Breaking News

Tabarmar Kashi Book 2 Page 36

TABARMAR KASHI*


Book 02 Page 36

A nutse da wani irin sanyi ya maida dubansa gareta,wani sashe daban take duba bashi ba. Har gasan ransa yaji bazai iya tafiya ya barta cikin office din ba, kamar bai gaji da kallonta ba
“Madam” ya kirayeta da wani irin amon sauti me laushi da sanyi. Tsigar jikinta tadan zuba saboda canzawar sautinsa a yau din, amma sai ta fuske kamar bata jishi ba.

Ya matsu ya Kalli qwayoyin idanunta,yanason yabar mata wani saqo me nauyi da narka zuciya,kamar yadda ya sani, sauran mata ma suka sani, idanunsa nada wani irin mugun tasiri da maganadisu me qarfi dake narka zuciyar mata da yawa,ya kuma tafi da tunaninsu. Uwa uba yana matuqar qaunar idanunta, tun a shekaran jiya daya qure musu dukkan kallo harda wanda ya wuce qa’ida ma idan akwai,kallon cikin idanunta na tuna masa yanayin da suka shiga gaba daya shi da ita a wancan ranar,yadda komai ya canza cikin lokaci qanqani. A ranar ya fara tabbatar da kyawun qwayar idanun nata.

Hannunta ya saki kawai sai ya rigo qugunta, sai gata
tsaye a gabansa suna fuskantar juna. Kanta kawai ta
sunkuyar ta hanashi kallon fuskarta bare akai ga idanunnata, abinda ya hanata kowanne yunquri na qwatar kan ta shine Karantar da tayi saima tana wajen

“Da mutane fa a gurin nan” ta fada qasa qasa wai don
kada saima din taji, saidai abinda bata sani ba,yadda tayi
cooling voice dinta ya sanya yaji tsigar jikinsa gaba daya
ta tashi,yadan ja wani numfashi hade da sheshsheqa

“| know, just i want to look into your eyes……please” jin
abinda ya fada ya sanyata maida idanun nata ta kulle
gam, tana nufin ba zata bashi wannan damar ba,har cikin zuciyarta abinda tayi niyya kenan, indai idanunta yakeson kalla zai bushe a wajen saima ce kawai ta zalunceta data ci gaba da zama a gurin, tana pretending kamar bata ganinsu,ita kuma tayi imanin dukka hankalinta yana kansu,banda ita da tuni ta tureshi daga riqetan da yayi.

Zanen fuskarta ya shiga kallo daki daki, tun daga
kyakkyawan eye brows dinta,miqaqqen hancinta mar
tsaho da tudu, shape din idanunta da kuma eye lashes
dinta masu tsaho ya dire zuwa kyawawan lips dinta da
suke yawna fuzgarsa,duk yadda yaso ya daure ya kasa

“Your lips look so lonely, would they like to meet mine?” Babu shiri ta bude fararen idanun nata tarr bisa fuskarsa da suka cika da tsoron kada ya aikata din. Qaramin murmushi ya subuce masa. Fuskarta ya kama ya hade fuskokinsu guri guda, abinda ya Sanya saima ba shiri cikin rawar hannu ta kwashe takardun da bata gama tabbatar da ingancinsu ba ta bude qofa ta fice

“Am dying to have my lips on yours one chance please!”

Duka garfinta ts tattaro ta turashi tana yin baya,numfashi take maidawa hadi da sanya hannunta daya tana gyara zaman hijabinta

“Why all these ne wai?, why?” Ta tambayeshi cikin zafin rai, zuciyarta na gaya mata shi kuma jikinta kadai yakeso, sha’awar ta kawai yakeyi, bashi da aiki sai burin son taba jikinta?.

Da baya da baya yaja ya jingina jikinsa da bango yana rufe idanunsa, tuni kowacce jijiya ta jikinsa ta amsa

“You stole my heart” ya fada can qasan
maqoshinsa,labbansa kadai sune suka motsa. Itadimma lallabawa tayi ta zauna zaman kujerun dake gurin, tsahon wasu mintuna shuru ba wanda yace da kowa komai,yayi ta maza yana qoqarin binne komai a ransa ya mige ya tsaya saman qafafunsa ya fara takawa

“Let’s go” ya fada a taqaice, sai ya kasa ci gaba da tafiya sanda ya isa bakin qofa,ya tsaya har ta qaraso. Lalubar hannunta ya sakeyi ya hade da nasa,ta ja zata fincike yace

“‘Kina cirewa ban yafe ba” laqwas taji zuciya ds gangar jikinta tavi, bata da wani sauran zabi sai ci gaba da binsa da tayi.

Kamar ya koma haka yaji lokacin da suka isa hall din, bai dauka zaman meeting din da mutane da yawa ba haka idanu sukayi caa a kansa shi da ita dukka suka mige suna masa barka da zuwa. Da ka ya amsa yana jin nutsuwarsa na raguwa. A nutse y jawo hannunta ya jawo kujerar da aka tanada saboda zaman CEO ya matso da ita gabanta,ya zaunar da ita a kai sannan ya koma bava ya tsaya yana dafe da kujerar, tamkar yaron gidan da uban gidan nasa.

A schedule na meeting din one hour ne meeting ne, amma cikin mintuna talatin ya sallamesu. Yadda suka shigo yanzunma haka suka koma office din yana riqe da hannunta,wannan shi ne ya zama muhimmin topic na tattaunawa a cikin company din a ranar.

Tunda suka dawo duk bavan minti dava zuwa biyu sai ya daga kai ya kalleta. A duk sanda ya kalletan kuwa sai wani abu mai qarfi ya fusgeshi tattare da ita. Wasu lokutan har sai ya tsaida abinda yakeyi ya zuba mata idanu yana kallonta cikin wani irin nutsuwa da wank lamari me matugar qarfi kaifi da kuma zurfi cikin zuciyarsa.
Bata fahimci komai ba, kawai ta fuskanci yau din yana ta sanyata zurga zurgar dauko wancan ajjiye wannan.
Yayi amfani gwarai da wannan damar wajen samun damar morewa kallonta ta yadda ranshi yakeso.

A karo na barkatai ya sanyata dauko masa wani book cikin tsararriyar book shelf dake gefen table dinsa,saidai akwai tazara tsakaninsa da ita. Sanda ta miqe don isa gurin sai ya daga kansa gami da ajiye biron dake hannunsa,a hankali yake sake qarewa tafiyarta kallo, komai nata unique ne, bai taba cin karo da mutum me uniqueness irin nata ba.

Ta maida hankalinta sosai tana duba masa littafin da
ya aiketa ta dauko din,ba kuma wai don zaiyi karatu bane,a’ah,kawai yanason yaga wannan kyakkyawan takun nata. Yadda take tura baki da bata rai saboda bataga book din ba ya sanyashi sakin murmushi yana jin wata gajiya da kasala suna bin sassan jikinsa,wanda shi kansa yasan ma’anar hakan a tattare dashi. Ya miqe a nutse yana sanya hannayensa a aljihun wandonsa, har ya isa gareta bata sani ba. Daga bayanta ta tsaya, dab da ita,tazarar data rage a tsakaninsu duka baifi taku daya rak ba.

Muryarsa ya sassauta sosai ya kuma rage tsahonsa yana son daidaita kanshi da ita ya dawo da kansa saitin kafadarta,cikin laushin murya tamkar wanda yake a buge yace

“Am so tired,can you give me a hug pleasssssse” cak ta dakata daga abinda takeyi tsigar jikinta tana tashi,yadda yayi maganar saitin kunnenta ta shigeta sosai,sam sam bata tsammaci tsaiwarsa a wajen ba,saita qame a tsayen, bata juyo ba bata kuma ci gaba da neman littafin ba. Ragowar taku dayan da ya rage shi ya qarasa, cikin sanyi da tashi ya zura hannuwansa ta saman cikinta.va kuma jawota a mugun slow ya manneta da jikinsa. Kamar wadda aka yiwa allura ta zabura tana juyowa da sauri da nufin kufcewa,saidai kuma babu damar kuncewar saboda yayi mata zobe gaba da hannunsa. Kai tsaye idanunsu suka jone guri daya,ya lumshe nasa idanun tare da budesu lokaci daya yana sakin wani lafiyayyen siririn murmushi da ya sanyata kasa jurewa kallonsa saboda wani tsalle da zuciyarta tayi ta kuma ce mata

“He was elegant” kanta takeson kawarwa amma ya hanata wannan damar,ya kama fuskarta ya riqe da kyau yana mata wani duba dake dauke da tarin ma’anoni masu wuyar fassarawa,wanda yakejin tamkar bakinsa bazai iya fadinsu ba

“Hold me please hold me so close, that your breath become my oxygen” ya fadi numfashinsa na fita da sauri da sauri saboda yadda ya kwadaitu da labbanta. Bai iya controlling kansa ba kuwa sai daya dangane da bakin nata kaman dazun,ya shiga sauke mata hot kisses ya hanata katabus da dukka wani yungurinta na qwatar kanta. Har tsahon wani lokaci kafin ta samu nasarar tureshi, taja baya tana kallon idanunsa da nata idanun da hawaye ya cikasu taf yana gab da gangarowa. Bai wani damu da kalar kallon da take masa ba, yafi damuwa da yadda bata qaunar ya rabi jikinta,wanda a yanzun yakejin cikin zuciyarsa bazai iya wani dogon zamani ba tare da ya rabeta ba,ji yake kamar wani magnetic ne a tsakaninsu. Murmushi ya sauke mata da idanunsa da suka sakeyin wani irin laushi

“Your eyes driving me insane madan ki daina kallona haka” ya furta yana gyara zaman sumar kansa da yatsunsa

“Only you can give me that feeling” ya furta a nutse idanunsa har yanzu cikin nata idanun da bata iya gani sosai saboda qwallar cikinsu.

Ba tare da kowannensu ya sakeyin komai ba sukaji an tura qofar office din, sautin takalma masu tsinin dunduniya ya soma tashi kafin daga bisani muryarta ta bayyana cikin sallama.

Har cikin jinin jikinsa sai da yaji wani abu ya tsarga,lokaci daya gabanin yakai ga juyowa dukka wata walwala da nishadi da ya samu a yanzu suka fara narkewa. Säahar ke fuskantar qofa,don haka da ita idanunsu ya fara jonewa.

Fara tas din mata, wanda har haskenta yaso zarce haske na dabi’a,tana da wani irin kyau shimfidadde akan fuskarta,saidai kuma a gangar jiki, irin matan nan ne da basu da hips kwata kwata,duk kuwa da cewa ita din ba wai siririya bace amma rashin hips din nata bayyananne ne ga duk wanda yasan tsarin halitta a gurin mace. A shape gown ce a jikinta ta wata shadda ‘var mali komai na jikinta cike yake da ado da gawa

“Sãahar, nanny N ko?, i see” ta furta tana jifan sahar da wani irin kallo, zallar kyawun da bata tsammaci samunta a tattare da ita ba yana bugar son bugar da ita,tako ina tana hangen wasu qualities kai tsaye daga gareta ta cikin hijab dinta kai tsaye, kyan suffa ciki da waje wanda cikin qasa da minti biyu wani azababben kishinta daya ninka wanda take ji a kanta kafin ta ganta ido da ido va lullubeta.

Farat daya kwanyar säahar tayi mata recalling muryar, take kuma ta fahimci wacece, idanunta ta maida kan toufeeq wanda tashi daya kamanninsa suka canza da wani irin bacin rai da zallar tsana

“Barka da warhaka uban ‘yata” ta fada tana rangaji tare da jifansa da wani irin shu’umin kallo da tasan yanaso ada

“Kar ka damu yanxu am single, naje na dawo kuma dukka don saboda kai” zare idanunta sãahar tayi daga kansu,tanaji a ranta bata da bugatar sauraren kowa a cikinsu,bata son jin komai daga bakinsu, don ba matsalarta bane, kowa yaji da matsalarsa, kuma kowa ya rige damuwarsa don haka ta fara takowa da nufin ta isa ga gurbinta na dazu ta dauki takalminta da hand bag dinta.

Cikin jikinsa yaji tahowarta, zuciyarsa kuma ta gama gaya masa abinda zatayin, ficewa zatayi ta barshi da ameesha,fuskar da ya jima da shafe babinta cikin rayuwarsa. Rabuwa yayi da ita har ta garaso dab dashi, bata taba tsammanin yana ganinta ba,sai kawai ji tayi ya tattarata cikin jikinsa yayi mata wata kyakkyawar runguma. Mamaki ya hanata motsawa, sai kuma yadda kunnuwanta suka jiye mata adadin qarfin bugun zuciyarsa da ya qaru matuqa, ala dole tayi luf tana jin bugun sosai cikin kunnuwanta,abinda zai shaida maka lallai yana cikin fushi

“‘Baki yarda da gargadin dana yi miki ba?” Duk da zuciyarta ta qone sosai da kalar rungumar da ya yiwa sãahar din wanda ita daya tasan gardinta da dadinta, da
kuma sirrin dake tattare da wannan ingarman girjin nasa
data jima tana kewa,ta kuma gaza samun
kwatankwacinsa acan inda take harin

“Babu me rabani da kai sai Allah moha….. you are mine
forever” cikin nutsuwa ya dauke kallonsa daga
kanta,yasa hannu daya ya jawowa sãahar kujera ya
zaunar da ita a kai

“‘Huta a nan” ya fada cikin kulawar da sai da Ameesha
taji kamar numfashinta zaiyi skipping na wasu daqiqu.
Tasan toufeeg ciki da bai fiye da kowa,soyayyarsa
kulawarsa da tsantsar iya ririta mace wani abune da ta
gama lalube daga gurin kaffff mazan data hadu dasu
bata samu wanda yake da koda rabin rabinsa baya
tattara abubuwa masu yawan da sai an tara maza dari
ba’a samu qwaya daya rak irinsa ba.

Wayar da ake kiran security kawai ya danna ya koma
ya tsaya kusa da sãahar kamar wanda yake bata kariya

“Inason ka bani dama mu fahimei juna, nayi maka kuma
bayani mu yafewa juna na dawo na kula da ‘yata” runtse
ido yayi,ju yayi kaman ta soka masa wuqa a qahon
zuciyarsa,har bayason ta furta fadeela diyarta ce.

Bazai iya bata yawun bakinsa ma a kanta ba sai yaja waya yayi kira zuwa wajen saima

“Come in” ya fada a kausashe yana ajjiye wayar saima da security uku suka shigo, mata biyu namiji daya
Migewa yayi sosai iyakar tsahonsa yana dubansu,hatta säahar satar kallonsa take ta qasan ido,yadda lokaci daya ya koma Muhammad toufeeq jarma din data sani farkon haduwarta dashi, kaman ba shine yanzun nan ya gama karyar da wuya da murya a gareta ba

“Who allowed that women to enter?” Kallon kallo aka fara a tsakaninsu,kowa yana tsoron magana yana kuma tsoron gaddarar yau ta fada kansa ta kora daga aiki, duk da cewa tunda ya dawo din ko ma’aikaci dava bai kora ba.

“We are sorry sir, don Allah, bamusan bakason ta shigo ba” daya daga cikin matan tayi qarfin halin fada zuciya a karye

“Take her outside, and daga yau,idan na sake ganin gilmawar fuskarta cikin kamfanin nan ku tabbatar kun rasa aikinku” yana kaiwa garshe suka cafketa su biyun,don kuwa ba zata jaza musu asara ba,don kaf fadin kano dama Nigeria basajin akwai company da zasu samu me dadin aiki da kuma albashi me tsoka wanda yayi kamanceceniya da kamfanin MT JARMA.

“Ni ka wulaganta haka?” Abinda ta iya fadi kenan saboda tuni suka garasa yin waje da ita. Sai a sannan ya waiwayo ga saima ,wadda kallon idanunsa kadai ya sanyata taji kamar zata saki fitsari a wandonta

“You are fired” ya fada kansa tsaye. Ya jima yanason rabuwa da zaman yarinyar cikin office dinsa,amma ya rasa da wanne irin laifi zai kamata,sai yanzun da wannan dalilin yazo.

“Nan din ba Bar bane ko club da zaki dinga barin mata anyhow suna shigo min,bayan kin sani tare muke aiki da iyalina a ciki” yayi mata bayanin yana juya baya ba tare dava dubeta ba. Kuka ne ya hanata cewa komai, kawai saita juva da gudu gudu ta fice saboda ta gama tozarta tako ina a gaban idanun matar da take bala’in jin zafinta da tsananin kishinta,wanda ita sam saiman bata cikin damuwarta a rayuwa.
[28/09, 9:21 am] +234 903 576 5837: “HUGUMA*

_TABARMAR KASHI_*

No comments