Breaking News

Soldiers Family 65-66

Page 65&66

 


__”cikin sauri ammy Tasha gabanta tana kuka tace, “ba abunda zakiyiwa zaraah domin alkhairi tayi basharri ba Kuma muda Kika zalunta Kuma alhalin ba muda laifin komai wanne hukunci kike tunanin Ubangiji  zai miki? Abbana shine ya miki laifi kuma abisa k’addara shinke bakya d’aukar k’addara ne? Shiyasa kike jayayya da hukuncin Allah har Kika halakaddakanki, shiru ammy tayi saboda kukan da yaci k’arfinta kana tace, “maye appey yayi miki da zaki nisantashi daga zuri,arshi? Kawai daya aurawa d’ansani? Miye mijina yayi miki kawai dayaso y’arki? Kekuwa wacce irin uwace? Shiru tak’arayi kamun tace, “shikenan duk abunda kikayimun Ni nayafe Miki domin koma yaya kike ked’in mahaifiyatace sai dai inaso kisani wlh muddin Ina numfashi ba,abunda kika,Isa kiyiwa zaraah Kuma Habeeb da mahaifinshi dakika cutar kije ke da hakkinsu Idan Zaki iya sauran laifuka Kuma keda maliccinkine bazan gusheba wurin tayaki da addu,a gun Allah yayafemaki Amma kisani inadanasanin kasancewarki uwa agareni, tak’arasa maganar cikin wani irin kuka mai Æ™onarai, hakan Kuma yayi daidai da wata irin girgiza da gidan yad’auka duka wadda tafi wadda yayi da farko lokacin da su mama sukashiga ciki, wannan ta banbanta domin Yar gini ke fad’owa cikin sauri bibo yace, “ba lokaci fa duk Wanda wannan ginin ya rutsa dashi wallahi sunanshi gawa kowa yayi k’ok’arin fita,,aiko ko bakinshi bai rufe ba suka shiga fira cikin sauri,,, Alyasat ya d’auko mama yayi da alhassan ya rik’o hannun abbe da Jalaludeen domin duka sunyi mutuwar tsaye Zeenah kuwa ko motsi batayi ba kuka kawai takeyi itada ammy saye kan kuwa ammy ya runguma ajikinshi yana son fitowa da ita yayin da ameesh,kan  yarik’o Zeenah

 

D’agowa zeenah tayi tace, “kufitoda mahaifiyarku ameesh,,kauda kanshi gefe yayi kamun yace, “munfi buk’ata kida antyn ma,Isha ahalin yanzu bana da lokaci” Dan Allah muje yafad’a Yana shash,shekar kuka,ammy kuwa ganin gidan naneman ruftowane yasa tayi sauri rik’o mahaifiyar tasu Amma cikin rashin Imani bazato ba tsammani Didi tafincikosu daga ita har Sayetkan dake rik’eda ita ta duk suka runtuma cikin ginin dake ruftowa kasa na darewa Yana fad’awa cikinta,,,aikin zafin mana ummansu Maheer ta figisu tare da ingizata ita suko tafitodasu,suna gama fitowa duka gidan na K’arasa rubtawa (Didi anzama tarihi dukkanin sharrinta yakoma kanta Bata anfana dashi aduniyaba Kuma batasan saka makonta lahira ba Allah yakaremu daga matagun k’addarori ya kare Mana imaninmu Kuma yabamu ikon d’aukar k’addara me kyau ko akasinta Dan alfarman sayidina rasulillah 🤲 (s.a.w)

 

 

Dukkansu kuka sukeyi ba mai rarrashin wani cikin bakin ciki dakunan Rai musamman ammy Wai ace mahaifiyarka ce zata iya cutardakai da duk Wanda yace Yana sanka “innalillahi wa innailaihhiraji un Allah humma ajirni fimuseebati wa ahaleeqni khairan minhaa 😥”

 

Ganin kowa dai zuciyarshi taraunata sosai yasa Zeenah rarrasarka kana tashiga Basu Baki itada ummansu Maheer hakan suka samu kowa yad’an tsagaita kana suka d’unguma zuwa gidan zeenah acan duk suka sauka,,,,dakyar ummansu maheer da zeenah suka samu ammy tayi sallah tayi wanka,,ganin wannan tashin hankali ya hana kowa walwalane yasa ummansu Maheer Kiran bibibo d’in tayimasa wani magana bayan tagaya Masa abunda takesan fad’a masane Takoma cikin gidan shiko yafita,,bajimawa Kuma yadawo dakanta takarb’i abunda ya,aikeshi nema tashiga had’a juice meshegen dad’i tasaka k’ank’ara aciki kana tabawa kowa da kanta takama biyarsu d’aya bayan d’aya tana Basu Kuma dolenka da anbaka kashanye har ammy da Mama Alyasat su Suhaif duk dai Wanda abun yashafa sai da yasha wannan had’in,,ai kamar karsu gama shanshi gabaki d’aya kowa yakoma kamar yadda yake kamun su baro Dubai cikin farin ciki da walwala duk anshafe musu abunda yafaru,,,atake firar yaushe gamo tafarke atsakaninsu inda ammy da mama hadda wasu yammata su ukku jikokin zeenah akashiga kitchen domin sama musu abunda zasuci cikin k’ank’anin lokaci kuwa suka had’a lafiyayyen girki irinna indiyawa medad’in gaske.

 

Suna kitchen d’in suna aiki alyasat namusu sintiri shidai Kar,awahalar Masa Mata duk abunda mama tad’auka zatayi yakarb’e jiyake kamar yamaidata ciki danso gawata muguwar Sha,awarta dake azazzalarshi kamar yaci Babu,,ammy tayi motarshi harta gaji seya tafi yadawo su Yusuf kuwa dariyarsa kawai sukeyi suna fadar suma dai bazasubar indiyaba sesun angwance,,akasaka dariya gabaki d’aya kowa kaduba Yana cikin farin ciki da walwala ahakan hardai aka kammala girkin,,,a dining ma saida akayita barkwanci kamun  akammala cin abuncin adawo babban perlon gidan Kuma abun gwanin Sha,awa Zeenah kuwa kamar tazuba ruwa ak’asa tashi saboda farin ciki domin kallon Yar cikinta takeyiwa ammy tamantamasam dacewar Yar yayartace.

 

Sai da dare yayi kowa yakoma bedroom d’in da,akabashi ya kwanta mama da Rasheeda d’aya daga cikin jikokin Zeenah d’aki d’aya suka d’auka yayin da ammy da Zeenah suke a d’aya suna firar yaushe gamo.

 

D’aya É“angaren kuwa na mazanne hadda bibibo acikinsu duk da sunsan ba mutin bane Amma basajin komai akanshi hakan suka sake su dukkansu a babban perlon inda aka saukesu suna fira,,Amma ummansu maheer tajima dayimusu sallama takomawarta saboda bibibo yagaya Mata abunda kefaruwa maheerah.

 

Firasukeyi kawai tsakaninsu hadda Alyasat sarkin miskilanci yau yaware sai fira akeyi,

 

“Gaskiya fa ninayi kamu a Indian Nan” cewar Lateep Yana dariya,tofa 🤔 kace, “India zamu rak’ashe kenan Waka kama” cewar Alyasat,kamun Lateep d’in yayi magana Alhassan yace, “wallahi yaya sat wannan yarinyar wadda ke sanye da kananun kaya wadda Bata rufe kantaba Dan wallahi naga Yaya Lateep Bata kallont…bek’arasa yaji saukar jifa abakinshi cikin sauri ya goce Yana dariya,,,shiko Zaid sarkin rashin walwala yaushene da murmushi Yana fad’ar Aiko Yaya Yusuf yayi kamun domin har aikena akayi d’azun nakarb’o contact d’inta,,dariya duk suka saka inda Yusuf ya waro Ido Yana fad’ar Zaid yaushe ka koyo surutu ganinka shuru2 yasaka nayi sirri dakai Amma kaima kakoma me bakin uku ko? Aiko sukace bazasubar dariya ba.

 

Shidai bibibo Yana gefe Yana kallonsu se murmushi yakeyi domin ba karamin burgeshi sukeyi ba Kuma Yana ankare da Alyasat da tund’azu duk da ya sake ana fira dashi Amma yatabbatar cewa atakure yake saboda jefi jefi yakan d’anyi tsaki Kuma yana dafe matarsa.

 

Alhusain ne yazo kusan bibibo yazauna kana yace ya maheer,,na,am bibibo ya amsa Yana kallonshi.

 

“Please Yaya Maheer Dan Allah kakoma maciji nagani Allah inasan ganin maciji Amma fa inajin tsoronsa shiyasa banama tinkararsa,,,dariya sukayi dukkansu hadda bibibo yace kana soja kakejin tsoron wata dabbar? “Eh mana ya maheer to inya cuttadanifa? Hakane Kuma cewar Maherr yak’ara dacewa Toni baka tsoronna cutardakai kakeso nazo maka macijin?

 

Kowa shiru yayi awurin sunajiran amsarda Alhusain zai bashi kawai se suka tsinkayo muryarshi Yana fad’ar nasan cewa bazaka tab’a cutar dani ba har abada baniba kowanina bazaka cutarba tunda kake da kyakkyawar zuciya koda gani sai kai zanzauna bazanji tsoro ba duk da nasan bajinsinmu d’aya ba Amma ibada yak’ini akanka 💯 baniba harmada Yan uwana dukkanmu munsancewa kaid’in na musamman ne ko,acikin jinsinku Dan Allah kadena cewa inji tsorinka ya maheer,,,wani irin k’ayataccen murmushi maheer yayi kamun yashiga kirgiza kanshi alamar tabbatar da zancen Alhusain gaskiya ne Kuma yaji dad’in dasuka yadda dahakan..suko dukkansu Y’an uwan nashi ajiyar zuciya sukashiga saukewa atare dajin dad’i kalaman alhusain.

 

Dukkansu had’a Ido sukayi suna murmushi kamun sumar da kallonsu ga bibibo Aiko sukaga harya zama wannan wasgegen macijin mematukar gima,,,Ido suka waro kamun Kuma sushek’e da dariya ganin alhusain dake kusanshi yawani takure Yana kallon macijin,,,shiko bibibo gabaki d’aya kanannad’e Alhusain yanabin jikinshi duka kana ya sauka yayiwa ko wannensu hakan Yana Hawa cikinsu Yana sauka se murmushi sukeyi suna tab’a jikin macijin kamun Kuma yasauka daga jikinsu yakama wata irin katuwar Dorinar ruwa daganan Kuma yakoma damisa  hakama yakoma Zaki yakoma Kura Kai dabbobi kala kala yarink’a komawa suko sedariya sukeyi cikin nishad’i,,sunjima ahakan kamun bibibo yadawo saurayinshi kamar yadda yake zaune daga farko,,kallon alyasat daketa had’a gumi yayi ya tabbatar da Sha,awar matarsace ke dawainiyadashi mik’ewa yayi Yana dubanshi yace sirikina yafad’a cikin tsokana,,, murmushi Alyasat yayi kana yace na,am babban yaya,,Aiko su Yusuf sukace mizasuyi inba dariyaba,,,shima bibibo murmushi yayi kana yac, “zo muje yayi gaba” tashi Alyasat yayi yabi bayanshi su Lateep ce tsokanar Shi sukeyi,,,suna fita suka nufi bedroom d’indasu mama suke shidai Alyasat nabiye dashi kawai domin baisan Ina suka nufaba,,,suna shiga yaga mama kwance da,itada wata budurwa Amma yadda yaga kwancinta saida hajiyarshi ta harba dak’arfi shiko bibibo ko kallon inda take beyiba yace mishi d’auko matarka muje,,ba musu Alyasat yasaka hannu yad’auko mama Yana d’aukota tana bud’e Ido domin ba bacci takeyiba ganinshine kuwa bakaramin dad’i yayimata ba hakan yasa ta kankameshi kamar wadda zata Fad’o shima yak’ara matseta ajikinshi,,ganin hakan yasa bibibo d’aukesu duka yab’ace dasu bediresu ko inaba se wani k’ayataccen hotel room mai shegen kyau ya diresu tare da juyawa tafita yaje yabiya kud’in d’akin kana yayi yafiyarshi gunsu Yusuf,,,suko Yana fita suka k’urawa juna Ido kamun suyiwa juna wata irin wawuyar runguma suna sauke numfashi tare da fad’ar I miss you atare kana suka had’e bakinsu wurida d’aya suka shiga kissing din juna kamar zasu cinye bakin juna.😂

 

 

 

 

 

 

*SOLDIERS FAMILY* na kud’i ne nera 500₦ kacal 👌 ga duk me buk’atar complete kuma 700₦ Idan kinshirya siya Zaki iya tuntub’ar wannan number 👉 07937092176 on WhatsApp kokuma kikira wannan number 👉 08107819124

 

 

 

 

 

 

 

 

Autar Alheri ✍️

 

*S F*

 

No comments