Breaking News

Auren Shehu Book 2 Page 7

7

 

Ta na mai nana ta maganar Usman cikin ran ta yanda ta ga rana haka ta ga dare, dan raban da ta sami ishesahen bacci tun ranar da aka wayi gari a Rugar Shehu.



Kamar yadda kowa ya kwanta da sanyi jikin zuwan su cangwai rugar da tsoron abin da Tanko zai iya aikatawa saboda korar da aka masa haka aka tashi washe gari, hakan bai hana mata dakan hura da zuwa tatsar nono asubahin fari ba. Bukkar da ke kusa da ta Atuwayye , matar taubashin Shehu ya sauke Rahila da Cangwai saboda aminta da yayi da ita sannan zaman da su ka yi a ?asar Benue da mijinta lokacin da su ke ganiyar ka?e shanu ya sanya ta ?an fi sauran wayewa.
Duk wannan kai komon da ake yi da Rahila ake yi, sakin jiki tayi tana aiki tana lura da rugar sosai, cangwai kuwa tuni ta shige cikin yan mata sa’annin suna ta hidimar gaban su.
Ko da aka kammala girki, Raqiba aka kwalawa kira don ta kai ma Zainab nata.
“Iyalle barshi zan kai”

Rahila ta yi saurin fa?i don dama neman hanyar shiga sashin Shehu take.
“Ayi haka, tun safe kike aiki fa, Allah ya miki albarka” fa?in Iyalle ta na mamakin sauyin halin da ta gani a tattare da Rahila.

“Ba komi Inna, ai mu masu laifi ne, duk abin da zamu yi don mu rage nauyin zunubinmu za mu yi”

“Aikuwa dai Shehu na son debbo ma, ga ta Ka?o maras daraja” .

Hansai ta ca?e tana mai ta?e baki

“Kinga ki iya bakin ki, ba da ni za a yi shari’a ba, in bai so ta ba wa zai so, da gani ai ka san yar birni ce”

Cewar Iyalle tana mai tashi daga wajen. Kalaman nan ne su ka ?ara sanya Rahila son zuwa ko don ta gane ma idon ta matar da kyau, gashi dai zuwan su jiya ta shaidi cewa yana kishin ta.
Da tunanin nan ne ta nufi hanyar sashin Shehu, da sallama ta shiga bukkar ba tare da ta jira an amsa ba duk da cewa zainab ba amsa sallamar su take ba.
Zaune ta iske ta ta baje kayan ta a saman gado tana ?aga su, neman mai gwara gwaran da za ta sanya take yi kasancewar duk sun yi datti.
Buga wayar ta take a tafin hannun ta kamar hakan zan sanya ma batirin charji har ya kawo

“A ce mutum ya zama kurma a ?ungurmin dajin nan ta ina zai fara ga waya a kashe ba charji”
Tace tana mai jan tsaki daidai lokacin da Rahila ke kai bakin ?ofa za ta fice daga ?akin. Jin haka ta juyo tana mai kallon hannun zainab, ko da ta shigo bata maida hankali ga hannun ta ba illa suturar da ta gani zube a gado musamman gajeren wandon zainab.

“Laaaaaaa!!! Wallahi irin abin da mai gidana ke magana da mutane in sun yi kinnafin, salla ko me ma sunan”

Tace tana ?ingere baki, duniya in akwai abin da ke birge ta yana bayan waya, don ta so Tanko ya bata ?aya wata rana da ya shigo da su ya ce mata ai kudi ne ma?udai in ya siyar da su

“in sun yi mene? Ya aka yi ke kika iya hausa”

Zainab tace cikin firgici da farin ciki. Firgicin ambaton kidnapping da kuma farin cikin wacce ta ke jin hausa, hakan ya sa Rahila ankarewa da subul da bakan da ta yi, ta yi saurin gyara maganar ta hanyar fadin

“A’a wai in sun dawo daga wajen Sana’a na ke nufi…”

“Laaaa hausa ki ke min? Ki na jin hausa? Kin iya hausa?”

“Ai kusan rabin matan rugar nan in ba ma fiye da rabi ba suna jin hausa, Ce mi ki su ka yi ba da ji?”

Cewar Rahila ta na mai duban Zainab wacce alamar mamaki ya bayya na a fuskar ta, kafin bacin rai ya maye gurbin mamakin, murya kasa kasa ta ce

“Babu mahalukin da ya taba min, ko na mu su magana ba su nunawa sun gane bare su amsa, sai tsinannan dariya kamar mahaukata!”

“Hmmmm kadan daga cikin aikin Usman kenan!”

Cewar Rahila ta na mai jinjina kai na.

“Usman kuma, akan wani dalili”
zainab tace cikin ?acin rai

“Zalunci! Ai babu azzalumi sama da Usman, Kinga da mahaifin Usman da na Tanko miji na uwa daya uba daya su ke, Amma Usman ya tunkude siriki na daga sarautar Rugar Shehu, haka kuma ya haye kujerat tare da ha?e dukiya gaba ?aya, ya kada shanu kaf be bar mana ko daya ba ya tai dajin ga, ya bar mu ba cin yau bare na gobe, bakin cikin haka ya kar siriki na har lahira, dole ta sa mu ka bi sahun Rugar Shehu, gaban ki dai aka yi komai jiya…..”
Ta kare maganar ta matsar kwalla. Cike da tausayawa Zainab ta furta

“Lalle ya cika azzalumi na gaske, tun da har ya iyayiwa jinin sa haka, ban yi mamakin abin da ya aikata gare ni ba……”

Nan ta kwashe komai ta fadawa Rahila, ta kare da

“Ni ban san yanda aka yi ba, zan dai tuna sanda na gama karatun jarabawar da zan zana, kawai sai wayar gari na yi na ganni kurgurmin daji hannun wannan azzalumin!”

“Surkulle kenan! Ai kiranye ya mi ki!”

Cewar Rahila ta na mai hango tarin dukiyar da Tanko zai samu ta sanadiyar Zainab, Dan kuwa kifi ne daga sama gashesahe, za su yi amfani da Zainab ta hanyoyi har biyu, na farko su kwaci Rugar Shehu ta hanyar hada baki da ita, Dan kuwa tun jiya ta gano Shehu na so da kishin Zainab, Zainab din ce dai ta kasa fahimta, haka kuma bayan sun kawar da Shehu su karbi kudi makudai na fansar Zainab, dan kuwa dai ba ta ga dalilin da zai sa Tanko ya ga Zainab ya mayar da ita salin alin hakan nan ba.

“ikon Allah, yanzu dai tun da na same ki baki munafunce ni ba kamar saura”
Maganar da ya dawo da Raliya daga wasikar jakin da ta fara. Jin Zainab na fadin

“ki min hanyar barin wajen nan ni kuma na miki alkawarin dukiya mai yawa sannan zan sa a kama azzalumin nan”
ya sanya Raliha murmusawa, kana ta bata amsa da
“In dai daga bangare na ne kar ki ji komai”

“Ni damuwata ma yanzu kaya na da duk suka yi datti, kazamai ne kaf dajin nan!”

Zainab tace ta na mai daga bumshort din ta biyu da su ka rage ma su tsafta.

“Laaaa wannan kamfai ne ko fatari?”

Yanda Rahila ta yi tambayar ne ya sanya Zainab dariya tare da fadin

“Bumshort sunan sa”

“Toh toh shi ma din a kasan tufa ake sawa ko? Kamar dai kamfe ko?”
“Ah ah, hakan nan din shi ake sawa, kuma kyau ya ke sosai, musammam in aka saka da yar riga kamar wannan…”
Ta yi maganar ta na mai daga shudiyar rigar ta, idanun Raliha har rawa ya ke tuni ta fara sakar zuci. Jin Zainab ta furta

“Ina ma birni na ke da na sa kin ga rayuwa, wannan dajin ma ina mutum zai saka….”

“Za ki iya mana!”

Rahila ta katse ta cikin farin ciki.

“Zan iya me?”

Zainab ta tambaya da zuciya daya.

“Sakawa, wannan hanya ce mafi sauki na tunzuru Usman, dan kuwa na lura ya na matukar kishin ki….”

“Mtswww kishin wa? Allah ya sauwake!”

Ta katse ta a fusace. Rahila na mai girgiza kai ta ce

“Na ce dai yanzun nan ki ka gama fadin na taimake ki ki bar dajin nan?”

Zainab ta girgiza kai alamar “eh”

“Toh ki saurara da kyau ki ji, mutum kamar Shehu sai fa kin masa bita da kulle dukan kabarin kishiya! Ni ba zance mi ki ga hanya daya da zan iya taimaka mi ki da shi ba matukar ba surkulle za mu yi ba, Usman kuwa babu surkullen da zai ci shi, ko siriki na ya buga ya bar shi….”

“Wani sirikin na ki? Ba kin ce ya rasu ba?”

Zainab ta tambaya cikin rashin fahimta, hakan ya sanya Rahila saurin gyara maganar na ta

“Ina nufin kafin ya rasu, eh kafin ya rasu din, toh dai abin da na ke nufi za mu ta gwadawa ne ko Allah ya sa a dace, yanzu dai ki fara da wannan shawarar da zan baki, ki saka wannan ki tai har fadar Shehu, na san matukar manya su ka gan ki da wannan shiga dole Usman ya ji kunya da kishi, kin ga a dole ya mayar da ke gun iyayen ki”

Zainab na mai tunanin ya aka yi wannan azancin be zo mata tun da ba ta amsa ma Rahila da toh.

“Anjima zan zo in je in wanke miki”

Rahila tace kafin ta fice tana barin zainab da auno kalar azabar da za ta sa a ma Shehu in ta isa gida. Ita kuwa Rahila tunanin yanda za ta isarwa mijin ta da wannan kyakkyawan labarin, dan ta san halin Usman duk hakurin shi matukar aka kai shi bango ya kan yanke hukunci mai tsauri, ko shakka babu idan har hakin ta ya cimma ruwa ya kori Zainab, mijin ta ya sami nama har gida, tsaf kame ta zai yi yayi gaba ko ba komai sa dan farfado.

Bayan fitowar Rahila Hansai ke tambayar ta dalilin dadewar ta a bukkar, tare da mata kashedi ta ce dai baki ta saki baki ta na ma Kado zance da Hausa ba, in haka ne ta kuka da kan ta. Cikin nuna kyamkayami ta ce

“Tir Allah wadar na ka ya lalace! Ina ni ina Kado maras daraja kamar wannan dai?”

Hansai na jinjina kai ta ce

“Gwara dai, babu ruwan ki da ita”

Zainab kuwa Raliya na fita ta aikata shawarar da aka bata. Shudin rigar ta damammiya ta saka, tare da bumshort din ta shi ma shudi, komai ya fitu zanzan duk da ramar da ta yi. Dan mitsitsin mayafi daya daga cikin doguwar rigar ta ta daura, dan shi kadai ya rage mata sauran duk tayi tutu akai.

Cikin annushuwan abin da ta ke shirin yi ta sa kai ta fito, wato ba Hansai da sauran jama’ar gidan ba, hatta Rahila da ta bata shawarar sai da ta bude baki cikin al’ajabi.

No comments