Breaking News

My Little Sister 15-16

Page 15 & 16

 

__________”Yana shafe mata hawayenta..Dakyar tahad’iye kukan tace dadyn Ahzad kana Ganin akwai ranarda wannan abun ze wuce kuwa? Kallafa kaga yadda sukayi mana yanzu betsaya yaci,abunci sabidaniba itama Bataci kimaiba Amma sunciyarda junansu agabanmu


batareda Muna wurinba Kuma Bada soyayyar yaya da k’anwaba soyayya ce irinta kauna da shakuwa Alhaji kadufa da kyau kaga karmu saki Baki Muna kallan wannan abun dagabaya yafi k’arfinmu…karkice Hakan halima insha allah ba,abunda yafi Karfin addu,a duk abunda yayi tsanani maganinshi allah mudage da addu,a allah yakawo mana mafita wacikin wannan Al,amaren..ameen y allah tafad’a kana tamik’e jiki asanyaye tana kwashe kayan wurin.

 

Tana fita tashiga motar ya sultan koda yafito aciki yasameta,,bud’ewa  yayi Shima yashiga kana yatada motar suka d’auki hanyar school d’insu Huzda…suna cikin tafiya sultan yajiyo yakalleta yace sweet sis…na,am sweet bro tafad’a tana kallanshi…shiru yadanyi nawani lokaci kamun yace tambayarki zanyi Kuma kigayamin gaskiy kinji karki b’oyemun komai..to sweet bro zangayama..ok good girl yanzu abunda nakesan nasani shin miyasa kikesan ki auri yayanmu?

 

D’agowa tayi tana kallanshi kana tayi murmushi tace bakomai my sweet bro haka kawai..haka kawai? Kodai wanine yace kice Hakan? “Aa bawanda yace nicedai nace shine mujina Kuma kaji Shima yace nice matarshiko? Tafad’a cikeda yarinta acikin maganarta…nisawa sultan yayi Yana k’ara Danne zuciyarshi kana yace hakane naji Amma ke bakisan Babu aure tsakanin blood brother and blood sister bane? Fuska Huzda tahad’e kamar zatayi kuka tace nidai Babu ruwana ko babushi Koma akwai Kuma allah idan kak’ara fad’ar Hakan zamu b’ata nidakai Kuma zangayawa ya zadna…Wani irin kallon tausayi sultan yabita dashi yaname jinjina wannan lamarin aranshi Kuma Yana tausaya musu dukkansu domin yanada tabbacin koda Huzda da Ahzad zasu mutu baza,a aura musu junansuba to balleshida bemasan inda yakamaba,,bekara cewa kimaiba har suka k’arasa school d’in tasu,,,yanayin perking tafito ahasale tawuce class ko sallama batayi mishiba balle tak’arb’i kud’i kamar yadda tasaba,,Hakan yasa sultan Kiran k’anwarta Rafi,a datazo wucewa yabata kud’in yace takaiwa Huzda d’in kana yaja motarshi yayi gaba.

 

 

 

Agidan abei kuwa

 

Zaune suke dukkansu a parlor ammy da abei yusif yuzarsiya ya muhfat,,sunkewaye katuwar ledar abuncinda ammy tashimfid’a musu sunacin abunci Amma Banda yuzarsiya Daketa famar juya spoon acikin abuncin,,ammy ce tad’ago tana dubanta kamun tace wai minene Hakan yuzarsiya? Kefaba yarinya bace kamar Huzda akanme shirmenta zedameki har kirik’a takura rayuwarki Hakan? “Miyafarune? Abei yatambaya..wlh Alhaji lamarin yarinyarnanne keda ban haushi wlh dubafa kaga tin lokacinda akayi abunnan takasa sawa rayuwarta nutsuwa kullun cikin kuka da tinani abuncin kirkima batasamu taci seta jawakanta wani ciwon nayi rarrashinta nayi lurarda,ita nabata Baki Amma duk abanza dukkanmu Nan bawanda beyimata nasihaba akan wannan Al,amareen Amma mutakesan Maida rayuwartane?

 

“Ya,Isa Koni hajara kirabuda,ita shirmene kawai itama haukarce tareda ita inba hakanba tayaya zaki Saka zancen Huzda aranki Kuma Ina kikataba Ganin anyi aure tsakanin Yan uwa na jini uwa d’aya Uba d’aya? Ko kintab’a jine?

 

Shiru yuzarsiya tayi tana saurarar iyayen nata kamun tabud’e Baki cikin muryar kuka tace abei duk naji zancenku Kuma bantab’a ganiba Amma abei kunajifa abunda ya Ahzad kefad’a akan Huzda ni wlh ayanzu ba kukan rashin aurenshi nakeyiba Ina tausayawa k’anwata ne domin kuwa nasan soyayyar ya Ahzad batin yanzu take arantaba idan anyi dubada yadda kalamanta ke fita daga zuciyarta Kuma Shima ya Ahzad d’in yabari soyayyar k’anwarshi tayi tasiri aranshi shine abunda ke sakani kuka domin nasan cewa duk yadda sukakaiga San juna bazasu tab’ayin aureba,,zancen aurena da ya Ahzad kuwa tuni babarshi tin inda yace Huzda yakeso agabana abei daga lokacin nake k’okarin cireshi araina domin bazan iya auren mijinda zuciyarshi naga wataba,,fatana anan shine allah yakawowa y’an uwana mafita acikin rayuwarsu,,tana gama fad’ar Hakan tamik’e dasauri tana rik’e kukanda kesan kub’uce mata.

 

Dukansu da kallo sukabita tabbas maganar yuzarsiya gaskiya ce to Amma ya,akayi har sukeyiwa junansu wannan son? Anya kuwa zuba musu Ido kamar yadda akace abune dazeyu? Ammy tafad’a amifili..”nisawa abei yayi kana yace munbarwa allah lamarinsa domin bamuda abunyi a wannan lamarin se abunda allah yatsara bakinmu addu,a ayanzu domin itace kawai mafita..to Allah yakawo mafitar ta alkhairi tafad’a araunace.

 

Hospital

 

Tsaye yake acikin bedroom d’inshi nacikin office Yana k’ok’arin cire kayanda yayi theater dasu yamayarda nashi,,seyaji sallamar Dr yaseer kana yabud’e k’ofar yashigo… d’agowa Dr Ahzad d’in yayi Yana duban Dr yaseer batareda yace komaiba Kuma befasa cire kayanshiba,,,shiko bekulashiba seda yagama sauya kayan kana Dr yaseer yace “Dr magana nazo muyi dakai Ina fatar zakabani hankalinka domin serious maganace..zama yayi Shima kamar bazeyi maganaba seda yagama Shan kamshinshi kana yace “okay Ina saurarenta…!

 

 

 

 

 

 

 

Autar alheri ✍️

 

*M S*

No comments