Breaking News

Hariji Book 2 Page 45-46

45&46

*Lamme use this medium in sharhi a comments naku,actually mutane da dama sun so ba Æ™uliya bane,ya auri ummi,buh assume Æ™addarar tace,finally ku biyoni gidan Æ™uliya‍♀️*

Tun da aka sanar dasu tsayuwar jirgi ,a


ka daura da shaida masu jirgi na jiransu su kalli dakin er uwarsu a maidasu kano ,batareda 6ata lokaci ba

Hajjo sune en gaba gaba da qawayenta,yayinda suka tsikara daurin ture kaga tsiya ,suka turo jelar daurin ta kunne suka ja tsawon matsatsen siket dinsu zuwa qasan duwawu,tun daga wargajejen get din da zai sadaka da katafaren sassan gidan suke rangada guda
“Ayyururi,yururi,yururi…Tako da qafar dama baki da basmalah,ummi É—iyar albarka
Itadai duqar da kai tayi ta kasa ko É—aga kanta wani irin shesheqa takeyi,ta kasa ma kukan zuwa wannan lokacin,ji take kamar an kawota gida mai daukeda taskokin azaba,wanda zai ajalinta!

Maimakon suga tsoffi en taryan amarya ,saidai sukaga masu aikin gidan dakayan abinci kula kula na kaji da drink,da lafiyayyen jolop mai yaji yaji ,yasha kayan hadi

Ai a take suka farma abincin nan da wawa,ba kishiyoyinta ba,harta en aikin tun yanzu sun gama rainasu ,vanda binsu da qasqantaccen kallo ba abunda sukeyi
“oh an kawo er qasqantattun gida” cewar wata baba mai kula da general kitchen na tsakar gidan
.
To er zanianyi shuka a idon makwarwa ,ashe zance ya fada kunnen uwale dake bayansu tana amsa wayar mai wada,a cewarta dakin ummi ba network ,wai sai daga varendar ,kaji wani tsatsuba ,ashe rabon za tajiyo tane
.
Tabaya ta dantso kwalar rigarta “ke maimaita abun da kikace don butsun uwarki!”
taqare tanahura hanci gamida watsa matsa daqwa daqwan idonta

Makyarkyata jikinta ya farayi “oh ni ‘yasu,wannan karon kuma iyalan daba aka kawo mana..allah ya ka’de datse datse in alhaji bayanan ,don in fada ne da tsiya to gidansa ta taras malama”
ta fada tana mata jan ido,amma a kirjinta karka tone ,saboda yanda yike dukan tara tara

Aikuwa batayi aune ba taji ta da6a mata naushi abaki ji kake turushhh! ,sai ga jini ya 6alle

Wani qara ta tsaga ,gamida neman dauki,aikuwa en aikin suka shigarwa baba,itama en uwanta suka furfuto
da fari lallashin uwale suka somayi “uwale kika sani ko dangin sane ,ki ja mata saki”
“Ba danginsa ba ko uwarsa ce ,taci kaza kazanta ”
“aikuwa badai baba ba”
“saiwa ,nace saiwa”ta hau tambayar wata tana nufarta ana riqeta.
“Kai ku barni in cicci bakinta,kai ni zan fada ki fada? ku cikani in hau ruwan cikinta”
fada yayi fada ,tun ana rarrashin uwale har suma en uwan suka tunzura ganin sun riqe uwale amma waincan na dura mata zagi
hargitsewa wajen yayi da dambe
ana fashe fashen gilas ,daqyar masu gadi suka raba,
Ummi banda kuka ba abunda takeyi ,musamman da ta fito taga yanda suka yiwa mutane jina jina

Gabansu taje tana son basu haquri,saiga Nnenna ,ta fito daga part dinta tana qwala kiran eli,mai aikinta,saye take cikin riga da wando na kayan sanyi mai leda ta gingima head phone tun daga saman kai har kunne,hakan zai tabbatar maka da duk bidirin da akeyi ba

Zaro ido tayi ganin en aikin sun kimu a inuwa duk an masu raga raga ,batasan sanda ta tsaga ihu ba
ta juya da gudu tana en qato da gora sun shigo masu gida ,a take ta fara dialling emergency call

Rushewa da kuka ummi ta sake yi,ta caka gwuiwarta a qasar floor din tana basu hakuri
“Kaico rayuwata”
“ke sharaf,robish,zauna ki zama gaula kishya ta taka ki,ba kiran emergency ba ta kira gindin bindiga,wainan tsinannun kishiyoyi za ayi a gidan nan,ummi shawara daya zan baki ki zage ,ki zama cikakkiyar Æ´ar ta’adda,kowa ta hareki da rigima ki aikata mata,er muciyar nan ki zaman tanazarsa a bayan qyaure kafin in aiko maki da gora da addah. ”
“Hhhh kice gida zai zama kwata,kaca ka ca kenan,wallahi har na hango wancan mai kama da zabiyar tasha yanka.. ”
“Ashsha allah ya kyauta,ummi ya da haka kuma?” Quliya ya katse su ,wanda shigowarsa kenan ,bayan ya samu labarin tashin hankalin gidansa ya zo a sukwane

Sai a wannan karon uwargidan ta keto ,ta sashenta,batayi wata wata ba,ta faɗa ta bayan ƙuliyar ta rungumesa tana sauke wawan ajiyar zuciya

“Alhajina mun auna arxiki,yau munga kuturun tashin hankali,alhaji da baa kawo dauki da wuri ba da kaga gawawwaki,gashi sunja duk yan uwana sun ware ta qofan baya,ni kuwa saura qiris in fadawa titin street din nan ,ta windon upstairs dina,quliya umurninka nike jira zan kori duk ma’aikatan gidan nan,saboda na lura an zugesu ,kar su takurawa amaryarmu! ”

taqare maganarta tana wani ruqunqumesa tana shinshinar wuyarsa

Sakin baki da hanci sukayi cikin tsananin mamaki,karuwanci ido biyu,lallai gidan en boko,itakuma kalar naki salon kenan makira! lallai da nice ummi sai na gallazeku,wanda zaisa ku gudu dake da waccan jaujau din kun bar ladanku” cewar hajjo ,tana farfar da ido tana taunan cingam.
Quliya mamakne ya ishesa..
Ashe abunda ake fadamun akan su haka ne?”
A nutse ya 6n6are ta a jikinsa ,sannan ya bude brief case dinsa ya basu daurin 1k guda uku
“Ahuta gajiya,jirgi na jiranku,uwargidata ke kuma duk hukuncin da kika yanke akan gidanki,to yayi,abunda kawai nikeso,ki kamo mun hannun qanwarki ki kawota sashena,kuma kuzo da Nnenna,daga nan bai sake magana ba ,ko ya saurari gidiyarsu ba ,ya wucesu,yina addu’a allah yasa su koma gida lafiya batareda sun kassara ko sun raunata wani ba again”
Yina bada baya ,ta waigo ta kallesu ta watsar ,sannan taje ta yaye fuskar ummi

“Hmmm en mata zaki iya kishi dani?,barka da zuwa gidana,saidai zan gargadeki ki jawa en uwanki kunne,wallahi zasu ja maki dana sani,so su tattara rashin mutuncinsu sukai kano zai musu amfani kafin yanzun nan insakar masu police dog suyi mun taya taya da naman jiki”

fuuuu ta wuce ,tana jiyosu suna danna ashariya,saidai natsuwa sukayi da sukaga wani ware house na karnuka lafta lafta jikinsu buzu buzu gwanin ban tsoro
gani suke kamar zasu cinye wayan ne ,su biyosu,aikuwa a take cikin tsoffin cikinsu ya karta,da sauri suka firfita zuwa wajen get ,sukayi parking kamar en gudun hijira..

No comments