Breaking News

Gidan Uncle 72

Duk da faduwar da gabanta yakeyi hakanan ta qwaqulo murmushin qarfafa gwiwa tace dashi “zaka dawo ka samemu cikin amincin Allah” yayi murmushi tare da kissing din bakinta ya fita da sauri suka dauki hanyar Adamawa.



Ta jima a tsaye a gurin daya tafi ya barta tana jera masa addu’ar dawowa lfy kafin ta koma cikin gdan lkcn twins dinta sun tashi dake tanada meyi mata raino ta basu sukasha ta miqa Mata su ita kuma ta kwanta har yanzu ciwon jikin haihuwar bai saketa ba sannan D.S ya kuma tara mata gajiya da D.S da Hameed batasan waye yafi wani jaraba ba sauqinta daya shi baya dadewa kuma penis dinsa batada girman ta Hameed amma jiya ta fada duk da bai shigeta ba saida yasan yanda yayi ya samu gamsuwa da ita sosai.

 

Wajen qarfe daya taji wayarta tana ring ta shiga dakin da sauri ta daga ta kara a kunnenta tace “Allah ya taimaki mijina badai har kunje Yola ba naga tfyr da nisa sosai” ajiyar zuciya taji anyi gabanta ya yanke ya sake faduwa kafin tayi mgn aka katseta da cewa “matarsa ce ke?” Cikin in…Ina da tashin hankali tace “a…eh ni… Ina matarsa ce” me mgnr ya kuma cewa “sun samu hatsari ne a hanyarsu ta zuwa Adamawa amma yanzu haka suna asibitin qashi na dala shine yace a kiraki a fada miki” wani salati ta saki tace “way… wayyoh Allah… Ni Umaimatu amma dai bai mutu ba ko?”

 

Bata iya jiran amsar dazai bataba ta kashe wayar cikin tashin hankali ta durqushe a gurin qirjinta yana tsananta bugu jikinta yana wata irin rawa daqyar ta iya sake daukar wayarta ta kira Daddy tana kuka tana cewa “Daddy Abu Nawwas Daddy karya mutu don Allah ya barni ka hanashi mutuwa Daddy…” Saurin katseta yayi da cewa “ya salam waye ya fada miki Umaimatu bafa shi bane qaninsa ne” Allah sarki baiwar Allah sai kuwa ta sauke ajiyar zuciya tace “Allah na gde maka daba mijina bane” hawaye Daddy ya share cikin rawar murya yace “ki… Kiyi hqr haka Allah ya tsara miki ga Hajiya nan zuwa da yayarku Zahrah zasu tayaki zama kafin yaji sauqi a dawo dashi kada kice zaki fita daga gdan nan” yana fadin haka ya kashe wayar bata samu damar yin tunanin komai ba taji shigowar motoci gdan aikuwa batasan sanda ta zabura ta miqe tayi waje a guje ba ambulance tagani da qananun motoci uku tayi wajen ta tsaya tana rarraba idanu kamar mahaukaciya zuciyarta takasa tuna komai Daddy da Abba mahaifin Sulaiman taga sun fito sai wata motar Dawood ne yayan Sulaiman da Nazir qaninsa dayar kuma Hajiya Sa’adatu ce da qannansa mata biyu sai ma’aikatan asibitin da suka fito suka bude ambulance din suka janyo wani dogon abu da mutum kwance akai jini sai diga yake ta qasan gadon daukar gawar.

 

Daddy yana qoqarin riqeta amma ina da tayi wata alkafura ta dira gabansu kafin su ankara ta janye yadin da aka lullubeshi ta matsa ta qara kallon fuskarsa da gaske ba gizo ba Sulaiman ne kwance babu numfashi a jikinsa fuskarsa wasai da murmushin sa na rahama ta dafe qirjinta tare da furta Innanillahi wa innah ilaihirraji’un tayi baya luuuuuu ta zube a qasa itama qanwar gawa da sauri Daddy da Hajiya sukayo kanta aka dauketa itama aka shiga da ita ciki aka kwantar da ita a gado babu irin ruwan da basu yayyafa Mata ba amma taqi dawowa hayyacinta hakanan aka kimtsa Sulaiman aka daukeshi aka kaishi gdansa na gsky zuciyoyi na kukan rashin managarcin mutum salihin bawa wanda bashi da tamka Hajiya Sa’adatu fadi takeyi.

 

“Wlh babana da nasan mutuwa zakayi da bazan takura maka kaje gaisuwar nan ba saida ka nunamin bakason tfyr na takura maka dake kaidin dane me biyayya haka ka tafi yanzu ka mutu babana ka mutu kabar matarka abar qaunarka ka mutu kabar yayanka masu kwanaki goma sha daya a duniya ka mutu ka barni kabar yan’uwanka kabar abokanka kabar kowa babana wayyoni kaina wayyoh Umaimatu dole ki suma kinyi rashi Umaimatu wannan mutuwa takice ke akayiwa mutuwa kin rasa miji me sonki da qaunarki kin rasa miji me tausayinki dason farin cikinki Umaimatu Allah ya mayar miki da alkhairi Umaimatu na rasaki yanzu kenan na rasa sukura ta qwarai wadda ta ginamin dana da tsarkakkakiyar soyayyah Allah na gde maka da baka dauki rayuwar Sulaiman ba saida ka cika masa burinsa na ganin yayansa”

 

Bayan ankai Sulaiman makwancinsa aka dauki Umaimah aka tafi da ita asibiti tashin hankalin dasu Daddy basu taba shiga wannan karon shi suka shiga ba akan Umaimah yau shi suka shiga Umaimah ma da ciwon zuciya wannan wacce irin jarabta ce suke fuskanta ne.
Bata samu kanta ba saida tayi kwanaki bakwai saboda kumburar da zuciyarta tayi twins kuwa sai madara ake basu bayan ta dawo hayyacinta mutuwar mijin nata ta dawo mata sabuwa tayi kuka kamar ranta zai fita tanajin dama ita ta mutu ta huta daqyar Hajiya ta shawo kanta da dadadan kalamai da misalai kwatankwacin nata da kuma irin nasarorin da zata iya riska a rayuwarta da wadannan kalaman Hajiya da Daddy sukayita kwantar mata da hankali amma duk sanda ta kalli Nawwas da Nawwarah sai tayi kuka saboda tunawa da kalmarsa ta qarshe yayana amanane a gareki inasonki Umaimah” wannan dalilin taci alwashin zata tsaya ta riqe masa amanar yayansa koda kuwa zata mutu babu aure ita aurenma ya fita a ranta tama hqr dashi gara ta zauna tayi rayuwarta ita kadai tunda bai karbeta ba.

 

Haka su Hajiya suka tafi da ita gda aka gyara mata dakinta aka zuba mata komai sabo duk wani abu da zai cire mata kewa saida suka sanya mata ga mai rainon twins dinta ita dakinta guda sannan ga Maliha da Shuraif da suke dauke mata kewa lkcn Allah yasa cikin hutu suke koda aka koma mkrntar ita bata komaba saboda abin na gdane ita daluba ce shi kuma marigayi D.S malami ne da sukeji dashi a Skyline University sunji mutuwarsa sosai hukumar makarantar tayi rawar gani sosai wajen ganin sun yiwa iyalan D.S wani abu aikuwa sunji dadi koda akazo rabon gado da Abba da Hajiya Sa’adatu cewa sukayi sun yafewa Umaimah da yayanta komai.

 

Rayuwar haka taci gaba da tafiya bason raiba sai bayan wata uku da rasuwar D.S sannan Daddy ya sanar da Hameed ya tausayawa twins tare da jin ninkin qaunarsu a zuciyarsa yasan rabonsu shine ya rabashi da mahaifiyarsu sannan rabonsa dabai qare a jikinta ba shine ya kashe mahaifinsu” da wannan tunanin ya biyo jirgi ya dira a 9ja batare daya fadawa kowa ba suna zaune a parlour da hijjab dinta na masu takaba ya shigo da sallamarsa Maliha da Shuraif sukayi tsalle suka rungumeshi Twince kuwa da suke koyon zama sai bangale masa baki sukeyi murmushi yayi me hade da kwallah yana tuna irin wulaqancin daya rinqa yiwa mahaifinsu lkcn da yana neman auren Umaimah ya sunkuya ya daukesu ya rungumesu a jikinsa wani kuka me qarfi ya kwace masa yayi saurin tashi daga gurin ya shige dakinsa da yaran ko gaisawa da Hajiya bai iya yi ba balle Umaimah tasaran zaiyi mata ta’aziyyar mijinta, itama batasan sanda mikin mutuwar D.S ya dawo Mata sabo…….

 

 

 

*UMMUH HAIRAN CE…✍*
[2/3, 11:53 AM] UMMUH HAIRAN CE…✍: *_GU_*

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

No comments