Breaking News

Zafin Kai 85


85

Qarfe ukun Daren ranar aka samu nasarar yiwa DD allurar qarshe cikin guda ukun daya kamata ayi masa duk bayan kwana biyu ake daya sbd ba qaramin qarfin gaske qwayoyin sukaiwa jikinsaba hakama duk allura Daya kudinta ba qaramin firgici zaka shiga ba na jinsu Dan haka sai ranar su dd babba suka dawo hayyacinsu yanda ya kamata suna fatan farfadowansa kowane lokaci,

Ta bangare Daya Kuma suna cikin fargaba da tashin hankalin ta inda zaa fara masa bayanin uwar ‘varsa ta Bata baa ganta ba tsawon kwanaki biyu.
Zeenah gabaki Daya ta jeme a iya kwanakin biyu sbd tashin hankali da damuwa,

Ga batan Bena ga D a kwance ga Amnah can gida kullum kira takeyi tace a Bata mummynta suyi magana basuda mafita dai kame kame suke mata kullum sbd maganar ma yarinyar abari tasan ba’asan inda mummy dinta take ba Bata taso ba Dan kuwa zata iya shiga mugun halin da basusan ya zasuyi da ita ba.

Karfe 5 na Asuba daidai DD ya budewa idanuwansa dasukai nauyi ahankali batareda ya motsaba sbd jikinsa da yayi Wani irin nauyi na kwanciyar kwanaki,

Ahankali cikin kasala da rashin kuzari ya sauke sanyayyan numfashi ahankali tareda lumshe idanuwansa va sake budesu anankali

Abu na farko Daya fara zuwar masa Akai shine sunan Bena Wanda shi kansa baisan wane hali zuciyarsa take ciki ba a yanzu kanta dama shi
Kansa.

Dakin Dayake ya juya Kansa ahankali ya kalla ya mayarda idanuwansa kan sauran kayan monitoring heartbeat dinsa da sauransu ya tabbatarda a Asibiti yake Kuma tabbas Bata Nigeria bane musamman duba da blue kayan
patients din dake jikinsa.

Babu kowa a dakin Dan haka ya sake rufe idanuwansa Yana sauke numfashi ahankali
ahankali a Jere Yana son fara calming
numfashinsa kafin yafara kokarin tashi zaune tini alerm na dakin ya fara qara me sauti daidai
misali na Kiran nurse zuwa ga dakin.

Yana tashi zaune ana Bude kofan Dakin nurse ce ta shigo sai Naseer a bayanta da sauri suka shigo Naseer na wuce nurse din ya Riga Isa ga DD din Yana Jin Wani farin cikin ganinsa zaune.

Bai tsaya komaiba Yana Isa ya rungumesa sbd da Bai tashi yau dinba shikenan baa San ranar tashinsa ba har shekara zai iyayi a kwancen
Amma Allah ya amsa adduar su ya tashi.

D baida Wani qarfi ko Dadin zuciya Dan haka
idanuwansa ya mayar kawai ya lumshe yana
kasa motsawa daga zaunen har nurse ta
duddubasa taje ya kirawo likita har guda
biyu da Wani nurse Daya namiji aka taru aka
dubasa dakyau aka sake diban jininsa Akai
gurin awo dashi Dan duba idan sauran drugs
din dake jinin nasa allurar ta qarasa qona su.

Barka da tashi likitocin sukai masa cikin
kulawa da farin ciki kafin suka fice daga dakin
suna sake tattauna maganar ciwon nasa
Suna ficewa ya Bude idanuwansa dake rufe
ya Dan Kalli Naseer dake cikeda farin ciki sai
kokarin Kiran su dd babba yakeyi a waya.

Magana yaso Yi Amma bayason ko Bude
bakinsa nauyin komai na jikinsa yakeji Dan
haka ya Dan ziro gafafunsa qasa ahankali
Amma yakasa miqewa tsaye sbd sunyi nauyin
da bazai iya tafiya da Kansaba Kai tsaye a yanzu daga tashinsa.

Yana Nan zaune Naseer ya kira su dd babba ya sanar musu take kowannensu yahau sujjada Yana godewa Allah sbd su kadai suka
Dan mummunan tashin hankali da fargaban dasuke ciki akan wannan halin Dayake.

Bayan ya gama waya dasu Naseer din dawowa yayi ya sake kallansa cikin kasa boye farin cikinsa yace “zan shirya Maka toilet yanzu ka Dan gasa jikinka kanl sake kafin zuwansu dad kaante”

Yana fadan Hakan ya nufi bathroom din da sauri ya shige kaman bana asibiti ba kaman a hotel Dan haka komai tsaf yanda DD din ke bugatan toilet hakama kullum sai anwanke an sake tsaftace komai na toilet din duk da babu me shiga Amma sbd suna jiran farfadowansa kowane lokaci shiyasa koyaushe ake cikin
Shirin duk Abinda zai buqata bayan tashin nasa.

Fitowa yayi da Kansa ya kama DD din Wanda baya iya tafiya haka Suka lallaba ya shiga toilet din dashi yakaisa har bakin bathtub Daya hada ruwan dumi sosai ya kawo masa komai Dazai bugata ya Jere masa harda sabbin towels guda biyu dasu toothpaste da toothbrush na wainda yasan asalin dasu DD ke amfani.

Zare rigar patient din dake jikinsa yayi ahankali tareda sakinta qasa tareda short din Dayake jikinsa ya shige bathtub din ahankali tareda kwantawa Yana rufe idanuwansa.

Shiru yayi cikin ruwan tsawon lokaci seda ya ji jikinsa ya Dan sake sake sbd ruwan zafin dake ratsasa sosai suka sakar masa da jiki tsawon lokaci kafin ya fito cikin ruwan duk acikin sanyi ya dauki brush ya tsaya yayi brush tareda wanke bakinsa da mouth wash kafin ya koma qarqashin shower ya sakarwa Kansa ruwan zafin sai alokacin ya sake sauke ajiyan zuciya.

Yanda ruwan yake sauka jikinsa ahankali ya sakashi ahankali ya fara dawo da tinanin halinda suka samu kansu a ciki kafin shigarsa wannan halin da baisan meya samesa ba har lokacin.,

Bai iya Tino wahalar dayasha ba kafin kasancewa da Bena a yanzu iya nutsuwa da yanayin duniyar da suka kasance a tare yake
Jin feelings din da dumin numfashinsu Daya ringa fita Yana sauka a lokacin harma da
Wani girmamammen lamari Daya risketa aciki
Wanda ya sakasa sallama mata duniyarsa gabaki Daya sune yake tinawa suna dawo masa acikin Kansa,

Bai taba kusantan kowace mace ba Dan haka baisan ya ake nufin Virgin ta kasanceba Amma dai a iya abinda yaji Yakuma tarar Bena din ta sake komawa Virgin bayan haihuwan ne? kokuma bata Haifa Amnah da kanta ba?
Idanma Cs Akai mata to ya akayi Bai taba Jin dinki a Mararta ba sbd yasha shafa Mararta tin kafin su zama Abu daya yanzu din.

Meyake faruwa ne?
Shine baisan komaiba akan wainnan abubuwan kenan kokuwa dai akwai abinda ya kamata y sani dinne Bai saniba?

Wainnan tinanin sune suka cika Kansa kafin na tashin hankalin da mamaki suka biyo baya sbd sai alokacin yake tinanin meya samesa ya shiga halinda ya shiga,
Idan ya Tina daidai mutuwa yaji yakusa yi da mummunan desire da zai kira da dark desire ma sbd a lokacin da Bena batazo ba zai iya afkawa duk macen Daya samu Wanda zai iya kashe Kansa idan Hakan ba a faru bayan ya dawo hayyacinsa sbd tsananin gyanqyaminsa da raayinsa na macen Dayake so ne har cikin zuciyarsa da ruhinsa kawai zai iya kwanciya da ita shiyasa bazai taba iya kwanciya da dayan matarsaba sbd zai cutatar da ita matigar ya kwana da ita babu digon sonta cikin ransa,
Yabarta ne idan yaga bazai iya adalci ba zai sallameta taje da budurcinta ta samu Wanda yake sonta har Zuciya.

Ya jima sosai Yana San jikinsa ya Dan samu karfi kafin ya gama ya fito daureda towel a qugu ya ratayo dayan a wuyansa Yana tafiya ahankali fatarsa ta sake haske sbd kwanciyar dayayi kwana biyu yayi fayau kaman mace me sabon shigan juna Biyu.

Ko Daya fito tini Naseer ya ajiye masa kaya da underwear sabbi na sunspel masu tsada.

Jikinsa ya goge a hankali da sauran rashin kuzarinsa ya gama ya saka underwears din da saka short wando me Dan tsayi kadan da black rugbay shirt sai alokacin yayi salloli
Yana gamawa yayi adduoinsa Yana tashi ko gadonsa Bai qarasaba su dd babba suka shigo dakin kowannensu a tsanake cikin jallabiya

Dan lokacin 7 harta wuce.

Dd babba ne ya fara ware hannu cikin farin ciki me tsananin gaske ya rungumesa tareda Dan bubbuga bayansa Yana kiransa da “my champ”
Shima dad kaante cikin farin cikin ya Dan rungumesa Yana Jin zuciyarsa na sanyi sbd
Daya rasa DD Shima kaman yanda ya rasa
Bilal da shikenan baisan ya rayuwarsa zata kasanceba.

Zeenah data shigo daga baya da gudu ta garaso ta fada jikinsa tareda rungumesa
Shima rungumeta yayi ahankali Yana Dan Jin sassaucin nauyin zuciyarsa dake azabtiwa da rashin ganin wadda yakamata ya fara Gani farko farko.

Hawaye Zeenah ta ringa yi Wanda ya sakasa
Bude bakinsa dole yayi mata magana da
cewan

“Meyesa kike Kuka?

Kin dauka zan mutu ne?

Wa zan barwa ‘yata da..
. Shiru yayi tareda
kasa qarasawa Yana dagowa ya Kalli su dad kaante Kai tsaye dd babba ya kalla Yace

“Bata zo bane?
Lafiyanta kalau right??

Zeenah na Jin Hakan ta dakata da hawayenta tana zamewa daga jikinsa tana Satan kallan dd babba dayace kar Wanda ya sanar masa halinda ake ciki.

Dd babba fuskewa yayi cikin basar da zancen da kulawa yace
‘tama kasan batajin dadi so tana Nigera sai ta warke sosai zata iya zuwa daga baya kokuma idan mun koma shikenan.”

Yanda yayi maganar yasaka DD Kai tsaye
Shima ba Wani shakka ko Wani Abu kunya yace

“Sosai ne batada lafiya??

Nayi forcing kaina sosai ne akanta har haka?
Did I really f… cikin Wani irin Jin nauyi dad kaante ya katsesa da cewa

“Rashin lafiya ne kawai Kuma ta warware inshallah.”

Naseer ma Kansa qasa yayi sbd nauyin maganar DD din Wanda Sam shi bai ji Wani komaiba sbd yasan tabbas ya nuna mata qarfi tinda Bai dauka zai sameta a yanda ya sameta din ba,and baitaba dauka haka ake samun
Kai acikin wannan rayuwarba shiyasa ya kasa controlling Kansa Dan haka idan har shine ya sakata a wannan halin Yana bugatan komawa
Nigeria cikin ganganin lokaci sbd yaga yanayin jikin nata kada tanacan tana Jin jiki sosai Bai saniba.

Dd Babba Kuwa bai damuba da zancen dinba sbd yasan shi Dan Kai tsaye Daman musamman ga wadda yake Jin yanxu bazai iya controlling Kansa akan Yanda yakeji a zuciyarsa ba shikuma Daman Hakan shine fatansa.

Yanayin yanda DD yayi shiru ne Kauai ya saka dd babba Dan shiga nazari sbd idan Basu nuna masa taji sauki da gaske ba ba lallai ya zauna anan din dasuke son ya zauna ba har su fara zuwa su samu mafitan nema Bena din da qaske sbd dole zasu masa dubara abarsa
Nan su koma su kadai.
Shima DD din a natse cikin sanyi ya karanci yanayinsu Daya bayan Daya Amma Bai kawo tinanin komai a ransa ba bayan na sosai ya nunawa matarsa qarfin Daya illatata may be.

Kowanne fuskewa yayi suka danne suna sake bayyanarda farin cikin tashinsa Dan haka tini suma yan Nigeria aka sanar dasu suka samu farin cikin farfadowansa Kuma ana sake shiga fargaban bayyanarda maganar batan Bena.

Shi Kansa bai sake nuna damuwa ko Wani yanayi ba gameda maganar Bena din saima ya
Dan ringa daurewa Yana nuna jarumtar qarfin jikin Dayake samu.

Har yamma suna Asibitin anata nuna masa kulawa kaman zasu hadiyesa shi dai Bai Wani sake sosai ba sbd zuciyarsa data kasa samun cikakkiyar nutsuwa,
Hakanan yakejin Sam hankalinsa ba kwantawa zaiyiba matigar ba Bena din yaji ba.

Washe gari ahaka suka sake wuni results dinsa sun fito babu sauran drugs din a jininsa
Amma sun Basu takardar Asibiti data hukuma
Datake bayyanarda bashine yasha da Kansa ba Basa Akai Bada saninsa ba Dan haka hukuman gasar ta Bada takardarta akan idan sun koma gida Nigeria Akai binciken gano komai zasu shiga cikin zancen Wanda zaa kama da qwayoyin.
##MAMUH#

 

* Arewabooks@Mamuhgee_*

No comments