Breaking News

Duk Karfin Izzata Book 2 Page 8

Book 2

*Episode 8*

…….After some minutes Yusuf ya É—ago kai a razane ya miÆ™e ganin halin za lamrat ke chiki, chike da tashin hankali da danasani ya kariso wajenta “subhanallah shine abun da ya furta lokachin da idon sa ya sauka akan


aika aikan daya aikata yayi dana sani sosai, ya ruÉ—e ya rasa ta ina zai fara taÉ“a ta tunani ya shigayi gashi gaba É—aya likitoci dake dubasu maza ne kai shi ko mace ba zai iya bari taga jikin matar shiba bare namiji yanzu ne ya kara jin zafin rasuwar Aiman, da yanzu Aiman na nan sai yaje ya tambayoshi abun da ya dace ya mata, yaya Aryan shine mai É—an saukin kai shima baya nan ko kwaya ya sha bai isa ya tinkari Bgs da maganar nan ba, ya shiga matsanan chin tashin hankali da danasani ko dai na sanar da yaya Khalid girgiza kai ya shigayi yana faÉ—in “No No” ba zan iya sanar da kowaba” chan kuma wata dabara ta faÉ—o masa chikin sauri ya diro daga kan gado ya É—auki short na shi ya mai da jikin sa ya fara laluÉ“ar wayar sa chan gefe ta karshen gadon ya hango wayar, chikin sauri ya É—auko tare da kunna hasken screen ya duba time karfe 11pm contact nashi ya shiga kan number Aunty farida ya danna kira, wayar tayi ringing har ta katse baa É—aga ba, sake kira yayi sai a karo na uku Aunty farida ta É—aga da murya irin na mai barchi tace “Hello Yusuf” shiru ya É—anyi yana tunanin ta yadda zai fara sanar da Aunty farida aika aikan da yayi “yaya Yusuf bakaji nane? “Aa Aunty farida ina jinki Ykk? “Lfy lau ya London? Ya Amarya Lamrat? “Uk Alhadulillah” “lfy kakirani a wan nan daren? “Eh Aunty babba lfy ba lfy ba” chikin sauri Aunty Farida ta miÆ™e zaune tana faÉ—in “subhanallah ba lfy ba kuma to me yake faruwa baka da lfy ne? Ko dai Lamrat che bata da lfy? Ko kuma sauran yan uwan namu dan yanzu prince yayi block nawa bana samun sa awaya” “Aunty farida ki kwantar da hankalin ki mana irin wan nan jero tambayoyi haka dukkan mu muna chikin koshin lfy daman” sai kuma yayi shiru ya kasa karisawa “dama me Yusuf? Kayi magana mana ko so kake ka bugamin zuchiyata ne haba mana” “no Aunty farida ki bari zan rubuta miki tex kawai” batare daya jira amsar taba ya katse kiran chikin sauri ya shiga rubuta mata massage, yana gamawa ya tura mata ba afi 2mins ba sai ga kiran ta ya shigo wayar sa,ji yayi kamar kar ya É—au call É—in saboda kunya amma ba yadda zai yi dole ya É—auka dan ga Lamrat nata zubar da jini, jiki ba kwari chike da jin kunya yayi picking tare da manna wayar a kunnen sa

“Kana jina Yusuf yanzu kasa ruwa mai zafi wadda hannu zai iya shiga chiki sai ka mata wanka ka gasa mata jini amma ka zuba detol a chikin ruwa san nan ba sau É—aya ba idan ruwan ya É—an yi sanyi sai ka sauya mata wani mai zafin, zai taimaka mata sosai amma ya zama dole ka kaita asibiti domin kaga lamrat karaman yarinya ce tayu ka jimata chiwo tun da ba waje É—aya muke ba bare nazo da kaina yanzu kayi mata wanka sai ka shirya ta kuje hospital” tun Aunty farida bata karisa magana ba ya katse kiran chikin sauri ya shiga Toilet ya haÉ—a mata ruwa mai zafi tsabar ruÉ—ewa yama manta Aunty farida tace ruwan da hannu zai iya tsayawa

Dawowa chikin É—akin yayi ya É—auki Lamrat chak kamar yar baby ya koma chikin toilet É—in da ita, chikin baf É—in wanka ya sanya ta, da sauri ta damke hannun sa dan zafin da ruwan yayi masa, wani irin ihu azaba ta saki tare da kankame hannun sa da karfi, kawar da kansa gefe yayi dan bai san ganin tashin hankali dake kan face nata, sosai lamrat ke masa kuka, jin kukan nata yake har chikin ranshi amma ba yadda zai yi dole ya nema mata lfy, sau uku yana chanza mata ruwa kafin nan ya mata wanka sarki ya saÉ“ota a kafaÉ—ar sa sudawo chikin É—akin saman sofa mai zaman mutun 3 ya kwnatar da ita yaje ya É—auko bargo ya rufe ta saboda rawan sanyi da take, komawa yayi wajen gadon gaba É—aya ya kwashe gayan dake kan gadon, kama daga bargon bet shirt fillows gaba É—aya ya kwashe su ya kai wajen ajiye kayan wanki ya dawo ya shiga dressing room ya É—auko wani set na bet shirt da blanket, yazo ya shinfiÉ—a da kansa, ya koma ya É—auko ta ya dawo da ita kan gadon sai kuka take, a hankali hankali idan ba ka kasa kunne sosai ba bazakaji kukan nata ba dan voice nata baya fita sosai, shiru yayi yana tunani wani kaya ya kamata ya sa mata dan bata da kaya ko set É—aya a gidan nan basu É—auki komai ba sai da safe daman zasuje shopping su saya musu kayan sawa, komawa chikin dressing room É—in yayi jim kaÉ—an ya fito rike da jallabiyar sa a hannun, hayewa gadon yayi ya É—agota ya zura mata jallabiyar tallaÉ“ota yayi da kyau a kirjin sa chike da so da kauna ga wani mugun tausayin ta da ya dira masa a rai kasa kasa ya fara “my baby am so so sorry pls ki dai na kukan nan kinji idan kinayi har chikin raina nakeji pls kiyi shiru kada kanki yayi chiwo kinji? Ko kallo in da yake lamrat batayi ba ta chigaba da kukan ta mai tsuma zuchiya, dafe kai yayi yana kara dana sanin abun da ya kai kata mata, wayar sa ya É—auko yana kokarin kiran yaya Aryan, sai ga kiran Khalid ya shigo, kwantar da lamrat yayi ya miÆ™e ya koma gefe dan kar Khalid ya ji kukan lamrat, picking call É—in yayi tare manna wayar a kunnensa ya fice daga É—akin ya koma Palo “Hello yaya Khalid” daga É—aya É“angaren Khalid yace “Yusuf ka fito muci Abinci mana tun É—azun muke jiran ka “No yaya Khalid kuchi kawai ni bana jin chin abinchi gaskiya” yana gama faÉ—in hakan ya katse ba tare da ya jira amsar Khalid ba dan baya son ya jefo masa wata tambayar da ba zai iya amsawa ba.

layin yaya Aryan ya fara kira, kira É—aya Aryan ya É—aga, chikin dashewar murya yace “Yusuf kun sauka lfy? “lfy lau yaya Aryan ya karfin jiki? “Alhamdulliah” “yauwa yaya Aryan pls alluran barchi nake son yiwa Lamrat” “akan wani dalili zaka mata Alluran barchi” shiru yayi yama rasa amsar da zai bawa yaya Aryan “Yusuf kana jina koma me dalilinka kasani dai alluran barci yana da illa ba kasafai akewa mutun ba sai idan ya zama dole, ka rabu da yar mutane karka sa mata wani chuta “to yaya Aryan wani magani ya kamata na bata domin ni gaskiya bana son kai ta asibiti kasan yadda tsarin kasar nan yake basu da Addini sosai” shiru yaya Aryan yayi yana nazari kuma yana son ya gano dalilin Yusuf na neman magani dan shima bai son tambayar Yusuf É—in tun da yaga sai wani kauche masa Yusuf É—in yake alamar bai son asan meke damun matar tashi, amma dole dai É—ayan biyu ne ko dai ta fara period ko kuma, yau ta karÉ“i bakonchin Yusuf “yaya Aryan ya kayi shirune? “Yusuf matar taka ta fara period ne? “Aa yaya Aryan ba period bane fa kawai” sai kuma yayi shiru, murmushi gefen fuska yaya Aryan ya saki dan ya gano me Yusuf ke É“oyewa “zan tura maka message É—in drugs da ya dache ka bata” “ok kawai Yusuf yace tare da katse kiran ya koma chikin É—aki.

Gaba É—aya sun haÉ—u a babban palon kasa domin chin abinci ban da Yusuf da Lamrat sai Bgs da baya nan shima, abinchi suke chi chikin kwanchiyar hankali chike da tausayi da tunanin me zai biyo baya Khalid ya dubi Hiyana ya fara magana “sister tashi kije ki kaiwa yaya prince abin chin sa ko” kallon Khalid yaya Ahmad yayi ya buÉ—e baki zai yi magana, cikin sauri Khalid ya É—aga masa hannu yana girgiza kai yace “bana bukatar maganar kowa wan nan umarnin Abba ne dan haka dole abi ko ana so ko baa so” jin haka yasa yaya Ahmad yayi shiru ita kuma Hiyana ta mike jiki ba kwari ta nufi kichin nasu, already jourfree mai Aikin su ya gama shirya abin chin yaya prince a chiki wani haÉ—aÉ—É—en katowar trey da kyar hiyana ta iya É—aukan trey É—in ta fito ta nufi É—akin nashi, tafiya take Kamar wadda kwai ya fashewa a chiki

Da sallama É—auke a bakin ta tashiga É—akin nashi yana kwanche saman katafaren gadon sa yana latsa waya daga shi sai short wannan haÉ—aÉ—É—iyar suran jikin nashi dake rikita mata da maza awaje lallausan bakin gashin kan nan nashi ya kwanto masa har kan fuska, kasan chewar bai É—aure ba kuma gashin na da tsawo sosai dan zai iya kai kusan tsakiyar bayan sa, É—amtsen hannun san nan kuwa kamar zasu fashe saboda karfi da samun horo mai kyau baki lallausan gashin dake kwance saman faffadar kirjin san nan kuwa sai kyalli yake, ga wani gashi mai tsantsi da taushi kwanche a chinyoyin sa har zuwa yatsun kafar sa haka ta sama ma gaba É—aya hannun sa baki lallausan gashin me mai kyau da sheki ne kwanche awajen har kan yatsun sa na hannu,

saman table dake tsakiyar É—akin Hiyana ta ajiye trey É—in, ta karisa Wajen gadon ta sugunna tare da sunkuyar da kai kasa, murya na rawa tace ” yaya prince ina wuni” shiru bai amsa ba ko kallon in da take bai yiba latsa wayar sa kawai yake “yaya prince ga abin chin ka chan na kawo maka”shiru kamar bai san da shigowar mutun a É—akin ba, jiki ba kwari hiyana ta miÆ™e ta fice daga É—akin, tana fita wani kukan bakin chiki ne ya zo mata da gudu ta wuche É—akin ta tafaÉ—a kan gado ta fara rera kukan ta, chikin kuka take faÉ—in “ni me nayiwa yaya prince yamin irin wan nan tsana haka sai kache ba musulmi ba ya Allah idan yaya prince ne alkhairin a gareni Allah ka kawomin mafita ta yadda zan samu kansa idan kuma shi ba alkhairi bane a gareni ya Allah ka gaggauta chiremin son sa a raina dan isar ka da karfin mulkin ka ya Allah nasan ba wan da ya isa ya bani abun da baka bani ba haka zalika ba wanda ya isa ya kwachemin abun da ka bani ya Allah ka dafamin, ya Allah kasan ina son sa ina kaunar sa tun farkon gani na da shi ya Allah ka dafawa rayuwata, kukan da yachi karfin tane yasa tayi shiru ta dai na magana ta chigaba da kukan ta mai tsuma zuchiyar mai sauraro har barchi yayi awon gaba da ita.

Yola Nigeria

A hankali Inna ta waro idon ta wani haske ne ya kashe mata ido da sauri ta runtse su

sake buÉ—ewa ido tayi a hankali, bin in da take kwance da kallo take sai wani jujjuya ido take sama, karaf idon ta ya sauka kan yaya Bello dake tsaye a Kanta ya harÉ—e hannu a kirji yana kallon ta, chike da mamaki tace “bello kai ne? Ina ne nan kuma? Waye ya kawoni? Ajiyar zuchiya yaya bello ya sauke tare da saukar da hannun sa kasa ya kariso in da take kwanche ya zauna a gefen ta burman nata ya fara magana “eh goggo habiba nine, nan kuma wajen mai magani ne, kuma ni na kawoki” yun kurawa tayi zata tashi amma ta kasa komawa tayi ta kwanta “yanzu Bello duk irin takurawa rayuwan ku da nayi bai sa kaki taimako na ba” “aa goggo habiba ki daina faÉ—in haka ko ba komai uwa É—aya uba É—aya kuke da Bappan mu kuma ni duk abun da nakeyi inayin sane dan Allah ba dan wani ba” kuka mai tsuma rai Inna ta fashe dashi chikin kuka take faÉ—in “Allah mai iko dan Allah Bello ku ya femin “goggo habiba kiyi shiru kinga yanzu kina chikin chiwo ni na yafe miki duniya da lahira Allah ya yafe mana tare” Shiru sukayi sai kuka kasa kasa Inna take, yaya Bello na rarrashin ta.

KANO

slowly zulaihat dake kwanche saman sofa ta tada kai da chinyar Aunty Amarya ta buÉ—e ido, da murna Aunty amarya ta fara faÉ—in “alhamdulliah alhamdulliah Allah mun godema ta farfaÉ—o” Ammi dake zaune a gefe guda ta taso ta nufo wajen tana faÉ—in “masha Allah” dogon tsaki Aunty amarya taja kafin tace “karki zo nan munafuka ba duk É—an ki bane yaja ai wlh da ya kashe yar mutane zai gane kurenshi” shiru Ammi tayi ta dakata da nufar tasu da take, Ummi dake zaune saman sofa mai zaman mutun 1 ta mike ta kama hannun Ammi ba tare da tayi magana ba suka fice daga É—akin sukayi part nasu.

Washegari Uk

Kwanche Lamrat take kan gado ta tada kai da chinyar yaya Yusuf sai kuka take,
Da kyar yaya Yusuf ya iya shawo kan ta ta dai na kuka kwata kwata taki chin abinci ita dai dole ya mai data wajen Ammin ta tun da kasheta yake sonyi, “my baby kiyi hakuri na miki alkawari ba zan sake miki hakan da zafi ba” waro ido waje Lamrat tayi chike da jin haushi tace “au daman yaya Yusuf zaka sake yimin hakan kenan? “My baby dole na sake yi maki mana idan ban miki ba taya zamuyi mu samu baby’s” “nifa yaya Yusuf bana son baby’s É—in na hakura kawai ka mai dani wajen Ammi na” “haba my baby idan na mai daki wajen Ammi ni kuma fa dawaye zan zauna kenan? “Ka zauna kai kaÉ—ai mana ai daman kai kaÉ—ai kake zaune ba da ni ba “to shike nan tun da haka kika che yanzu dai zan mai daki wajen Ammi ni kuma sai na samo wata baby na Aura ta aifamin baby’s masu kyau” kuka mai karfi Lamrat ta fashe dashi a razane yaya Yusuf yace “my baby lfy kukan me kuma kike “ni yaya Yusuf ka kaini wajen Aunty hiyana ta wlh ni yanzu bana son ka tun da dai wata mata zaka aura” dariya mai karfine ya kwache masa, dariya yake sosai har da rike chiki, ganin yana mata dariya ne yasa ta kara sautin kukan ta sosai, ba shiri ya dakata da dariyan da yake “sorry my baby tuba nake ni ai ke kaÉ—ai kin ishe ni ba ruwa na da wata mace ni kam wasa nake” “ni dai yaya Yusuf ka kaini wajen Aunty hiyana tun jiya fa ban ganta ba”tana magana tana shesshekar kuka “to kiyi shiru idan kina son zuwa wajen su nima yanzu zanje na shirya na je wajen aiki sai karfe 2 na rana zamu dawo sai mu kai ku wajen shopping dan ku zabi kayan da kuke bukata” “to nayi shiru ka kai Ni” mikewa yayi batare da ya sake magana ba ya kwantar da kanta a saman gadon ya sauko kasa ya shiga dressing room jim kaÉ—an ya fito hannun sa É—auke da jallabiya baki ya dawo kan gadon É—agota yayi ya zura mata jallabiyar san nan ya miÆ™e ya É—auke ta chak ya nufi waje da ita, a babban palon kasa ya samu su Zahra gaba É—ayan su suna zaune suna hira hiyana ce kaÉ—ai bata wajen, saman sofa mai zaman mutun 3 ya direta chike da jin kunya lamrat ta fara gai da Zahra, shi ko juyawa yayi chikin sauri Zahra na gai da shima bai bi ta kan taba ya haye sama.

Da sallam hiyana ta shiga betroom É—in Bgs sanye take chikin doguwar hijabi har kasa fari tas, hannun ta É—auke da katon trey mai É—auke da kayan breakfast nashi, tsaye yake gaban mirrow sanye da uniform na sojoji yana kokarin É—aure gashin kansa ta baya, kasa kasa hiyana ke satar kallon sa ba karamin kyau kayan suka masa ba kamar dan shi akayi su, sai wani fitinannen kamshin da yake zubawa kamar anyi É“arin turare ajikin sa, sosai take shakar kamshin turaren nashi

table É—in tsakiyar É—akin ta nufa da niyyar ajiye masa abincin, turus ta tsaya ganin abincin da ta kawo masa jiya da daddare ma ko taÉ“awa bai yi ba, shiru ta tsaya tana tunani shin na ajiye masa breakfast É—in ko zai chi ne ko kuma dai na haÉ—a har da na jiyan na mayar kitchen tun da ba zai chi ba, tayi nisa chikin tunanin da take, sai ganinshi tayi ya wucheta ya nufi kofar fita, chikin sauri ta tsugun na kasa murya na rawa tace “ina kwana yaya prince” ko kallon in da take bai yiba ya fice daga É—akin, shiru tayi ta kasa miÆ™ewa dan ji tayi gaba É—aya jikin ta ya mutu, yanzu ya zatayi da abincin nan, da Æ™yar ta miÆ™e ta fice daga É—akin ta mai da breakfast É—in kitchen san nan ta dawo ta É—auki na jiyan ma ta mai da kitchen chike da É“achin rai ta koma É—aki ta kwanta

Misali karfe 2pm gaba É—ayan su suna zaune a palon kasa suna hira wayar Zahra dake hannun Lamrat ya fara ringing, chikin sauri Lamrat ta miÆ™awa Zahra wayar, ansa Zahra tayi ganin sunan Aunty farida ne ya bayyana a kan screen É—in yasa ta yin picking da sauri ta sanya wayar a hand-free dan su hiyana su gaisa da ita gaba É—aya, daga É—ayan É“angaren Aunty farida tace “Auta ykk? Ya Uk? “Aunty farida muna lfy ya junior? “Junior yana lfy ina Hiyana? “Gatanan Zahra tayi maganar tana miÆ™awa hiyana wayar, chikin sanyin murya hiyana ta fara magana

“Aunty farida ina wuni” “lfy lau my Hiyana ykk y mijinki? “Muna lfy ya junior” “yanzu dai bar zanchen wani junior mu fiskanchi abun dake gaban mu, kinga yanzu mijin ki yayi blocked É—ina, waro ido waje Hiyana tayi “yau Aunty farida ke da kanki yaya prince yayi blocked? “Eh my Hiyana nima na sha ruwan mamaki amma wan nan duk bashine matsalar ba kinaji kyalesa idan ya huche zai buÉ—e Ni, yanzu dai kina yin abubuwan da na tsara miki ne? ko kuma dai kin chigaba da zama shiru shiru “Aa Aunty farida inayi jiya ma na kai masa abinchi yau ma kuma na kai masa” “good my Hiyana abu na gaba da zan faÉ—a miki ya kamata ki rage tsoronsa kuma na faÉ—a miki ki daina sanya manya manyan hijaban nan da kike sanya wan kina jina ko? Zan sanya yaya Khalid ya sai muku waya gaba É—ayan ku dan mu rinÆ™a waya sosai kinji ko? Hiyana zatayi magana sukaji diran motochi su Bgs a chikin gidan alamun sun dawo daga wajen Aiki, chikin ruÉ—u hiyana tace “Aunty farida gasu yaya prince sun dawo aikin” “good my hiyana yanzu yana shigowa ki bishi É—aki nasan yana shiga É—aki zai zauna saman sofa yaÉ—an huta to yana shiga ki bishi ki chire masa takalmi da socks kinji? Shiru Hiyana tayi tana tunanin ta yarda zata fara tunkaran Bgs har ta chire masa shoe “my Hiyana kimin alkawarin zaki min hakan kinji? “Aunty farida na miki alkawari zanyi tana magana wasu zafafan hawaye na bin kunchin ta, hannu Zahra tasa tana gege mata hawaye chike da tausayin ta, katse kiran tayi ta ajiye wayar a gefe ta rike hannun Zahra tanan kokarin fara magana kenan, sukaji takun tafiyar su Bgs nan take suka nitsu É“oye fuska hiyana tayi chikin chinyoyin ta dan hawayen nata sunki tsayuwa kuma bata son su yaya Yusuf suga tana kuka.

Bgs ne a gaba ya shigo kafin Zahra ta É—aga masa gaisuwa ma ya haye sama abun sa, miÆ™ewa Hiyana tayi chikin sauri ta bi bayan sa, a tare su Khalid suka shigo gaba É—ayan su suka baje a palon kowa ya zauna kusa da matar sa, chike da so da kauna suke gaisawa da juna “ke Amrat tashi kije É—aki ki É—auko min laptop di na” chewar yaya Fahad, da gudu Amrat ta miÆ™e ta haye sama

A É“angaren hiyana kuwa

Tana zuwa bakin kofar É—akin yaya prince ta tsaya ta goge hawayen ta, san nan ta shiga É—akin da sallama yana zaune saman sofa mai zaman mutun 2 ya É—an jingina da jikin sofan ya lumshe ido, a nitse ta tako zuwa gaban sa jikin ta har rawa yake, ta sungunna, ta kai hannunta kan takalmin sa, da kyar ta ita sai ta hannun ta ya dai na rawa, igiyar ta kalman tafara kwanchewa, da kyar ta iya É—an É—aga kafar tasa ta zame ta kalmin haka ta zame É—ayar ma, É—an É—aga kafar wandon nasa sama tayi ta kama bakin safar kafar tasa ta zame ta a hankali, zubawa kafar tasa ido tayi, ba karamin kyau dogayen yatsun kafan sa suka mata ba, ga wani bakin lallausan gashi a kwanche a kan yatsun, farchen (kunba) kafar sa farare tas sai kyalli suke bata san lokachin da ta kai hannun sa saman yatsun nashi ta shafuso su ba wani gigitachen mari ya sakar mata a kumatu wadda yasa ta mikewa tsaye ba shiri tare da fasa wani razanannen ihu chikin tsawa yace “get out” a guje ta fice daga É—akin ta nufi nata

Tana shiga É—akin ta ta chire hijabin jikin ta, ta sanya karfi ta yagashi gida uku chikin sauri ta É—auko face Mark ta sanya a fuskar ta É—aukan hijabin nata tayi ta taka saman gadon ta ta É—aura hijabin a jikin Ac tanayi tana kuka mai suma rai, daure hijabin nata tayi sosai chikin kuka tace “banga anfanin rayuwata ba wlh Bappa ya rasu Inna ta rasu diyana ta É“ata yaya prince da yake matsayin mijina ya tsane ni to me kuma ya ragemin sosai ta gyara face Mark dake fuskantar ta yadda zatayi saurin mutuwa kar numfashi ta ya fita É—aure wuyar ta tayi da kyau san nan ta sauka daga kan gadon kafar ta na lilo a tsakiya sai karkarwa take ta zaro blue eyes nata waje sosai saboda shake wuyar ta da hijabin yayi,

Amrat na fitowa daga ɗakin su rike da laptop ɗin yaya Fahad, daga ɗakin hiyana taji wani irin numfashi da take da sauri ta nufi ɗakin tana nura kofa taga hiyana na kokarin mutuwa dan gaba ɗaya har jikin ta ya fara saki, wani razanannen ihu Amrat ta saki wadda ya dira a dodon kunnen kowa dake gida, gaba ɗaya su Khalid suka miƙe a tare suka hauro dai dai lokacin Bgs ma ya fito daga ɗakin sa dan jin irin ihu da Amrat ta saki, kusan tare suka shiga ɗakin Hiyana.

Bgs na ganin halin da Hiyana ke chiki yaja wani dogon tsaki tare da karisawa chikin É—akin da hannu É—aya ya damki kafafunta tare da chire hijabin da ta É—aure wuyarta ya sauko da ita kasa sai wani tangal tangal taka alamar ta jigata, wuyar ta ya damko ta bayan ya fara janta har suka fito waje, chike da bachin rai Khalid yace “haba Bgs menene haka? Bai bi ta kan kowa ba yayi waje da ita chikin bayan motar sa ya jefata ya shiga gidan gaba yau da kansa ya ja motar da gudu suka bar gidan, a razane Fahad yace “ina key É—in É—ayar motar nan dole na bisu dan nasan halin yaya prince yanzu wani abun zai mata, tun kafin Fahad ya karisa maganar yaya Khalid ya shiga motar sa ya tayar da sauri Fahad da Ahmad suka shige chikin motar da gudu suka bi bayan Bgs

sai kuka su Zahra suke suna addu’ar Allah ya kuÉ“utar da hiyana daga hannun Bgs

Wajen saman wata gatuwar dutse dake zubar da ruwa kasa Bgs ya tsayar da mota fita yayi ya buÉ—e gidan baya ya damko wuyar Hiyana ya jata har zuwa bakin dutse kallon kasan dutse Hiyana tayi katuwar rafine awajen a tsorace ta dawo da kallon ta kan shi, so take ta chire face mark dake fuskantar ta masa magana amma kafin ta É—ago hannu ya daga mata tsawa chikin tsawa yace “ba mutuwa kike son yi ba to ga hanyar da zaki mutu chikin sauki, yana gama faÉ—in hakan yayi wurgi da ita kasan dutsen ya juya abun sa…..

 

Masu karatu Bgs fa ya buga min kai yau sai mun haÉ—u gobe idan mai dukka ya kaimu naso na muku 2 page amma bani da charji shiyasa na muku long page Ashe karatu lfy azo a bani hot comments

NEW TEAM
THE TALENT TROUPE WRITER’

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*


*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
by(xeemat….love)

*4, JINI DAYA*
by(mrs bbk)

The Talent Troupe Writer’s 

*DUK ƘARFIN IZZATA*

Story And Written
⬇️
*Star lady*

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai

No comments