Breaking News

Hariji Book 2 Page 41-42

41&42

Ummy kam tsintar kanta tayi cikin tsananin damuwa,sai kurum taji gabanta ya tsinke ya fadi,da batasan dalili ba,komawa kan gado tayi ta kwanta,ta daura hannunta akai ta karanto qafa uku na *Laƙad ja akum* ,sai


ƙafa sha ɗaya na *ƙulhuwallahu* Ta tofe jikinta ,ta kudundune kamar mejin barci.
Cikin mintocin da basu wuce biyu ba,kawai ta hango wani kyakyawar balarabe ,yina nufota cikin 6acin rai,shi zaki aura bayan kin hanani auran za6ina?
“Karka manta da karin maganar hausawa, *A bari ya huce…* “Aikuwa baki isa ba saidai duk kowa ya rasa…”
A furgice ta miqe wani gumi na tsatstsafo mata,ta kasa gane waishin barci takeyi ko a farke take ganinsa ,kuma wayeshi wai? ta yaya nayi addu’oin da nasan innayi qaryar mugu ya iya tunkarata,sai kuma inyi wannan ya bayyana mun?
‘daukar abun tayi a kawai mafarkine ,sai tayi tofi a hannunta na hagu sau uku ta juya kwanciyarta tayi adduar barci ta koma barcinta,ba ita ta farka ba sai bayan la’asar lokacin anci nemanta an gode,angwaye sunzo har sun wuce,ashe tana daki tana barci
Haka biki ya qarasa kadahan kadahan,biki salam bako event sai walima da malamansu na islamyya suka zo sukayi masu nasiha,da hajara ta tada qayar baya sai cewa tayi “Anty hajjo zaku iya yin abunku ,amma ni bazan yiba albarkan auren nike nema,kuma ina fatan ko in rufesa ko ya rufeni to bazanso shedan in gayyatoshi gidana ba ,ta hanyar gayyato jikokinsa

Tsaki hajjo tayi ,kaawai tana fita ta kira Dj,t.k ,qarfe shida ya ajiye kayan aikinsa a filin kofar gidansu,sai bayan magriba suka kunna duma,
Hajjo da qawayenta dake gefe sun mammanne da samarinsu suna qwaqular juna,fitowa sarari sukayi gamida shigowa filin suka hau dj da fada,haba wannan ai yawane,kusa mana waqar da zata motso mu mu shiga fili kunqi,sai wasu shirme kuke sawa,,,wai bakuda irin su *Hajiya gwalene*? ”
hakuri ya basu,sannan ya fara lalubo waqoqin batsan a cikin laptop dinsa ,dake cikin wasu windows

Aikuwa waqar bujen rakiya ya saka masu
da gudu suka shiga fili ,tana bude qafarta tana qasa qasa da duwawu qawayenta na tayata ,tana wani irin girguza tana jan wuyar rigarta qasa

Nonuwanta na tsalle ,aikuwa mazan layi da suka abubuwa bononza kutsowa filin sukayi suka kashe generatorn suka shiga sa6a en matan a kafad’a suna wucewa dasu dakunan su da gudu…

Ummi tayi allah wadai da wannan lbarin amma ya zatayi ,tunda hajjo ta ja mata ,amma an É—auke É—iyoyin jama’a ita da akan keken mazane an qyaleta ,sai zunduma ashar takeyi ,wai ta gane hannun wanda ya tumbular mata nono ,É—an bala ne,mijin maÆ™ociyarsu,kuma sai taci kaza kazansa…
sadiya matarsa koda taji ana shiga mutuncin mijinta ,a take ta daura É—amara da gyalenta ,ta hau surfa bala’i
“ke hajjo hawainiyarki ta kiyayi ramata,ya akayi kikasan hannun mijina har kikasan shine..?”
“ke dabba,sau nawa dan bala yina cina,tun kan a aureki muke tare da dan bala…yanzune na nuna masa gindina bai ciwuwa masa ,yike karime karime,ko a kwatanta maki yanda goran nasa yike ne?

da qyar aka rabasu ummi kam ,sai kuka take,wannan abun kunya dame yayi kama?
itakuwa uwale dama tuni alhaji mai wada yazo ya dauketa ,bayan ya kawo masu balangu maishi da katon uku na lemu,wai en biki da zasu kwana sa motsa baki,ya É—auketa suka wuce wani otel acan zasu kwana

“umma ,me yasa mijina yace sai bayan sati zaa tafi dani? Wallahi na qosa in tafi ,na koa…” kurum sai ta tsage da kuka

“To sannu isashiya ,ai dai maganin qarya hallara kwana nawa ya rage? ko kema nunamun zakiy ,ke din harija ce,kin qosa wa miji?,to suma en uwanki da suke bin maza lalura ne,tunda bazan jikasu in sha ba,amma bacin haka da sune da aurensu wa zai ji?

cuno baki tayi ta dauki hijabinta ta fara nafilolin bayan isha’i
a yayinda hajjo ita kuma ta fice kiran en sanda wai tunda sadiya ta zageta akan dan bala ,sai tasa an nemosa an bi mata ba’asin lagudar mata nono da yayi.

***
Nnenna tana kuka ta fito daga part dinta tayi sashen uwargdan da sauri. knocking takeyi kamar ta6a66iya,

Maid dinta ta bude kofar da gudu tayi upstairs tana qwalla kiranta.
Anty futo alhaji ya auro mana qanwar karuwai! Tantiran Æ´ar bariki!! Harija!!!

No comments