Breaking News

Amatulmaleek 68


AMATULMALEEK


Mamuhgee

#ZafafaBiyar




68

*MUFEEDA'S FRAGRANCE*

   *GIDAN KAMSHIII* 

Munada kayan turaruka kala kala kama dasu

Turaran wuta

Turaran jiki

Turaran Kaya

Humra milk

Humra black

Kwalacca

Turaran moping

Freshener

Daidai sauran su 

Ta a Very affordable price.

Zaku iya tuntubar mu a wannan 

07040986690

Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE 

*MUFEEDA'S FRAGRANCE*

   *GIDAN KAMSHIII*



**********

Bacci sosai anty Farha da Amatu suka samu Wanda ya Dan sassauta jikin Amatun Dan haka sai a lokacin ta dawo cikakkiyar hayyacinta ta tashi da asuba tayi sallah ta janyo wayarta Dan Neman maamah tajita sbd tsoro ma itama yafara shigarta na tafiyar tasu dan Koda anty Farha ta janyeta daga tafiyar Sam Bata kanta sosai Dan ko tsayuwa Bata iyayi yanda ya kamata Daman Kuma Bata cikin wainda zasuyi tafiyar mota a tsarin tafiyar.


Sam Bata samun wayar maamah duk Kiran datakeyi Dan haka ta hakura ta ajiye wayar.


Dauke wayarta anty Farha tayi tareda kashewa gaba Daya ta jefa Jakarta batareda Amatun ta saniba Dan hanata shiga ko samun Kiran da zai damar da ita Dan kuwa umarnin kukawa da Amatun datasan ko ASH be fada ba to Hakan yake expecting daga gareta.


Har dare yakuma yi su maamah Basu iso ba suna can suna dukan hanya Dan haka da wannan Daman anty Farha tayi amfani ta ringa kulawa da Amatun sosai tareda hanata shiga damuwar abinda ya faru din sedai Amatun ta kasa cire damuwar halinda ASH din yake ciki a yanxu.


Dare nayi da wuri Amatu tayi bacci anty Farha ce kawai ta rage a farke har kusan 12 na dare saiga su mum Aisha sun iso.


Securities na gidan barka da zuwa kawai sukai musu Babu Wanda ya amsar musu kayansu Kuma a napep suka iso Karan farko na rayuwar Husnah da mum Aisha dasuka hawo napep.


Gabaki dayansu su ukun Babu Wanda yake dubuwa sbd azabar hanya da yunwa da masifaffiyar wahalar dasuka sha,

Kowannensu kaman an tsomasa cikin yashi an fitar sbd qura.


Daqyar suka iso ciki barka da isowa anty Farha kawai tayi musu suka bita da kallan mamakin dayake Neman kashesu ta yanda suka riqasu isowa dakuma alaman cikin Hutawa Farhan take ba alamar mota suka biyo.

Kenan jirgi su suka biyo Kuma sun tabbatarda sbd Amatu ne aka sakosu jirgin sukuma aka jefawa hanyar Lagos su duk balain da zai cisu a hanyar ya Dade Bai cinyesu ba kenan.


Maamah ma Sam Babu qarfi a jikinta ga ciwon Rai ga ciwon jiki,

Daki kowannensu ya samu ya fada daqyar suka iya Kai kansu toilet suka sakarwa kansu ruwan zafi kowannensu yayo wanka Husnah ko abinci Bata iya ciba daga zaune tayi sallah ta zube a gurin tafara baccin wahala kaman ta mutu.


Mum Aisha kuwa abinci ta nema taci ta koshi kafin tayi sallah ta kwanta a watse.


Maamah Kam sallah tafara yi itama bayan wankan Bata iya cin abinci ba ruwan zafin tea kawai Tasha Wanda anty Farha ce ta kawo mata tana sha ta kwanta itama.


Kafin bacci ya dauketa Babu abinda takeji a zuciyarta Yana cinta da qunarta irin Jin rayuwar gidan ASH TALBA ta fita ranta gaba Daya,

Babu abinda takeso irin ta Dan tafi ta samu Hutu da Nutsuwar zuciya sbd takasa yarda da Husnah data Rena da hannunta zata iya turo Wani ayiwa Amatu fyade,fyadenma irin na wulaqanci tinda a cikin gida,a cikin gidan ma a lokacinda aure yake kan Amatun Koda kuwa baa son auren ai dai akwaisa Amma a Turo Wani Dan haiqe Mata...


Cikowa idanuwanta sukeyi da hawaye masu radadin gaske da baqin cikin zuciya me tsanani.



Koda gari ya waye Amatu sai ganinsu maamah din tayi sun iso taji tayi farin cikin ganin isowarsu lafiya sbd mahaifiyarta sedai Bata shigewa maamah din sosai ba sbd ganin kowa sedai kallan kallo musamman mum Aisha tanason magana Amma tana tsoron Wani tashin hankalin yanzu batareda sun San me ASH zaiyi dasu ba akan abinda ya faru ganin idansa a Greece.


Husnah qin fitowa tayi daga dakinta sbd kasa iya kallan maamah da batace komaiba akan abinda mum Aisha ta fada hakama Bata sake kallan ko inda take ba Dan haka Se takejin tana shiga shakku da fargaba ga Dad dinta da ko tinawa tayi da shi sai taji hankalinta na Neman gushewa da tashin hankali.


Haka suka wuni suka sake kwana gida kaman gidan mutuwa Babu me walwala kowa Motsawan ASH yake jira,

Babuwa Wanda ya iya kunna wayarsa sbd shakka da tsoro anty Farha ce kawai ke wayoyinta a gidan Kuma kullum sai tayi magana da Mr Jameel Wanda take bawa tabbacin lafiyar Amatu Dan tasan ASH na buqatan Jin Hakan Kodan samun qwarin gwiwan fuskan balain da suka Saka sa a ciki.


Case din dayake kusan police case ne shiyasa Sam Baya samun Daman komai da kowa daga karshe dai aka case din ya mutu ya samu Daman fuskantar Abeedan wadda tini ta sake komawa cikin mawuyacin hali me ban tausayi.


Mr Jameel ne ya duba footage na gidan Dan tabbatarda abinda ya faru lokacinda suke kokarin kashe case din ko zasu samu abinda zai Taimakawa kashe case din Amma abinda ya Gani din ya Sakashi shiga sabon takaicin tabbatarda tarin kolo mentals ne suke zagaye rayuwar ASH.


Mafi abinda yafi daga hankalinsa shine maganar fyaden da ake fada cewan Husnah ce ta aika Naufal,Tayaya zaace 'yar ASH din ce zataiwa matarsa Hakan bayan a lokacin ma ko noticing dinta ASH din beyiba bare ta damu har da Saka wannan mummunan abin ya faru.


Rasa yanda zai fadawa ASH yayi sedai ya tura masa clip na video din ta wayarsa batareda ya iya fada masa da bakinsa ba.


Bayan ya turawa ASH clip din waya yayi a Yola take ya sallami masu ayyukan gidan guda Daya ya bari hakama securities tini ya sallamesu yabar Daya.


Su mum Aisha na zaune daki kwatsam suka ga wutar gidan ta dauke gaba Daya.


Mamaki ne ya Saka dukkaninsu fitowa Husnah Dake tsananin tsoron duhu tini tafara rawar jiki tana fitowa Neman Wanda zata raba amma ko maamah Bata Gani ba bare iya tinkararta mum Aisha kuwa zafi ne Sam bataso tini tafara Jin kaman zata siqe.


AmatulMaleek Dake daki ma zafin ne ya fara damunta Dan haka anty Farha ta fita Babu jimawa ta dawo mata da rechargeable fans guda uku da manyan fitila sbd tasan aikin Mr Jameel ne wuta a gidan Kuma Se abinda hali ya bayar.


Ko maamah Dake daki Kai tsaye tinaninta yake akan hukuncin abinda ya faru ne zasuyita amsa shiyasa Bata daga hankalinta ba saima sanyi da jikinta ya sake yi.


Tama Rasa tayaya zata fuskanci Amatu akan abinda dukkaninsu sukaji cewan Husnah data fifita akanta itace silan lalacewan ma komai na rayuwar tasu Suma suna zaman zamansu a bangaren masu aiki cikin rufin asiri da Kwanciyar hankali Amma ta tura Naufal ya lalata musu komai gasu yanzu a bagiren da bama Susan sunan alaqarsu ba Dan kuwa a yanzu Amatun gujewa raban maamah din takeyi sbd tashin hankalin da kullum Baya qarewa.



Kwana biyu sukai Babu wuta a gidan take suka fara Neman rasa nutsuwarsu,

Mum Aisha guduwa takeson yi daga gidan saiga Naufal an tattaro an kawo mata a boys quarters na gidan take ta sake shiga tashin hankali sbd tabbas hadesu guri Daya da Akai umarnin ASH ne to me Hakan ke nufi?

Ko dai ta dauke Naufal din su gudu ne to Amma batada gidan kanta ma Bare ta gudun,lalacewan Naufal ta hanasu Tara abinda ya kamata su Tara din gashi komai na Neman kwabewa.


Husnah zaucewa tafara yi,ga rashin sanin halinda mum dinta take ciki sbd ASH ya rufe duk wata hanyar da kowa zaisan me Abeeda take ciki,

Hakama shi kansa Babu Wanda zai taba gwada kiransa yace ya samesa,

Kudi dasuke yanda suke so da su kusan dama gurin Mr Jameel suke karba to Shima kansa shakkar kiransa sukeyi bare ASH da haukansu bema Kai can ba.


Dawowan Naufal ya Saka hankalin maamah fita daga gidan gaba Daya ba a kanta ba akan Amatu dan haka ta Yanke shawarar dauke Amatun su tafi daga gidan kafin ASH ya dawo ayi duk abinda zaayi.



Duk wannan tashin hankalin da kowa yake ciki na Amatu daban ne sbd rashin yin period dinta wata biyu harda Dori ya Sakata shiga mummunan tsoro da firgici,

Kewan ASH da tinanin halinda yake ciki Yana ranta gashi ya Hana kowa ji daga garesa to yanzu Kuma data fara fahimtar halinda take ciki Jin tayi itama tana Neman zaucewa Dan batasan tayaya zata fara tabbatarda idan ciki ne a jikinta Dan haka ma ta fara Hana kanta yawan fitowa itama tana rife jikinta sosai Dan Hana maamah ko kowa fahimtar halinda take ciki duk da Bata tabbatar ba.


Anty Farha Dake zaune tana waya a bedroom dinsu kallan Amatu datai shiru tayi Nisa a tinani tayi tana nazarinta.


Tana gama wayar Amatun ta kalla tana ajiye wayar gefenta tace


"Amatu meyake damunki ne?

Ni na Rasa wannan yawan tinanin da damuwan,

ASH ne??


Juyowa Amatun tayi ahankali tana kallan anty Farha din jikinta na sake mutuwa da yanda maamah zasu San ciki ne da ita ga ASH Baya Nan,tsoro ma takeji na maamah din.


Magana zatai anty Farha din ta katseta da cewa


"Abuja fa nakeson komawa sbd komai acan ya Dan tsaya ana buqatan zuwana gashi kina cikin wannan halin,.abinda ma yasa nayi tinanin tafiyar sbd ganin mutan gidan kaman kowa ya nutsu kafin dawowan me gidan Amma bazan.......


Shigowan maamah dakin ne ya Saka farha da Amatun kallan kofar suna kallanta a natse.


Itama a natsen ta qaraso har inda kujera take ta zauna

Amatu ta Bude Baki ta gaidata hakama anty Farha.


Amsawa tayi a sanyaye tana kallan Amatu data kasa dagowa ta kalleta,

Qurawa Amatun idanuwanta tayi sosai tana kallanta,

Ita duk lokacinda ta Kalli Amatu hankalinta mummunan tashi yakeyi sbd yanayi da kaman datake mata da masu ciki,

Da ace zaman aure Amatun keyi da tabbas zatace ciki ne da ita Amma Sam ta kasa tantacewa ita gaba Daya ma kanta neman juyewa yakeyi shiyasa zata dauki Amatun su tafi ganin gida acan zata gane idan ma Wani abin na jikinta su San abin yi kafin ma kowa ya sani.


Bude Baki tayi tana dawo da kallanta kan Farha tace


"Farha inaga ni da Amatu ganin gida zamu tafi kafin dawowan ASH.....


Wayar da farha ke kokarin dauka ta fasa tareda dawo da kallanta kan maamah din tana cewa


"Ganin gida Kuma maamah?

Ina kenan?


"Kauye zamu je inshallah"


Mummunan faduwa gaban Amatu yayi sbd tsoro da firgicin abinda zai kadaitata da maamah batareda ta tabbatarda da gaske cikin ne a jikinta ba,tsoro takeji su tafi suna zuwa zaa gane ciki a jikinta batasan me maamah zata mata ba.

#MAMUH#



*_AMATULMALEEK_*


By Mamuhgee 

And

*_YANCI DA RAYUWA_*

By Hafsat Rano 

Na kudi ne

For more page ku biya

500 for littafi Daya

1k for duka books din biyu

at👇

0022419171 access bank Maryam sani

09033181070

No comments