kwandon, idanuwanta na akan gefen fuskarshi, ya ƙanƙame pillow aƙirjinshi, jikin shi har wani kerma yake yi saboda tsabar 6acin ran da yake ciki, Zuciyarta ce ta dinga tunzurata akan kada ta kuskura tace zata lallashe shi ta ƙyale shi wata’kil yayi hankali, gani take ma idan taci gaba da lallashin shi zai ƙara lalacewa ne, ƙwara ta koya mishi hankali, jinjina kai ta ɗanyi alamar gamsuwa da shawarar da zuciyarta ta bata,

“Idan kaga dama ka tashi ka ɗauki naman kaci, idan kuma baka ci ba, matsalarka ce” Takarasa maganar tare da watsa hannayenta, Irin bata damu din nan ba, wuce wa tayi zawa gaban table ta ƙara ɗauko wata fitilar ta kunna ta, kaitsaye ta nufi gadon deeja, domin ta yi mata yaji ƙi, tun ɗazu da safe take ta son taje wurinta amma damuwa ta hanata, zuciyarta tayi mata nauyi a ƙirjinta, shiyasa ta tagaza tashi daga saman gadon ta yi kwanciyarta,

Daga gefen gadon deeja ta zauna, tana haska fuskarta da fitilar hannunta, da alama tayi nisa acikin baccinta, har cikin zuciyarta taji daɗin yadda deeja ta samu sauƙi, don jiyan nan zuciyarta ba ƙaramar karaya tayi ba, harta fara fidda ran da zata rayu, sai gashi Allah ya taimake su, deeja ta wartsake, a hankali ta ɗaura yatsun hannunta saman fuskar deeja ta ɗan shafata, kafin ta soma karanto addu’o’i tana tottofa mata,

“Bazan tashe ki daga bacci ba My lovely sis, gobe in sha Allah, idan kika farka daga bacci zanzo in yi maki ya jiki, Allah ya ƙara maki Lafiya, ” janye hannunta tayi daga kan fuskar deeja ta mayar dashi saman sumar kanta, dake a hargitse duk ta yamutse babu gyara, aranta ta ayyana cewa, idan deeja ta samu lafiya sosai jikinta yae kyau zata gyara mata gashin kanta, ta kuma yi mata kalaba, kalar tasu azeeza, sauƙin ma ita gashin nata bai kai nasu tsayi da yawa ba, ya dai sauko har saman kafaɗarta, baƙi wulik, kamar na ɗiyar roba, Ta jima zaune tana kallon deeja, daga bisani ta miƙe hannunta ruƙe da fitilar tabi gadon kowannan su ta tottofesu da addu’o’i, lokacin da ta dawo zata wuce gadonta, Sai da ta saci kallon shimfiɗar danish, Still bai ɗauki naman shi yaci ba, duk sai taji ba daɗi, Duk yinin yau baici komai ba, ko ruwa bata tunanin yasha mutun sai kace aljani, anya kuwa zata biye mashi, kodai taje ta lallashe shi ya tashi yaci?

A ƙasan gadonta ta ajiye fitilar hannunta, wurin ya ɗanyi haske hada ƙarin ɗayar fitilar dake a kusa da gadon danish,

daga Gefen gadonta ta zauna tana kallon bayanshi, still babu alamun yayi bacci, yatsun ƙafarshi basu daina yin kerma ba, Zuciyar imani ce ta zo mata, ta miƙe taku ɗaya biyu, ta zuƙunna abankin gadon shi, Cikin sanyin murya ta ambaci sunanshi”Danish” shiru bai amsa mata ba,

“Fushi kake yi da ni, saboda kawai na faɗi gaskiya,” ta ɗanyi maganar tana hararar bayanshi,

“Its ok komai ya wuce, bazan ƙara ba, pls ka tashi ka ci naman nan kasha fruit din idan ma baka Iya Ci da hannunka sai in baka abaki, ba wani abu bane, ni kawai bana so ne ka kwana da yunwa, dama ka faɗa mini cewa saboda ni ne baka Ci abinci ba, To yanzu ni naci kaima saika tashi kaci, ko ba haka ba My man”? Bakinta ƙumshe da dariya tayi maganar, babu alamun zai tanka mata,

Cikin zolaya tace”dama ance mutun mai haƙuri bai iya zuciya ba, yau na tabbatar da hakan, danish yayi fushi da angelar shi,” babu irin lallashin da bata yi mashi ba, amma yaƙi tanka mata a ƙarshe ranta ya 6aci a fusace tace”Kai ni fa ko daddyna bana zama in lallashe shi kamar yadda nake yi maka, don ma ka samu ina kula ka shine kake wani shamin ƙamshi, to shikenan, Nasan me zanyi, Zanje ne kawai in dura tagar nan ta cikin toilet, kome zai faru ya faru, ” tana kai ƙarshen maganar, ta miƙe da sauri ta ɗauki fitilar dage ƙasa gefen gadonshi, Ta nufi sashen makewayinsu har ta kusa kaiwa bakin ƙopar shiga, Kamar walƙiya taganshi agabanta tsaye yana faman lumshe idanuwanshi, doguwar sumar kanshi duk ta yamutse, Tsananin mamaki ne ya kamata, da sauri ta ɗan juya ta kalli gadon shi donta tabbatar idan shine dagaske, bata ga kowa ba, sai taga kamar 6acewa ya yi daga saman gadonshi ya faɗo gabanta,

Kafin ta yi mashi magana ya riga ta cewa”zan ci shi kenan ko”? Ɗaga kai tayi alamar eh, ya ruko hannunta acikin nashi yaja ta suka koma Cikin ɗakin, a gefen gadonshi ya zauna, Suna fuskantar juna shi da angel, tana azaune saman nata gadon, ta tsareshi da ido tana jiranshi ya kammala Ci, kwandon Ya dauka ya ɗaura shi saman laps dinshi, A tsanake ya kai hannu ciki ya ɗauki yankan nama yana ci, Bayan ya gama taune shi duka, Ya ɗauki sauran 6allin apple data rage mashi yakai baki yana gatsa, jefi jefi yakan ɗan ɗago ya saci kallonta, Ko uwarsa Albarka yadda ta tsare shi da ido,

“Zaka sha ruwa”? Ɗaga mata kai yayi alamar eh, ta miƙe tsaye sai da tafara ɗaukar kwandon, Kafin ta nufi gadon batool, A ƙarƙashi ta tura kwandon ta ɗauko mishi robar ruwa guda ɗaya, Ta dawo ta miƙa mashi, yasa hannu ya kar6a ta koma saman gadonta ta kwanta tana facing ɗinshi, Buɗe murfin bottle ɗin yayi tare da kwafata abakin sa, kusan rabi ya sha, bayan ya gama shan ruwan, ya maida murfin bottle ɗin ya ajiye ta daga ƙasa, Sannan ya gyara kwanciyarshi, suna fuskantar juna, kallan ƙurulla suka shiga yi ma junansu, bakomai take tunawa ba, face yadda ya sha gabanta ɗazu saboda tace zata dura tagar nan, tarasa gane dalilin dayasa baison tasan komai dangane da kurkukun, Ta fahimci cewa danish yasan komai, shiyasa yake lalla6ata don kada ta gani taja musu wata matsalar, Abunda kuma bazai ta6a yiyiyuwa bane,

Da wannan zancen zucin bacci yayi awon gaba da ita, shima danish ɗin tuni bacci ya ɗauke shi,

A washe garin ranar, kafin kowa ya farka daga bacci, batool ce tafara tashi tana miƙa tare da Yin hamma, ta sauko daga saman gadonta, cikin sauri ta nufi toilet saboda wani irin fitsari daya matseta, Ya ɗaure mata mararta, hada ɗan gudunta wurin shiga toilet, batare data yi locking door din ba, hannayenta ta sanya wurin zame wandon jikinta ta zuƙunna tana Yin shi, bayan ta kammala ta kunna fanfo ta yi tsarki, Ajiyar zuciya ta sauke tare da miƙewa tsaye tana gyara wandon Jikinta, kafin ta nufi ƙopar fita, harta miƙa hannu zata buɗe sai ga azeeza ta faɗo cikin toilet ɗin. jikinta sai kerma yake yi, batool tace”lafiyarki kuwa kika faɗo mini Cikin toilet ba neman excuse? Batare da azeeza ta kalli batool ba tace”ke dallah fitsari ne ya matse ni, ni ina nasan da mutun a ciki, ” tana faɗin hakan ta wuce cikin toilet ɗin, girgiza kai batool tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta fito daga waje, taja mata ƙopar ta rufe, tana ƙoƙarin shiga cikin ɗakinsu, Tajiyo muryar azeeza daga Cikin toilet tana kwala mata kira na fitar hayyaci, da sauri ta koma ta nufi ƙopar toilet ɗin, Fitowa daga Ciki azeeza tayi idanuwanta azazzare hannunta dafe da saitin ƙirjinta tace”Batool, naga ɗigon jini a cikin toilet wurin magudaji ke ce kika zubda shi”? Wata irin mummunar faɗuwar gaba ce tazo ma batool, nan da nan walwalar fuskarta ta ɗauke, amatuƙar ruɗe tace”Bani bace, sai dai ko kece da kika shiga ciki yanzu, saboda ni har na fito banga wani ɗigon jini ba”aruɗe azeeza tace”Wlh bani bace, Ae ni yanzu na shiga, Ko tsugunnawa ban kaiga yi ba, naga jinin, hakan na nufin daga Jikin ki yake, ” a tsiwace batool tace”Nifa bani bace na zubda shi ba, wlh bani bace” tuni hawaye sun wanke fuskarta, Azeeza ta fashe da kuka tana faɗin”Wlh kece, Ae ni ban kaiga yin fitsarin ba, Ki yadda ko karki yadda naki ne daga Jikin ki ya fito,” shaƙo wuyan rigar azeeza batool tayi da hannunta biyu ta jijiigata, cikin shessheƙar kuka tace”You’re lying to me azeeza, Kina so ki ƙala min sharri ne, Kiji tsoron Allah, ki faɗi gaskiya,” Hankalinsu yayi matuƙar tashi, Kowa Ya haƙiƙance Yana ƙoƙarin kare kanshi,

*Jinin wanene AZEEZA OR BATOOL ❓❓❓*

(Mu haɗu next page, shin kuna son ayi maku update gobe ko abari sai friday da bana yin update ku samu long page? ina son jin ra’ayin ku,

*Assalamu alaikum Barka da warhaka, Ga masu son cigaba daKaranta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, 5 days a week, Inka biya za’ayi adding naka a paid group kuma za’a sanyaka a comment section, Sa’annan Ba’a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*

*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*

*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*

*3196407426*
Bature Hafsat Muhammad
First bank

*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (0816985 6268) ko kuma ta (08103884440)*

*Kada Ku bari A baku labari💃 Salon na daban ne🤩*

No comments