Breaking News

Amatulmaleek 65

 the sweetest story#


AMATULMALEEK

Mamuhgee

#ZafafaBiyar




65

*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*

*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍

*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*


MAGANIN SANYI 

MAGANIN NONO 

MAGANIN HIPS 

MAGANIN SLIMMING 

MAGANIN NANKARWA

GYARAN AMARE

SET MAIJEGO

MALLAKA 

SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI

TURAREN WUTA

MATSI

MAGANIN NI'IMA

BACK TO VIRGIN SET

INFECTION FLUSHER


08142800199

07068558096


************

Suna barin gidan Babu Nisa suka Isa asibitin da zaa duba Husnah din duk da Mr Jameel har anty Farha sunsan ko ruwa aka zuba mata zata farfado Amma suna buqatan dai Taga likitan sbd yanzu ne zasu hargitsa gidan da tashin hankali cikin Daren gwara idan tashin hankalin zasuyi su bari da safe suyi saisu fuskanci ASH din gaba dayansu da kansa.


Yana miqasu asibitin ya tafiyarsa sbd yanda zuciya ke ingizasa Daya Siya musu tickets cikin Daren asubar fari subar qasar su koma inda suka fito.

Anty Farha kawai ya bari tareda su itama ta tsaya dinne duk da baa zama asibitin Amma sbd ta tare kowannensu daga komawa gida ta tsaya Dan har maamah din sukace likita ya duba Dan yanda numfashinta ke Neman yankewa sbd mummunan tashin hankalin datake ciki na kasa yarda ko gasgata Amatu Bata dakinsu a Daren Sam Bata yarda ba da abinda ake kokarin fada da tabbatarwa Amatu da ASH.


Mum Aisha kuwa gaba Daya hankalinta da nutsuwanta Bata taredasu a asibitin Yana gidan dasuka baro da abinda dai ya tabbata kenan Amatu ta zama matar ASH.



A gida kuwa tinda suka shige saman a palon ya fara zaunawa da ita a jikinsa suna fuskantar juna ya Ciro bakinsa daga nata Yana bin lips dinta dasukai Wani Dan ja da Kuma Hasken deep tsotsan daya musu.


Rigar jikinta yakeson zarewa Amma akwai sanyi bayason sanyin ya shigeta Dan haka gaban rigar dake Bude ya zira hannunwansa Yana mannota jikinsa kirjinsu ya hade da Dan karfi kadan,

Atare suka sauke ajiyan zuciya me hade da numfashi Yana ambatar sunanta kaman ransa na Neman fita,

Itama lumshe idanuwanta da baccin cikinsu ya gama tafiya gaba Daya tayi tana shafa bayan wuyansa ahankali kaman tsutsa na masa tafiya zuwa wuyansa da kirjinsa tareda sauke masa numfashinta masu dumi a cikin kunnensa na dama tini ya qarasa kuncewa.


Dago kanta tayi lokacinda ya sake ambatar sunanta ta Kalli fuskarsa kishinsa kawai taji Yana suka tareda mamaye zuciyarta tareda sonsa me tsananin gaske a lokaci Daya.


Cikowa idanuwanta sukai da hawayen galabaitan zuciyarta ta hade fuskansu tareda kama fuskansa da tafin hannuwanta ta hade bakinsa da nata wata irin fitinanniyar kiss me kunce Kai ta fara yimasa tana tsotsan lips dinsa da harshensa a lokaci Daya tana sake zagayo kansa da hannuwanta.


Kasa riqe kansa yayi daga rabata da rigarta gaba Yana shigarda ita jikinsa sosai Dan Hana sanyin shigarta ya miqe da ita har lokacin tana sake kashesa da nata salon kiss din.


A cikin bedroom din nasa kusan sabuwar duniyar suka Bude suna bajewa Dan kuwa Saida yagama susucewa gaba Daya tukuna suka Isa lafiyayyar gadon dakin suka hau suna watso kusan Rabin pillows din gadon ka suka Kai guda shiga qasa.


Lafiyayyar soyayyarsu suka sha ahankali kwance kafin tafara tinanin saukowa ta koma dakinsu kafin safe Wani ya fito yasan Bata Nan.


Bai bari ta koma din ba Dan Babu abinda ya shafesa da Wanda zai fito yaga Bata Nan din Dan haka wanka sukai ya kwanta cikin jikinta sbd gajiyansa da stress dinsa dayaji ya sakesa gaba Daya Wani baccin nutsuwa da Kwanciyar hankali ne ya daukesa itama dole tayi baccin a Nan sbd yanda ya kwanta jikinta bazata iya zamewaba Dan a zagaye da qugunta hannunsa duka biyun suke.


Babu Kiran sallah da alarm ake tashi sallan asuba dan haka Koda alarm din yayita yi ahankali qasa qasa Basu ji ba Saida sukai lattin sallah sosai.

Suna idar da sallah jikinta na Dan rawa ta silale ta sauko Jin gidan tsit tayi tinanin Basu tashi ba Dan haka tafara saukowa da sauri ahankali sedai ko gama saukowa bataiba ba aka Bude kofar shigowa dukkaninsu suka shigo gaba ki dayansu Banda mr Jameel da Bai shigoba.


Anty Farha ce agaba sai maamah da Husnah tukuna mum Aisha data shigo karshe ranta a hade sbd takaicin kwanan zaune kawai datai a asibitin.


Rawa jikin Amatun ya Dan dauka tana kallan maamah datai mata kallo daya ta dauke idanuwanta daga kallanta sbd zuciyarta zata iya bugawa.


Husnah ma zuru tayi tana kallan Amatun kallo na qurullan data iya gane ko yau din Babu bra a jikin Amatun hakama kusan gaba Daya qamshin Dad dinne yake tashi daga kayan jikinta.


Anty Farha ce tayi saurin yin gaba tana Jan Amatun da cewa


"Neman mu kikeyi ne?

Asibiti muka kwana Husnah ba lafiya lokacin kina kitchen kinje daukan ruwa Amma dai......


Maamah data kasa riqe bacin ranta da renin wayon da farha takeson kawo mata ta Saka hannu ta riqe hannun Amatun daga hannun Farha ta dawo da ita gabanta idanuwanta da sukai jajir akan Amatun data kasa kallanta har rawa da karyewa muryan maamah din keyi ta Bude Baki tace


"Amatu daga dakin ASH kike??


Qasa ta sake yi da kanta tana kasa cewa komai bayan hawayen Dake cikowa daga idanuwanta.


Magana anty Farha ta matso zatai Dan kare Amatu maamah ta daga mata hannu cikin tsananin bacin Rai tareda dawo da kallanta ga Amatu batace komaiba ta kama hannunta Rai a tsananin bace ta fizgeta zuwa cikin dakinsu ta Turo kofar.


Sakin hannun Amatun tayi Kai tsaye fushinta da tsananin zafin zuciyarta na qaruwa ta maimaita tambayarta tana tsoron amsar da zaa Bata Amma dai tanason Jin idan akwaima ko alalar gaisuwar datake shiga tsakanin Amatun da ASH batareda sanintaba.



Kasa amsa tambayar Amatu tayi idanuwanta na sauyawa zuwa ja hannuwanta na kakkarwa.


Cikin zafin zuciya Daya kasa boyuwa Maamah ta daga murya a zafafe tace


"Meya kaiki sama?

Menene alaqarki da zuwa saman?

Menene abinda su Mum Aisha suke fada???


Wannan Karan gudu hawayenta suka qara ta Bude Baki Babu abinda ta iya furtawa Se "kiyi hakuri maamah....


Wani ba zatan Mari ne maamah din ta dauketa dashi Wanda ya Sakata gigita sbd ba zatan saukansa da Kuma dukanta da baa taba yi ba.


Ita kanta maamah datai Marin rawa jikin ya dauka a fusace batama sanin me take fada tace


"Da gaske su Husnah suke kenan kina zuwa dakinsa ko me??

Kin taba kwana a dakinsa ne ko me nake Shirin Gani ko ji???


Kuka mara sauti ne ya kufcewa Amatu tana toshe bakinta da hannuwanta sake rawa tana kasa amsa tambayar maamah cikin matsanancin tashin hankali da tsoro.


A fusace maamah ta damqota tana jijjigata cikin fushinta Dake tsananta take sake maimaita tambayar da gaske ne tana zuwa dakin ASH?


Kukanta ke tsananta tana kasa amsa tambayar har lokacin hakama rawa jikinta keyi sosai sbd tashin hankali da tsoron Bata taba kaiwa wannan matakin ba da mahaifiyarta.


Maamah ma hawayen ne suka kufce mata tana fasa kuka sbd Bata taba tinani ba hakama Bata taba zata ba har lokacin ma ta kasa yarda da Hakan shiyasa takeson Amatun ta Bude bakinta da kanta ta fada mata.


Kukan maamah din ya sake gigita Amatun ta shiga tashin hankalin dayafi na farko tana fashewa da sabon kukan da Baya fidda sauti har lokacin sedai shesheka.


Cikin kukan maamah ta sake cakumo Amatun tana Neman illata sbd bacin Rai ta riqe hannunta Daya qam kaman zata tsaga mata shi tana Jin kaman karta tsaya Se tayiwa Amatun shegen dukan da zata Bude Baki ta fada mata gaskia duk da bazata taba yarda Amatun zata iya Hakan ba Dan haka cikin Nemo taurin zuciya ta share hawayenta tana kallan Amatun tareda Dan sassauta murya tace


"Amatu idan har kin yarda ni mahaifiyarki ce,nice na dauki cikinki na haifeki kimun alkawarin daga yanzu bazaki sake ko kallan ASH TALBA ba'a matsayin mijin yar uwar mahaifiyarki ba,kimun alkawarin babu alaqar da zata taba shiga tsakaninki dashi ba bare har abinda su Aisha suke magana ya tabbata,

Abeeda ta tashi bayan shekaru ko ke bazaki so abinda zai sake Sakata cikin Wani mummunan halinba tinda uwace a gareki,

Wannan auren na kaddara ne Kuma shi da kansa zai warware Miki shi ya sauke Miki nauyin auren tinda Abeeda ta tashi,

Abeeda kadai ce matar Dayake kallo a macen da zaiyi rayuwa da ita,

Babu abinda Zaki samu ko Qaru dashi da wannan auren zai lalata kuruciya da lokacinki sbd ke da ASH kaman sama da qasa ne akwai tazarar abubuwa da yawa da suka nesanta ku,

Ki dubi kauna da amincin dayake tsakanina da Abeeda ki tattara maganar ASH da aurensa ki aje a gefe kiyi rayuwarki,

Kimum wannan alqawarin Amatu,

Kimun alkawarin Nan Amatu ki tabbatar min da kin yafe auren Nan tareda ajesa a gefe kwata kwata kada yar uwata ta koma halinda ta fito.......



Amatu tinda take Bata taba gasgata da gaske mahaifiyarta data haifeta tafi son farin cikin kowa akanta ba,

Tafison Abeeda da yar Abeeda akanta,

A yau taji komai na duniya ya isheta ya fita kanta,

Ayau mahaifiyarta ce take rokonta akan ta koma bazawara sbd kada farin cikin 'yar Abeeda Dan kuwa Abeeda yanzu Babu Wanda yasan me takeso meye bataso...


Katseta maamah tayi da sake maimaita mata kalmomin alqawarin datake son ta daukan mata idanuwanta jajir akanta.


Gudu hawayenta masu tsananin zafi suka qara tana dauke kallanta daga Maamah din kuka me qarfin gaske yana kufce mata.


Kukanta ya Saka maamah fahimtar alaqawarin data nema tai matan yayi mata tsauri Dan haka hankalinta ya sake tashi sosai sbd idan har Amatu batai mata wannan alqawarin ba to alama ce ta ASH din Yana cikin zuciyarta.


"Innalillahi wainna ilaihirrajiun" maamah din tafara furtawa tana Neman Yanke jiki ta Fadi Amatu ta tarota sedai da qarfi maamah din ta tureta tana daga mata hannu alamar ko tabata kada ta kuskura tayi.


Hakan datai ya Saka Amatu sake fashewa da kuka kafin tayi Wani yunkurin Husnah ta shigo dakin tana ganin halinsa maamah ke ciki da gudu ta iso gurin tana riqo maamah itama ranta da jikinta duk a mace hawaye kawai ke ciko idanuwanta tana hadiyewa.


Anty Farha ma shigowa tayi sbd takasa hakura tsoro da tashin hankalinta kada su tada balai da masifarsu su Saka Amatun a cikin Wani halin.


Suna dakin ASH ya fito a shirye sbd kiransa da Akai asibiti yanzu din akan yau zai dawo da Abeeda gida Dan haka ko breakfast Bai tsaya yi ba hakama mum Aisha Dake palon Bata bari yasan da akwai abinda yake faruwaba ta hanasa fahimtar komai harya fice daga gidan.


Yana fita mum Aisha ta shigo dakin tana sake rura wutan Dake cin zuciyar maamah da Husnah.


Anty Farha kuwa ayau maamah kasa riqe kanta tayi tai mata tas cikin tsananin bacin Rai duk da har lokacin kanta ya kasa dauka bare yarda da Amatun da gaske taje dakin ASH a Daren.

##MAMUH#



*_AMATULMALEEK_*


By Mamuhgee 

And

*_YANCI DA RAYUWA_*

By Hafsat Rano 

Na kudi ne

For more page ku biya

500 for littafi Daya

1k for duka books din biyu

at👇

0022419171 access bank Maryam sani

09033181070

No comments