Breaking News

Amatulmaleek 67

 

AMATULMALEEK


Mamuhgee

#ZafafaBiyar



67

*MUFEEDA'S FRAGRANCE*

   *GIDAN KAMSHIII* 

Munada kayan turaruka kala kala kama dasu

Turaran wuta

Turaran jiki

Turaran Kaya

Humra milk

Humra black

Kwalacca

Turaran moping

Freshener

Daidai sauran su 

Ta a Very affordable price.

Zaku iya tuntubar mu a wannan 

07040986690

Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE 

*MUFEEDA'S FRAGRANCE*

   *GIDAN KAMSHIII*



***************

Anty Farha ce ta saki ihu cikin matsanancin tashin hankali da firgici 

ASH kuwa taku biyu yayi ya Isa inda Abeedan ta fado Yana tarota jikinsa gaba Daya da sauti me girma yake Kiran sunanta Yana jijjiga fuskarta Dake fidda jinin da baimasan na Ina ne yake fitowa ba.


Mr Jameel kuwa Wani irin tafasa zuciyarsa da gangar jikinsa keyi sbd tsananin baqin ciki da tashin hankali harma Da bacin ran da shi kansa baisan yanada shiba lokacinda yake kallansu mum Aisha din da maamah s da Husnah din a jere a saman Wanda alamu da komai ya bayyana qarara dambe ne sukeyi a saman suka jehota Kokuma sainsa da tashin hankalin da suka Saba.


Husnah ce ta sauko da gudun datake hada stairs kusan hudu hudu ko uku uku hankali da ganinta na Neman gushewa,

Maamah kuwa zubewa tayi a gurin sbd ganinta Daya dauke lokaci Daya tareda bugun zuciyarta,

Mum Aisha hannu ta Dora Akai tana neman sakin ihu.


Amatu ma bayan tayi ahankali tana zamewa qasa zuciyarta na dauke bugawa da Mafi girman tashin hankali da balain dayafi karfin kwakwalwanta.


Ambulance Mr Jameel ya kira Yana tare Husnah da mum Aisha da suka nufato inda ASH yake da Abeedan a jikinsa Yana cigaba da ambatar sunanta Dan ta Bude idanuwanta Amma Sam Babu alaman zai samu Hakan.


Cikin qanqanin lokacinda ba'a dauka ba ambulance ta iso hankali tashe aka dauki Abeeda Akai asibiti da ita batareda da kowa yabi ta kansu ba ASH din da Mr Jameel ne kawai sukabi bayan ambulance din.


Suna wucewa anty Farha da kafafunta ke rawar tashin hankalin lamarin sama ta hau da sauri ta kamo Amatu Dake zube qasa idanuwanta a waje zuwa jikinta tana ambatar sunanta cikin tsananin kulawa da kokarin dawo da ita hayyacinta.


Dagota tayi takamo ta suka sauko Bata tsaya da ita palonba ta wuce da ita daki.


Husnah data kasa dawowa daidai sai alokacin ta fasa Wani irin kuka me Qarfi da ihu tana zubewa qasa zaune duka jikinta jijjigan tashin hankalin da Bata taba shiga ba takeyi Dan kuwa idan mum dinta ta mutu sune suka kasheta.


Maamah ma kaman mara laka ko Daya a jikinta ta sauko ta shige dakinsu ta zube tsakiyan dakin tareda fasa nata kukan me tsananin gaske cikin matsanancin tashin hankali da Wani irin gigita.


Mum Aisha kanta a gigicen take sbd bayyanar ASH a daidai lokacinda abin ya afku ita shine babban masifaffen tashin hankalinta da Bata tsoro.


Dan haka itama tini tafara rawar jiki tana sake gigicewan.


A daki kuwa anty Farha kokarin kulawa da Amatu takeyi ganin yanda ta shiga shock me qarfi Dan kuwa abin tashin hankali ne me girma mara lafiya irin Abeeda ace an jeho daga stairs.


Hawayen ne masu tsananin zafin gaske suka fara tsiyayowa Amatun kafin kuka me sauti da qarfin gaske ya zo mata ta silale qasa tana cusa kanta cikin qafafunta tana yinsa sosai tareda fatan Babu abinda ya samu mum Abeedan.


Duk anty Farha ma na cikin tashin hankalin lamarin Amma ta danne kokarin rarrashin Amatun takeyi tana Bata tabbacin babu abinda zai samu Madame Abeeda inshallah.


Gaba dayansu gidan Babu Wanda yake hayyacinsa bayan anty Farha datake iya kokarin ganin Babu Wanda ya zauce a cikinsu Dan kuwa kusan dukansu zaucewa kowa keyi gashi tsananin tsoron ASH ya Hana kowacce tinanin binsu asibitin dubo halinda Abeeda take ciki.


Anty Farha din da suka gama ciwa mutunci da safen itace dai ta ringa binsu Daya Baya Daya tana dawo da kowa hayyacinsa musamman mum Aisha datafi kowa shiga tsoron ASH Husnah da maamah kuwa tashin hankalin rasa Abeedan ne yake Dan kokarin fin tsoron ASH din Dayake cike da cikinsu duk da Shima din tsoron abinda zai iyayi sukeyi.


Dayake dare ne kusan kowa dakinsa ya shige suka zauna jigum jigum hankalinsu da idanuwansu a yanayi na rashin sanin Ina suka kwana.


AmatulMaleek kuwa zazzabinta cikin tsakar Daren har tsoro ya bawa anty Farha Dan haka Amai ta ringa yi Wanda ya Saka kowa fitowa daga dikinsa.


Daman Husnah neman dalilin fitowa takeyi sbd tashin hankalinta na Dayan bangaren maamah akan Jin itace tasaka ayiwa Amatun fyade,Sam maamah ko inda take Bata kallaba bare tinanin akwai mutum tareda ita,

A aynzu batada karfi ko bawa komai hankalinta sai taji yanda Abeeda take zatai tinanin Husnah da abinda tayi mata din.


Cirko cirko suka tsaya Babu Wanda cikin awannin da aka barsu din Bai fada ba yayi zuru zuru a dare daya lokaci Daya sbd rashin sanin meye zai faru.


AmatulMaleek ta galabaita sosai Dan haka ko zama daqyar anty Farha ta zaunar da ita taje ta kawo mata tea me zafin gaske ta fara Bata.


Banda Husnah daga mum Aisha har Maamah datake Neman shiga sabuwar shock of her life zubawa Amatu idanuwansu sukai mum Aisha ta Bude Baki murya na rawa tanason magana Amma ta fasa sbd yau tashin hankalin na musamman ne,

Magana ce a bakinta Amma ba damar furtawa sbd a wannan tsaka me wuyan dasuke tada Wani balain ba nasu bane Dan haka tayi shiru harsun samu fita daga wannan mummunan tashin hankalin Amma tabbas wlh ta tabbatarda ciki ne a jikin Amatun,Dan haka tana cikin sabon tashin hankali Amma dai tashin Abeeda yanzu shine fatanta Dan duk yanda takeson Abeedan ta mutu Bata so ya kasance ASH ya taddasu dumu dumu sun jeho masa mata ba da Bata saman Kokuma da Bai taddasu ba zata iya zame kanta Amma gaba dayansu ya taddasu Dan haka tasan Allah ne kadai zai fiddasu wannan masifar shine rashin mutuwar Abeeda a lokacin.


Maamah ma kusan tinanin mum Aisha ne yakeson shigarta Amma tashin hankalin datake ciki yasa Bata yarda da abinda idanuwanta ke ganar mata ba bare Kuma yarda da lamarin Dan haka a rude tayiwa Amatun sannu tabar dakin hakama mum Aisha tana ji tana Gani ga abin tada fitina da magana Amma yau ba dama.


Suna ficewa tana gama Shan tea ta kwanta ko baccin awa Daya bataiba lokacin sallan asuba tayi suka tashi sukai sallah Banda ita da anty Farha taqi tadawa sbd ta ganin yanda ta galabaita din tabarta ta samu baccin.


Qarfe 7 saura Amatun ta sake farkawa ta tashi ahankali sbd ta samu Dan kuzari ta nufi toilet Tayo fitsari da alwala tana fitowa ta tada sallah.


Tana sallamewa ko tashi daga inda take bataiba Mr Jameel ya shigo gidan  da sauran duhun asubar.


Baice komaiba ya buqaci su fito da kayansu jirgin da zasubi awa Daya ya rage ya tashi.


Hankali tashe suke kallansa Amma ba Daman magana shima Bai tsyaa komaiba Yana fada ya juya ya fice waje Yana jiransu sbd gaba Daya a siqe yake dasu kaman ya kwashesu yakaisu asibitin mahaukata yakeji yakai ya zubar ayita banka musu alluran hauka ko zasu huta da balainsu Daya ishi kowa har Yan aikin mansion din TALBAs sun dai gaji da masifarsu bare me gidan gashinan sun ja masa masifa Yana ganin ya samu Madame abeeda taji sauki.


Mum Aisha tasan zaayi Hakan Dan haka itace ta fara fitowa da akwatinta kafin maamah da Husnah dasuka so ko so Daya ne sunje sun duba Abeedan sunsan halinda take ciki Amma Sam Babu fuska Dan kuwa sanin wannan umarnin daga ASH ne Kila.


Anty Farha ce ta fito da nata kayan Dana Amatu suma suka fito Dan Mr Jameel cewa Yayi dukkaninsu kowa da kowa gida sukai su fito.


Babu me wanka a cikinsu bayan Amatu sbd itama ta sake samun qarfin jikinta ne anty Farha ta Sakata wanka da ruwan zafi sosai sharp sharp ta shirya cikin Riga da wandon Jean Se qatuwar jacket me tsayi da kauri tayi Rollin harda safa da facemask suka fito.


A yanda suka fito jikin kowa a mace idanuwa a jeme har lokacin Mr Jameel Babu wadda yacewa komai kawai kayansu ya zuba cikin babbar motar Daya zo da ita takaisu airport.


Tin a cikin mota ya bawa Farha tickets dinsu duka ta bawa kowa nasa da kanta tana kallansa cikin kulawa da sanyin jiki sedai ta kasa cewa komai sbd yanayinsa Babu walwala ko annuri ko kadan Kuma so da daman tin Madame abeeda na lafiya kalau kusan harma da duk me muamala Hulda da ASH ta Mr Jameel ake karanta ko gane halinda ASH yake ciki Dan kuwa mode din Mr Jameel shine yake bayyanar da mode din ASH Dan haka rashin annurin fuskar Mr Jameel da bacin Rai da damuwar dayake kwance a fuskansa yasa dukkaninsu sanin ba sauki ta gurin ASH din Dan haka Babu wanda ya sake ko Tari har suka iso airport suka sauka ko motan Bai fito ba farha ya kalla da idanuwasa Dake da Dan ja ahankali cikin nutsuwa yace


"Ki kula da L.A din,kema ki kula,Allah ya kaiku lfy"


Gyada masa Kai tayi a sanyaye itama zuciyarta na sake shiga damuwa.


Ko zama basuyiba aka kira flight nasu suka wuce kawai janye da kayansu Babu me qarfin jiki.


Kowa a zuciyarsa matse yake da son sanin halinda madame Abeeda take ciki Amma Babu dama Babu kuka alamar zama a bari su sani bare alamar sanin.


Jirginsu na dagawa mum Aisha ta sake ajiyan zuciya a boye Dan harga Allah a tsinke take ganin takeyi ASH miqasu zeyi ga hukumar qasar tasan sedai labarinsu ba dai su din ba.


Husnah hawayenta har sun bushe sun Dena saukowa sai jajir da idanuwan sukai,

Maamah ma dai kukan ya tsaya Se nauyin Daya danne mata kirji da zuciya.


Tafiyar zaman makokin wahala sukai me tsayin gaske har suka sauka Nigeria ga mamakinsu motan data zo daukansu daga Lagos sun dauka masauki zata kaisu sai kawai aka Sakasu motar zuwa Yola ba jirgi ba take hankalinsu gaba Daya ya tashi anty Farha ta zame da cewan Amatu batada lafiya zasu bari ta warware zuwa da safe su biyosu.


Mum Aisha ma take tace bazata iya bin mota ba hakama Husnah Amma Kiri Kiri aka sakasu mota sunaji suna Gani Husnah Se kuka take sbd tsoro da fargaban hanyar hakama mum Aisha jininta take yafara kokarin Hawa sbd tsoron hanya,maamah ce kawai Bata damuba sbd ba shine a gabanta ba tashin hankali biyu ne suke nukurkusanta,na yanayin ciwon da Amatun keyi da Kuma halinda Abeeda ke ciki.


Anty Farha suna wucewa ticket ta Siya musu suka hau jirgi duk da Yola sukai sbd Mr Jameel ya sanar mata can Akai dasu maamah sun Dena zaman Abuja gaba dayansu har Husnah.


Koda suka is mota Mr Jameel ya aika aka daukosu suka nufo mansion din ASH na Yola din.


Akwai masu aiki already a gidan sedai main gidan a rufe yake Dan haka bayan isarsu take aka bude koina masu aiki suka hau gyara,

Amatu daqyar ta iya tsayawa aka gama gyara koina gidan yayi fes qamshi da sanyin AC suka gauraya koina.


Dakinta data taba zama lokacinda suka baro kauye bayan auren suka sauka wanka tayi da ruwa me zafi sosai sukai sallah taci abinci sosai take ta kwanta bacci ya dauketa.


Itama anty Farha wanka tayi ta Saka kaya marasa nauyi ta kwanta baccin gajiya dana Daren jiyan da Basu yiba

Su kuwa su mum Aisha na can suna bugun hanyar lagos hankalinsu a tashe da tsoron hanya.

#MAMUH#



*_AMATULMALEEK_*


By Mamuhgee 

And

*_YANCI DA RAYUWA_*

By Hafsat Rano 

Na kudi ne

For more page ku biya

500 for littafi Daya

1k for duka books din biyu

 at👇

0022419171 access bank Maryam sani

09033181070

No comments