Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

Amatulmaleek 73

AMATULMALEEK

Mamuhgee

#ZafafaBiyarT





73

*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*

*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍

*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*


MAGANIN SANYI 

MAGANIN NONO 

MAGANIN HIPS 

MAGANIN SLIMMING 

MAGANIN NANKARWA

GYARAN AMARE

SET MAIJEGO

MALLAKA 

SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI

TURAREN WUTA

MATSI

MAGANIN NI'IMA

BACK TO VIRGIN SET

INFECTION FLUSHER


08142800199

07068558096



*************

AmatulMaleek da sosai zuciyarta ke zafi itam da bacin Rai tsayawa tayi tana yiwa Husnah Dake ihu kallan takaici da mamaki me girma Dan Bata dauka da gaske Batada hankalin ba sai yau din.


Anty Farha na zuwa saurin janye Amatu Dake tsaye tana kallan Husnah tayi

 mum Aisha kuwa Husnah din ta riqe tana daka mata tsawa cikin tashin hankalin abinda zata janyo musu ana zaune cikin fargaba.


Ihun kukan baqin ciki da zafin zuciya da tafasan jini Husnah ke saki tana kokawan qwacewa tana ambatar ciki ne a jikin Amatun Kuma Bata yarda na Dad dinta bane.


Anty Farha data kasa daukan kalaman Husnah din hannu ta daga zata fizgo Husnah din a saketa tayi abinda zatai su Gani hannunta Amatu da idanuwanta suka rufe ta riqe tared daga nata hannun ta saukewa Husnah lafiyayyar Marin Daya Sakata dauke wutan mamaki da tashin hankalin ita Amatu zata mara,


Ita kanta Amatun yau ranta yakai maqurar Baci sbd maganganun Husnah din da tamkar karuwa ne take kiranta dashi da kalamanta.


Husnah qwacewa tayi daga jikin mum Aisha da itama mamakin Marin ya kasheta Dan abu ne da Basu taba dauka ba ko tsammata daga Amatu.


Qwacewan da Husnah tayi a fusace tana sake maimaita kalamanta yayi daidai da qarasowan maamah sama din hankali tashe sbd girman da balain yayi har bangarenta ana jiyosa.


Isowanta yayi daidai da kalaman anty Farha Dake tare Husnah tana cewa


"Wallahi hauka ya dibeki kika taba Amatu bayan kinga cikin Dad din naki dayake jikinta nice zan fara Baki mamaki kafin me cikin da kansa tinda ke haukarki batajin bari......


Kalaman ne suka raqe saurin qafafuwan maamah data qaraso gabansu ta tsaya tana kallan cikin Amatun dayake kallanta tana kallansa.


Rawa qafafunta suka dauka tayi saurin dagowa ta kalli Amatu da gaba Daya Jin takeyi kaman ta mutu ta huta da abinda take ji Dan kuwa mutuwarta kawai Kila zata kashe rigimar aurenta da ASH dayake haukata kowa harma da ita da auren yake kanta.


Maamah kokarin fahimtar komai takeyi a tsanake Amma Hakan ya kasa yiyuwa Dan kuwa cikin datake Gani a gaban Amatu shine Mafi girman shock data samu a rayuwarta bayan na rasuwar Abeeda.


Rikicewa tayi bakinta na rawa itama tace


"Cikin ne kenan da gaske a jikinki Amatu?

Cikin ne dai kike dashi?

Ciki fa Amatu?

Cikin haihuwar mutum fa Amatu..


Maganar maamah ya Saka tashin hankalin Amatun qaruwa mum Aisha kuwa maimaita ciki yayi wata biyar Kam da alama take fada Wanda yake sake juyar da kan Husnah Yana gigita maamah data kasa fitowa daga shock din ciki a jikin Amatun har ya fito haka...


Amatu rawa dukkanin jikinta ya qara dauka idanuwanta na yin ja 

Maamah a rikice batamasan lokacinda tafara cewa


"Daga ina cikin ya fito a jikinki Amatu?

Cikin waye wannan nake Gani a jikinki Amatu??.......


Husnah sabon kuka me Qarfin gaske ta saki tana maimaitawa kunnuwan Amatu kalaman maamah din.


Mum Aisha data ga abin ya qarasa rikicewa sakin Husnah tayi tana Neman zamewa daga rigimar sedai ko Taku biyu bataiba maamah Tayo kan Amatun koina nata Yana rawa zata shaqeta taji inda ciki ya fito jikinta anty Farha tayi kan Amatu hakama Husnah kan Amatun tayi tana qarawa kukan baqin cikinta karfi mum Aisha ma ihun ta saki tana yowa kansu tsoron su taba Amatun takeyi sbd cikin...


ASH ne ya bayyana gurin Haydar da Abdul suna bayansa cikin mamaki da tashin hankalin meyake faruwa suke kallansu Abdul na yowa kan Amatun da anty Farha ta tarewa maamah kamowa,

Abdulhameed mamaah ya riqe sa sauri Haydar kuwa Husnah ya kamo kafin su furta komai Amatu Dake bayan anty Farha ta Yanke jiki ta zube a jikin ASH da taku Daya yayi ya tarota jikinsa jajayen idanuwansa akan qaramin cikinta Daya tsayar da komai nasa.


Duk Wanda yake gurin tsit yayi jikin Husnah Dana mum Aisha harma da maamah din Yana Dan daukan rawa 

Hakama Haydar da idanuwansa suka sauka akan cikin dayake jikin Amatun sakin Husnah yayi jikinsa na Dan rawa kansa na sarawa ta ko Ina.


Anty Farha ce idanuwanta suka sauka akan jinin Dayake gangarowa daga qasan Amatu ta fasa Wani irin ihun salati tana Kiran sunan Amatun a ajikin ASH.


Abdulhameed ma maamah ya saki da sauri Yayo kan Amatun Yana kokarin taba ta Amma tana jikin ASH ba Daman Hakan Dan haka suka tsaya cikin tashin hankali da tsoron kada cikin ya samu matsala.


Miqewa ASH yayi da ita a ajikinsa ya dauketa ya nufi kofa da ita da sauri anty Farha ta bi bayansa hakama Abdulhameed da Haydar Daya rikice gaba Daya ya Dena gane komai a take.


Mr Jameel dayake jiyo hayaniyar cikin gidan Yana tsaye cikin baqin takaici da mamakin hankali irin nasu da bayan kisar da sukai Basu dawo hankalinsu ba haryanxu kenan gashi su kawu bello isowarsu kenan daga kauye sunzo gaisuwa kusan su ukun duka se uzaifa,

Suna tsaye suna gaisawa Yana musu barka da zuwa sama sama Dan hankalinsa Daya rabu.


Yana ganin fitowar ASH da Amatu a jikinsa yayi saurin Isa mota cikin mamakin yauma kisan suka gwada kenan ya Bude motar ASH din ya shigar da Amatun ya rufe motar tareda juyowa ya karbi key ya shiga motar Babu abinda ya furta ya tada motar yaja 

Securities dake tsaye cirko cirko sukai saurin Bude masa gate ya fita da Wani irin mugun speed.


Rabonsa Daya ja mota da kansa harya manta baimasan yaushe ne ranar Daya tuqa mota da kansa ba sai yau din Dan haka Mr Jameel ya fada dayar motar tareda anty Farha suka bi bayansa Abdul ma key din wata motar ya Karba a hannun drivern Dayan motar Dake aje Shida Haydar suka bi bayansu.


Ba Dan sunso ba kowannen dole ya qarawa motarsa gudu sbd su samu Isa da ASH din Dan gudun dayake yi zai Isa ne harma a shiga da Amatun batareda sun isoba.


Su kawu iKon Allah suka tsaya kallo da mamaki da tsoron ganin abinda yake faruwan duk basu gane waye ASH din ya fita da ita ba jini duk jikinsa.


Tsoro ma kawu ashiru yaji shi Yana Neman kamasa daga zuwansu sai cin karo da mugun Abu saikace wainda suka taho da baqar kafa.


Mum Aisha da baqin cikin Husnah da maamah ya danne zuciyarta Dake tafasa kaman zata babbake ta kallesu tana Jin inama Wani balain ne ya samesu su taru su halaka akan sabuwar masifar dasuka tado musu akan Wanda haryanxu basusan meye hukuncinsu ba gurin ASH din.


Maamah ta kalla zuciya na tafasa tace


"Na dauka Husnah haukarta ta tabin hankalin data samu ne Ashe harda qarin gadon haukar uwar riqonta,

Ke yanzu da Abeeda ta rasu Bata duniyar meye naki na tada masifar ciki idan ya bayyana a jikin Amatun inace sbd Abeedan ne kike wannan haukar Ashe dai Daman can da ciwon rashin tinaninki kikazo,

Uban waye zai mata ciki bayan ASH din dasuke watsewarsu a tare,

 yanzu Dan Allah bakiji kunyar tambayar waye yawa yarki ciki ba bayan kina sane da tashin hankalin da Akai a Greece to na uban meye ne idan ba na kwanan datai a dakinsa ba,

Idan ba cikin ba to musulinci taje karba a dakin nasa kenan."


Maamah rasa cewa komai tayi sbd maganganun mum Aisha din bama ta ganesu Sam hakama ita ta yanda Amatun zatai ciki harya fito haka batasan dashi ba shine yake girgizata Yana Neman buga zuciyarta,

Da Abeedan Bata rasu ba kenan haka zasu wayi gari kwatsam suga cikin ASH a jikin ba shiri.

Tayaya Amatu 'yarta data haifa a cikinta zata boye mata irin wannan babban alamarin?

Shin yaushe Amatun ta janye daga gareta haka bayan ko Tari tayi Bata boye mata?

Meyasa ta munafurceta munafurci me girma irin wannan?.


Kasa daukanta qafafunta sukai tana Neman zubewa zaune kan kujeran kusa da ita khaltume ta shigo jiki a sanyaye da abinda yaketa faruwan basuda iKon ko kallawa ta Kalli maamah ta sanar da ita ana nemanta a waje baqi daga kauye sunzo gaisuwa.


Maamah na Jin Hakan gabanta yayi mummunan faduwa idanuwanta suka sake sauyawa zuwa ja ta Kalli khaltume bakinta na Dan nauyi tace


"Daga kauye?


Gyada Kai khaltume tayi tana juyawa ta sauka


Mum Aisha datake a qule kallan Husnah tayi tana cewa


"Wallahi tallahi tsaf zan sanar da ASH komai Babu gargada na abinda kikaiwa matarsa Dan bazaki sakani a masifar da ba hanyar fita ba, ubanwa ya Hana ki auren bare ki dauki cikin Duk da rasuwar mahaifiyarki Baki tuba ba kenan...


Juyawa tayi tana sauka gaba Daya zuciyarta tafasa takeyi shikenan tana murnar ASH Bai ce musu komaiba yanzu mahaukatan gidan sun debo musu sabuwar masifa batama San Ina zata Saka kanta ba da wannan mugun balain matiqar cikin Amatun ya zube.


A palon baqi na ASH dayake harabar gidan aka saukar dasu kawu suna zaune sanyin AC da qamshin arziki duk ya cikasu ga Kuma abubuwan sha duk an Jere musu saisha sukeyi ahankali suna tande Baki cikin sauti mara qara suna jiran fitowansu maamah da Amatun.


Mum Aisha ce ta shigo palon idonta a rufe da bacin Rai me tsanani 

Suna ganinta suka ajiye lemukan hannunsu suna kallanta a mutunce cikin girmamawa suka fara gaisawa suna mata gaisuwan rasuwar.


Amsawa tayi tana kokarin fara magana maamah ta shigo itama jiki ba qwari ta zauna tana gaidasu a mutunce da girmamawa tana tambayar mutanen gida tana boyewa tareda danne damuwanta.


Amsawa sukai Baki a washe suna mata gaisuwan rasuwar itama kafin kawu bello yace Ina Amatu itama.


Shiru maamah Tayi,

Itama mum Aisha datazo da niyar miqa qarar maamah din gasu kawun fasa fada Tayi tana jiran amsar da maamah zata bayar.


Jin shiru yasa kawu ashiru Shima sake tambayar Amatu harma da Abdul duk da sunsan Abdulhameed shi Baya qasar Yana gurin karatu.


Shigowan khaltume da wayar mum Aisha dinne a hannu ya Saka mum Aisha kallanta tana kallan wayar Taga Kiran Naufal ne ta karba wayar tana ficewa duk a rude sbd tasan tasu tazo karshe Kila.


Tana fita kawu bello ya tsayar da kallansa da kyau kan maamah Yana cewa


"Asmau matsalan ciwon ji kika samu ne?

Allah sarki to Allah ya Baki Lfy 

AmatulMaleek muka ce Ina take ne ita ma mu gaisa".


Dagowa tayi tareda sauke numfashi da ajiyan me zafi ta bude Baki tace


"Amatu Bata Nan sun tafi asibiti"


Dukkaninsu kallanta sukai kawu ashiru ya amsa zancen da cewa


"Asibiti Kuma?

Waye ba lafiya?


Uzaifa ne ya katse kawun da cewa


"Baba Amatun ce fa aka fita da ita muna shigowa ni naso na ganeta gaskia"


Kawu yusufa da sai alokacin ya shiga zancen yace


"Amatun ce ba lafiya kenan?

Allah ya Bata lafiya to yasa dai da sauki"


Suka amsa gaba Daya suna shiga Wani zancen sbd sunso komawa a ranar Amma Nisan basusan yakai haka ba sosai gashi Kuma Basu samu ganin ASH din ba.


Fitowa Akai dasu aka kaisu Daya Daya Dake bq tareda Kai musu lafiyayyan abinci da abubuwan sha aka aje musu kafin su samu ganin ASH din ko yau din ko gobe.

#MAMUH#



*_AMATULMALEEK_*

By Mamuhgee 

And

*_YANCI DA RAYUWA_*

By Hafsat Rano 

Na kudi ne

For more page ku biya

500 for littafi Daya

1k for duka books din biyu

 at👇

0022419171 access bank Maryam sani

09033181070

Post a Comment for "Amatulmaleek 73"