Breaking News

Gidan Aunty book 2 Page 12

BOOK 2

Page 12??

NIGERIA ????

6 hours 10 Minutes ne ya kawosu Nigeria, gabaki d’ayansu babu Wanda be lumshe ido ba da ya sha’ki iskar Nigeria musamman Yah moh da tahee da suke ganin komai kamar a mafarki, Mimi da momy ma sai bin ko ina suke da kallo dan wannan ne karansu na farko da suka zo Nigeria.



Wata Blank tinted cars ne guda uku suka zo d’aukarsu, momy da dady suna guda d’aya , Mimi da tahee ma d’aya sai Yah moh tare da junior , kai tsaye motocin kan babban titin da zai sadashi da mai tama suka nufa , cikin wani ‘kayataccen gida meshegen kyau , duk da kallo d’aya zaka masa kasan saban gidane amma sosai yayi kyau tun daga wajan sa . Suna cikin main gidan Suka ga komai na anfanin rayuwa akwai a cikin gidan kamar ana rayuwa cikinsa , ko ina tass sai faman kamshi da sanyi ke tashi, gabaki d’aya 5 bedrooms ne acikin gidan sai 3 palour ne had’e da bedroom da toilet a ciki, momy da day nasa ma suka hau , tahee da Mimi suka d’auki d’aya me falo, daga ‘bangaran hagu shima yah moh ya d’auki d’aya , yau junior baki ya mutu sai bin ko ina ya ke da kallo, gabaki d’ayansu agajine suke shaf shaf mimi tayi wa junior wanka , suma sukayi kafun su rama sallolin da ake bunsu, basu tsaya cin abincin da aka kawo musu ba sukabi lapiyar gado su uku, junior rungume da tahee . Kiran sallah isha’i ne ya tayar da tahee , Mimi alokacin ta farka , sai da Suka idar da sallah kafun kowannansu ya samu nutsuwa sai lokacin suka d’auko abincinsu, shima junior Tashinsa tahee tayi duk da ‘karancin shekarunsa ta koyar dashi yadda zai yi sallah da su karatun, Alhamdulillah kuma yna ‘ko’karin yin hakan.suna gama cikin abincin suka fito babban falon, momy Suka tar kawai, “ har kun tashi daga baccin kenan”, cewar momy , amsa mata sukai gabaki d’aya da “eh”, kafun mimi ta furta “ momy Dady da yah moh fa? Sunaga bangansu ba”, batare da momy ta kalleta ba ta bata amsa “ sun fita zasuyi d’an shopping “, kamar wacce aka zabura Mimi ta matso kusa da momy “ Haba momy amma kuma kika ‘ki tashin mu? Muma sai da sai muzaga gari”,hararar ta momy tayi “Ance miki kowa bashi da hankaline kamarki?sabida kece amarah yawo daga zuwa sai fita yawo ,kishiga taitayinki”, turo baki Mimi tayi kamar wata ‘karamar yarinya “ Haba momy, kinsan fa wannan ne karo na nafarko dana fara zuwa Nigeria, mai yasa kike mun hakane ,” momy bata, bata amsa ba sai hararar ta da tayi , tahee tana gefe sai faman dariyar dramarsu take , inda sabo sun saba da wannan rigimar, shigowar su dady ne ya katse musu hanzarinsu, gabaki d’aya sannu da zuwa sukai musu bayan junior ya gudu wajan tahee “ momy munje yawo babu ke, Big dadi ya siyo mum guns da cars, if I saw an evil person , I will just shoot them all”, gabaki d’aya dariya suka saki , kafun tahee ta furta “ but hope kayi masa Godiya ?” Kansa yayi nodding kafun ya furta “ yes nayi , bari ma Kigani “, sai ya ‘kara juyawa ‘bangaran yah moh “ Big Dady thank you for everything “, hancinshi kad’an tahee taja “ good boy”,shima hancin nata yaja “ good momy , I love you !”, sai yai mata peck a goshi , gabaki d’aya kuma sai kowa ya tsaya kallansu dan ba ‘karamin kyau sukai ba . Muryar Mimi ce ta dawo dasu hankalinsu “ Dady shine kuka tafi yawo ko kafad’amun mu biku ko, kasan wannan ne karo na nafarko zuwa Nigeria , and nayi complain momy tace wai haryanxu bangirma ba”. Murmushi dady ya saki “ rabu da ita , gobe kushirya driver ya fita daku, haka nan momy bazata yi muku kulle ba ,ko?” Ya kalli junior , girgiza masa kai junior yayi “ junior is a good boy”, gabaki d’aya dariya suka saki , ledar da suka shigo dashi suka bawa kowa , ganin dare nayi, junior a wajan yah moh yace zai kwana shiyasa tahee suna shiga suka bace tsirensu gwanin burgewa suna ci Suna hira suna shirya yadda plan d’insu zai kasance, dan kansu suka hakura ganin dare na ‘karayi suka kwanta. (Asuba tagari ) ??.

WASHE GARI

Tun ‘karfe sha biyu Mimi ke ro’kan tahee su shirya zaga gari Amma tahee tayi Burus da ita acewarta futar yamma tafi dad’i, hakan ne kuwa ya faru basu suka fita ba sai bayan sallar magaruba lokacin gari yayi sanyi duk da yanayin kamar damuna na ‘ko’karin shigo wa , gabaki d’ayansu kowa ya ci wankansa kana ganinsu kaga kyawawan yan mata da kud’i da nera ya gama zama a jikinsu.dukansu kwalliyr abaya sukai Tahee red colour, Mimi kuma Rambo colour ta saka ,junior kuwa shima wankan ‘kananan kaya Mimi tayi masa , idan ka gansu su uku bazaka ta’ba cewa Tahee tana da aure ba , sabida yadda ta ‘karayin wani fresh musamman junior da yake da shekara uku.BMW d’insu ba’ka da dady ya bar musu da Wanda zai kasu suka hau, kai tsaye babban mall din JABI LAKE MALL ya nufa nasu, dukda kasashen da suke zuwa sai mimi taga mall din yayi mata kyau , Tahee kam murmushi kawai take “ Yaushe zanganka ? I missed you badly, please “, ita kad’ai take tunaninta cikin zuciya bata ankara ba sunzo shiga sukai karo da wata , gabaki d’ayansu lokaci d’aya suka d’ago suna bawa junansu hakuri , ganin barin da tahee tayi matane ysa ta tsugunna tana kwashe mata kayanta , junior da Mimi na taya ta, juyowar da budurwar zatayi sai naga ba kowa bace face Zahra , dukda tsawan shekara hudu itama ta canza sosai ta zaba budurwa abunta , cikin sakin murmushi tahee ta furta “ kiyi hakuri ban kula ba”, itama zahra murmushi ta sakar mata “ Haba wallahi karki damu ai ba ke kadai ce me lefi ba hardani”, sai ta tsaya kallan tahee kuma kafun ta furta “ fuskarki sai tayi mun shige da ta oumman mu kamar ita tahaifeki, kaman ninku har ya baci” da Sauri tahee ta kalleta bata san lokacin da ta furta “ oummanku ?”,zata kuma mata wata tanbaya idanun zahra ya sauka kan junior , eyes dinta ta zaro gwanin ban sha’awa “ Kanin kune wannan?kyakkyawane shi. Koda yake karna cika ku da surutu sunana zahra ku fa “, ganin yadda take da fara’a ga tahee na ‘ko’karin share ta yasa tayi saurin cewa Sunana Mimi, sabida wani tunani da yazo mata , da murmushi ta kalli tahee “ kefa ?” Tahee zatayi magana junior yayi saurin cewa “ sunanta SweetLove”, Ajiyar zuciya Mimi tayi jin abunda junior yace , itama murmushi Zahra tayi zata kuma magana khaleed ya fito , shima bin fuskar tahee yayi da kallo yana tunanin inda yasan ne fuskar Amma sai kuma y share ya kalli zahra“ tun d’azu nake nemanki kinsan oumma na jiran mu”, kayansa zahra tayi “ sorry yaya khaleed , bari na d’auki kayana “, tana kai ‘karshen zancanta ta d’auki kayanta tayi wasu tahee sallama , suma daga nan suka shiga sukayi siyayyar da zasuyi, sosai suka zaga abuja ba lefi kafin su koma gida a gajiye .

**Haka suka ci gaba da rayuwa batare da kowa yasan da zamansu ba hatta shima yah moh yana taka tsan tsan da inda zai shiga , sai da suka shafe 1 month guda a Abuja, hakan yayi Daidai saura wata d’aya da sati uku bikin yah khaleed. Mimi da tahee na neman hayyar da zata sadasu da gidan Nahyan amma gabaki d’aya babu wannan damar. Suna zaune shiru kowa yana neman mafita saiga yah moh ya dawo gida , kana kallan fuskarsa zakaga yana cikin annashuwa,” yah moh meyasa ka farin ciki haka ?” Wani murmushin ya ‘kara saki “ kun shirya fara aikin ?”, kallan juna sukai alamun basu gane ba , hakan yasashi ‘kara sakin wani murmushin tare da tura musu wani file “ ku shirya gobe zaku goma Lagos amma ba da wannan fuskar ba , musamman ke tahee zata ganeki, face d’in da kuka taho dasu za a kawo miki artist tasa miki, “ har yanxu basu fahimci abunda ya ke nufi ba shiyasa tahee tace “ yah moh har yanxu ban gane me kake nufi ba “, mikewa tsaye yyi “ duk plan d’in ku nasanshi, kuna neman yadda zaku shiga gidan ai ko, suna da biki nan da 2 month , naji labarin Ammeey tana neman yar aiki, nasan yanxu kinfi kowa sanin halinta keya kamata keje ame aikin ta shiyasa nace za’a sa miki face, ke kuma mimi ummey itama tana bukatar me aiki sai ki bar fuskarki, kubi ta ka tsantsan , bata da Imani ko kadan , na ruga nasanar wa momy da dady , ina ‘kara Jaddada muku , kubi a hankali duk abunda yake faruwa kuyi ‘ko’kari kusanar dani , later on akwai cameras da zan baku ‘ kanana inaso kowani part kusaka batare da sanin kowa ba musamman Ammeey , tana da wani lumbu shima a part d’inta ki tabbata kunsaka . Abu na biya da zan sanar daku Aikine zai had’a ku ba ‘yan uwantaka ba , kada kuyi gangancin da za a gane shirin ku ko asan kuna da ala’ka “.yana kai Karshensa yabar falon. Wani irin daka tsalle Mimi tayi “ yes finally zanga ummey”, itakam tahee wani irin farinciki da annashuwane ya kamata ko bakomai zata ga farin cikinta , zata ‘kara sashi a idanuwanta , ita kadai take tanbayar kanta , ya yake ? Har yanxu be manta taba?” Da wannan tunanin suka shiga shirin zuwa lagos gobe bayan uban kayan gwanjon da Suka je suka siyo kamar na almajirai, tabbas sun shiryawa kowa, musamman tahee da take jin ta kamar tayi tsuntsuwa.
Washe gari kamar yadda aka tsaya da wuri artist tazo ta saka wa tahee fuskar,idan ka ga fuskarta bazaka ta’bacewa Itace ba. har wani mai artists din ta basu da zasu shafa , suna shafawa kuwa fatarsu tayi dan duhu kamar sun taso daga wahala . Amaimakon subi jirgi Sabida fuskar da aka sa musu da wuri suka bi tamota, suna shiga matar da Ammey tasa, takawo mata mai aiki aka kai tahee duk da cikin zuciyarta tana mamakin yadda Yah Moh yasamo wad’annan information din gabaki d’aya , Tahee tana shiga cikin gidan ta fara washe ha’kora kamar wata sauna daga ga abu sai ta fara binsa da kallo kamar ‘yar ‘kauyen gaske , wani ne ya rako tahee shima kana ganinsa kaga me aikin a fakaice ya bawa tahee letter sabida acikin gidan yake aiki kafun ya fara washe baki ganin ta hajiyar tafito har ‘kasa ya dur’kusa” hajiya ran gida , hajiya sarautar mata, hajiya ga yar aikin da kikace kina bu’kata” kallan tahee tayi da Sauri itama ta zube ta fara yiwa matar kirari kamar wata marokiya, yadda take mata kirarin ne yasa hajiya sakin murmushi, “ kincinye jarabawa an d’auke ki , yanxu zan kaiki gidan”, damn hajiyar bata damu da ko wace me aiki bace tunda an bata kud’in ta class a hannu. “ fargaba da farin cikine ya bi ya tsayawa tahee a zuciya tana tunanin gamonta da shi idan ta shiga gidan ,” kallanta matar tayi “ taso mu tafi “ da Sauri tahee ta d’auko daurin kayanta tana bin bayar hajiyar “, basu d’au dogon lokaci ba suka suka kama hanyar BANANA ISLAND , mintuna kad’an ne ya kaisu .Tahee naganin kofar gidan zuciyar ta ‘kara tsinkewa take awajan wata iriyar iska tafara ratsata, gudun kar hajiya saude ta fahimceta yasa tafara washe baki ganin babban gida . Gate d’in farko da ‘ aka bud’e ne yasa tahee ta firgita da har saida hajiyar ta kalleta amma batace komai ba…

 

????GIDAN AUNTY????

07041879581
MSS LEE

No comments