Breaking News

Amatulmaleek 63

 YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK


Mamuhgee

#ZafafaBiyar



63

*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*

*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍

*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*


MAGANIN SANYI 

MAGANIN NONO 

MAGANIN HIPS 

MAGANIN SLIMMING 

MAGANIN NANKARWA

GYARAN AMARE

SET MAIJEGO

MALLAKA 

SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI

TURAREN WUTA

MATSI

MAGANIN NI'IMA

BACK TO VIRGIN SET

INFECTION FLUSHER


08142800199

07068558096


*******

Husnah saukar da idanuwanta tayi akan hasken Amatun Daya Qaru sosai hakama maamah ma Amatun take kallo kaman sabuwar baquwar da Basu taba Gani ba,


Har lokacin da Husnah ta qaraso bakin gadon tana kallan fuskar Amatu batareda ta gasgata Dad dinta zai iya dauko Amatun ya kawo har inda mum dinta take ba ta waiwayo Baki a sake ta Kalli maamah tace


"Wannan AmatulMaleek ce fa,

Dad ne ya zo da ita fa." Kasa qara cewa komai tayi sbd kasa daukanta da kafafunta keyi ta silale ta zauna kan kujeran Dake dakin tana dauke kallanta daga Amatun zuciyarta na shiga Wani hali.


Maamah ma kusan silalewan tayi ta zauna tana kasa dauke idanuwanta daga Amatun Dan ita kaman ba Amatun data Haifa bace take Gani a gabanta Dan sauyawanta yayi yawa.


Anty Farha ce ta shigo dakin Dan sanin su maamah sun dawo dole ana Nan ana magana Kila sbd tin farko tacewa Amatun ta sauka a dakinta Amma tace dakin maamah zata sauka batasan Husnah na tareda maamah bane a dakin.


Tahowa tayi tana yi musu barka da dawowa tana kallan reaction nasu Daya kasa boyuwa da ganin Amatu.


Amatun tafara Dan kira tana tadawa baccin,


Husnah na ganin Hakan tayi hanyar toilet ta shige ta rufo kofar Dan zuciyarta zata iya tsayawa daga bugawa idan Amatun ta tashi taganta dakyau.


Tana shigewa toilet Amatun na farkawa ta Bude idanuwanta ahankali tana Dan motsawa cikin kasala da mutuwar jikin.


Tashi zaune tayi ganin maamah da anty Farha,

Kallan maamah takeyi tana sake gyara zamanta daga tashin datai daga kwance farin cikin ganin mahaifiyarta na cike fuskarta Yana bayyana ta Bude Baki cikin kulawa da kewa tace


"Maamah sannu da dawowa,nayi kewanki sosai"


zama maamah din tayi tareda sauke numfashi me nauyi tana danne tarin abubuwan Dake ranta da tarin tambayoyinta da mamakinta ta amsawa Amatun tana Dan sake mata fuskarta tana mata barka da zuwa itama tana Dan soka tambayar ya Akai haka kawai tazo din ba sanarwa Kuma tareda ASH ko har anyi hutu ne?.


Dagowa Amatu tayi ta zubawa maamah din idanuwanta sbd a bayyane tambayar itace abinda yafi farin cikin ganinta mahimmanci.


Bude Baki tayi a sanyaye tace Hutu takeyi Kuma ba kowa gidan ne shiyasa aka taho da ita.


"Daga Abujan kuka taho Nan Kai tsaye kokuwa Kuma Saida sukai kwanaki a Lagos dinne?

To a Ina kika sauke ke a Lagos din tinda ke Daya ce,nasan kin zamar masa dawainiya da kinyi zamanki ai muna kusa da dawowa tinda gasu khaltume a gidan dasu karima duk zasu debe Miki kadaici da kewa??


Numfashi Amatu ta sake saukewa tana bawa maamah din amsa Kai tsaye da cewa


"Banice nace zanzo ba cewa Akai na shirya shine aka taho Dani,Lagos din Kuma bamuje ba daga Abuja muka wuce"


Amsar data bawa maamah din ya saka maamah Jin Dan sanyi sanyi ta Kalli farha dake tsaye tana kallan iKon Allah tace 


"Farha a dakinki zata zauna ko tinda Nan ni da Husnah ne zamu matsu kuka Kinga ba jituwa sosai yanzu tsakaninsu kuje can dakinki kaman zaifi Kwanciyar hankali.


Ita kanta Amatu tafi son komawa dakin anty Farha din sbd kallan da maamah ke Mata ko anan din ta kwana to bazata rintsa ba sbd tambayoyin da maamah zata ritseta dasu.


Saukowa Tayi daga gadon ta miqe tsaye tana kokarin nufar kofa maamah ta bita da kallo sosai ita gaba Daya Amatu ta sauya mata tsoro ma Hakan ke Bata tareda Sakata cikin firgicin irin Hutu da Amatun ke samu tana sauyawa zuwa kaman matar ASH din dai da gasken.


Fitowa sukai dakin har lokacin bacci ne cikin idanuwan Amatun gashi Daren yaqara tsalawa sosai.


Hanyar sama Farha ta kalla ta dawo da kallanta kan Amatu kafin ma tayi wata magana motsin saukowa saman sukaji.


Amatu bataji motsinba Dan haka ita hanyar kofar dakin anty Farha din take sake nufa kanta tsaye.

Anty Farha ce Taga saukowan ASH din Dan haka ta dakatar da Amatun tana Dan gaidasa a natse tareda sake masa sannu da hanya ta juya ta wuce hanyar bedroom din ta shige.


Cikin sanyi da kasalan bacci Amatu take kallansa tana Dan lumshe idanuwanta sbd qamshinsa Daya shiga hancinta lokacinda ya matsota sosai.


Shima kallanta yakeyi cikeda kulawa Yana kamo hannunta zuwa jikinsa Yana taba fatan wuyanta ahankali Dan Jin zafin jikinta datake yi da daddare cikin kulawa da sauti me tsananin taushi yace


"Yaya?ya kikeji yanzu?

Kina Jin damuwar jikin ne haryanxu?

Shud I call likita yazo yanzu ya dubaki?

Kinci abinci?

Zaki iya bacci a tareda agurin Farha dinne??


Shigewa tayi jikinsa da kyau cikin sanyi ta shaqi qamshinsa tana Dan lumshe idanuwanta tareda gayosa da hannuwanta kafin ta Bude Baki qasa qasa a sauti me laushi itama tace


"Naci abinci,banajin komai yanzu bacci kawai nakeji,no need a kira likita yanzu zuwa da safe zan warware"


Rungumeta yayi Yana Bata Daman sake shaqansa da kyau kafin ya Dora lips dinsa ahankali tsakiyar fatan kunnenta ya sauke mata kiss ahankali ya dago Yana kallan idanuwanta Dake Wani lumshewa yaji Wani irin duk kasala na cikesa ya Bude Baki yace


"Baccin fa?Zaki iya gurin Farha?muje sama ki kwana acan hankalina zai rabu da baccinki"


Tafin hannunta ta Dora akan gefen fuskarsa ta shafo cikin Wani yanayi na tsananin so da Baya boyuwa da shegen feelings tace


"Zan kwana gurin anty Farha,su maamah fa na gidan kaje ka huta da kyau tinda ka gaji baka huta ba tinda muka iso,Yaya jikin Mum Abeeda??


Bakinta ya fara kalla ya shafi lips dinta da yatsar hannunsa kafin ya amsa mata da jikin Abeedan alhmdlh sauki da cigaba ya fara zuwa.


Daqyar ya barta ta tafi dakin anty Farha ta shige kafin ya juya saman Shima bayan ya dauki ruwa.


Anty Farha da batai tinanin dawowan Amatun dakin ba kallanta tayi da mamaki tana cewa


"Yaya na ganki kuma?


gado dakin Amatun ta fada tana cewa


"Anty Farha kin manta maamah dasu mum Aisha na gidan Nan duka ne"


Daga haka batama iya cewa komaiba ta gyara Kwanciyarta baccin ta sake rufe idanuwanta sai numfashin baccinta anty Farha taji Yana fita ahankali.


Bata ce komaiba anty Farha Se takaicin su mum Aisha din Daya rufeta harma da maamah wadda ta Hana rayuwar Amatun yin gaba bare Baya,

Data rufe ido ta amsa auren da wata haukar su Husnah din sedai suyi bayan idonta tinda Koda auren Amatun a hannun ASH ko Babu kusan gidansa a hannun maamah din yake tinda matarsa ta kwanta Amma sun ishi kowa da masifar yau daban gobe daban,wlh suna tada rigima Mr Jameel zata fadawa a sake mayar dasu inda suka fito ko a tura su Umrah can suje suyita fama.



Washe gari da safe Mr Jameel anty Farha tafara kira tinda safe ta sanar masa su maamah zasu fara halinsu Dan kuwa da safe Kiri Kiri maamah ta hana Amatu fitowa daki har Saida ASH ya fito ya fice daga gidan.


Shiru Mr Jameel yayi Yana nazarin maganarta kafin ta Sako masa zancen turasu Umrah ko Maidasu gida.


Cikin mamaki yace


"Wace Umrah Kuma?suje har gaban dakin Allah su rokesa auren ya mutu kenan?

Suna tashin hankali Yola zan turasu gaba dayansu acan jirgi ze diresu su zauna gidansa na can shikenan acan zaa samu Yan aiki a zuba musu, Naufal ma dayake asibitin Abuja transfer zaa masa zuwa can din su qarata"



Shiru anty Farha tayi sbd idan antura su can madame Abeeda Dake kokarin dawowa Kuma Yaya zaayi da ita ga Kuma zancen Amatu tinda ana cewa maganar auren dole boye mata zaayi kota halin Yaya,ita Sam bataga Wani amfanin boye maganar bama tinda dai auren fa bame warwarewa bane gwara a fada kowa yaji me Rabon ganin Badi ya Gani me qararrun kwana Kuma haka Allah yaso.


Shiru me Jameel yayi Dan Shima dai yasan fadawa madame Abeeda tana wannan halin gaskia bame yiyuwa bane kaman yanda Kuma a gurin ASH boye aurensa ace ya ajesa gefe kwata kwata for now bame yiyuwar bane.


Bayan fitan ASH Amatu ta samu fitowa bayan riqeta da maamah tayi a daki da maganganu da Kai tsaye duka na bugun cikinta ne taji duka abinda ya faru da suka baro ta ita kadai mansion din.


Husnah tareda Dad din ta fice Dan haka har lokacin Bata Hadu face to face ba da Amatu.


Mum Aisha kuwa da safe Se ganin Amatu tayi a gidan itama kusan mamakinta Bai boyu ba ringa kallan Amatun tayi tana shiga tashin hankali da tsoro Dan kuwa Babu abinda yazo tinani da zuciyarta Kai tsaye Amatun ta gama zama cikakkiyar mace sbd komai nata ya sauya.


Tareda anty Farha da mum Aisha din sukai breakfast a dining tana kaucewa kallan mum Aisha dayayi mata yawa Dan kuwa mayyar kallan dole mum Aisha din ta koma tana rasa tinani da zargin kamawa.


Sai guraren 12 suka fito gaba dayansu aka tafi asibiti dasu suka je duba Madame Abeeda.


Koda suka Isa asibitin Amatun na sanye da doguwar glazisias pencil gown me taushin data lafe a jikinta kalar dark purple Se jacket me laushi ta Balenciaga kanta ma ba Wani kayan nauyi rolling ne mara nauyi Se glasses Dake fuskarta sbd Rana da haske sosai da bataso.


Ita da anty Farha ne a Bayan sosai suna magana Se maamah da mum Aisha a gaba sunyi musu Nisa akwai tazara a tsakaninsu sosai.


Suna Isa dakin Kai tsaye mum Aisha ta Bude batareda tayi knocking ba sbd sanin ASH na ciki fatanta ASH din na riqe da Abeedan Amatu ta Gani.


Suna shigowa Husnah Dake gefen Abeeda bayan angama dorata a wheelchair sedai Bata gama zaunuwa ba gyarata Husnah keyi Dad din ya shigo dakin a natse daga gurin gama ganawarsa da likitoci akan tafiyan Abeeda.


Mum Aisha kasa hakuri tayi ta qaraso ahankali daidai Husnah zata gyarawa mum dinta rigar jikinta ta Kara mata kafarta take Husnah din ta fada kan Abeedan da qarfin gaske Wanda yayi daidai da isowan ASH ya janye Abeedan Yana janye Husnah gefe wadda ta dago da sauri ta kalli mum Aisha din cikin mamaki me girma da tashin hankali sedai da ido mum Aisha din ta nuna mata kofa da su Amatu ke kokarin shigowa anty Farha na gaba Amatu na bayanta a natse.


Da sauri Husnah ta Maida kallanta kan Dad dinta Dake gyarawa Abeedan zama a natse da kansa cikin kulawa,da sauri ta dawo gurin Dad din ta marairaice fuska idanuwanta na cikowa da hawaye tana cewa


"Dad Babu abinda ya same ta?banganiba bansan ya Akai na fado kanta na daki fuskanta sosai bansaniba,ko zaa kira likita ya dubata idan.....

##MAMUH#



*_AMATULMALEEK_*


By Mamuhgee 

And

*_YANCI DA RAYUWA_*

By Hafsat Rano 

Na kudi ne

For more page ku biya

500 for littafi Daya

1k for duka books din biyu

 at👇

0022419171 access bank Maryam sani

09033181070

No comments