Breaking News

Duk Karfin Izzata Book 2 Page 1

*Star lady*

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai

Book 2

*Episode 1*


 

Ni gaskiya Abba na sak.. bai kai ga karisa maganar ba Abba ya daka masa tsawa chikin fushi da bachin rai ya fara magana “wlh Safras ko bayan rai na kasaki hiyana ban yafe maka ba itace zaÉ“in da na maka itace nake son gani a matsayin matar ka, ni ko kishiya ban yar da ka mata ba.

Dafe kai Bgs yayi da karfi ya damki lips nasa na kasa da hakoran sa ya datse da karfi kan kache me jini ya fara zuba gaba É—aya ya fasa lallausan lips nashi hannu biyu yasa ya samki kansa wani irin gigitachen kara ya saki kafi Su Abba su farga ya zube kasa wanwar ko motsi bayayi da alama ya suma, da gudu rundunar jibga jibgan sojojin sa su kayo kansa shi kanshi Abba ya tsorata da ganin halinda Bgs É—in ya shiga na dama ya fara yi a zuchiyar sa “me yasa ma tun farko na haÉ—a Aure nan yanzu gashi abun yana son yafi karfi ina da tabbacin wlh hiyana zata sha wahala san nan mawuyacin abu ne Safras yaso ta, innalillahi wa inna ilaihir rajiun ba zan iya barinka ka saki hiyana ba domin idan nayi hakan na chutar da ita idan kuma na barka da ita tofa idan abu yazo da karar kwana zaka iya kasheta, ya Allah ka kawomin mafita Allah ka taimake ni ka kawomin É—auki amma nayi nadama gaskiya kuma bayi kuskure

Sojoji uku ne suka É—auki Bgs suka kai shi mota, san nan suka dawo suka É—auki Aiman shima suka kai shi mota, fitowa Abba dasu Khalid sukayi kowa ya koma chikin motar da yazo da gudu motochin suka fita Masallaci a jere, kai tsaye gida suka nufa

tun daga nesa suke ta faman danna horn chikin sauri jibga jibgan sojojin masu tsaron gate ɗin suka wangale musu, kutsa motochin chikin gida sukayi kai tsaye parking space suka nufa, suna kashe motochin wasu jibga jibgan sojoji masu jini a jiki ƙo sassu masu ji da lfy, suka kariso wajen su biyu suka ɗauki Bgs zuwa babban palon Abba wasu sojoji biyu suka ɗauki Aiman shima sukayi chikin palon Abba, nan take Abba yayi kiran gaggawa akan gaba ɗaya family su hallara a Palo sai lokachin Abba ya lura da Aryan da Yusuf basa nan da mamaki Abba yace

“ina Aryan da Yusuf Chikin sanyin murya Ammi tace “Yusuf dai yana É—aki tare da lamrat shi kuma Aryan ban san ina yake ba” chikin faÉ—a Abba ya fara magana “me Yusuf kuma yake wajen lamrat yanzu duk tashin hankali da muke chiki bai isa yasa ya tsaya kusa damu ba” “a’a ranka ya dade lamrat fa Allah ya mata rasuwane”chewar Ammi, a razane Abba ya É—ago tare da faÉ—in”what!? Me ya samu lamrat É—in daman bata da lfy ne!? “Aa lfy ta kalau tana tsaye kawai ta yanke jiki ta faÉ—i “subhanallah kai Umar jeka kira Yusuf É—in kace ya tawo da lamrat, kai kuma Khalid kiramin layin Aryan muji ai na shi kuma ya tafi” da sauri Umar ya juya ya fita shi kuma yaya Khalid ya chiro wayar sa ya fara ne man layin Aryan.

Dogon salati Khalid yaja lokachin da ya kammala waya da Aryan gaba É—aya mutanen palon suka É—ago suna kallon sa “menene ya faru kuma Khalid!? Chewar Abba “Abba diyana ce aka sace yanzu haka Aryan ya tafi Maiduguri gaba É—aya jama’ar palon suka É—au salati har da Aunty amaryan

Wani razanannen Ihu hiyana ta saki wadda yasa Bgs farfaÉ—o daga sumar da yayi yanke jiki tayi ta faÉ—i kasa sumammi ya, da sauri su Ammi su kayi kan ta suna kiran sunan ta chikin tashin hankali “hiyana!!! Hiyana!!! Amma ina shiru ko motsi batayi

Chikin tsawa Bgs yace “kai dalla kuma mutane shiru Allah yasa ta mutuma kowa ya hu..bai karisa maganar ba green eyes nashi ya sauka chikin idon Abba dake aiko masa da sakon harara miÆ™ewa yayi a fusache ya nufi hanyar fita, kamar daga sama yaji yo muryan Aiman yana sambatu da alama ya farfaÉ—o juyowa Bgs yayi chikin takun sa irin na jaruman maza ya nufi kujerar da Aiman ke kwanche sai faman sambatu yake

“Abba kada kamin haka wlh ba zan iya jure wa ba ba zan iya hakura da diyana ba zafi zuciya ta kemin pls Abba ka tausaya min mutuwa zanyi dai dai lokacin Yusuf ya shigo É—auke da gawar lamrat idon sa yayi jawur sosai kamar wuta gaba É—aya jijiyoyin kansa sun miÆ™e sai wani huchi yake kallo É—aya zaka masa kasan yana chikin matsanancin bachin rai da tashin hankali

“Kai Aiman kamin shiru wlh ko na tsine maka dan tsabar rashin zuchiya yarinyar nan zakache kana so” chewar Aunty amarya tayi magana chike da bachin rai da bakin chiki, dafe sai tin kirjin sa Aiman yayi yana juyi kamar zai mutu

Nan take Bgs yaji zuchiyar na masa zafi chike da É“achin rai ya É—ago green eyes nashi ya sauke su kan Aunty amarya chikin tsawa da É—aga murya ya fara magana “wlh idan kika sake magana a palon nan babu abun da zai hana ni kakkarya ki, kashe shi kike son yine yaji da wanne yaji da raÉ—aÉ—in chiwon da yakeji ne ko kuma yaji da bala’i in ki!? Shiru Aunty Amarya tayi tana zare ido dan tasan hali Bgs tsab zai iya aikata abun da yace, Ba karamin daÉ—in abun da Bgs yayiwa Aunty amarya Abba yaji ba duk da tashin hankali da yake chiki sai da yaÉ—an yi d
Murmushin jin daÉ—i

“Yusuf Ai lamrat bata mutuba tashin hankali ne ya hana ka kane hakan baga hannun ta na motsi ba” chewar Khalid dake tsaye ta bakin kofar shigowa, a sukwane, Yusuf ya kai kallonsa kan hannun lamrat dake É—an motsi chikin sauri yace “haidar bani ruwa, kasa kasa Bgs yace “karka zuba mata ruwa ka kyaleta ta farka da kanta, ba karamin daÉ—i Abba yaji ba da alama Bgs ya fara saukowa

Da gudu Umar ya dawo chikin palon chikin ihu yake faÉ—in “Abba Allah yayiwa yaya Ahmad chikawa yaya Ahmad ya rasu yanzu shigana É—aki na samesa ya rasu wani gigitachen tsawa Bgs ya dakawa Umar “akoi wanda ya tambaye kane!!? Yana maganar yana kallon Aiman dake kwache, wani irin juyi Aiman yayi ya kankame kirjinsa da sauri sauri numfashi sa ke fita sai murkusoso yake yana juyi chikin rawar murya da kyar maganar sa ke fita yace “Ahmad ya rasu wayyo Allah wani miÆ™a yayi nan take hannun sa suka juya

da gudu Abba ya dawo kusa da shi yasa hannu ya danne kirjinsa ya riƙesa da kyau yasa ɗayan hannun Sa ya kamo kumatun Aiman ɗin ya fara karanto masa kalmar shahada sosai Abba ya sake danne kirjin Aiman ɗin da karfi dan yana son Aiman ya karɓi kalmar shahada, duk dauriya irin na Khalid sai da yayi kwalla da kyar Aiman ya fara karɓan kalmar shahada da Abba ke ta mai mai ta masa, bai kai ga karisawa ba rai yayi halinsa, chikin karyewan zuchiya Abba ya saki kumatun Aiman tare da zame hannun sa daga kan kirjin Aiman ɗin yayi baya baya ya koma ya zauna a gefe duk kokarin da Abba yayi ya danne hawaye sa amma abun ya chi tura nan take kwalla ya fara bin kumatun sa wani na bin wani, gaba ɗaya mutanen palon kuka suke ban da Bgs wadda idon sa suka sauya sukayi jaa sosai kamar wuta ya sunkuyar da kai kasa yana kukan zuchi

Mutuwar yara biyu lokachi guda wannan azaba dayawa take wai yau me ya shiga gida na ne Alhadulillah Allah na godema chewar Abba Khalid Yusuf duk kwalla suke sun kasa magana, sunkuyar da kai kasa Fahad yayi saboda kwallan da ya chika masa idon, bakajin sautin komai a palon sai sautin kuka da shessheƙa

Abu É—aya Bgs yake tunawa shine Aryan, yaya Aryan zai ji lokachin da ya samu labarin rasuwar É—an biyun sa da kuma Ahmad tabbas Aryan zai shiga tashin hankali mara misaltuwa.

Kutashi kuje ku shirya asamu a musu sutura mu kaisu gidan su na gaskiya, chewar Abba yayi maganar yana goge kwalla tun Abba bai gama rufe baki ba Bgs ya miƙe chikin sauri ya fice daga palon ya nufi part nashi

chikin rawar murya Khalid yace “Abba bazan iya zuwa ba bazan iya ganin yadda za’a saka Ahmad da Aiman a chikin kabari ba, bani da wan nan jaruntar É—ago green eyes na shi Yusuf yayi zai yi magana kenan sukaji sallama daga bakin kofar shigowa palon

Nan take kowa ya daka ta da kukan da yake

aruɗe suka kai kallon su bakin kofar shigowa kasan chewar sunji irin voice na Ahmad ne, zubur Abba ya miƙe chikin zafin nama Yusuf ya kwantar ta lamrat a kasan kapet ɗin shima ya miƙe, muryan sa har kerma take wajen furta Ahmad daman baka mutu ba!?

Murmushi yaya Ahmad yayi tare da Æ™arisowa chikin palon yace “ban mutuba Yaya Yusuf ina raye Allah ya raya ni kuma ya tai makeni sana diyyar hiyana, gaba É—aya jama’ar palon suka zubawa Ahmad ido suna juran karin bayani, nan ya fara basu lbr yadda hiyana ta taimaka masa har izuwa yau da ta bashi ruwan addu’a ya sha bayan na sha ruwan adduar da ta bani É—azun ne sai naji gaba É—aya jijiyoyina sun rike basa motsi nan take naji numfashi na ya É—auke daga nan kuma ban sake sanin komai ba sai yanzu nan dana farka naji ni garau kamar ban taÉ“a chiwoba.

Alhamdulliah Alhamdulliah kawai mutanen dake chikin palon ke furtawa chikin sanyin murya Abba ya fara magana “yanzu mace mai irin wan nan halinne Safras zai che baya so lallai kuwa da É—azun ka saki hiyana da ka tapka babban kuskure arayuwar ka” “Abba me kake shirin faÉ—ane wache hiyanar kuma ba dai hiyana da tamin addua ba Abba nifa yanzu ma da kaga nazo palon nan, nazo sanar da kai chewar ina son hiyana ne ina son ta kuma zan Aure ta,

tirkashi chike da tashin hankali Khalid ya fara magana “Ahmad sai dai kayi hakuri domin hiyana dai matar Bgs che yanzu, kai in ta kai che maka gaba É—ayan mu yau Aka É—aura auren mu, chikin tashin hankali Ahmad yace “yanzu shike nan hiyana tayi Aure innalillahi wa inna ilaihir rajiun hasbunalluhu wani mal wakil, shikenan ba komai nasan haka Allah yaso wai ina Aiman da Aryan da Bgs ne? A sukwane Abba ya É—ago yayi saurin chewa Aiman baya nan yana Maiduguri wajen Aunty farida, juyawa Ahmad yayi yanufi hanyar fita yana faÉ—in zuwa Maiduguri ya kamani a yanzu nan kenan dan ina matikar son naga É—an uwana kuma shima nasan yayi kewana sosai zai ji daÉ—i sosai idan ya ganni yana kai karshen maganar ya fice daga palon ba tare da ya lura da yanayin fuskokin su Ammi ba Allah ma yasa Aiman na kwanche a kujerar bayan ne shiyasa Ahmad É—in bai ganshiba, dafe kai kawai Abba yayi yana addu’ar Allah ya kawo masu mafita dago ido yayi chikin bada umar ya fara

“Kar wanda ya kuskura ya sanar da Ahmad rasuwar Aiman yanzu ku kyalesa ya tafi Maiduguri dan musamu muyi jana izar Aiman É—in, idan É—aya daga cikin ku yayi kuskuren sanar dashi yanzu tofa za’ayi gawa biyu kunga yanzu ya tashi daga chiwo dan haka ku kyalesa, Abba ya karisa maganar dai dai lokacin da hiyana ta farfaÉ—o

Sambatu ta fara yi tana faÉ—in “wayyo Allah na lamrat ta mutu diyana ta É“ata na shiga uku na dan Allah wadda ya sace diyana ya dawo da ita ya É—auke ni ko kashe ni ma yake son yi ya kasheni ni dai ya dawomin da yar uwa, wayyo Bappa na Inna ta” gaba É—aya palon ba wanda bai tau sayawa hiyana ba harta Aunty Amarya wadda yanzu mutuwar Aiman yasa tafara na damar rayuwar ta da abun da tayi

miÆ™ewa Abba yayi ya koma kusa da ita hannun ta ya kamo chikin nashi murya kasa kasa ya fara magana “hiyana kiyi hakuri kinji jarabawa che Allah ya jarabce mu gaba É—ayan mu kiyi kokarin muchi jaraban nan kinji? Kuma ita lamrat bata rasuba doguwar suma tayi zata farfaÉ—o nan ba da jimawa ba, diyana kuma zamu gano ta kinji ko? Jin abun da Abba yace yasa hiyana miÆ™ewa zaune da sauri tana faÉ—in “yanzu lamrat na raye wayyo Allah Alhadulillah Alhamdulliah Allah na godemaka, shiru Abba yayi yana kallon ta tunani yake
ya wan nan marainiyar Allah zataji idan ta samu lbr yanzu matar Safra che ita mutumin da ya nuna mata tsantsar tsana da kiyayya agaban idon ta, gakiya nayi na damar haÉ—a wan nan Aure dan nasan mawuyachin Abune Safras yaso yarinyar nan tun da ya furta da bakin sa ya tsaneta gaskiya nayi ganganchin sauri haÉ—a Auren nan.

To masu karatu bari mu leko yaya Aryan kuma muga wani wai nar yake toyawa tun da munji yadda Aunty amarya tafara karɓan hukunchi abubuwar da ta aikata hakkin mutane ya fara bibiyan ta

Maiduguri

Gaba É—aya chikin birni da kauye Aryan ya baza sojojin sa ta ko ina an rufe hanyar shige da fice duk in da yake tsammanin zai ga diyana awajen an duba babu ita babu lbr, yashiga tashin hankali mara misaltuwa yama rasa ina zai sanya kanshi bayaji baya gani haka ya baza sojoji ta ko ina anyi sanarwar a gidan redio jaridu gidan Tv amma shiru babu diyana ba lbr Aryan kamar zai zauche wani azaba da raÉ—aÉ—i yakeji a zuchiyar sa sai jin faÉ—uwar gaba yake time to time kuma yana yawan jin voice na Aiman a kunnen sa yana faÉ—in “É—an uwana ina kaunar ka ina matikar son ganin farinchi kin ka gaba É—aya Aryan ya rasa meke damun kwakwalwa sa da take ta tariyo masa voice É—in Aiman

To masu karatu dan Allah kumin afuwa wlh ina hanyane shiyasa kuma bani da charji amma idan na isa gida na samu charji to gobe zaku sammu sakon zafafan page har 2 yanzu dai ayi kuskuren baki da wan nan ina ganin addu’oe ku ina godiya

NEW TEAM
THE TALENT TROUPE WRITER’

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*


*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
by(xeemat….love)

*4, JINI DAYA*
by(mrs bbk)

*5,YA FITA ZAKKA*
by(mum Sayyid)

*Baby*
By (Mhiz innocent)

*STAR LADY*2

The Talent Troupe Writer’s 

*DUK ƘARFIN IZZATA*

Story And Written
⬇️
*Star lady*

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai

No comments