Breaking News

Auren Shehu Book 2 Page 6

6

Ha?e ran da yayi bai sa sun fasa ?arasawa har in da su ke ba, su uku ne namiji ?aya da mata biyu da za a iya cewa miji, mata da ?arsu ne don ?ar ba za ta wuce shekaru goma ba.
“Me ya kawo ku nan Tanko”


usman ya fa?i cikin tsawa, ya kara da

“Bello me kake nufi kenan? So kake ka nuna ka isa a Rugar nan ko me ye dalilin ka na shigowa da wainnan iblisan?”

Ya cigaba da fa?i yana mai kallon Bello wanda ya sha jinin jikin sa jin lafazan Usman. Gyara tsayawa zainab ta yi cikin nishadi wanda ya kira jinin sa ya mata aikin da ta dade tana yi baya kama shi, amma kuma kallo ?aya ta yi ma wanda ya kira da Tanko ta hango kamanni na jini tsakanin su sai dai shi din baki ne, sabanin Usman da ya ke farar fata. Duk da ba jin yaren ta ke yi ba za ta tsaya ta kalli dramar da za a yi.
Haka ma sauran jama’ar gidan su ka fito suna mai kallan Tanko cike da mamaki da al’ajabi, dan kuwa babu wanda be san mugun halin Tanko ba. Daliban Shehu kuwa musammam kanana cikin su har rawar jiki su ke ganin yanda Usman ke bambami.

“ka dubi girman Allah Shehu, ka dubi nasaba da martaban ka, ka dubi darajan yarinyar nan Cangwai da ta fito daga tsatsonka ka yafe mana”
Macen ta fa?i tana mai share hawaye.
“Baffa Allah ya masa cikawa bayan kun baro sa, ba mu da kowa shi ya sanya muka ce mu zo cikin ?an uwa mu zauna, wallahi duk wani mugun abu na bar shi a dajin falgore, Tanko mai kyawun hali ne nan, ka yafe mana”

Tanko ya ca?e cikin fullanci yana mai rusunawa kamar zai yi sujada. Cikin lafiya da nuna rashin tausayi Usman ya furta

“Rugar nan tsarkakakke ne babu ?igon mugun aiki a cikinta, saboda haka baku da matsuguni ku fice kafin na saukar da fushi na akanku”
yayi maganar ya na mai nuna masu hanyar ficewa daga ?angaren nasu. Daga Tanko har matar shi zubewa su ka yi gwiwowi biyu, hawaye na zuba daga idanun sa ya ce

“Ka taimaka Shehu, ba mu da matsuguni Shehu, duniya ta juya mana baya, idan ma ba za ka karbe ni ba ka duba Rahila da Cangwai, Raliya diya mace ce, ko ba komai Cangwai diyar ka ce….”

“Cangwai ba diya ta bace!”
Usman ya katse shi cikin tsawa yayinda ya kai kallan sa ga yarinyar da Tanko ya kira Cangwai, be gushe ba ya kara da

“Na sani! Ka sani! Na san ka sani! ku kama hanyar ku tunkafin rai na ya fi haka baci”
Maimakon su juya Tanko ya shiga waige waige yana mai rokon mutanen da ke wajen da su sanya baki Shehu ya yafe musu a nan ne ya hango zainab da ke tsaye. Ba shigar da tayi na doguwar riga ka?ai ya ?auke hankalinsa ba har da bambamta da tayi da sauran matan rugar, in bai yi ?arya ba irin matan birni da su kan sace don neman kudin fansa ne.
‘toh me ta ke yi a rugar shehu’ ya tambayi kansa. Gaba ?aya ta manta abin da ya ke yi ya saki baki yana kallon zainab tare da zantawa da zuciyar sa. Yanda ya saki baki ya na kallan ta ne ya sa Usman ya kai kallo gare ta, ganin Tanko ya sa shaf ya manta da ita. Wani irin bakin kishi da tun da ya zo duniya be taba jin irin shi ba ya taso masa har kahon zuciyar ta, musammam da ya lura Zainab din ma Tankon ta ke kallo

“Me kike yi a wajen nan? maza shige ciki!”

Shehu ya daka mata tsawa da firgici ya hana mata musawa cikin sauri ta shige bukkan, sai da ta shige sannan ta ji haushin kanta na yin biyayya da ya daka mata tsawar. Daga bakin assabari ta la?e tana kallon yanda mutane ke ro?on usman yana botsarewa.
“Kai an yi azzalumi! komai aka yi wani zalincin ya ke aikatawa! Wannan masifa har ina! Ina ma ina jin abin da su ke fada! Ya Allah idan har wannan bawa zai iya aikata sharri da zalinci ga jinin sa, Allah kai kadai ka san irin zalincin da zai iya aikatawa kai na, ya ke kuma kan aikatawa, ya Allah ka mana maganin shi.

“Zan iya karbar Rahila da kuma diyar tsohuwar mata Cangwai saboda raunin su na ‘ya’ya mata! Wajan ka dai babu shi Rugar Shehu, idan har hakan ya maka toh, idan be ma ka ba su ma din kana iya tafiya da su!”

Cewar Usman wanda kallan da ya ga Tanko ya na yiwa Zainab ne dalilin shi na biyu na rashin yarda ya zauna a Rugar Shehu. Rahila matar Tanko ta na ji tana gani Tanko ya mata sallama tare da mata alkawarin zai dawowa da ya sami matsugunni. Kukan Rahila da Cangwai be sa Usman ya tausaya ma su ba, sai ma sallamar yara da yayi daga karatu, shi da Bello su ka tasa Tanko gaba, sai da su ka tabbatar yayi nisa da Rugar Shehu, sannan Usman ya ce da shi be hana shi zaman dajin ba matukar ya kiyaye kusantar Rugar Shehu.

Tuni labarin zuwan Tanko ya kadaye Rugar, ranar da jimamin abin da ya faru aka wuni, ita kan ta Zainab sai da zuciyar ta ta dan yi rawa sanadiyar ganin rikidewar Usman cikin kankanin lokaci duk da sam ba ta fahimci ainihin abin da ya gudana a tsakar gidan ba.
Usman kuwa tun bayan da ya tasa kyeyar Tanko, haka kuma ya tabbatar ya ja kunnan Bello be iya komawa sashan shi ba gudun kar ya kara saka Zainab a idanun sa, wani irin bacin rai ke addabar zuciyar duk sanda ya tuna yanda Tanko ya shagala ya na kalle Zainab, wacce ta tsaya kerere da ita ko mayafi babu.

Sai bayan da ya idar sallar ishai sannan ya koma gida ya tarar Zainab na zauna sai surutai ta ke. Fadi ta ke

“Babu ruwa, babu wuta, babu bandaki, babu siturar arziki! Babu waya! Babu club! Babu mai jin hausa! babu Jin dadi! Babu babu babu, babu civilization! bambamcin wannan daji da kabari shi ne can lahira ne! wannna wani irin rayuwa ce!…Ammy in ma ke ce ki ka kullace ni dan Allah ki yafe min, Dady…. Dady ka mutu ka bar ni da masifa Dady! Auren Shehu masifa ne Dady!”

“Akwai maza amma ko?”

Da sauri ta kai kallan ta ga Usman sam ba ta san da shigowar sa ba, tsaye ya ke jikin bango hannu sa harde a kirjin sa, yayinda hasken acibalbal ya haske fuskar sa, idanun sa har kyalli su ke tsabagen bacin ran da ya ke tattare da shi.

“Na’am?”

Ta mayar masa cikin rashin fahimta. Maimakon ya bata amsa, sai ya wuce ciki ya dauko wasu acibalbal har biyu, ya kunna haske sosai ya gauraya dakin, sannan ya dawo ya tsaya gaban ta, idanun sa cikin na ta ya furta

“Maza da ki ka fi so a rayuwar ki, akwai su ko? Na ga yanda ki ka kasa boye maitar ki sanadiyar ganin Tanko….”

“Tanko? Wanene Tanko?”

Zainab ta tambaya dan kuwa gaba daya kan ta ya juye ta kasa gane in da Usman ya dosa. Zainab na murmushi bayan ta gano bakin zaren ta ce

“Ya ba zan nuna maita ta ba bayan na ga namiji iya namiji? Ai wannan dajin kaf babu namiji da ya amsa sunan sa namiji kamar wannan….ya ma ka kira sunan sa?”
“Zainab!!!!”
Ya daka mata tsawa ya na mai kiran sunan ta na ainihi a karo na farko cike da gargadi, duk da hantar cikin Zainab ya kada ba ta fasa fadin
“Ga shi baki, ga faffadar ka fada…..”
“Zainab!!!!!”
Ya kara daka mata tsawa tare da daga hannu kamar me shirin marin ta, har ta kai ga runtse idanu. Jin ba ta ji saukar marin ba ta bude idanun ta a hankali ta kai kallan ta gare shi. Idanun sa sun yi jajur sai huci ya ke
“Me ya sa ka fasa? Ka mare ni mana! Ka dake ni! Idan har ba ka daga hannu ka dake ni ba Usman ba ka isa namiji ba!”
Murmushin mugun ta ya sakar mata kana ya na mai ja da baya ya furta

“Idan har duka shi ne zai gwada mi ki isa ta namiji, Ni kuwa zan dake Abu, Amma duka mai dadi Abu ba irin wanda ki ke tunani ba, Irin wanda za ki dena maitar duk wani damiji face ni Usman…”

Ya na gama fadin haka ya fice da sauri dan kuwa yanda ya ke ji zai iya aikata abin da zai zo yayi dana sani.

*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2

 

 

No comments