Breaking News

Gidan Aunty book 2 Page 7-8

Page 7&8??

Kai tsaye khaleed yana fita daga part d’in dada part d’in ummey ya nufa itama ya mata sallama bayn gift d’in da ta basa ya kaiwa zahra, mahma ma da dada gabaki d’aya sai da suka bawa zahra gift, king baya gida


shiyasa basuyi sallama sea ta waya, lokacin da zai tafi sai kallan part d’insu ilham yake ko zai ganta amma babu ita babu alamarta, murmushi ya saki lokacin da ya tuna kunyarta, ji yake kamar ya je part d’insu ya dubata amma yasan hakan ba meyuwa bane . 2:30pm na rana jirginsa ya tashi zuwa Abuja, 1hour 15mins ne ya kawosa Abuja , yana fitowa harabar Airport ya tarar da zahra na jiransa, hannu ta mi’ka masa kamar wasu friends sukayi shaking , fuskarta cike da farinciki ta furta “ Nayi missing d’inka yaya”. Nima nayi missing d’inki cewar khaleed , suna zuwa gida ya tarar da oumma ta had’a masa favorite food d’insa wato dambu da kuma zo’bo da yake matukar so, sun d’an ta’ba hira kad’an bayn ya bawa zahra gift d’inta kai tsaye d’akinsa ya nufa ya watsa ruwa, so yake ya runtsa amma kuma ya kasa Sabida muryarta da yake san ji, phone d’insa ya d’auka kamar zaiyi dialing wata number da yayi saving da MINE ?? sai kuma ya fasa , sau biyu yana ‘ko’karin kiran wayar , daga karshe ajje wayan Kawai yayi yana lumshe ido , shi kad’ai yana sakin murmushi abunsa.

*******Ilham ko data gudu, kai tsaye part d’insu ta wuce har mamy na tanbayarta lapiya amma bata amsa musu ba sai faman sakin murmushi take ita kad’ai , tana shiga d’aki ta kulle ‘kofar tare da kallan d’an ‘karamin box din brown colour meshegen kyau, yana bud’e wata sarki ce aciki sai faman walwali take yi ita kadai, zaro idanuwa ilham tayi sosai sarkar tayi mata kyau musamman Heart d’in da ke jikin sarkar ya fi komai d’aukan hankalinta, gaban mudubinta ta’karasa har Zata saka sarkan sai ta fasa , yar ‘karamar letter d’in dake jikin box d’in ta bud’e , wasu ‘kananan flowers ne Suka fara fitowa daga jikin paper ne me design din flower a jiki, kan gadanta ilham ta koma tana sakin ajiyar zuciya , letter d’in ta soma karantawa cikin zuciyar ta, daka ‘karshe ma pillow d’inta ta d’auka taba boye fuskarta ita kadai sai faman sakin murmushi take, lokaci zuwa lokaci tana kallan sarkar da ya bata da kuma letter d’in, gabaki d’aya yinin ranar da tunanin khaleed ta yini , ko me zatayi sai ya fad’o mata arai musamman lokacin da yake furta “ ki kulamun da kanki”, rufe idanuwanta tayi gabaki d’aya tana tuno abunda ya faru d’azu, sai taji kamar bata kyauta ba, amma wani zuciyar na fad’a mata Daidai ne abunda tayi.

????

karfe 9:00pm na dare gabaki d’aya familyn Nahyan suna falon dada banda king da gabaki d’aya ynxu baya shigowa part d’in ko wannan su, a wannan karan har da Ammeey a falon, duk Wanda ya kalli fuskarta zai san tana cikin damuwa, amma babu Wanda ya kawo wani abune yake damunta sai canzawar king da kowa yasan tafi kusan ci dashi, hatta part d’in ta yanxu baya shigowa , abunda ya ‘kara tayar mata da hankali sabida ‘kullun maganin da bokansu ya bata, indea ba a cikin abinci tabasa ba nan da sati d’aya toh komai zai iya lallacewa, a binciken da tasa ayi mata akan tahee kuwa , hatta bokansu baya iya ganin komai a duk lokacin da yake bincike a kanta cikin abun tsafinsu, sai hasken da yake kashe masa idanuwa da tsoratar dasu, bakomai ne yafi d’aga mata hankali ba musamman dawowar tahee da boka ya tabbatar masu, sannan a wannan karan tabbas idan ta bari tahee tashigo cikin gidan komai nata data d’au shekaru tana ginawa zai rushe rushewar da bazea ta’ba gyaruwa, duk da maganar boka ya girgizata sosai amma duk da hakan bata karaya ba , sannan tayi Al’kawarin bazata ta’ba barin tahee ta cikin familyn nan ba , yanxu burunta kawai king yaci gubar da bakan tsafinsu ya bata, shiyasa ta fakaice da had’a wa duka family d’in dinner , sannan ta had’awa king favorite kunun a yarta da ta zuye duka gubar a ciki yanda ci d’aya zai tsinka masa komai na jijiyoyin jikinsa. Amma gabaki d’aya babu king babu alamar sa gashi ta hana kowa ta’ba zoban da tayi masa, sau hud’u Ammeey tana gwada kiransa a wayrta , amma ko sau d’aya be d’aga mata kiran ba, hakan ba ‘karamin ‘bata mata rai yayi ba , har wajan 9:30 king ne shigowa , kowa ya damu da’kin shigowarsa Amma duk sun masa uziri, gumine ya soma gesowa Ammeey ganin saura mintu na kudun ayar data sawa magani ya canza zuwa launin’baki,rai a’bace Ammey ta d’auki kunun ayar zata tafi, gabaki d’aya mutanan falon kallanta sukai, murmushi tasakar musu cikin rarrabewar murya ta furta “ zan sa masa a fridge ne kafun ya dawo”, girgiza Mata kai abeey yyi, “ no karki damu ki dawo kawai kiyi zamanki “, a rud’e Ammey ta kallesa “ Dama akwai abunda nakeso na saka a ciki sai yanxu ya fad’o mun”, ki barshi kawai, cikin zuciyar Ammey kamar taje ta sha’kesa ta furta bazan dad’e ba yanxu zan dawo ai, gudun kar ya sake magana tayi saurin juyawa , lokaci d’aya momy da ummey suka bita da kallo, hakanan kawai ummey take jin kamar akwai abunda ya kamata ta sani , amma kasan cewar ta mace me ‘boye komai sai ta ajje zancen a gefe, wayar ilham ce ta soma ‘kara gabaki d’aya sai hankalin kowa ya koma kanta, ganin number ba suna ne yasa ta d’an mi’kewa “ Dama husna ce ta kira ni”, gida mta kai sukayi kafun ta wuce , kallan juna sumayya da firdausi sukai, da ido suke nunata Suma ‘kunshe dariyarsu.

Saida ta tabbatar ta shiga d’akinsu ta rufe , alokacin kiran farko har ya katse, kafun wani ya sake shigowa kamar bazata d’auka ba , sai kuma ta d’auka bakinta d’auke da sallah, ajiyar zuciya taji an sauke ajiyar zuciya, gabantane ya soma fad’uwa jin anyi shirune yasata cire wayan a kunnan , still ba ayi magana ba , ‘karamin tsaki taja zata kashe taji ance mata “sorry “, da Sauri ta ri’ke wayarta dake neman fad’uwa ‘kasa dan sam batayi zatan shi bane , da ‘kyar bakinta ya iya furta “ yaya khaleed barka da dare ya hanya “, shiru be amsa ba, kara maimaita tayi nan ma be amsaba,hararar wayar tayi kamar ta kashe sai taji saukar muryarsa kuma “ I missed you “, shiru ilham tayi tana saurarar bugun zuciyarta, me yake nufi da maganganunsa,” Ba’amsa?” Ya tanbaya nan ma shiru tayi ta kasa amsa masa murmushi yasaki kad’an kafin ya furta “ shikenan, kula mun da kanki kinji? Good deary “ sea Kuma kit ya kashe kiran , bin wayar tayi da kallo kamar me jira ya ‘kara kira , ita kadai sai tsaki take ga wani irin feeling dataji yana tasoma ta tunda ‘kafarta har zuwa saman kanta, a gefe ta ajje wayar lokaci zuwa lokaci tana dubawa, a haka bacci ya d’auketa tare da wayar a hannunta.

A ‘bangaran Ammey kuwa wani bakin cikine ya tokare mata ma’koshi , tana komawa part d’inta a zuciye ta jefarda jug d’in take a wajan ya fashe gabaki d’aya kunun ayar ya zube a’kasa , ko cikakken muntuna biyu be ba daga kalar kunun ya koma ba’ki ‘kirin dashi, sai a lokacin ta ankara da abunda tayi, cikin mummunan ta shin hankali ta d’ora hannayenta aka tana kwarara ihu ko damuwa da Ajiyata batayi, gabaki d’aya ta fita hayyacinta, zoban hannunta ta murza take a wajan ta ‘bace battttt.

YOLA

Cikin matsanan ciyar tashin hankali Ammeey ta bayyana cikin babban falonsu dake cike da kayan shirka , sabida tashin hankalin da ta shiga a wannan karan ko damu da kulle fuskarta batayi ba kamar yadda ta saba ,ragowar abokanan shirkar tata ko wannansu na zaune cikin jajan ‘kyalle daga cikin su zuwa ‘kaurinsu ko kaya babu a ciki, cikin kururuwa Abar kauna take kiran sunan gunkinsu, kusan sau uku be amsa ba kuma babu Wanda yayi magana cikin mutanan wajan, a na hud’in ne data kara kiran sunanta taji saukar tsawar da tunda Tashi ga cikin kungiyar ba a ta’ba yi mata ba Sabida ita d’in kullun me nasara a fagen aikinsu.
Cikin kausash shiyar muryarta mara dad’in ji ta daka wa Abar ‘kauna tsawa da har saida tayi suman wucin gani, cikin muryarta mara dad’in sauraro rai a’bache ta kalli Abar’kauna “ kinyi sake , kinyi sake , kin yi saken da damar ki ta kubuce miki, tabbas kisaka aranki daga rana irin ta yau , ginin ma sarautar da kike ‘ko’karin kammala lawa ta rushe, rushewar da bazata sake tashi ba har sai kin dawo da yarinyar ta kikayi sanadiyyar barin ta gidan, tabbas Abar ‘kauna kina cikin tsaka , Sabida lalatawa dodan tsafi aikin sa, idan baki kashe sa nan da kwana bakwai ba , to tabbas yayi miki nisa hakan na nufin lokacin tonuwar asirin ki ya bude, dama d’aya kike da ita , ki dawo da yarinyar cikin gidan sannan ki bawa dodan tsafi Jinin ta dana cikinta,
Idan ta dawo kuma zaki iya shiga kasada komai zakiyi kuma baze kara tasiri akanta ba , sabida tana tare da Jini guda hudu da kikayi kokarin rusawa, dawowarta kamar tonuwan asirinkine,ta ‘karasa tana sakin wata yar iskar dariya mara dad’in ji, lokaci d’aya wani ‘bakin hayaki ya cika falon tsawan mintuna kafun ya washe babu wannan Matar, wata iriyar kururuwa Ammeey ta fara a haukace kamar ta ‘babbiya, sam ta fita cikin hayyacinta, fad’i take sai na kashe ka , sai na ka she ka, gabaki d’aya bata jikin hayyacinsa , suma sauran mutanan zagayeta suka somayi suna wani irin surutai kafin lokaci taya gabaki d’ayansu su bace duka .

????

A ‘bangaran king gabaki ya ‘kara sauyawa sama da ydda aka sansa a baya , kwata kwata baya murmushi , baya fara’a sannan baya yiwa kowa magana sai dai ya zuba maka narkakkun kyawawan idanuwansa masu ladaftar da mutum,gabaki d’aya ya sauya ya zama wani irin Miskili na bugawa a jarida , ga saurin zuciya da ya koya , hatta abinci yanxu baya sai ummey ko samreen sun soma kusa sannan da d’ar zaici spoon kad’an , yana shiga sabgar kowa a gidan shiyasa kowa ya kara shiga taitayinsa, lokacin da Amray ta samu labarin farfad’owarsa da murnarta ta dawo gidan, alokacin dada ta sa masa kukan sai yasha furar da ta dama masa ganin baya cin komai hatta furar da yake mugunso, cikin iyayi Amrah ta shiga cikin falon,sabida tsananin farincikin da ta shiga lokacin da taji labarin ‘batan Tahee , shiyasa tazo da confidence d’inta bayan kwallin da mamanta ta bata acewarta Indai suka had’a ido da king daga lokacin ta mallakeshi komai zata iya sasa, tana shigo wa kai tsaye ta sauke idanuwanta da suka ji kwalli , Daidai lokacin da yake d’ago idanuwansa, cikin sa’ a idanuwanta suka shiga cikin nasa , da Sauri ta d’auke nata idanuwan sabida wani irin abu daji ya shigeta, lokaci d’aya farin ciki ya kamata ganin sun had’a idanuwa dashi, cike da kwarkwasa ta ‘karaso inda yake mo motsawa beyi ba , kai tsaye kan kujerar da Yake ta nufa tare da zama daga gefensa, be ce mata komai ba , har ta rangwafo daniyar ta’basa , bata Ankara ba sai saukar gigitaccen marin da yasaka kunnuwanta toshe wa lokaci guda , ga wani jiri jiri da ya soma d’i barta bashiri ta saki wani gigitaccen ihu Sabida azabar marin da taji, bata gama jin zafin marin ba ta sake jin saukar wani lafiyayyen marin dama da hagu , a wannan karan ihun da tayi saida mahma da dada sukaji, da sauri suka fito alokacin da ya ‘kara dagewa ya tsinka mata mari, d’an kwalin kanta ya dam’ka da karfi dayasa attachment dinta Fito wa , wani irin ball king yayi da ita , mahma da ya fara bata tsoro da sauri tazo zata ri’keshi yanda yake a zuciyen nan bai san lokacin da ya hankad’ata ba itama , a rude dada ta la’be bayan kujera cikin tashin hankali ta fara danna wayar ta da’kyar ta lalubo number abeey sabida rud’ewa, lokacin yana falonsa shi da ummey, da sauri suka nufi part d’in dada , lokacin da king ya ‘kara saukewa amrah kyakkyawan marin da se da hannunsa ya Fito a fuskarta, cikin ‘bacin rai da kausash shiyar murya dake firgita mutum ya daka mata tsawa “ minti biyar na baki daki bar gidan nan, wallahi ko me kama da ke na ‘kara gani a cikin gidan nan , sai dai uwarki ta sake Haifo wata, Tashi kiban waje “ cikin azaba da fitar hayyaci amrah ta mike da kyar ga hawaye da majina dasuka ‘bata mata fuska, ko bin takan jakarta batayi ba ta arta a guje ko tunanin inda zataje batayi , cikin tashin hankali ta fita daga cikin gidan tayi tafiya me dogon zango rai a bace ta d’auko coccine me tafawa zuga, tun tana tuni har ta soma ganin biyu biyu amma bata hakura ba , ta cigaba da shaye shayenta tana tu’ki , bata Ankara ba wata mota tazo ta bangajeta, sai motar tata ta soma kifawa kanta ya bugu Sabida abun shaye shayen da ta Shaka me ‘karfi d’aya sata yin accident d’in.

***** Abeeey na zuwa falon dada rai a ‘bace ya wanke fuskar king da mari, ummey ba hatta dada da mahma saida sukayi suman tsaye shima king a zuciye ya d’ago fuskarsa ya kana kallan abeey “ Ni ? Mari?” Shima sai alokacin abeey ya kula da abunda yayi, amma be nuna ba sai ma had’e fuskarsa da yayi , cikin sama sama da murya ya furta “ Ina iliminka yake da zaka saka hannu ka mari mace? Akan Wana dalili zakace karta kuskura ta ‘kara dawowa cikin gidan nan, kar ka manta wannan gidan gidanane da kudina na Gina sa , baka da hurumin da zakace kar Wanda yafita “, murmushi king ya saki da ya bawa kowa mamaki, “ really? Gidan ka ko? Toh kasani zan bar maka gidan naka inyaso ko wa kake so sai ya shiga “, zamewa ummey tayi a kasa ta kasa cewa komai, mahma ce tayi saurin shan gabansa ganin yana kokarin tafiya hankali a tashe “ No son , please ka kwantar da hankalin ka , let’s talk”, gabaki d’aya idanuwansa ya rufe ransa yayi mugun baci, cikin murmushi da bekai har zuciya ba ya furta “ why ? Me zan zauna nayi? I lost my beloved brother ? I lost my wife ? My baby ? And mahaifina yana fad’a mun gidan sane , to ki fad’a masa zan bar masa gida, long time ago na rasa farin cikine ? Menene yayi saura?nothing”, yana kai zancensa ya soma tafiya , mahma zata dakatar dashi abeey shima cikin daka tsawa yace ya rabu dashi ya tafi, tashin hankalin da ba ‘a sa masa date , sai a lokacin dada da tayi suman tsaye ta saka sallallami , ganin king yanar part d’in, cikin kuka ta furta “ yanxu zayyadu baka da imani? Duk halin da yaran nan yake cike bazama lalla’basa ba shine zaka kore sa ? Toh wallahi bari na fad’a maka , idan har tahanuni na yabar gidan toh Nima na barshi kenan “, da mugun shock abeey ya kalli dada da ranta ya baci itama cikin daka tsawa tace wa mahma ta d’auko mata mayafinta , dole mahma ta d’auko ganin yadda ran dada ya baci, Allah sarki ummey abun tausayi ta kasa cewa komai sai binsu da kallo da take . Kafun Abeey yasa a dakatar da king har ya fice daga gidan a zuciye, hakuri ya fara bawa dada da tace itama tafiya zatayi, da ‘kyar suka samu suka shawo kan dada har da ummey dake bata hakuri, akan cewa ran sane ya ‘baci Amma zai dawo insha Allah.

Gabaki d’aya a cikin gidan babu Wanda y samu labarin futar king har Ammey data ci alwashin ganin bayansa a yau, har dare kuma king ne dawo ba hakan ne yasa kowa yaji abunda ya faru, hatta Ammey sai a lokacin ta Samu labari take a Wajan wani irin zazzafan zazzabi ya kamata da ko motsi bata iyayi Sabida bakinciki da yake kokarin kashe ta .

***** king kuwa rai a mugun bace ya bar gidan cikin mugun speed ko zaki be d’aukaba, kai tsaye airport ya nufa cikin jirginsa , ba ‘bata lokaci jirginsa ya Dashi zuwa America.

AMRAH

Da kar aka samu wasu suka kira police station Sabida hatsarin da ya faru , suma suna zuwa aka dauki amrah sai asibiti, likitocin ne suka bukaci ganawa da yan uwan Amrahn amma aka sanar musu basu san kowa nata bai wayarta da ita mata lallace , Take a wajan likitoci suka tabbatar musu da matsalar kwakwalwa da amrah ta samu sabida mugayen kwayoyin da take ta ammali dasu .

Har washe gari babu king babu alamarsa sai a lokacin hankalin abeey ya kara tashi, d’aya daga cikin masu kula da jirginsu ya kira , abakinsa yaji labarin tashin jirgin king , kuma babu Wanda yasan wata kasa ya tafi, take a Wajan shima Abeeey ya yanke jiki ya fad’i.
Sau da yayi 2 days yana jinya , tun suna sa ran dawowar king harkowa yashiga damuwa , lokacin da khaleed ya kira ilham , kuka ta fashe masa dashi cikin tashin hankali ya tanbayeta me yafaru gabaki d’aya ta kwashe ta fad’a masa da ‘kyar ya kwantar mata da hankali akan cewa zai ne mosa. Babu inda khaleeed be duba ba da binciken da yasa ayi masa ko akwai Wanda yaga king amma kowa ce masa yake ya dad’e basa king a cikin idanunsa ba .
Kowa da abunda yake sakawa cikin zuciyarsa ummey Sosai ta shiga cikin damuwa , samreen ce kawai me kwantar musu da hankali dukda natan ma a tashe yake . Ammeey tun tana irga kwanaki ko zai zawo har sati d’aya ya zago hakan yasa har ciwo sai datayi kowa ya d’auka sabida barin king gida amma tsantsan tashin hankali ne ya kwantar da ita .

Saida amrah tayi 2weeks a hospital kafun mamanta ta samu labarin hatsarin da tayi cikin tashin hankali da doctor yace dole sai ankai amrah asibitin mahaukata sabida anan za afi kulawa da ita , ba ydda mommynta ta iya dole haka ta hakura aka kai amrah asibitin mahaukata, suma lokacin da familyn NAHYAN suka samu labari gabaki d’aya sai da Suka je dubata banda Ammeey da ynxu ta zama shiru shiru abun duniya ya dameta.

Haka rayuwa ta cigaba da kansancewa cikin familyn , kusan kullum sai khaleed ya kira ilham , tun yana boye mata feelings dinsa har ya fito ya furta yana santa. Sosai suke zuba soyayyarsu wani lokaci har hira suke da zahra idan ya kirata har maganar taje kunnan dadi, sosai kuwa sukai farinciki da hakan

Watanni sun cigaba da shud’ewa har lokacin king be dawo gida ba , sai 5 month suka san yana America dukda kome suke ciki yana sane amma ya sharesu, ba yadda ba ayi dashi ya dawo ba Amma yaki , a cikin wannan lokacin ne Abeey yasan da soyayyarsu ilham shima sukai hakan yayi masa dadi.

??????

4 YEARS LATER

 

????GIDAN AUNTY ????

07041879581
Mss Lee ??

No comments