Breaking News

Tabarmar Kashi Book 2 Page 47

Book 02Page 47


To dama shi din me neman kuka ne aja jefeshi da kashin awaki inji hausawa lea, maida hannuwansa yayi ya rufeta ruf

“Na baki amanar kanki da kanki, kiji tsoron Allah ki kulamin da kanki,Allah ya sani na barku kuyi tafiya ne a bisa harshen maji, saboda duk duniya babu alfarmar da zata roga na kasa yi mata, ki kularmin da amanar kanki da kanki,i love you and am gonna miss you” wadan nan sune kalaman da suka yiwa säahar abokan zama har cikin jirgi. Yana tsaye bai matsa a gurin ba har jirginsu ya tashi,ya kuma nausa dasu qasar Germany ba tare da Muhammad toufeeq jarma yasan abinda zasuje yi can ba.

_tofa, Allah ya kiyaye tsautsayi da asara,muje zuwa
dai,munata gangarewa_ ??

*_GERMANY_*

HOMBURG

Zweibrücken Airport_

K’arfe biyu agogon qasar Germany jirginsu ya
sauka a Zweibrücken airport dake homburg, bisa
jagoranci da kulawar asibitin wanda sajjad ya hadasu da dukkan wanda ya dace da zai musu jagora akan komai kafin isowarsa da ya shirya yi ba tare da ya gayawa sãahar din ba suka sauka a leaonardo hotel dake kusa da Saarland university hospital main campus, inda anan ne suka suka shirya ganin prof Dr med Klaus fassbender wanda shine shugaban department na neurology and epileptology na jami’ar gaba daya.

Miss Sophia da mr Stephan sai da suka tabbatar da komai yayi settling, hatta da layin wata na kira suka bata sannan suka ce su huta, sai zuwa gobe ne appointment dinsu da Dr Klaus.

Ta window din dakin hotel dinsu akwai kyakkyawan view na garin Saarland,ta fidda kayansu tana ajjiyewa a inda ya kamata, ita kuwa fadee na daga can tana kallon garin tana zuba mata surutu har ta gama,gamawarta nata yayi dai dai da isowar ma’aikatan restaurant na hotel din da lunch dinsu.

Karba tayi tayi godiya ta rufe qofar tare da kiran fadeela tazo taci. Kusan duk wani motsi na fadeelan na kan idanunta,zuciyarta nata karyewa,sai a yanzun takejin kamar tayi wauta data taho gari ya gari ita daya da yarinyar mutane, zuciyarta a raunane tana duban yarinyar,Allah shine masanin gaibu, zata tashi ko kuma komai zai sake rikicewa ne?,ko kuma ita zata zamo sila na garuwar ciwon nata?. Da sauri ta kawar da wannn tunanin ta hanyar kiran sunan Allah, ta sauko ta jawo abincin suka fara ci tare.

Ko da suka kammala layin ta saka a wayarta,afifa ce mutum ta farko data fara kira sannan maama dinta,sai kuma mahaifinta Dr girema

“Baki kiramin abby na ba” fadeela ta fada tana karyar da kai. Dan murmushi ta saki tana juya wayar a hanunta,fadeela nason sakata yin abinda batayi niyya ba, amma tausayin yarinyar takeji, kowanne motsi na yarinyar tausayi yake bata,ta kuma kawota qasar da babu kowa nata sai ita,itace uwa da ubanta,to amma bata da tabbacin tana da number nasa a wayarta,don haka ta fara kiran nadeeya.

Kiran nadeeya din shi ya dauke hankali fadeelan daga kiran abby din,suka dinga hira kafin daga bisani sãahar ta karba wayar

“Nadeeya ki turawa fadee number abby” dariya nadeeyan ta saki a boye

“Fadee ko ummin faddee, aunty N kada dai ace har kin fara missing yaa moha?”

“Kinga sister nadeeya,kin fara rainani ko?”

“Tuba nake aunty N,waye ni da raina matar babban yaaya,so kike yayi tamaula da ni?, already na miki saving number din nasa a wayarki saboda rana me kama da wannan” sai kiran ya yanke. Wayar kawai ta sauke tana kalla,sai kuma murmushi ya subuce mata, yaushe har nadeeya din tayi saving number bata sani ba? ,sal ta fara binciken contact nata, amma ku suna me kama da nashi babu,daga qarshe tayi finding out suna guda daya da iya saninta dai ba ita tayi saving number din ba FOREVER. A bisa dole ta saki dariyar da batayi niyya ba,ko yaushe ya zama forever din oho?. Tana shirin editing ta canza suna taji fadeela na kiranta tazo ta kunna mata tv,dole ta ajjiye wayar ta fita gurinta.

Washegari miss Sophia da mr Stephan ne suka sake dawowa, already ta shirya saboda tasan da zuwan nasu. Tun daga yadda suka samu asibitin ta tabbatar afifa ta zaba musu gurin da yafi dacewa. Sun gana da Dr Klaus ya kuma yiwa säahar dukkan tambayoyin da suka dace,ya shirya komai ya kuma bada gwaje gwajen da za’a fara yi mata kafin a fara zancan surgery.

Cikin kwanaki hudun duka basu wani zauna ba,ta bada hankalinta dari bisa dari akan aikin fadeelan da zirga zirgar asibitin, don ma wasu abubuwan da yawa basu zasuyi ba daga asibitin ne. Kwana take saman abun sallah tana addu’a,sunyi waya da maji tun randa suka iso da daddare, kuma daga ita har afifa suna samun update na yanayin da ake ciki, dukansu kuma neman visa ta shigowa Germany sukeyi kafin ranar aikin,saidai dukansu basu gaya mata ba.

Cikin kwana biyar kacal komai ya kammala, Dr Klaus kuma ya tabbatar mata part na brain din fadeelan dake bada matsalan seizure din nata za’a iya removing nasa,so ta cancanci surgery, amma kafin nan zasu bata treatment na sati biyu, zasu rigeta a asibitin. Kukan farinciki ne ya qwace mata, bakinta ya kasa gajiya da addu’a da fatan samun nasara a gareta da fadeelan baki daya. A ranar suka bata daki da komai da komai, su zasu dauki nauyin kula da ita,basa buqatar majinyaci,akwai qararrun ma’aikatansu da zasu bata duk wata kulawa data dace. Tayita roqon alfarma su barta gurinta amma suka bata haquri kan haka tsarinsu yake,dole a ranar ita kadai ta koma hotel, saidai sam bacci yaqi zuwar mata,kewar fadeelan takeyi sosai,sai tayi alwala ta hau abun sallah kawai ta tsaya gaban ubangiji.

******Bai taba kawowa zata dauki wadan nan kwanakin ba tare data nemeshi ba,cikin kwanakin gaba daya karsashi da komai nasa ya ragu,yana jin kamar yayi missing wani part na jikinsa, komai yana yinsa ne kawai cikin qarfin hali da juriya,bai taba kawowa cewa ta kama zuciya da rayuwarsa har haka ba sai a wannan lokacin

“Wanann wanne irin abu ne?” Ya tambayi kansa da kansa a wani dare da bacci ya qauracewa idanunsa. A nutse ya miqe ya sauka daga saman gadon nasa,yana sanye da wasu silk pyjama bagaqe da suka fitar da zallar kyansa cikin hasken dakin da bashi da yawa,yana bugatar wani abu da zai debe masa kewarta,yana jinsa kamar mara lafiya, kowanne sashe na jikinsa yana bugatarta. Slippers dinsa ya zura,ya miqa hannu zai dauki wayarsa dake kan bedside drawer sai wanilabu yaja hankalinsa. A nutse ya miqa hannu cikin wani glass bowl dan garami ya dauko wani abu. Dan kunnenta ne,dan kunnen da ya fadi a wancan ranar cikin elevator,a wancan lokacin da yake matuqar jin zafi da haushinta, zafin da ya tabbatar yana jinsa ne a sannan saboda yadda zuciyarsa ta kasa jin qinta a ransa kamar vadda yakejin na sauran mata,yana tsoron faruwar wani abu tunda har zuciyarsa ta kasa jin wannan emotion din a kanta sai wani feeling na daban. Wannan abun dai da yake gudun faruwarsa sai gashi a yanzu ya tsinci kansa dumu dumu a cikinsa, dumu dumu din da ko gefenta bai taba isa ba sai a wannan lokaci, mummunan kamu na soyayya me wahalar cirewa a rai, soyayyar da ya fuskanci tamkar tanason jefashi zuwa ga son maso wani. Yana shaugi da burin ganin martani me zafi daga kan fuskarta,duk da ya sanya zuciyarta tayi laushi yadda ya kamata, amma mizanin soyayyarsa a zuciyarta yana hasashen kamar bai kai ba,yana tsoro da fargabar sake, afkawa wani ramin da baisan iyakacin zarfinsa ba a kanta. A kullum ya tuna kulawa da tattalin da ya bawa ameesha da sakamakon da ya samu daga baya sai gwiwarsa ta karye akan lamarin soyayya. Kissing na earring din yayi, sannan yasa hannu ya jawo drawer din ya zura,baikai ga rufewa ba dairy dinta daya dauko yaja hankalinsa.

Qasan ransa ya gayawa kansa ya samu abun debe kewa,sai ya fiddoshi yana budewa,ya sake bude page din farko ya maimaita rubutub rannan, sai ya zare slipper din da ya sanya ya maida jikinsa kan gadon ya zauna sosai vana sake bude next page.

Kai tsaye a kuma tsanake ya fara bin rubutun dake shinfide cikin tsari da kuma qwarewa, tun daga farkon haduwarta da ADAM,a nan ya dinga gaza jure wasu abubuwan ya dinga jin wani abu me kama da zallar kishi yana tabashi saidai zuwa sanda zai kammala karanta labarin zuciyarsa da ma gangar jikinsa sunyi tubus

_Thats me,hurt in private, heal in silence,we fall, we learn we rise_

_My dear heart,one day you will heal to such an extent that you will smile as if it was never broken in sha Allah_

“In sha Allah” din shima ya maimaita a bayyane yana rufe bangon qarshe na littafin,fararen zagayayyu idanun nan nasa sun canza launi, kwanyarsa ta cika da abubuwa masu tarin yawa,ya mots lips dinsa a hankali

“We are all hurting and healing in silence, tabbas we go through one similar condition, i have made many errors in my life,but loving you is definitely the thing i have done right!” Ya furtawa kansa da kansa yana lumshe nasa idanun,tashi madubin rayuwar na haska masa,cikin jiki da zuciyarsa wani irin gamammen aminci da kanta yana gauraye jinin jikinsa, da gaske! Allah yaso wanke musu kowanne bacin rai da suka shiga,shi yasa ya jarrabesu a mabanbantan gurare da kuma mabanbantan mutane. Hikimarsa!, Ya hadasu zaman tare na har abada a sannan shine zasu Fi fahimtar muhimmancin funansu

“Exactly!” Ya fada yana bude idanun nasa. He really missed her,yana jin kamar zai zauce da son ganinta, me yasa tun tuni bai karanta diary din ba? ‚sai yanzu da tayi nesa dashi.

Saman gadon ya zauna sosai yana duba number dinta, saidai duka kiran da zaiyi matan a kashe layin,ya sani dama ba samunta zaiyi ba,kawai idanunsa sun rufe ne da son jin muryarta.

“A ina zai samu number dinta?” Itace tambayar dake masa yawo akai. Har zai kira nadeeya ya tambayeta sai kuma ya fasa gudun raini. Maji ya tuna, don haka ya maida akalar kiran nasa gareta, KARON FARKO da wani qulli ya warware daga tsakiyar kansa ba tare da ya sani ba. A dai dai lokacin kuma hajiya qarama tayi wata mummunar firgita cikin baccinta,ta kuma miqe ta zauna sosai saman gadonta a gigice tana dube dube.

Fadeela ta gani cikin asibiti, asibitin ya cika da yan uwa da abokan arzigi wai ana tayata murna ta warke daga ciwonta,yarinyar tana ganinta ta karbi wuga daga hannun säahar dake yanka mata fruit tayo kanta da gudu, tana tsaka da gudun ta farka a mafarkin.
Jikinta sharkaf da gumi ta sauka daga gadon,ko ina na jikinta rawa yakeyi tanason ta fassarawa kanta da kanta mafarkin. Kai tsaye ta isa drawer din data killace magungunan da take sauyawa fadeelan dasu,ta fiddosu gaba daya ta fito falonta dasu.

Zaman dirshan tayi saman carfet ta zazzagesu,ta kuma hau irgasu daya bayan daya tsaf har ta gama

“Turqashi” ta fada a bayyane tana goge gumin fuskarta.

Yau kwana d’ai d’ai har kwana sittin bata samu damar bawa fadeela maganin ba

“Ko warkewar ne ma a gaske ai sai tayi, tunda na zauna yarinya qarama tana son firgitani da kawomin tsaiko akan aiki na” ta fada a fili kamar wadda ke magana da wani.

Tattara magungunan tayi ta maida cikin leda tana rayawa a ranta yanzun nan komai duhun dare sai ta isa dakin fadeela ta aiwatar da shirinta.

Daxu daxu ta dawo daga Cotonou order din wasu atamfofi,bata da masaniyar ma fadeelan basa gidan yadda ta saba ba,sai kawai ta sauka a sashenta tana huce gajiya.

Mayafi ta yafa,ta kuma taka a hankali ta fita a sashen nata. Farfajiyar gidan tsit take,babu kowa sai hasken fitilu da kuma kukan qananun qwarika dake cikin tsirran dake baibaye da gidan.

Babu tsoro ko fargaba ta sanya spare key ta bude qofar falon ta kuma saka kai cikin takatsantsan. Bata tsava a ko ina ba sai dakin fadeelan, ta tura ta shiga ta sauke ajiyar zuciya ganin babu kowa,ranta ya bata yau a sassan toufeeq din zasu kwana kenan, don tana lissafe da duk sanda basu kwana a nan din ba suna sashensa

“Bagar matsiyaciya,kin kusa fita daga rayuwata, kin kusa barin gidan nan,gidan nan gidan meenal ne, toufeeq da abinda ya mallaka dama wanda ubansa ya mallaka duka na meenal ne da abinda zata haifa” ta sake fadi a fili cikin sumbatun da batasan tana yi ba.

 

Zafafa biyar
????????????
????????????
[04/10, 8:52 am] Mimah Yusuf: *HUGUMA*

No comments