Breaking News

Kurkukun Kaddara 52-53

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*


_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E52-53 free pages

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

Launin ja, tun daga kan fuskokinsu zaka shaida irin tsantsar farin cikin da suke aciki, tun kafin ma su sanya kayan ajikinsu har sun fara Imagining irin kyan da zasu yi musu, tsohuwa dai sai murmushi take yi tana kallonsu, daga ƙasan Uniform ɗin nasu, wasu haɗaɗɗun rigunan sanyi ne masu dan banzan kyau, launin bright rust red da kuma dark brown, sai faman ɗaɗɗaga rigunan suke yi suna kallonsu, sun rasa bakin magana saboda tsabar murna, ga wasu hats haɗaɗɗun hulunan gayu na mata dana maza masu kyan gaske, Ƙasan akwatin gaba ɗaya sabbin takalmansu ne kala bibbiyu, zubin anckle boots da kuma slippers, Yara fa sun zama ƴan gayu, kaf saida suka zazzage kayan akwatin suna ta kallonsu suna yaba kyawunsu haɗi da nuna irin farin cikin da su ka yi.

Tsohuwa tace su buɗe ɗayan kwatin su duba kayan dake acikin shi, tasan zasu Yi farin ciki, akwai wata ƴar kyauta data sanya musu aciki, taban mamaki, Jin wannan maganar yasa suka tattara uniforms din da komai na akwatin farko suka maidasu ciki suka datse shi, cike da zumuɗi Angel ta buɗe musu akwati na biyu, a danƙare yake da kaya, abu na farko da suka fara Cin karo dashi, hankys ne launin ja da baƙi, mai ɗauke da sunayen kowannan su, sun yi matuƙar Yi musu kyau, Hada mayukan gyaran Jiki dana gyaran gashi, da Set na kayan gyaran akaifa, ga wasu ribboms na ɗaure gashi, Yawanci duk basu san yadda zasu yi amfani dasu ba, amma tunda ga angel sunsan zata Yi musu bayanin komai.

“Tsohuwa, kince akwai gift da kika sanya mana, Ta na ina? Ko su ne waɗannan kayan”? Angel ce tai mata tambayar tana kallonta,

Tsohuwa tace”Ku duba daga can ƙasan akwatin zaku same ta” Jiki na rawa suka ɗaɗɗaga kayan har suka taddo wrapping sheet ɗin dake nannade da wani abu, wanda shape ɗinshi daga sama round ne mai faɗi, ƙasa kuma ya ɗan tsuke, kallon juna suka yi cikin ƙagara da son ganin menene aka nannaɗe haka, kowa ya baza ido suna jiran ganin menene, A tsanake angel ta soma warware wrapping sheet ɗin awani slow, Sai da ta taddo ƙarshen shi ta yakice paper ɗin da aka nannaɗe shi, A hankali take bin shi da kallo, Su azeeza duk suka zazzaro idanuwansu ganin wani abun ban mamaki da basu ta6a gani ba, shin kunsan menene? Nasan Kun ƙosa kuji, To ba komai bane face*MADUBI,*

wani irin farin Cikine ya bayyana akan fuskar angel da ƙarfi ta ambaci sunanshi MIRROR, yayin da take kallon kyakkyawar fuskarta wadda yaushe rabon da taga suffar face dinta tun tana atare da daddynta tsawon shekara huɗu da watanni yama kusa ci ka 5yrs,

Ya burge ta sosai, madubin Round shaped ne mai matuƙar ɗaukar ido, Yadda kasan ƴan ƙauyen ido sama, Haka suka kewaye madubin Suna Kallon fuskokinsu, sun saki baki kamar lehen sakarai, In ka cire mutun ɗaya wanda Yaja gefe ɗaya kamar baya maraba da ganin sabon abunda basu ta6a gani ba, su kuwa sai ihu suke Yi suna Murnar ganin fuskokinsu kamar suyi hauka, Ɗakin nasu ya cika da Hayaniyar su, abun nema ya samu, Tsohuwa dai sai murmushi take yi tana kallonsu, Sun tasa madubin gaba Na tsawon lokaci, sai faɗi suke wai dama haka fuskokinmu suke? azeeza tace Wai Allah na, dama haka nake da kyau? Komai na fuskata ɗan ƙarami mai kyau, Hanna tace”Nima fa kyakkyawace, Idanuwana farare ƙyal, ga dogon hanci, ” deeja tace”duk da ban kai ku kyau ba, amma Nima ba daga baya ba, Manyan kyau ne dani,” tana rufe baki yasmin tace”ni matsalata idanuwana ƴan mitsi mitsi kamar zasu shige ciki, hancina luluyayye, har ƙwara bakina ma, ” gaba ɗaya suka kwashe da dariya hada tsohuwa, parveen dai ta ƙura wa madubin ido ita da Rubina sai kallon fuskokinsu suke yi kamar zasu lashe su, har sai da haris Yakai hannu ya danƙwashi kawunansu tukunna suka zabura, suna faman wurga mashi harara,

“Idan kun gama kallon ƙurallan ku bamu abun muma mu duba kyawun fuskokinmu” Wani irin kallo parveen tai mishi tare da cewa”shawara kyauta haris, Ka haƙura da duba abun nan, saboda Ina jiye maka tsoron munin fuskarka da zaka gani, zai iya sawa zuciyarka ta buga” kafin haris ya bata amsa deeja ta riga shi cewa”Ki Iya bakin ki Parveen, Ƙarya kike kice wai haris bai da kyau, don kawai yana da duhun fata ne, kuma ahakan Ba ƙaramin kyakkyawa bane, kawai kina yi mishi baƙin Ciki ne,” takai ƙarshen maganar tana jifarta da harara, hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma haris ba, koba komai deeja ta yabe shi, abunda ma ya ƙara burgeshi, da kanta ta ruƙo madubin daga hannun angel ta kanga mashi saitin fuskarshi, Atare suka haɗa faces ɗinsu suna kallon juna ta cikin madubin sai dariya suke saki,

Satar kallon danish angel tai don taga a wani yanayi yake ciki, Yana zuƙunne a tsakaninsu javed da mubeen, yaɗan duƙar da kanshi ƙas, Yayin da idanuwanshi suke akan yatsun hannun shi, Aranta tace Shi kuma haka zai ƙare! Kowa Yana kallon fuskarshi acikin mirror, banda shi, wama ya sani ko aljani ne, shiyasa yake tsoron Ya haska fuskar shi Cikin madubi, Amma dai zanso Ya kar6i mirror ɗin nan kodan yaga irin baiwar kyan da Allah yae mishi…….” kasa ƙarasa maganar tai ganin yana ƙoƙarin ɗago da kanshi da alama yaji ajikinshi ana kallonshi,

da sauri ta duƙar da nata kan ƙasa tana faman tsuke baki, koda ya ɗago Bai ci sa’ar haɗa ido da ita ba, Sai suka haɗa ido da Haris Ya sakar mishi murmushi yana faɗin” Deeja bani abun nan in haska ma Sarkin kyau fuskarshi, Nasan yau danish ko bacci bazai iya yi ba idan har yayi tozali da kyakkyawar fuskarshi,” Ya ƙarasa maganar tare da sanya hannu Ya ruƙo madubin, Ya ɗan yunƙura ya miƙe ya nufi danish, sai dai kafin ya ƙarasa danish yae saurin kifa kanshi saman gwiwarshi, bubbuga bayanshi haris yae tare da cewa

“Kar ka bani kunya mana, Kowa ya share ka sai ni na damu dakai, pls bro Ka ɗago ka kalli fuskarka,” batare daya ɗago da kanshi ba yace”Haris i can’t bana son ganin shi, pls ka janye shi daga saiti na, zai iya affecting lafiyata,”

jin wannan maganar ta Danish yasa duk suka ɗago da idanuwansu suna kallon shi, Lamarin ya ɗaure musu kai,

Deeja tace”But why danish? Kowa fa ya duba fuskarshi Kuma lafiya lou ba wani abu daya cutar damu, sai kai zaka ƙi kallon fuskarka? Javed yace “Haba danish idan ma saboda abunda ya faru a tsakanin mu dakai ne yasa kace ba za ka duba abun nan ba, Ina mai baka haƙuri just for today a matsayin mu na ƴan uwa mu kalli fuskokinmu acikin baƙon abun nan,”

Lamarin yae matuƙar ɗaure musu kai, sai roƙonshi suke yi suna yi mishi magiya akan ya kalli madubi amma ɗan tahalikin nan yaƙi ɗagowa, rai aɗan 6ace Haris Ya damƙi sumar kanshi da niyar ya ɗago da kanshi Ya tursasa mishi akan ya kalli madubin, aikuwa rai a6ace danish ya bangaje haris Madubin dake hannun shi ya kubce zai kife ƙasa, Jiki Na kerma Ƴan matan su kayi sauri ruƙo shi, Ran haris ya ƙara 6aci ya shiga zazzaga mishi masifa, deeja tace”Su rabu da shi, dama baya atare dasu, Shi kaɗai yasan dalilin shi na ƙin kallon madubin, danish ba abun yarda bane, Tsohuwa dai tana atsaye tana binsu da kallo bata tanka musu ba, duk wanda yai magana idonta na akan la66ansa.

Naufal yace” Ku ku ka damu da shi, ae gaya nan ya baku kunya, Kar Allah yasa ya kalli madubin, don ma ya samu ana lalla6a shi ne, Kuma wlh da ace Madubin nan ya fashe silar hankaɗe haris da kayi, Da ka ji ajikinka, shashasha” yana huci yai maganar,

“Ni dai A iya sani na, Aljanu ne basu son kallon madubi ko su gifta Ta wurin da aka ajiye shi, idan su ka yi suffar mutane saboda baya 6oye ainihin suffarsu ta jinni, na ta6a kallon wani film da irin hakan ta faru, ina da tabbacin cewa danish Ba cikakken mutun bane, Yana da alaƙa da aljanu,” Angel ce tai wannan tunanin acikin ranta,

Gyaran muryar da tsohuwa tayi musu ne yasa suka ɗago suna kallonta, Banda Danish daya kifa kanshi saman gwiwowinsa.

“Ku ƙyale shi, Idan ya nu na baya son abu to ku daina ƙoƙarin tursasa shi, kuma kada hakan yasa ku zarge shi, Danish ɗan uwan ku ne, tamkar uba yake agare ku shi da Haris, Tun ɗazu Na lura da irin wariyar da ku ke ɗan nuna mishi, shin meya faru atsakaninku ne? Ko wani zai iya faɗa mini”? Tai tambayar tana bin faces ɗinsu da kallo, Deeja ce ta kwashe duk abunda ya faru tsakaninsu tun daga kan batool daya bi cikin toilet ya ruƙo hannunta ya damƙa ma giant ita, har izuwa irin bugun da suka yi mishi, da kuma yanke alaƙar da suka yi da shi” tun kafin deeja takai ƙarshen maganarta, tsohuwa ta soma girgiza kanta, Yayin da idanuwanta ke akan Danish daya kifa kanshi, duk sun lura da irin damuwar dake akan fuskar tsohuwa, magana ta soma yi cikin nuna 6acin ranta ga abunda suka yi mishi

“Kada ku kuskura ku ƙara ɗaga hannu kuce zaku ta6a lafiyar jikin shi, bama shi kaɗai ba, Kowa ma, Nayi mamakin jin cewa kun haɗa kai kun bugeshi sai kace wani jaki, ko a shekaru Danish Ya ɗare maku amma ahaka kuka rufe ido kuka jibge shi kamar bawan ku, ina hankalin ku ya tafi ne? Musamman ke angel,” tai maganar tana nuna angel da sandar hannunta, Yatsina fuska angel tae tare da cewa”Ae ni ban ta6a shi ba, lokacin da suka jibge shi, Na suma bana ahayyacina kuma da ace idona biyu saina 6alla hannun shi daya ruƙe batool, saboda baida tausayi mugu ne shi, inaji ina gani Ya raba ni da batool ɗita, tana kuka ina kuka” daƙyar angel ta karasa maganar tare da ɗaura kanta saman laps ɗinta tana shessheƙar kuka tunawa da irin abunda ya faru aranar, gashi har yau babu alamun za’a dawo musu da ƴar uwarsu,

Deeja tace”Har ga Allah danish ya ƙona mana rai, yayi mana abunda bazamu ta6a mantawa ba, tabbas shi dan uwanmu ne amma baya atare damu, akwai wata mummunar manufa atare dashi, In ba haka ba meyasa duk irin shaƙuwar dake a tsakanin shi da batool bai duba wannan ba, ya rasa dame zai saka mata saida sharri, ae wlh duk abunda ya faru da batool alhakinta na akan wuyanshi, Kuma jira muke ta dawo muga awani hali take aciki, kafin mu ƙarasa yanke mishi hukunci” Daga cikin zuciyarta take magana, fuskarta babu alamun wasa, tsohuwa sai jinjina kai take yi, Tana kallonta, sai da takai ƙarshen maganarta tukunna tace”Aikuwa indai kuka ce zaku Cigaba da ta6a lafiyar jikin shi da rabon wata rana ku rasa madafarku, nayi mamaki da Danish ya ƙyale ku har kuka jibgeshi, bayan yana da ƙarfin da zai Iya rama abunda ku ka yi mishi, amma saboda ƙaunar da yake yi maku sai baiyi hakan ba, Saboda baya son wani acikin ku ya cutu, baku da masoyi a duniyar nan daya wuce Danish, shi tamkar jagora ne acikin rayuwarku, ku daina raina shi, akwai ranar da zaiyi maku amfani, amma muddin kuka ce zaku cigaba da nuna mashi wariya acikunku, to tabbas kuwa xakuyi danasani mara amfani…….” Tunda tsohuwa ta soma kora musu jawabi, suka kasa kunne suna sauraronta, batare da suna fahimtar taƙameman abunda take son ganar dasu ba, donsu ana su tunanin basu ga amfanin da zai iya yi musu ba, in banda ya hau gado ya naɗe kamar wani basarake,

“Ba lallai ne ku fahimce ni ba, saboda na karanci hakan akan fuskokinku, Shawarace nake baku kyauta, Bana so ku yi danasani Anan gaba, ” har suna haɗa baki wurin furta Kalmar danasani, deeja tace akan me zamu yi danasani? Bata bata amsa ba, tace”Ku tattara kayayyakin nan ku maidasu cikin akwatin, Ku rufe shi, sannan Ku kawar dasu gefe inaso muyi magana daku kafin in tafi” da sauri Su haris suka mayar da kayan da suka curo cikin akwatin suka datse shi, tare da jansu gefe ɗaya suka jingine su jikin table ɗin dakinsu,

bayan sun dawo Tsohuwa ta basu umarnin su miƙe tsaye, Gaba ɗayansu suka yunƙura tare da miƙewa suna kallonta, duk sun ƙagara da suji me take son faɗa musu,

Ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo na ɗan wani lokaci kafin ta soma magana cikin muryarta ta tsoffi,

“Tsawon shekara da shekaru Ina Rainon Yara agidan kurkukun ƙaddara, Ban ta6a samun Yaran da suka kwanta min araina ba naji ina ƙaunarsu har cikin zuciyata irin ku ɗin nan ba, Kun ciri tuta, domin kuwa kun kafa tarihi acikin rayuwar tsohuwa tamira…….” murmushi ne ya bayyana akan fuskokinsu, Inka cire mutun huɗu, Angel, deeja, Haris da Danish, Babu walwala attare dasu,

“Naso ace ina da hanyar da zan Iya taimaka maku, saboda ƙaunarku da nake yi sai dai kash bani da damar yin hakan, Amma ina fatan nan gaba idan muna da tsawaicin kwana mu sake haɗuwa daku, duk da nasan zaiyi wuya ………” Kallon kallo suka shiga yiwa junansu, Kamar sun fara fahimtar inda zancenta ya dosa,

“Tsawon lokaci Ina atare daku, Duk da ban amfane ku da komai ba, Amma nafi waɗanda su ka yi silar zuwan ku kurkukun nan, Na raini wasunku tun suna ƙanana tun basusan kansu ba, har suka fara tasawa suna rarrafawa yanzu gasunan sun girma gwanin ban sha’awa, wannan abun farin Ciki ne kuma abun ayaba mini ne, ga wanda yasan ya dace” tai maganar fuskarta ɗauke da murmushi, bayin Allah duk jikinsu yai sanyi, Sai kallon suke yi,

“Acikin ku akwai waɗanda suke Yi mini kallon muguwa maƙaryaciya, Mara amfani, Akwai ma wadda tace dani da tukunyar fulawar dake acikin toilet dinku bamu da banbanci, ” duƙar da kai ƙasa angel tai, Cikin jin Nauyin maganar da tsohuwa tayi,

“Ba za ku ta6a sanin amfani na ba, sai ranar da bana atare daku, A ranar zaku tuna da irin mahimmancin da nake dashi acikin rayuwarku, kuma a wannan lokacin zaku yi danasanin rashina atare daku, Amma bana son hakan ya karya zuciyoyinku, Inaso ku ƙarfafa ma juna gwiwa kusanwa ranku cewa, ko babu ni, ko babu wani acikin ƴan uwanku xaku Iya rayuwa! Domin kuwa ba’a halicci duniya don mu dawwama acikinta ba, dole ne akwai ranar da kowa zai barta, ko muna so ko bama so…….” dakatawa ta ɗanyi da yin maganar idanuwanta sunyi jawur a yayin da take kallonsu.

“Abunda yasa na buƙaci abaku waɗannan sabbin kayan saboda Inaso nima wata rana ku tuna dani acikin rayuwarku, A ƙalla dai nayi muku abun kirki……..” bata ƙarasa maganar ba, sakamakon shessheƙar kukan da suka fara, Batasan ya akai suka ɗagota ba tunkafin ma takarasa zance, girgiza kai ta ɗanyi tana murmushi tace”Jikokina kenan, meyasa zaku karaya tun yanzu? Haba Kar muyi haka daku, kada ku bari hawayen ku su xuba, akwai ranar da zasu yi maku amfani,”

“Dan Allah ki fahimtar damu me kike son faɗa mana? Gaba ɗaya kin jefa mu acikin ruɗani” azeeza ce tayi magana,

“Bankwana nake Yi muku! ” wani irin bugu zuciyarsu tayi, Tsabar tashin hankali ne ya bayyana akan fuskokinsu, Sam sun kasa furta komai,

“Dama na faɗa maku cewa, Ni mai raino ce, a ƙa’idar aikin masu raino na gidan kurkukun ƙaddara, da zarar yaran da yake raino sun mallakin hankalinsu, to za’a canza wanda zai dinga kula da su ne,”

A matuƙar ruɗe suke kallonta, Wasu har sun fara matse ƙwaalla, ashe basu ji komai ba,

“Zanje naci gaba da rainon ƙannanku masu taso wa, Ku kuma Za’a canza muku sabuwar da zata cigaba da jagorantar rayuwarku, sai dai fa zaku ga banbancin domin kuwa, Ni ba komai bace akanta, bansani ba kota kawo muku ziyara…..” Cikin sanyin murya danish ya bata amsa da cewa”tazo, namanta ban fada musu bane”

Tsohuwa tace”Bakowa bace face TSOHUWA ZAFREEN! Ita ɗin takasance ɗaya daga Cikin shuwagabannin dake ruƙe da gidan kurkukun ƙaddara! Kaifi ɗaya ce, zuciyarta bata da banbanci da dutse, a rashin tausayi Cikin kaso ɗari tana da casa’in da tara…..” tashin hankalin da ba’a sama shi date!! Tuni gwiwowinsu sun jima da sagewa, Zuciyarsu ta tsorata sosai, tunkafin ma suyi toxali da tsohuwa zafreen, Kusan atare ƴan matan suka zube saman gwiwowinsu, banda angel da mazan,

Sai kuka suke yi suna rokonta akan karta bari akawo musu tsohuwa zafreen, Idan ma yazama dole ta rabu dasu to ta taimaka ta hana akawo musu ita, abarsu suyi rayuwarsu batare da kowa ba, zasu Iya kula da kansu,”

Cikin raunin murya tsohuwa tace”Ae ni bani da ikon da zan hana tsohuwa zafreen zuwa wurinku, Saboda A matsayi ko ƙafarta ban kama ba, wani abun ɗaure kai ma, Ita da kanta ta nemi da abata sashen ku don taci gaba da kula daku, saboda ita ba cikin ma’aikata take ba, Shugaba ce Ra’ayin kanta ne zuwa wurinku, kai Danish ae ka ganta, Tana da babban muƙami, agaban rigarta taurari uku ne, idan baku san ma’anarsu ba, bari in sanar maku, duk wanda kuka gani da Star uku agaban rigarshi To shugabane na gidan kurkuku, A mataki na ma’aikatan prison daga star ɗaya yake farawa zuwa star biyu kafin ka samu taurari ukun nan, Idan kuka duba Jikin rigata babu star ko ɗaya saboda bani da wani matsayi agidan kurkukun ƙaddara, Raino kawai nake yi”

Cikin shesshekar kuka su parveen suke faɗin wayyo Allah mun shiga uku mun bani mun lalace, tsohuwa dan Allah kada ki rabu damu wlh zamuyi biyayya, zamu biki sau da ƙafa, Tun yanzu mun gane kuskuranmu…..”

haƙiƙa sunyi matuƙar bata tausayi sai dai ba yadda zatayi, haka Allah ya riga daya ƙaddara musu rayuwarsu, amma fa zasu ci baƙar wahalar da ba lallai bane su Iya rayuwa, Angel duk tafi su shiga damuwa, ita gani take hada ƙarin donta ƙetare Iyakar data faɗa mata na cewa duk ranar da ta kuskura ta yi leƙan asiri to bazasu sake ganinta ba, amma kuma ae koda ta dura tagar bata ga komai ba, sai ma wahalar da tasha, sai dai idan ko dama ƙarya tayi mata data faɗi hakan tun da ta saba canza magana,” numfasawa tayi tare da kallon tsohuwa tace.

“Idan ma saboda sa’in sar da muke Yi atsakanina dake ne yasa zaki tafi ki barmu, ina mai baki haƙuri, zan ma iya zuƙunnawa saman gwiwowina akan in roke ki, dan Allah badan halin mu ba, kiyi haƙuri ki cigaba da zama damu…..” da sauri tsohuwa ta ɗaura idanuwanta kan wadda tayi maganar, tayi mamaki ganin angel ce, idanuwanta sun Cicciko tab da kwalla duk da basu zuba ba,

Wata irin mahaukaciyar dariya tsohuwa ta tuntsire da ita, Jikinta har jijjiga yake yi saboda tsabar yadda take yin dariya kamar zata kife ƙasa, Duk suka ƙura mata luhu luhun idanuwansu da suka canza launi saboda kukan da suka sha,

Daga bisani tsohuwa ta dakata da yin dariyar tana kallon angel tace”Unaisa kenan, Ban ta6a tunanin zaki Iya furta hakan da kanki ba, lallai kun tsorata da tsohuwa zafreen tunkafin zuwanta, to agaskiya dai ba taimakon da zan Iya yi maku, shawarar da zan baku shine, koda gigin wasa kada ku kuskura tana magana kuna kallon cikin idanuwanta, na farko kenan, sa’an nan, ba’a sa’insa da ita, musamman ke unaisa, Kina da gangancin ya6awa mutun magana, ina mai gargaɗin ki da ki kiyayi harshenki, wurin Yi mata magana, abu na ƙarshe da zan fada maku, idan tana awuri ba’a tsegumi, ko ƙyafcen ido, da yafu ce, Har kisa tana iya yi, idan har akai hakan agabanta, idan har kuna son ku ci ribar zaba da zafreen, to kuyi mata biyayya tamkar zaku bauta mata, idan ta bada Umarni, Jiki na rawa kuyi gaggawar yi mata shi, babu musu, idan har baku kiyayi abunda na fada muku ba, tabbas zaku yiwa mutuwar ku kutse tunkafin lokacinku yayi, ” wani irin wahalallan yawu kowannan su Ya haɗiya, wasu har sun fara jin zazza6i ajikinsu, sun tsorata da tsohuwar nan da za’a kawo musu,

“Ba lallai bane, kullum ku dinga ganinta, kamar yadda kuka saba ganina jefi jefi, saboda ita ɗaya ce daga Cikin shuwagabannin kurkukun, zaima yi wuya a sati ku ganta, Zata iya ɗaukar tsawon kwanaki bata leƙo ku ba, Ta inda zaku samu sauki kenan, domin kuwa baiyanarta ba alkhairi bane……”

Muryar su azeeza ce ta katse mata hanzarinta,

“Tsohuwa yanzu shikenan tafiya zakiyi kibarmu? Fuskokinsu sharkaf da hawaye hada majina,

Daƙyar ta ƙaƙalo murmushi akan fuskarta tace”ƙwarai kuwa tafiya zan yi in barku, babu tabbacin zamu ƙara haɗuwa, ni dai shawarata agare ku shine, Ku daina gaba da junanku, ku hada kanku, kuma ku kawar da idon ku ga duk wani abu da ɗan uwanku Danish zaiyi, ku daina fushi dashi, hakan zai iya haddasa mashi matsala acikin zuciyarshi,” ajiyar zuciya ta ɗan sauke kafin ta ɗago suka haɗa ido da angel,

“Jikata unaisa, Baki ya mutu, tsohuwa zata tafi ki huta da ganin mummunar fuskarta, meyasa banga kina farin Ciki ba”? Tai tambayar tana sakin ƴar dariya, angel kuwa fuskarta aɗaure take, ta tsuke baki, baiwar Allah damuwa ce danƙare akan fuskarta, ” a hankali tsohuwa take buga sandar hannunta, wanda ke nuni da cewa akwai wani abu da hakan ke nufi, sai dai basu fahimci dalilin dayasa take bubbuga sandar ba, dakatawa ta ɗanyi still idonta na akan angel taci gaba da cewa

“Ƙaramarsu babbarsu, ki cigaba da taimakon su kamar yadda kika saba, Inajin daɗin hakan sosai, haƙika zuwanki cikin rayuwarsu tamkar bayyanar haske ne acikin duhu, ki haɗa ka ƴan uwanki, kada ki bari wani abu ƙalilan ya shiga tsakaninki da waninsu, kuso junanku, ku sama ma kanku farin ciki, duk runtsi duk wuya kada kuyi kuskuren da zaisa ku raba kawunanku, idan har kuna son cimma burinku, Inaso ku ɗauka cewa ku kamar

*MUKULLAI NE NA MABUƊIN WATA ƘOFA GUDA ƊAYA WADDA ZATA SAMA MAKU FARIN CIKI ACIKIN RAYUWARKU, TABBAS KUNA DA DAMA*

Amma fa dole sai kun yarda da kanku, kun haɗa hannu, domin kuwa Ƙofar farin cikin nan tana atare daku, Sa’annan

*KU NE MAKULLAN DA ZAKU BUƊE TA*

Nasan a yanzu bazaku ta6a fahimtar kalamaina ba, sai nan da wani lokaci, Aranar da kuka fita hayyacinku, wasu ma basa araye, To awannan lokacin ne zaku gane me nake nufi…………”

Tunkafin ta ƙarasa maganarta, Da ƙarfi Ta buga sandar hannunta, wata irin ƙura ta mamaye idanuwansu, Kafin wani lokaci hayaƙin ya washe, Sai dai koda suka buɗe idanuwansu, ba su yi nasarar samun TSOHUWA TAMIRA ba, Ta riga da ta tafi, ta barsu da kewarta, sun shiga ruɗanin maganganun data faɗa musu, ga fargabar da suke aciki na baƙuncin TSOHUWA ZAFREEN, Lamarin yayi matuƙar gigitasu, yinin ranar da jimamin rashinta suka Yi shi, babu wanda bai matse kwalla ba acikinsu, Sunyi kuka tamkar ransu zai fita, sunyi danasanin duk wani abu da ya shiga atsakaninsu da ita, dama ance sabo turken wawa, hatta angel da tafi kowa tsanar tsohuwa a yau Saman gado ta haye ta rungume pillow tana matsar kwalla, fuskokinsu sunyi jawur gwanin ban tausayi, babu wanda yai kwakkwaran motsi acikinsu, kowa yana tuna irin rayuwar da suka yi da tsohuwa Tamira, Har giants suka kawo musu abinci basu motsa ba, badan Allah yasa parveen tayi tunanin kwashe musu abincin Cikin kwando ta ajiye musu shi ba, da sun yi asarar shi, duk irin zumuɗin da suke yi na sabbin kayan da aka kawo musu babu wanda Ya ta6a su, Kai hatta akwati nan basu ishe su kallo ba.

Sai da yunwa ta fara kai musu karo tukunna suka fara neman abinci, A lokacin dare ya nutsa Haka suka zazzauna saman dining carpet dinsu, parveen ta ɗauko musu abincinsu, Yadda kasan waɗanda akayiwa dole, Suna cin abincin suna matsar kwalla, Musamman parveen idan ta cunkusa Naman abaki, tana tauna Tana ambaton sunan tsohuwa, shikenan ta tafi tabarsu, Yanzu ya zasuyi, Bayan sun kammala cin abincin, babu wanda yai tunanin yin wanka, ga jikinsu sai tsami yake yi, ahaka suka haura saman sabbin gadajen nan kowa ya kwanta, zuciyoyinsu cike fal da jimamin rashin tsohuwa Tamira, da kuma fargabar irin rayuwar da za su yi da tsohuwa Zafreen, ɗaya daga Cikin shuwagabannin kurkukun ƙaddara, suna daga kwance suke Yin fira, Haris yace daga Jin sunanta babu imani atattare da ita, Ni inaga toilet zan koma da kwana, zaifi mini kwanciyar Hankali, ashagwa6e azeeza tace Ni dai Allah ƙarƙashin gado zan dinga 6oyewa duk idan naji takun tafiyarta”

parveen tace nidai in har bazata hanani cin abinci ba, babu ruwana da shiga huruminta, zanyi mata biyayya kodan in tsira da Ciki na,” deeja kuma tace”Allah ya jiƙanmu badan mun mutu ba,” rubina tace”Ai kawai mu ɗauki shawarar tsohuwa mu bita sau da ƙafa, Har Allah ya kawo lokacin da zamu Rabu da ita,” dogon tsoki javed yaja mai sautin gaske kafin yace”Kunga surutun ya isa haka, pls kowa ya lallashi zuciyarshi, Ku rungumi pillows dinku, aja bargo a lullu6e jiki, kowa Yae bacci, zuwan tsohuwa Zafreen ba fashi,” Sai da duk suka gama surutansu, tukunna Angel ta soma magana muryarta adisashe tace”In sha Allah, babu abunda zai faru, koda tazo bazata Iya cutar damu ba, Ni babu bawan da nake jin tsoronshi aduniyar nan, In ba mahalicci na ba, saboda nasan babu wanda ya isa ya cutar dani face da izninsa, Allah shine maganin duk wani mugu mai kafirar zuciya, kafin ayi azzaluman kurkukun kaddara Anyi waɗanda suka fisu, irinsu fir’auna yanzu duk babu su a doron duniyar nan sai dai kajisu a tarihi,’ Tunda angel ta ambaci sunan fir’auna, nan fa suka addabeta akan ta basu tarihinshi suna son Sanin wanene shi, tace musu su yi haƙuri yanzu kanta ke yi mata ciwo, amma ta yi musu alƙawarin idan taji sauƙi zata basu tarihin Annabi musa (AS), bayan haka saida ta kwantar musu da hankulan su, kafin ta samu bacci ya ɗauke su,

Lokacin da dare Ya ratsa, Angel ta sauko daga saman gadonta, zuciyarta duk ba daɗi, ahaka ta lalla6a ta nufi toilet ɗinsu, ba don komai ba, sai don ta duba awani hali furen batool yake aciki, Tana sanya ƙafarta Cikin toilet din ta hango furen batool da alamun lemar ruwa ajikinshi, kamar zufa haka ya tsastsafo ajikin ganyen shi, nan fa hankalinta ya ɗan tashi, da sauri ta ƙarasa inda tukunyar fulawar take, Ta zuƙunna tare dakai hannu tana shafa Jikin ganyen shi, sosai ruwan ke tsastsafowa, Duk saita rasa sukuni, ta shiga damuwa, muryarta na ɗan rawa ta soma faɗin”dan Allah batool ki daina kuka, Ina atare dake, ban manta dake ba, kina araina, kullum ina yi maki addu’a, Duk da nagaza zuwa in taimake ki amma nasan cewa Allah yana atare dake kuma zai kare ki ne,”

cikin shessheƙar kuka angel take lallashin Furen, Batasan cewa Danish Yana tsaye bakin ƙopar toilet ɗin ya la6e yana kallonta, tsananin tausayinta ne ya kama shi, sai dai baijin zai iya zuwa ya lallashe ta, saboda alƙawarin daya ɗaukar mata, abunda baisani ba ita kanta, A halin yanzu a matuƙar ƙagare take da son su shirya da juna don ba ƙaramin azabtuwa take yi ba,

Shiru ta ɗanyi tana ƙarewa furen kallon, ganin Ya daina tsastsafo da ruwa ajikinshi, wani iko na Allah sai taga furen ya kwanta cikin ƙasar tukunyar, alamar mamallakin shi bacci yake yi, murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, aranta ta raya cewa Batool taji lallashin da take yi mata shiyasa tayi shiru ta kwanta tana bacci, A hankali ta mayar da idanuwanta kan furen daddynta, tafi yarda dana batool akan nashi, saboda shi bata da tabbacin yana raye koya mutu, Jikin furen yayi kore shar dashi, kuma iccen yaɗan miƙe ba kamar lokacin farko da ya fito a lanƙwashe ba, Ziraran yatsun hannunta ta ɗaura asaman furen daddynta tare da shafa ganyen shi, a fili ta furta I wish kana araye daddyna, har yanzun kana nan acikin zuciyata, ba abinda ya sauya daga ƙaunar da nake yi maka, I luv u so much, zan cigaba dayi maka addu’a kaida batool ɗina da kuma ƴan uwana prisoners, Alƙawarine na ɗaukarwa kaina,”

murmushi tasaki tana faɗin”Har na tuna lokacin da na ƙala maka sharrin cewa kai ba mahaifina bane, ɗan yankar kaine, aranar kasha bugu wurin ƴan ƙato da gora, kuma duk da abunda nayi maka hakan baisa ka guje ni ba, saima ka ƙara ƙaunata, ashe babu rabon xamu ƙare rayuwarmu atare…..haka na dinga burin in zama house wife, ashe da rabon in zama prison wife, Gidan hutun da nake burin inyi aure, har ina faɗa ma aunty aneelerh zan auri hamshaƙin mai kuɗi saboda masu aiki su dinga yi mini hidima ina daga kwance, sai gashi na ƙare agidan kurkukun ƙaddara, wayyo Allah na, babu daddyna babu aunty aneelerh da uncle uzair, babu mommy adamana da uncle abdallah, babu makaranta, babu house wife, duk waɗannan burinkan sun tashi a tutar babu…..”

daƙyar ta ƙarasa yin maganar saboda kukan da yafi karfinta, ta kifa kanta saman gwiwowinta taci gaba da kuka, tana fadin nayi danasani daddyna ka yafe mini, wlh ina matuƙar ƙaunarka, dama saida ka fada mini cewa bani da tamkarka a duniyar nan yanzu na shida hakan…..’

Duk wannan suratan da take yi akan kunnan Danish, Ya ɗan jingina kanshi jikin ƙopar toilet ɗin, Ya natsu yana sauraronta, Hakanan taji aranta kamar akwai mutun abayan ta, a hankali ta ɗan dago da kanta, tana ƙoƙarin juyawa ta kalli bayanta danish yai saurin fita daga Cikin toilet din ya tsaya daga waje, Yana faman sauke ajiyar zuciya,

Baiyi tsammanin ta biyo shi ba, Sai dai yaji ta ambaci sunan shi,

“Danish”! Kasa juyawa baya yae don ya kalleta, duk yabi ya kama kanshi,

“Shine kana ji inata kuka ko kazo ka lallashe ni” Yayi mamakin jin abunda ta ce, cije lips ɗinsa yae kafin yace”Saboda me zanzo in lallashe ki? Ko kin manta alƙawarin dana ɗaukar miki? Batare daya juyo ya kalleta ba, yayi maganar,

“Meyasa kake bibiyata? Nasan saboda ni kazo bakin ƙopar toilet din nan ka tsaya, Allah kaɗai yasan tun lokacin da kake kallona, kaga kuwa Alƙawarin Ya jima da karyewa,”

girgiza kanshi ya ɗan yi tare da cewa”bana sa6a alƙawari, idan kin manta bari in tuna maki, kin ce kada na kurkura na ƙara hada ido dake kinaso in nisanta kaina agare ki, Tabbas nazo bakin ƙopar toilet din kuma na kalle ki amma ban bari mun hada ido ba. Hope kin fahimta yanzu ban karya miki alƙawarinki ba, Tun da bamu haɗa ido da juna ba kuma banzo kusa dake ba,”

Harara ta shiga jefa ma bayan shi, kamar ƙwayar idanuwan zasu faɗo ƙasa, wani irin kewarshi take ji kamar tae hauka, tayi danasanin sanya shi ya ɗaukar mata alƙawarin nan, ta manta cewa Prisoners basu Iya karya alƙawari ba, ta inda suka banbanta da mutanan dake rayuwa awaje kenan, majority dinsu basa ƙarya kuma basu Iya gulma ba, musamman DANISH!

Takaici ne ya isheta, Can dai tace”Idan nace na fasa alƙawarin fa”? Danish ya bata amsa da cewa”Idan kin fasa Ni bansa fa, bazai ta6a yiyuwa ba” yana faɗin hakan Ya wuce cikin dakinsu yabarta a tsaye tana faman cizon le6enta,

Daga bisani ta gyaɗa kai tare da wuce wa ta nufi cikin dakin, a kwance ta same shi saman gadon shi ya rungume pillow, ta6e baki tayi kafi ta nufi nata gadon ta haye ta zauna daga tsakiyarshi ta ɗaga hannayenta sama tana jera addu’o’i, Cikin harshen larabci,

ta ɗauki tsawon lokaci daga bisani ta shafa hannayenta saman fuskarta, kafin ta gyara kwanciyarta, Sai da ta lumshe idanuwanta, Zuciyarta ta soma tariyo mata maganganun da tsohuwa ta faɗa musu kafin tafiyarta, tabbas akwai wasu kalamai da tayi aciki waɗanda suka ɗaure mata kanta, ta kasa fahimtar inda suka dosa, Duk irin kaifin basirarta, ta gaza gano menene tsohuwa take nufi, da tace musu su dauka cewa su makullaine da zasu Iya buɗewa kansu ƙopar farin ciki, tayaya kenan? daƙyar ta samu bacci ya ɗauketa a daren ranar,!

Ko a washe garin ranar babu wanda ya sanya sabon uniform ɗinshi acikinsu, damuwar rashin tsohuwa ta hanasu sukuni, ga fargabar zuwan tsohuwa Zafreen, da kuma new prisoners, daga Sunji motsin ƙopa a firgice suke kallon ƙopar, don suga wanane, a ƙarshe sai su ga bakowa, Kunnuwansu ne kawai suke Jiyo musu hakan, sakamakon sanya rai da suka yi, wasa wasa yau har tsawon 2 weeks da tafiyar tsohuwa babu wani sabon Labari, ta ko’ina shiru kake ji, su kaɗai suke rayuwarsu, hankalinsu har ya ɗan kwanta don a tunaninsu, An ƙyalesu ne su yi rayuwarsu su kaɗai, Bakomai yafi ɗaga musu hankali ba, face rashin batool don a lissafinsu yau Wata ɗaya kenan babu Ƴar uwarsu acikinsu, Ba’a dawo musu da ita, har sun fara fidda rai da sake ganinta 🥺

*PRISONERS💔*

Yau tun da sassafe Angel da hanna suka taimaka ma ƴan uwansu mata wurin gyara sumar kansu, gwanin ban sha’awa kowa saida suka wanke mashi sumar kanshi, suka gyara musu ita, su kansu ba ƙaramin daɗi suka ji ba, ganin yadda sumar kansu tayi kyau ga laushi da kyan gani a ido, ga wani irin ƙamshi da gashin nasu yake fitarwa mai daɗin shaƙa, Bayan Sun kammala gyara ma su azeeza, Hanna da angel suke koma toilet, saboda su wanke nasu gashin kan, sai da angel ta kammala wanke ma hanna, ya rage saura ita, duk yadda hanna taso ta wanke mata gashin kanta, hakan ya faskara, saboda uban yawan dake gare shi, Gashi ya nannaɗe yadda kasan taliyar indomi, Tun tana nish tana ƙoƙarin tattaro gashin kan Angel, kamar hannunta zasu 6alle, a ƙarshe data ga abun yafi ƙarfinta, sai ta fita tabar angel acikin toilet ɗin, sai gasu sun shigo kusan su Shida hada su javed da naufal, wai sun zo wanke mata kai, ashe bayan da hannah ta fita daga cikin toilet ɗin, ɗakinsu ta shiga taje ta kira su, donsu taimaka mata, mamaki Ya kama angel, ganin sun shigo suna nannaɗe hannuwan rigunansu, Kusan dambe akayi acikin toilet din, tana faɗin ita bata so su barshi ta haƙura da wanke gashin, Su kuma suka ce bata isa ba, Yadda aka wanke ma kowa gashi, Itama sai sun wanke mata nata, ko tana ko bata so, A lokacin Danish Yana la6e bakin ƙopar toilet din yana kallonsu, don ba ƙaramin nishaɗi ya samu ba, ganin yadda suke ta yawo acikin toilet din sai zagaye shi suke yi, Ita tana gudu su kuma suna bin bayanta hannayensu ruƙe da shower gel da comb, da sauran abubuwan da zasu yi amfani dasu wurin wanke mata gashin su gyara mata shi, Sai da kowannansu Ya gama galabaita, tukunna suka samu ta basu haɗin kai, Su shida suka wanke mata gashin kanta, tadaici azaba, har wani jiri take gani acikin idanuwanta, saboda yadda suke ja mata gashin, Bayan sun kammala wanke mata shi, waɗanda ke ruƙe da combs, suka soma sharce mata shi, daga bisani suka bi da mayukan gyaran gashi suka shasshafa mata, ‘ Lokacin da suka kammala, Sunyi mamaki Ganin irin yadda gashin kanta ke ta ɗaukar ido, yayi dark brown dashi ya warware tamkar hijabi yayi mata abayanta, ta yi farin Ciki sosai da suka taimaka mata wurin gyara mata gashin kanta, ta ƙara jin ƙaunarsu acikin zuciyarta,

Kafin marece ya doso, ɗaya bayan ɗaya suka soma shiga toilet suna Yin wanka, saboda yau sun shirya canza Uniform dinsu, sai ɗauki suke Yi zasu sanya sabbin kaya, Bayan sun kammala Yin wankan, Ya rage saura Danish Yaƙi zuwa yai wanka, Hatta mazan sun wanke sumar kansu, amma shi duk ya takure kanshi, Ya hana kanshi sukuni acikinsu, duk da ayanzu babu wanda yake nuna mishi wariya, tun ranar da tsohuwa tayi musu faɗa akan su daina ware shi acikinsu, tun daga ranar suka daina gaba da shi, Shi ɗin ne dai kamar baison suna kusanto shi, Kuma bakowa yaja hakan ba face Angel, ita ɗin dai ce da baya son ya karya mata alƙawari.

Ganin baida niyar tsohuwa ya wanke sumar kanshi Yasa haris zuwa har saman gadonshi, Ya damƙo hannun shi ya janyoshi, Har saida ya sauko daga saman gadonshi suka nufi toilet, Yana fadin Allah idan bakai wanka ba, Ni zanyi maka da kaina, kowa yana nishaɗi sai kai kaɗai duk kabi ka takura rayuwarka sai kace wani bare, Idanma don abunda ya faru ne ae mun yafe maka komai ya wuce mana, tun da ya riga daya faru,” Kamar wani ubanshi haka haris ya dage yana tayi mishi faɗa, har suka shiga cikin toilet din, bawan Allah yai shiru bai tanka mishi ba, haris bai fito daga cikin toilet din ba sai da ya taimaka mashi ya wanke sumar kanshi, Kafin Ya fito yabarshi aciki, don yayi wankan,

Kafin wani lokaci, duk suka hallara acikin ɗakinsu, Angel ta janyo musu akwatin kayansu Ta bude shi, a hankali take zaro uniforms ɗin tana miƙa musu, da yake tasan numbers ɗinsu, shiyasa ba ta sha wahala wurin banbanta na kowa ba, Bayan kowa ya kar6i nashi, nan fa suka soma sanya su ajikinsu, Cikin dabara, Idan suka cire tsohon wandon, sai su zura sabon a jikinsu ta yadda tsiraicinsu bazai fita ba, kafin ma su sanya kayan ajikinsu saida angel ta biya musu addu’ar sanya sabbin tufafi, duk suka yi banda Danish, Ya ruƙe kayan a hannunshi yana zaune gefen gadonshi, babu alamun zai zurasu ajikinshi,

Uniform din sunyi bala’in yi musu kyau, yadda kasan ɗaliban high school na ƙasar Korea, Tabarakallahu ahsanul khalikin, Kyau ne ya haɗu da kyau, abunka ga farare kayan sun fiddo da hasken fatarsu, Sun bi shape din jikinsu sun zauna musu cuf cuf, Especially angel, Wow abun ba’a magana, Yarinyar dama can kalar kyau ce, Ƙarshe ce afagen kyau, Hatta ƴan uwanta su azeeza sai santin kyanta suke Yi, duk da irin kyan da su kayi don itama azeeza ba daga baya ba, jajayen kayanta sun mayar da ita tamkar fure awurin kyau, musamman in tayi dariya fararen hakoran nan suka bayyana ajere kamar gonar auduga, tubarkalla,

Danish fa sai satar kallon angel yake yi da zarar Ta juyo zata fuskanci inda yake sai yae saurin kawar da kanshi gefe, baisan cewa ta lura da irin satar kallon da yake yi mata ba, hakan ba ƙaramin dadi ya yi mata ba,

bakomai Yafi ƙawata kyan uniform ɗinsu ba face Cotton scarves din da suka daura awuyansu, da kuma igiyar wrap coat dinsu da suka daure, Sai takalmansu, da kuma ribbom da matan suka ɗaure Sumar kansu dashi, Banda angel saboda sanin yawan gashinta shiyasa bata yi gigin sanya ribbon ta daure shi ba, don zai iya tsinkewa, hatta giants da suka zo kawo musu abinci, sai da suka yi musu wani abu daya basu mamaki, da hannu suka yi musu thumbs up, wato alamar jinjina, wannan abun dai ya gigitasu, basu ta6a yi musu hakan ba sai yau da suka ga sun ɗauki wanka, angel dai bataji dadi ba, saboda tasan ƙarshe duk wannan gayun da suke Yi, abanza zai tashi, tun da ba fasa daukarsu za’ayi ba, sai daga baya tadinga danasanin Gyaran gashin da su kayi da sabbin uniform ɗin da suka sanya ajikinsu, don ba ƙaramin fiddo da kyawun surar jikinsu kayan su kayi ba, hakan zai ƙara ma ƴan iskan ƙaimi wurin biyan buƙatarsu da su, zasu ji daɗin gur6ata musu rayuwa, in ba haka ba taya akai giants da basu magana Yau kawai don sunga sunyi kyau shine suka yi musu alamar jinjina wato sun burgesu da suka yi gayu, aiko dai akwai matsala babba!!

 

*Idan Allah yakaimu na Kammala Free pages of Takun farko, zan ɗauki hutu, kafin acigaba da middle step, saboda in samu natsuwa kafin in dasa, ba jimawa zanyi ba, ƴar tazarace, Ga masu son cigaba da Karanta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, Inka biya za’ayi adding naka a paid group kuma za’a sanyaka a comment section, Sa’annan Ba’a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*

*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*

*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*

*3196407426*
Bature Hafsat Muhammad
First bank

*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (0816985 6268) ko kuma ta (08103884440)*

No comments