Breaking News

Amatulmaleek 53

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar


53
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

***************
Daqyar ruwan ya wuce ta maqoshinta kaman ta hadiye garwashi haka ta jisu tana kallansa idanuwa a wahale zatai magana ya dakatar da ita da cewa

“Mum ki nutsu fa karki halaka akan wainnan mutanen da Babu Wanda zai Gani da kyau”

Kallansa tayi sauran ruwan na qarasa dawowa ta hancinta
Shine ya zari tissue Yana goge mata ahankali zuciyarsa na tafasa tana zuba quna zaiyi magana mum din ta taresa da cewa

“Meye ne kake fada Naufal?
Me nake ji?
Ni bangane ba kamun bayani kafin na taka dungun qafar taka ka qarasa”

Jifar da tissue din hannunsa yayi Yana kallanta Shima ciwon ransa na dawowa sabo yace

“Mum kinaji fa nace Miki wannan tsinanniyar sauran haukar Husnah ce ta nadan tarkon zuwa mansion din fa,
Itace ta kira ne,
Sako ta turan akan naje mansion din ba kowa,
Dana ga sakonta sharesa nayi ban kulaba Amma ta sake Kirana ta Kuma sake kira…

Dan shiru yayi,
Mum da zuciyarta ta kawo maqoshinta kallan baqin ciki da zafi tana jiran sauran zancen a kufule da siqewa tace

“Kai Kuma mayen da maitarsa Bata kwantawa akan Amatun ta kwashi shegun qafafunka kaje ko???

Hade fuska yayi ransa na sake daukan zafi da radadi yace

“Daman akwai sauran abubuwana danake son dauka a mansion din Jin Hakan su naje dauka bawai Dan Amatun kadai ba sai gashi wannan tsinanniyar yarinyar tasa ASH yamun wannan rashin imanin”

Kasa magana mum Aisha tayi tana kallansa idanuwanta jajir kaman zasu koma cikin kanta tsaban bacin Rai
A kufule ta dauki roban ruwan data gama sha ta jefa masa a Kai hannuwanta suna rawan bacin Rai da baqin ciki me girman gaske data rasa Yaya zatai dashi,
Abu biyu take tsananin muradi a yanxu shine fasa kan Naufal din Taga idan jini zai fito ta samu tabbatarda kan mutane da qwaqwalwan mutane ne dashi Bata karfe ba,sai Kuma Husnah da zata buga kanta da stairs na gidan ubanta ta fada mata ASH din datake tayar da hankalin mutane akansa bama Ubanta bane qanin ubanta ne Kuma Mijin uwarta ko gadonsa batada shegiya me tabin hankali ‘yar gawa taqi Rami.

Kafin Taga Husnah Naufal din dayake gabanta zata fara cin ubansa taji toshewan kan data samesa da zai bi maganar Husnah sbd idonsa ya rife da kwadayin farar fatar Amatu.

Kallan mum din yayi lokacinda robar ruwan ta sauka kansa da zafi ya taba kansa Yana sake dawo da kallansa kan mum din tasa zaiyi magana cikin kunyar da baimasan yanada itama ta katsesa da cewa

“Ni kaddarata ta haihuwa acikin zuriar masu tosashen Kai ce,
Babu abinda yake cikin kanka daga mata Se mata,
Dana San haka zaka zama da a hannun ubanka zan barka ka tashi acan sai nasan baqin cikin labarin lalacewanka kawai zan riqa ji batareda nagani ba baqin cikin yamun yawa,
Uban meye ne Amatun take dashi da ka nace ka rufe ido da tosashiyar qwaqwalwanka harka qare da qafa Daya duk akan macen da gata Nan kanajin kana gani Se Hange shi Wanda ya rabaka da qafar Daya Ya mallaketa,
Duk wannan rashin hakurin naka da masifaffen kwadayin matan ya Saka Amatu ta samu Isa ga Daman zama ASH din,
Da ka hadiye kwadayinka da duk bamu zo Nan inda muke ba aynzu……

“Mum wlh yaudarata Husnah tayi nikuma kaya zan dauka a mansion din,wlh Bazan barta ba Husnah din ai……

“Kamun shiru da toshewan basirarka ka barni naji da komai,
Husnah dinma tafika hankali da tinani tinda har tasan ta inda zata cutatar da wadda bataso,
Kai kuwa idonka ya rufe maimakon data tura maka sakon ka tattara komai ka kaiwa ASH ka nuna masa Dan dawo da yardarsa gurinka ya yafe Maka akan abinda ya faru Baya Amma Se Kawai ka kwashi qafafunka kaje lalata masa mata ko? Ta barka da Arziki ka raso qafa Daya gurin rashin danganarka”

Shiru yayi maganganun mum Aisha din na cin zuciyarsa suna qara masa damuwa da baqin ciki me qarfi.

Katse shirunsa tayi da cewa

“Karka kuskura naji kayi Wani abun akan kowa,
Kabarni Daya bayan Daya kowa zaisan ya tabani, Husnah zatasan da was takeyi Dan ko uwarta nafi qarfin iskancinta bare ita,ba ta iya Kai labarin Azo ASH Baya gida ba?itama nata labarin zata samu bayan na fasa bakinta da kanta”

Sai alokacin ya sake dagowa ya Kalli mum din Yana Dan Jin sanyi a ransa Dan yasan ba sauki Husnah zata gurbi abinda tai masa.

Kasa zama tayi asibitin ta tattaro ta dawo gida Dan zuciyarta tafasan datakeyi ko Naufal din zata iya rufewa da duka duk girmansa da jinyar dayake kuwa sbd abinda takeci ya wuce bacin Rai tafasan zuciya takeyi.

Ko data dawo gida Babu ma Wanda yasan ta dawo bayan su khaltume ta shige bedroom dinta tana Ciro wayarta numbern Husnah ta Nemo ta danna mata kira zuciyarta na tsalle Dan kuwa da Husnah na gidan ayau da wlh sedai ASH ya Tararda Rabin Husnah din badai cikakkiyar ta ba Kuma ta fada masa abinda zai Sakasa yiwa shegiya auren Sadaka da duk Wanda ya samu.

Husnah na ganin Kiran mum Aisha taji gabanta ya Dan Fadi kaman bazata dauka ba sai kuka ta daure ta dauka cikin rashin son magana sosai.

Ko gaisuwarta mum Aisha Bata amsa ba tace

“Ki tattara komai naki ki dawo Abuja kafin ASH ya dawo Dan idan ya Riga ki dawowa shine zai fara Jin abinda kikai na turawa Amatu Naufal Dan ya la…….

Tashi zaune Husnah tayi da sauri daga kwancen datake tana satar kallan su mummyn porthcrt Dake tareda ita kafin ta miqe ta nufi bedroom ta shige tareda tura kofar tana cewa

“Mum Aisha ni Kuma?
Ni bangane me kike nufi ba?
Wane Uncle Naufal din?

Tsoki mara sauti mum Aisha ta sake tareda cewa

“Ki zauna porthcrt jiran bayani har ASH ya rigaki dawowa kisha mamakina”…kashe wayarta tayi tareda jefar da wayar Dan kuwa saita Maida Husnah abin tausayi da wannan maganar da ita zatai amfani ta juya kusan kowa a gidan yanda takeso.

*********
AmatulMaleek kuwa jikinta ya sake warwarewa kaman ma Bata taba yimata komaiba harda dinki Dan haka ta koma zuwa school Kuma ta Dan sakewarta sbd anty Farha na gidan Sam Bata barinta shiga damuwa ko tinanin dayake sanyaya jikinta duk da ta fahimci sosai maamah ta sauyawa Amatun takuma San dalilinta Dan kusan yanzu itace sirrin Amatun da maamah Dan ita kanta maamah din zuwa yanzu dole ta yarda Farha na kaunar Amatu da gaske haka Kuma hankalinta ya kwanta da alaqarsu sedai Sam taqi yarda da duk wata nasiha ko maganar da Farha ke Mata akan auren Amatun qarshe ma doka da rantsuwa tayi akan kar a sake Mata maganar duk da Amatu batama San anty Farha na kokarin yiwa maamah nasiha akan lamarin ba.

Ganin yanda Farha ta dauki auren Amatun da mahimmanci sai ta sauya mata kwata kwata ko fuska ta Dena sake mata Kuma daga Farha din har Amatun sun fahimci sauyin maamah din sai jikin Amatun yayi sanyi ta sake shiga damuwa.

Duk zata school tare suke fita da anty Farha su ajeta spa dinta su wuce idan sun dawo saisu biyo su dauketa su dawo gida.

A kwanakin duk da tana cikin damuwan maamah wasu lokutan Hakan Bai Hana hutun datake samu bayyana ba ga Kuma kulawa sosai da anty Farha ke Bata,
Komai nata ya sake upgrading zuwa babban matsayi Dan komai nata kusan an sauya ya sake zuwa babba,
Designer ne take bugu yanda ya kamata,kudinsu maamah Bata saniba da sai ta kusan kwanciya asibiti sbd damuwa,ita kanta Amatun bawai kudaden da ake kashe mata din ta saniba komai haka ake kawowa anty Farha ta jerasu inda ya kamata komai ya zauna.

Har wannan lokacin tinda ya tafi basuyi magana ba Dan batama kunna wayarta Se dare Kokuma idan zatai magana dasu Abdul ko Haydar Dake cikin farin cikin tashin mahaifiyarsa.

Tana kunnawa zataga text dinsa zata karanta ta rubuta masa lafiyanta kalau da thank you kawai ta sake kashe wayar.

A zuciyarta Babu ranar da tinaninsa Baya azabtar da ita Amma Kuma tana Jin jikinta na sanyi tareda mutuwa tinawa da a gurin matarsa dayake tsananin so ya tafi Dan murna da farin cikin son kasancewa da ita.

Ita kanta anty Farha Bata damu da rashin son kunna wayan da Amatun keyi Dan haka suka share suna abubuwan Dake gabansu kawai.

A wannan gabar maamah tafara matsuwa da Farha ta tafi sbd ta samu cikakkiyar Daman magana da Amatun akan abinda takeso tai mata magana kafin ASH ya dawo.

*****Husnah a porthcrt ta shiga tsananin tsoro da firgicin maganar mum Aisha Dan haka ta tattara zat dawo Amma su mommyn can din suka hanata dawowa Dan haka hankalinta yayi mummunan tashi Amma ba Daman fadan abinda yasa takeson komawan,
Tayita Kiran numbern mum Aisha Amma Bata dauka idan kira 100 zatai mata,

Hankalinta Bai tashiba tafara Neman haukacewa sai datai magana da Dad dinta taji a satin ze dawo Dan haka ta tattara ta Siya ticket sedai su mummyn suka wayi gari ta gudu Abuja Dan kuwa hankalinta ma Baya jikinta idan ba Isa tayi Abujan ba.

Ko data iso gidan ba kowa Se maamah da masu aiki Dan haka ko zama batai ba ta sake kiran mum Aisha Amma Bata dauka ba Dan haka ta zauna bakin gadonta jikinta na rawa ta tura mata sakon cewan ko dawo tana gida.

Tafiyar sakon befi da mintina biyu ba mum Aisha Tayo mata reply da sunan asibitin da suke.

Kallan sakon tayi a karo na babu adadi tana tinanin mezataje tayi acan din.

Shiru tayi tana Jin zuciyarta na shiga damuwa da tsoron maganar ta Isa kunnen Dad din duk da tasan bazai iya fushi da ita ba ko mata Wani hukuncin akan Amatu da ba ‘yarsa ba Amma Kuma batason yaji sbd Haydar ze tsaneta, Haydar ze iya fushi da ita Yama shareta.

Miqewa tayi tana daukan wayarta kawai Se qaramar chain handbag ta nufi kofa ta fito ta sauka ta fice batareda Maamah ma tasan ficewanta ba.
Da kanta ta karbi key taja motan sbd Bata buqatan kowa da zai iya ji Ko da tsautsayi cewan tanada Saka hannu a cikin maganar fyaden Amatu.

Tana ficewa mansion din su Amatu motansu na shigowa Amma Sam Batama lura dasu ba kaman yanda Suma Basu dauka itace ta dawo harta fita dinba.
###MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

No comments