Breaking News

Kurkukun Kaddara 50-51

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*


_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E50-51 free pages

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

Kaitsaye idanuwansu suka sauka akan sabbin gadajen da aka jera a cikin ɗakin nasu, gaba ɗaya suka zazzare idanuwansu saboda tsabar mamaki duk suka bi suka ruɗe, Sun saki baki suna kallon Ikon Allah saboda ba su yi tsammanin zasu yi arba da wani baƙon abu a cikin ɗakin su ba, da mamaki akan fuskar parveen Tace”Kuna ganin abunda nake gani kuwa? ko dai idanuwana ne suke nuna min ba dai dai ba”? Azeeza tace”Ae duk mun gani sabbin gadaje ne har kusan goma sha biyar tare da Akwatuna Biyu, ko a ina aka same su”? Danish ne ya basu amsa da cewa Ɗazu da safe kuna bacci giants suka kawo su, akwai ma kayan amfani da aka sanya mana a toilets” deeja tace”hakan na nufin zamu kar6i baƙuncin wasu prisoners ɗin”? Tai tambayar fuskarta babu walwala, domin kuwa ba abun farin ciki bane agare su, da duk wani mai hankali ba zai so wani bawa ya ɗanɗani irin rayuwar ƙuncin da suke yi ba.

“Innalallahi wa’inna ilaihirraji’un! Ni dai har ga Allah bana farin ciki da zuwan waɗannan Sabbin prisoners ɗin, Saboda bana so suma su ɗanɗani irin rayuwar da muke Yi acikin kurkukun nan” Deeja ce tai maganar, Haris yace”ni kaina bana son mu ƙara yawa, muna fama da kanmu xa’a ƙaro mana wani ciwon kan” hibba tace” ni babban baƙin ciki na, Mu da muke fatan wata rana mubar kurkukun nan, sai gashi ana ƙoƙarin kawo mana wasu har mutum goma sha biyar zamu ƙara cunkushewa, tashin hankali kuma zai ƙaru” hannah tace mu je mu duba gadajen ni sunyi mini kyau, Dama mu ma a canza mana sababbin,” wani kallon harara deeja tai mata “Wato ke ta gado kike yi, to Allah yasa acanza miki gadon kiyi ta zama cikin prison ɗin, mu kuma Allah ya bamu sa’ar fita daga cikinsa” hanna tana ƴar dariya tace ba amin ba, Aniyarki tabi ki,”

Agaban gadajen suka tsaitsaya cirko cirko suna ƙare musu kallo, Sabbi gal dasu sunyi matuƙar yin kyau, Azeeza da parveen hada ƙoƙarin hawa saman wasu daga Cikinsu suna faɗin Bari su ɗana kafin baƙi su ƙaraso, azeeza tace ita yau ma asaman sabon gado xata kwana, suma sauran su ka ce duk anan zasu kwana su sha lagwada,

sai da suka gama kallon gadajen kafin suka koma kan akwatunan suna kallonsu tare da Floor laps ɗin da aka ajiye musu, ba ƙaramin daɗi suka ji ba, dama fitilun dake gare su sunyi kaɗan, Idan dare yayi sai dai mutun yai ta yawo da fitila zuwa toilet, amma yanzu sun yanke shawarar zasu ɗauki ƙananun fitilun guda uku, su ajiye su a kowani toilet, don su sawwaƙawa kansu.

a cikinsu an rasa wanda zai buɗe boxes ɗin nan, duk sunyi tsammanin Ba mallakin su bane, na sabbin prisoners ne da za’a kawo shiyasa basu ta6a su ba, saima suka kawar dasu zuwa bakin gadajen, bayan sun gama da ɗaki, eve tace”su je su duba toilets suga sabbin kayan da aka sanya musu, Parveen ta bubbuga ƙafa tare da cewa”Mu fara Cin abinci tukunna idan ku ba ku jin yunwa ni ina ji” sai da ta yi maganar suka tuna da cikinsu, hankalinsu gaba ɗaya yana akan Kayan da aka kawo musu,

Atare suka nufi dining carpet ɗinsu suka zazzauna, Kowa ya natsu zasu fara Cin abinci,

Duk wannan abun dake faruwa angel da danish suna kishingiɗe saman gadajensu, sun Juyawa juna baya babu mai fuskantar wani, kowa da abunda yake saƙawa acikin zuciyarshi, ita dai damuwarta batool ɗinta, ko awani hali take ciki? Fatanta Allah yasa maganar da danish ya faɗa mata akan furen nan ta zama gaskiya,

Bayan su parveeen sun kammala Cin abinci. Sauran da suka rage ma angel da danish, Haris yace su je su ɗauko kwandon batool a kwashe musu nasu aciki, Nan fa duk jikinsu yae sanyi tunawa da batool ɗinsu, duk da dama tana acikin ransu ba yadda za su yi ne, tsakaninsu da ita addu’a ce kawai.

Hanna ce taje ta ɗauko kwandon batool dake a kusa da gadon danish Kifin da suka ajiye mishi tun jiya duk ya bushe jikinshi, hada ƴar rabin gwandar da baici ba, nuna musu kwandon tai tare da cewa”Fried fish din ma ya lalace bari naje na zubar dashi, in wanko basket din sai asanya musu abincin aciki…..” tunkan ta ƙarasa maganar parveen tai wuf ta sanya hannu ta kar6e kwandon tana faɗin”Inji wa yace maki ya lalace, bani nan ki gani, yanzu nan zan sanya shi a hanya…” Murmushi suka saki gaba ɗayan su yayin da suke kallonta, A ƙasa ta zuƙunna ta ajiye kwandon tare da kai hannu Ciki tana tatta6a Jikin kifin, azeeza tace”amma parveen baki da hankali, tun jiya fa yake a buɗe cututtuka duk sun hau jikin shi a haka zaki ce? Salon Cikin ki ya 6aci,” Harara parveen ta watsa mata tare da cewa”Bai shafe ki ba ae cikina ne ba na ki ba” duk yadda suka so su hanata Cin fried fish din nan taƙi ji, tai kunnan uwar shegu dasu, Zama tayi na musamman tacinye shi tass bayan ta gama da kanta taje toilet ta wanko kwandon tass ta shigo dashi Cikin ɗakin ta miƙa ma Hanna kwandon, tasa hannu ta kar6a ta zuƙunna gaban farantin da niyar ta ɗibar musu wanda suka rage musu, Muryar Angel ta dakatar da ita,

“Kada ki haɗa mini abinci dashi, Ki ware mini nawa daban” idanuwanta arufe tai maganar, batare data motsa daga kwancen da take asaman gadonta ba, Haris yace ki ɗibar mata nata ki je ki taimaka mata taci, Ni kuma zan kaima Danish nashi, ta amsa mashi da toh,

Kafin marece yayi saida suka shiga cikin kowani toilet suka dudduba sabbin kayan da aka sanya musu, bakomai yafi burgesu ba face Hair gel kodan sabo da gashin kansu, sun samu na gyara shi, basu fara amfani dasu aranar ba, saboda sunfi so sai angel ta samu sauƙi ta taimaka masu wurin gyarawa.

A daren ranar Saman Sababbin gadajen nan kowannansu ya kwanta, in ka cire mutun biyun nan, Angel da kuma danish suna asaman gadajen su, jiki duk ba daɗi da ga ita har shi, ko wanka sun kasa tashi su yi, room ɗinsu yayi wani irin haske tamkar da rana saboda sabbin fitilun nan da suka kunna hasken su ya gauraye ko’ina gwanin ban sha’awa, Cikin nishaɗi suke ta wasa da pillows, Idan wannan ya jefa ma wannan sai shima yaɗauko pillow Ya jefa ma na kusa dashi, yadda kasan basu da wata damuwa bayin Allah, Angel tana jiyo hayaniyar su suna yin fira bayan sun gama wasa da pillown deeja tace”Nifa gani nake kamar zamu dawwama acikin kurkukun nan, tunda ga wasu ma za’a ƙaro mana” Parveen tace”ai kwara su zo suma su ɗanɗani irin zaman da muke yi, su ji in akwai daɗi,” Azeeza tace muguwa parveen yanzu har wasu kike yi ma fatan suyi irin rayuwar da muke yi”? Parveen tana dariya tace”Nifa na faɗi hakanne kodan mu samu a ƙyale mu adaina ɗaukarmu mu tsaffin prisoners, su kuma sabbin sai acigaba da ɗaukarsu, Kunga mun hutu ko ba haka ba,’

Murmushi angel ta ɗan saki, yayin da idanuwanta suke fuskantar ceilling, ta ɗan ɗaga murya tana faɗin”parveen maganar da ki kayi sam ba ta yi mini daɗi ba bai kamata kina yi musu mummunan fata ba, tun kafin zuwansu ma, Ni tausayinsu ma nake ji, su da basu san komai ba, wlh ko maƙiyina bana yi mishi fatan shiga wannan kurkukun ƙaddarar, ballanta su da za’a kawo mana, musamman in ya kasance daga waje za’a kawo su, Ba ƴan asalin cikin kurkukun bane”

jin wannan magnar ta angel yasa parveen tace”patient Ashe baki yi bacci ba, da ace nasan idonki biyu da ban furtata ba,” dariya su kayi gaba ɗayansu, Angel tace”Oh, wato ni sarkin yin wa’azi ko? Kiji tsoron Allah parveen, Nidai komai na faɗi inayi ne don in taimaka muku wurin gyara rayuwarku,” hanna tace”ai kina ƙoƙari kuma muna jin dadi sosai, muna fatan Allah yabarmu tare dake har bada, har mu shiga aljanna,” murmushi angel ta ɗan saki, tare da yunƙurawa ta miƙe zaune saman gadonta ta jingina bayanta jikin bango, ta wutsiyar idonta take satar kallon danish, Ya rungume pillow sai bacci yake yi, aranta tace shi ko tsamin jikinshi baiji, ” can kuma ta ta6e baki tana faɗin to ni meye ruwana dashi, ” ta ambaci hakan tare da jan tsoki, Muryar Javed ta jiyo daga inda take fuskantarsu Yana ta yi musu faɗa akan su yi musu shiru sun hanasu runtsawa, su kuma sun dage sai zuba suke yi kamar kanyar da bata da daɗi,

kasa kunne ta yi tana sauraron firar da suke Yi, sai taji akan gidan daddynta su ke magana, lamarin ya ɗan bata mamaki, jin parveen tana faɗin ai wlh idan suka gudu daga Cikin kurkukun suka koma gidansu angel ita acikin kitchen zata dinga kwana, ko dan ta dinga dafa abunda take so”

Sakin baki angel tai tana sauraron ikon Allah, aranta tace wato ita parveen burinta na duniya shine abinci, taci abinci bata gajiya, mai iya rainonta sai manomi, amma wannan in baka da ƙarfin jari saita naƙasa ka,” bata kammala zancen zucin nata ba, ta jiyo muryar azeeza tana faɗin”Ni dai ba ruwana da wani abinci, Idan Allah yasa muka bar kurkukun nan muka koma gidansu angel, A ɗakin daddynta zan dinga kwanta, nima ya rungumeni kamar yadda yake yi ma angel suna kwana tare,” Haris yace”Sannu uwar son banza, menene alaƙarki dashi da har xaki kwana a ɗakinshi Ya rungume ki,” zum6ura baki tae ashagwa6e ta bashi amsa da cewa”Ae ta faɗa mana cewa, Daddynta yana son ƴa’ƴa, Kaga kenan muma zamu zama kamar angel awurinshi” naufal yace”Kuna yaudarar kan ku dayawa, ku ɗan sarara mana, kada wata rana zuciyarku ta karaya, a garin sanyawa rai abunda bazai ta6a yiyuwa ba,”

Kafin wani ya kuma cewa wani abu angel tace”Inji wa ya faɗa maka cewa bazai ta6a yiwuwa ba? Ƙarancin imanin ku shine zaisa mu dawwama acikin kurkukun nan, bai kamata kuna sage musu gwiwa ba, Idan Allah yaso a yau ɗin nan zamu iya barin kurkukun nan wannan ba abun mamaki bane, amma nasan zaiyi wuya ku yarda da maganata har sai ranar da Allah yasa muka ku6uta inda rai da lafiya, tukunna zaku tuna da wannan maganar dana faɗa maku!!!”

Haris yace”kada ki damu, Ni zan tuna maki, wannan ba wani abu bane” yana magana yana dariya kamar wani zautacce, Ya raina maganarta, ba ƙaramin haushi taji ba, tadai yi shiru ne ta ƙyale shi saboda sanin irin jahilcin dake ɗawainiya dashi.

Lokacin da bacci yai awon gaba dasu ita kaɗai ta rage bata kwanta ba, kamar yadda tai alƙawarin xata dinga raba dare biyu domin ta samu damar yin addu’o’inta, tana Cikin yin addu’oin hawaye ta ko’ina akan fuskarta, danish ya farka ya ɗan miƙe xaune saman gadonshi yana kallonta, ganin tana ƙoƙarin juyowa ta kalli inda yake yasa shi yin saurin kawar da kanshi gefe, gudun kada ya sa6a alƙawarin daya ɗaukar mata, saukowa yai daga saman bed din shi Ya janyo bargonshi Ya nufi Cikin toilet dashi, Tana ta bin bayan shi da kallo Cike da mamakin me zai yi a irin wannan lokacin, tsawon mintuna sai gashi ya shigo ɗakin chest ɗin shi ɗaure da bargon, Alamar ya wanke uniform ɗin, Sun ishe shi da tsami, Sai lokacin ta tuna da yadda jikinta yake, ta dage tana ta yin addu’o’i batare data tsarkake shi ba, Yanke shawarar zuwa toilet din tayi don ta wanke kayanta ta samu tayi wanka, tana ƙoƙarin saukowa daga saman gadon ƙasusuwan jikinta suka rurruƙe har wani sauti suke badawa ƙas! ƙaƙas!! wani irin raɗaɗi taji ajikinta, ta ɗan cije la66anta tana faman ambaton wash Allah na, duk akan kunnan danish dake zaune saman gadonshi, Ya lumshe idanuwanshi, Tun da yai wanka sai yaji daɗin jikinshi, wata irin ni’ima ta saukar mishi, yaso ace suna shiri da juna daya taimaka mata wurin yin tafiya don ya fahimci cewa so take itama ta yi wankan,

Ba yadda ta iya dole ta haƙura da yin wankan tayi zamanta tsakiyar gadon, a haka baccin yai awon gaba dasu,

A kwana atashi ba wuya wurin Allah, Yau tsawon Sati biyu kenan ba’a dawo musu da batool ba, babu ita babu alamarta, Kullum sai sun sanya ran zasu ga an shigo da ita amma sai suji shiru, hatta sababbin prisoners da suke tsammanin za’a kawo musu har yau ba azo dasu ba, rashin dawo musu da batool yafi komai ɗaga musu da hankali, ganin sun sanya damuwa sosai yasa angel ta faɗa musu maganar da suka ta6a yi ita da batool, a inda take ce mata, tana so su haɗa hannu wurin sama ma junan su farin Ciki koda kuwa babu wani acikinsu, wannan maganar tayi matuƙar karya musu zuciya, domin kuwa ranar da angel ta faɗa musu ita, kusan kwana su ka yi a zaune suna jimamin rashin ta, sunyi matuƙar yin kewar ƴan uwarsu fiye da tunanin mai tunani, a ƙarshe da suka rasa abunyi sai suka koma suna biye ma angel, atare da ita suka zuwa toilet wurin tukunyar fulawar nan don suga awani hali batool take aciki, tun da ta basu labarin Abunda danish ya faɗa mata na cewa batool ɗinsu ce a jikin Jan furen nan shi kuma koren Na daddynta ne, abun ka ga masu ƙarancin hankali ga kuma ƙuruciyar dake ɗawainiya dasu duk sai suka yarda da zancen danish, a rana sau uku suke zuwa wurin furannin nan domin su basu ruwa, da safe da rana da daddare, wani lokacin har tsakar dare suna zuwa duba furen suga a wani yanayi yake, idan suka samu furen batool yana tsastsafo da ruwa ajikinshi, haka zasu zauna sunata kuka suna lallashin furen amatsayin batool suna yi mashi magiya akan yayi haƙuri ya daina kuka, Suna atare dashi, Idan kuma suka samu furen ya kwanta cikin ƙasar dake a ruƙe dashi, sai su yi ta jin daɗi suna faɗin batool bacci take yi, kada su takura mata su tafi su barta ta huta, duk wannan haukan da suke yi danish yana kallonsu, Ya rasa gane wani irin kaine dasu, shi yayi abu don ya faranta ma angel rai, su kuma sun ɗauka dagaske ne, gashi har suna ƙoƙarin zautar da kansu akan furennin bogi.

A kowace rana idan dare yai kafin su kwanta bacci sai sunyi ma batool addu’a Akan Allah ya kare musu ita aduk inda take, tsawon kwanakin nan sunƙi sakewa da Danish suna atare dashi ne, badan sun yarda dashi ba, musamman angel ko kallo bai haɗa ta da shi, bawan Allah duk ya shiga damuwa daurewa kawai yake yi, amma rashin tanka mashi da take yi ba ƙaramin illata zuciyarshi take yi ba, yanzu takai ga ko wasa suke yi da zarar ya tsoma baki, to zata zame hannunta ne tace ta fasa, ƙiri ƙiri ta guje shi ta maida shi abokin gabanta, a ƙarshe daya gaji da irin wulaƙancin da take yi mishi, aikuwa ya janye jikin shi daga gare ta, Ya nisanta kanshi da duk wani abu da zai haɗa shi da ita, hakan ba ƙaramin takurata yai ba, itafa tafi son yai ta binta tana yakice shi, sai gashi reshe na neman ya juye da mujiya.

*PRISONERS❤*

A wata rana suna kwakkwance saman sabbin gadajen da suka gaje na baƙin prisoners sai sharar baccinsu suke yi, babu wanda ya farka acikin su, Gari tuni Ya jima da wayewa, A wannan lokacin ne motsun buɗe dakin tsohuwa Ya karaɗe Cikin ɗakin, A hankali ta buɗe ƙopar Hannunta ruƙe da sanda kamar kullum, fuskarta babu walwala, tsufanta ya fito sosai, jikinta na sanye Cikin rigar ta, Ta gado Launin Ja, Cigaba da dogara sandar tayi yayin da take tun karar Cikin dakin, Tayi mamakin ganinsu kwance saman sabbin gadajen da aka kawo maimakon ta gansu A saman nasu beds ɗin, Murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, a fili tace”Zaman Prison yayi maku daɗi Jikokina, Kuna hutawarku Cikin walwala, Sai dai kun manta da Tsohuwa Tamira,”

Sai da tabi kowani gado ɗaya bayan ɗaya tana binsu da kallo, tun daga kan gadon haris da deeja, zuwa nasu Javed da rubina, a bakin gadon da angel take kwance ta ɗan dakata tana kallonta, ganin wani irin sabon salon kwanciya, ta wawware ƙafafuwanta, har sun sauko daga ƙasan gadon, gashin kanta duk ya tarwatse ya barbazo saman mattress ɗinta, fuskar tsohuwa asake tace”Unaisah mutuniyata sarkin tsiwa Ina matuƙar yinki,” tana ambaton hakan taɗan ja da baya kaɗan, ta daddage ta buga sandar hannunta a ƙasa, Nan take ta bada wani irin sauti kamar fashewar bomb, agigice suka farka suna faman zazzare idanuwansu, saboda tsabar ruɗu parveen da rubina suka sauko daga saman gadajensu, Da gudun gaske suka nufi toilet zasu shige su 6oye, azeeza da tafi kowa jin tsoro tuni ta jima da shigewa ƙarƙashin gadonta, tsohuwa ta rikitar dasu, babu wanda ya lura da ita, sai da suka gama tsorata, Tukunna Ta soma Yi musu gyaran murya, Nan fa Hankalin kowa Ya dawo kanta, sai faman mutsustsuka idanuwansu suke yi, Na cikin toilet da suka 6oye sai gasu sun fito hannunsu ruƙe cikin na juna, azeeza ta leƙo daga ƙarƙashin gado don ta ga wanene yai musu gyaran murya tana yin tozali da fuskar tsohuwa sai gata ta fito tana faman sauke ajiyar zuciya,

Da alama ta nishaɗantu da abunda ta yi musu, Sai tiƙar dariya take Yi, su kuwa sai faman sauke ajiyar zuciya suke yi hada masu dafe ƙirjinsu, hanna tace”Tsohuwa kin bamu tsoro, ƙiris ya rage in saki fitsari a wando,”

Dakatawa ta ɗanyi da yin dariyar da take yi, Ta dago tana kallonsu tace” Naji daɗin ganin ku cikin ƙoshin lafiya, Ina fata baku da wata damuwa”? Tai tambayar tana jiran amsarsu, atare suka haɗa baki wurin cewa”Ƴar uwarmu batool ba a dawo mana da ita ba, almost 2 weeks kenan, bamu san awani hali take ciki ba,” shiru tsohuwa ta ɗanyi na wani lokaci kafin tace”ku ƙara haƙuri idan da rabon za’a dawo da ita, to za ku ganta ne, amma abunda nake so daku, ku daina sanya damuwa aranku” tsohuwa na rufe baki muryar Danish ta ratsa kunnanta,

“Long time, ba mu ganki ba, kin daina zuwa wurin mu” Murmushi tayi tare da nuna shi da sandar hannunta tace”Shikaɗai ya damu dani, dama nasan babu wanda zaiyi kewata acikin ku idan bashi ɗin ba, maimakon da kuka ganni ku tambayeni lafiya na ɗauki tsawon lokaci banzo wurinku ba, amma babu wanda yae tunanin hakan,” ta karasa maganar tana kwa6e fuskarta, hada jefa musu harara tana murguɗa musu baki, gaba ɗaya suka kama tiƙar dariya ganin yadda take murmura idanuwanta yadda kasan na gwaggwon buri, da alama yau wasa tazo tayi musu,

“Kodan bani da amfani awurinku ne shiyasa kuka ƙi damuwa da rashina” shiru suka ɗanyi, angel dai tana zaune ta jingina bayanta jikin bango,

Haris ne yai ƙoƙarin cewa”taya za’ae mu ƙi yin kewarki tsohuwa? ae munji daɗin irin taimakon da kika yi ma deeja, gashi ta samu sauƙi sosai ta wartsake,” yakai karshen maganar tare da ɗan juyawa yana kallon deeja dake zaune gefen gadonta dake kusa da nashi, muryarta aɗan disashe tace”Nima inata so inyi maki godiya amma ban samu damar ganin ki ba, ranar da aka ɗauki batool, azeeza ta sume muka rasa ya zamuyi da ita, mun yayyafa mata ruwa ajikinta amma bata farka ba, Har ƙopar ɗakinki muka ƙwanƙwasa don kizo ki duba jikinta baki buɗe ba, shiyasa muka yi tsammanin ko baki nan ne,”

Jinjina kai ta ɗanyi tare da cewa”Hakane na ɗanyi nisan kiwo, Yanzu ma zuwa nayi don In duba ku ko akwai wani abu da kuke buƙata kafin in tafi” Basu fahimci me take nufi ba

“Mu ba abunda muke buƙata, Batool kawai muke so a dawo mana da ita” acewarsu parveen,

Tsohuwa tace”zata dawo ne, yanzu dai ku faɗa mini me ku ke so kafin in tafi, inji idan zan Iya yi maku shi”

Ta6e baki angel tai tare da cewa”kamar dagaske, nasan ko mun nemi taimako awurinki bazaki Iya yi mana shi ba” Kallonta tsohuwa tay, kafin tace”Me ki ke so Unaisah”? Yadda tayi maganar ba bu wasa akan fuskarta,

“Ki nuna mana hanyar da zamu fita daga Cikin kurkukun nan” shi ne abunda muke so” maimakon tsohuwa ta bata amsa saita fashe da dariya tana ɗan girgiza kai, daga bisani da ta tsagaita da yin dariyar tace”Kin buƙaci abunda bazan Iya yi maku shi ba, saboda yafi ƙarfina, Abunda nake so ki fahimta shine, Ni bakowa bace a gidan kurkukun nan, tun ban mallaki hankalina ba nake acikinsa, tsawon shekara da shekaru na rayu acikin kurkukun nan a matsayin prisoner kamar dai ku din nan, Nima tun ina ƙarama na taso acikinsa, Na jure duk wata gwagwarmayar dake acikinsa kafin na kawo wannan matsayin da nake dashi acikin kurkukun, ba lallai bane ku yarda dani ba, amma zan fada muku gaskiyata, Ni ban ta6a fita daga Cikinsa ba, Anan aka haifeni anan na rayu acikinsa nayi aure har na hayayyafa, akwai ya’yana da jikokina acikin kurkukun nan suna rayuwa”. Tunda ta soma kora musu jawabi, angel take binta da wani irin kallon rainin wayau har sai da takai ƙarshen maganarta, sannan angel ta soma magana

“Idan har dagaske bakisan Hanyar fita daga Cikin kurkukun nan ba, to taya akai kikasan tarihin rayuwata? Kinsan komai agame dani, bayan haka ke da kanki kika faɗa mini cewa Mashine ko mota bazasu ta6a Iya kawo mutun Cikin kurkukun nan ba, kenan ƙarya kike yi mini”?

Dogon numfashi tsohuwa taja kafin tace”banyi maki ƙarya ba, tabbas hakane, Duk da bana fita daga cikinsa amma ina iya sanin meke wakana awajen kurkukun nan,” lamarin yayi matuƙar ɗaurema angel kai, Wannan wata irin baƙar ƙaddarace? Kenan itama tsohuwa tun tana kamarsu ta ke rayuwa agidan kurkuku matsayin prisoner? Itama batasan kowa nata ba? anya kuwa zata Yadda da maganarta? Kafin angel tayi yunƙurin ƙara tambayarta wani abu, muryar naufal ta katse mata hanzarinta,

“Tsohuwa mun ga canji sosai, ga sabbin gadaje an kawo ga kuma akwatuna guda biyu, bayan haka kuma acikin toilets ɗinmu an zuba kayan amfani acikinsu, mun yi mamakin ganin sauye sauyen nan, kamar zamu dawwama acikin farin ciki ne ”

Tuntsirewa tsohuwa tayi da dariya tana faɗin”Ae ba’a dawwama cikin farin Ciki a gidan kurkukun ƙaddara, Waɗannan sabbin gadajen da ku ka gani, Ƴan uwanku ne za’a kawo, Nan badajimawa ba, daga yau zuwa gobe zaku Iya ganinsu, Sa’annan kayan amfanin da aka zuba muku acikin makewayinku, Nice nayi fafutuka wurin ganin an sanya muku su…..” dakatawa ta ɗanyi da yin maganar, haƙiƙa sun ji dadin jin cewa itace ta sanya aka kawo musu kayan amfanin, a karo na farko kenan da tayi musu abun kirki, gani suke kamar akwai wani abu da take so ta fada musu, wanda ba lallai bane yayi musu daɗi ba,

Duƙar da kai ƙasa tsohuwa tayi na wani lokaci, suna ta kallonta, kafin ta ɗago idanuwanta akan fuskokinsu, sai suka ga kamar ruwan hawayene kwance acikinsu.

Kafin su yi yunkurin yi mata magana ta riga su cewa”Ku ɗauko mini akwatin nan da aka kawo muku” da sauri naufal da haris suka je suka janyosu agabanta suka kwantar da akwatin nan,

“Kunsan menene aciki”? Suka haɗa baki wurin cewa a’a, murmushi ta saki tare da cewa”Sabbin Uniform ɗinku ne masu kyan gaske, tare da takalma, da sauran abubuwan da nasan zaku buƙata, Zaku Iya buɗewa ku gani”

Wani irin farin Ciki ne ya bayyana akan fuskokinsu, Jiki na rawa suka zuƙunna agaban akwatunan haris ne jagaba wurin buɗe akwatin farko, Kaya ne danƙare acikinshi, A ninke suke an jera su, uniform ɗin farko Launin baƙaƙe ne sun sha banban da kalar style din na jikinsu,

“Mutun Uku, Su fiddo da kayan a hankali sai ku dudduba a tsanake” acewar tsohuwa,

Suka amsa mata da toh, haris da deeja ne sai angel suka sanya hannayensu cikin akwatin suna zaro kayan tare da ɗago dasu suna warware ninkin da aka yi musu, haɗaɗɗun riguna ne masu kyan gaske, basu da banbanci da Wrap coat, suna da igiyoyi guda biyu a jikinsu, tsayin su zai kai har gwiwowinsu, sannan suna da dogon hannu, gefe da gefe akwai aljihu ajikin rigunan, yadin jikinsu mai matuƙar kyau da ɗaukar ido, kowace shirt tana da ƴar vest launin red acikinta, Uniform ɗin farko masu launin Black, Mallakin angel da batool ne tare da Danish, Numbobinsu ne akai no 1 no 2 zuwa 3, A bayan rigunan, wani abun mamaki daga ƙasan numbers na jikin uniform ɗinsu, Kowa da sunan da aka sanya mishi su ukun nan, da turanci aka rubuta sunayen anyi amfani da launin Ja, A bayan rigar Batool an rubuta

*HEART BEAT*(Bugun Zuciya) rigar danish an rubuta *PRISON SHIELD* (Garkuwar kurkuku) yayin da ita kuma Angel abayan rigarta aka rubuta *DESTINY* Wannan suna dai ya ɗaure musu kai, Har tsohuwa su ka tambaya menene ma’anar sunayen tace masu kada su damu, suna ne kawai, Angel bata yadda da sunayen ba, basu kwanta mata aranta ba, tabbas akwai dalilin dayasa aka rubuta musu sunayen abayan rigunansu, su ukun nan, Ita dai fatanta Allah yasa ba wani mugun abun bane.

kowace riga tana da dogon wadonta masu kyan gaske, Uniform dinsu azeeza sunyi kyau sosai launin Ja, iri ɗaya ne dana su Danish banbancin kala ne kawai, Sai kuma rubutun dake abayan rigunansu Angel, babu anasu rigunan sai dai numbobinsu, abun burgewa kowace riga tana da cotton scarves, Irin ɗan mayafin nan da mazan indiya suke ɗaurawa asaman wuyan su.

 

*Idan Allah yakaimu na Kammala Free pages of Takun farko, zan ɗauki hutu, kafin acigaba da middle step,Ga masu son cigaba da Karanta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, Inka biya za’ayi adding naka a paid group kuma za’a sanyaka a comment section, Sa’annan Ba’a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*

*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*

*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*

*3196407426*
Bature Hafsat Muhammad
First bank

*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (0816985 6268) ko kuma ta (08103884440)*

No comments