Breaking News

Auren Shehu Book 2 Page 5

Auren Shehu 2

5

Ko da ya isa gidan Hansai ba ta dena kuka ba, Iyalle ce ta masa bayanin rashin darajar da Zainab ta aikata musu, da kuma kwashe ruwan shan gidan da ta yi ta ja zuwa bukkar Shehun, Allah kadai ya san abin da ta yiwa


Hansai sa’ad da ta leka dakin dan kuwa har lokacin Hansai ba ta dawo hayyacin ta ba. A fusace ya wuce bukkar ba tare da ya tambayi Hansai baasi ba, ya na sa kai cikin bukkar kafar sa ta sauka kan sauran ruwan wankan Zainab mai jirwaye da be gama shanyewa ba, haka kuma idanun sa ya sauka kan dan fantarin ta da ta wulgar gefe.

“Me ya faru a dakin nan?”
Cewar Usman a fusace.

“Au dama wannan bukkar daki ne? Caf ai ina na gane? Bayan hada jiki da irin ka ai sai an yi saukar dauda, wanka na yi……”

Wani irin mugun kallo da ya jefe ta da shi ne ya sanya ta dada gyara zama tana mayar masa da martani da irin kallan da yake mata. Tsiwar da ta ke masa be sa ya kasa ganin kyawun ta ba, duguwar rigar jikin ta ya mata kyau sosai musammam yanda ya bi jikin ta ya zauna daram. Haka kuma da niya ta yiwa bakin ta ado da jan janbaki duk dan ta boyewa Shehu halin kunci da ya saka ta ciki, dan ta lura ya gan ta cikin bakin ciki shi ne babban burin sa.

“Wanka ki ka yi cikin dakin nan? Yanzu fisabilillahi dakin nan ya miki kama da wurin kwana?”

Ta na mai daga gira ta ce

“Wallahi kuwa wanka na yi, ka fa san tsatona, ko bandakin masu gadin gidan mu ya fi bukkar nan daraja, bare na Zee, ka manta daga in da ka sato ni ne?”

Ya na jinjina kai ya kara da

“Da ruwan shan gidan nan gaba daya ki ka kashe ki ka yi wanka?”

Ta jinjina masa kai alamar
“Eh wallahi”

Usman yayi shiru kamar mai nazari, sannan ya furta

“Abin da aka yi bayan gida….”

“Kashi? Eh shi ma ni na yi wallahi!”

Yanda ta yi saurin katse shi duk bacin ran sa sai da dariya ta kusa kwace masa, wato lalle ya gane so ta ke ta tunzura shi ya yanke hukunci a kan ta, lalle ‘yaro yaro ne’ cewar Usman cikin ran sa, ya na mai murmushi ya furta

“In dai kashi ne ai mu muna maraba da shi, gwamnati ba ta ba mu takin zamani, dama da kashin mu ke taki, daga na dabbobin har na mu na mutane, Nan gaba in za ki yi sai ki min magana ni zan raka ki har daji yankin shukar mijin ki, kin ga sai ki saki jikin ki ki kasayar da hujja, yanda shuka za ta fito mu sami amfanin gona, yanzun ma ba ta baci ba na sa yara su kai daji…..”

Yanda Zainab ta yi da fuska kamar mai shirin yin amai ne ya kara kawata nishadin Usman, be dena murmushi ba ya kara da

“Hansai kuma fa? Me ki ka mata?”

Zuciyar ta na tashi tsabagen tashin hankalin da furucin da Usaman ya saka ta, Ganin yanda idanun sa ke rawa jikin ta ya bata murmushi ya ke, cikin rashin fahimtar dalilin annushuwan sa duk wannan aika aikan da ta masa ta ce

“Ka tambaye ta mana! God you sting!”

“Abu duk lalacewar ki sai na tankwasa ki, idan ba haka ba ban Isa Shehu Usman ba, kin ci darajar amanar da mahaifin ki ya bani da kuwa sai kin kwashe kashin ki da hannun ki, haka kuma zan tambayi Hansai, matukar wani abu ki ka mata mai muni wallahi sai na aika kwatankwacin shi kan ki sai dai ita din ce ta ce ta yafe….”

“Allah ya sa kar ta yafe! Na tsane ka! Na tsane ku! Wallahi da ni ke da kai na da tuni na kashe kai na da wannan rayuwar azaba da ka saka ni…..”

Shiru ya mata ya juya zai fita, har ya daga assabarin ya sauke, kana ya juyo ya na murmushin mugunta yayinda ya ke duban Zainab da idanun ta su ka cika da kwalla, ya ce

“Alhamdulillah, Alhamdulillah wannan shi ne kwatankwacin bakin cikin da na ke so na dasa zuciyar ki, ki sani wannan sumin tabi kenan domin kuwa nan gaba ba ni kadai za ki tsana ba Abu, na mi ki alkwarin kamar yanda ki ka tsani rayuwar wannan Ruga har kina tunanin kashe kan ki, sai kin tsani kan ki fiye da yanda ki ka tsane ni, wannan shi ne buri na, dan haka duk wannan abubuwan da ki ke aikatawa sun yi kadan su sa na karaya, ki sake sabon shiri…”

“Allah ya sa! Allah ya sa! Macuci! Allah ya isa”

Cewar Zainab cikin gunjin kuka. Yana dariyar jin dadi ya fita ya bar ta tana kukan takaici. Zuciyar sa fara sakamakon halin da ya bar Zainab ciki ya koma wajan Hansai. Wanda sai a sannan ta masa bayanin ganin Zainab da ta yi ba kaya ta na wanka tsakar daki, fadi ta ke

“Wallahi Kado batta mutunci, haka tibi tibi na gan ta…”

Cikin rarrashi Usaman ya mu su jawabi da

“Ku yi hakurin zama da Abu matukar kuna so na zauna da ku, idan kuma hakan zai zama da takura ku yi hakuri ku bari na hada nawa ya nawa na dau iyali na mu koma can birni…..”

“Ah ah za mu zauna da ita Shehu, me yayi zafi da mu ka samu ma Allah ya dawo da kai, ai hakuri ya zama dole!”

Iyalle ce ta yi saurin katse shi. Cikin goyan baya sauran ma su ka yi alkawarin hakurin zama da Zainab, ita kuwa yar budurwa wacce ake kira Raqeeba zuciyar ta ce ta dada cushewa, lalle auren Shehu matukar yana tare da Kadon nan tasa ba karamin abu ba ne, ta yanke hukuncin lallba gyatumar ta Hansai cikin azanci ta bijirowa Usman da maganar auren.

Kamar yanda ya shedawa Zainab, yara ya sa suka kwashe kashin su ka kai daji, wanda da su ka dawo ko wanke hannu ba su yi ba su ka cigaba da hidimar gaban su.

Bayan da ta ci kukan ta ta koshi ne yunwa ya sako ta gaba, gashi bayan abin da Usman ya sheda mata ko ruwan Rugar Shehu ba ta sha’awan sha. Duk yanda ta so ta roki afuwan Usman da ya mata rangwame ya mayar da ita gida taurin kai ya hana ta. Sai da la’asar ta yi sannan ta sauko daga kan gadon karar, ta ci sa’a kasa ta shanye ruwan wankan ta, sai dan ragowa da ba a rasa ba. Daga can gefe in da dama be jike ba ta shimfida ledar dakin ta yi sallah.

Rabon da ta yi sallah mai cike da nutsuwa kamar ta ranar tun tana jami’a sai yanzu da Usaman ya kawo ta Rugar Shehu. Gun Allah ta kai karar shi, ta na mai rokan Allah ya fitar da ita daga hannun shi ya kuma mata sakayya da gaggawa. Kukan yunwan da cikin ta ya ke mata ya sa ta tuna da ajiyar kwararen da ta tura karkashin gadon, ta na adduar Allah ya sa ta sami abin da za ta iya ci ba tare da ta tuna kalaman Usman ba ta janyo su waje. Ganin dafaffen kwai ta yi hamdala, dan kuwa shi ta ci sai da cikin ta ya dan tasa sannan ta yi hamdala ta na mai duban ruwan shan da aka aje mata. Ko dan daukan fansa dole ta rayu, dan Usman dai sai ta ga bayan sa matukar ta na numfashi, kudirin da ta ke yi a ranta kenan yayinda ta daga kwaryar ruwan ta kai daidai saitin bakin ta ta na mai zubawa ba tare da ta yarda kwaryar ta sauka bakin ta ba. Sai da ta kusa kwarewa ta aje, azahiri ta na furta
“Idan har ban ga bayan wannan almajirin ba ban isa Zeee ba!”

******

Yanda Zainab ta ga rana haka ta ga dare, itacen korar sauro da Usman ya kunna mata a bukkar be sa Zainab ta iya bacci ba saboda zugin da kafarta ta ke mata duk da kumburin ya ragu, da kuma taurin gadon karar Usman da yake ikirarin ta godewa da ta samu ya iya bar mata.

Duk yanda ta so musgunawa Usman ko ya ji haushi ya mayar da ita abu ya ci tira, haka kuma ba ta fasa yi masu kashi ko wanka in da ta so ba, Usman na dauke kai ya sa yara su gyara. A haka har Zainab ta yi kwana uku Rugar Shehu, gaba daya ta fita hayyacin ta, kafa kam Alhamdulillah ta warke sosai ta bar zuciyar Zainab da jinya, tun tana kuka har hawayen ya sauke sai dai na zuci.

Da Safe bayan ya tashi daga zaman fada, ya zauna wajan bitar karatu da ya saba yi tare da yara maza. Zaune su ke tsakar gida, sun saka Usman tsakiya kowannan su dauke da alqur’ani ko kuma allo sanadiyar rashin wadatuwar alqur’ani cikin Rugar. Kai kawo da Zainab ke yi a tsakar gidan na ba gyara ba dalili ya sa Usman kasa nutsuwa. Sanye ta ke cikin daya daga cikin doguwar rigunan da ta zo da shi, ramar da ta yi be saka kirji ko hips din ta raguwa ba, illa dai kashin wuya da tsayin wuya da ta kara, ba sururu Zainab kadai ba hatta tafiyar ta ma abin sha’awa ne ga duk mai kallo, duk sanda ta gifta sai ya bita da idanu hatta daliban na sa sai da suka fahimci hankalin Shehu yau dai ba ya gare su.

Sallamar Bello da kuma ganin wanda su ke biye da shi ne ya sanya Usman hade rai kamar hadari yaAuren Shehu 2

 

No comments