Breaking News

Hariji Book 3 Page 75-76

75&76
*Alheri writers asso.*

Ummi kam,gajiya da tunane tunanin ta ,tayi ta fara dan gyangyad’awa ,aikuwa karaf ba zato ba tsammani taji hannu dan bawanka akan cikinta ,zillo tayi ta gwale duk idon ta ,ta zuba masa su cikin alamar tsoratarwa


Shegen sama,maimakon ya tsorata kurum sai ya hau yi mata murmushi yina gyada mata Kai ,sannan yina yunqurin Kai hannunsa ,saman tudun qirjinta

Aikuwa cikin zafin nama ta fincike hannunsa tayi jifa dashi gefe sannan,kuma batayi wata wata ba ta kifesa da mari,wanda saida yaga gilmawar wasu tartsatsi ✨

A gigice ya dafe wajen kafin yace “Ni kika mara??”

“Qaramin dan Tasha ,ashe kanajin Hausa ? Da ka isheni da larabci,wannan kadanma nayi maka nagaba in nayi maka saina sauya maka kamanninka,don harda mahangur6a zan hada maka”

Lumlumshe idonsa ya kamayi ,yanda take magana zafi zafi ba qaramar qara masa shauqinta yikeyi ba,komai nata abun burgewa ne,maganarta komunta sanyi sanyi
Sosai baiso ta daina tsiyan ba,don haka a jikinsa yaji inama ya qara takalota,koda zata qara kwasa masa wata Marin ,indai zatayi magana yaji sanyi a ransa?

“kina da kyau”

Ya fada cikin wani murya mai tarwatsa qwalwar en mata

“Kai kanada lafiya?” Ta fada tana zaro masa Ido

Dariya ya kwashe dashi harda tafa hannu “yes Na fada maki abunda ke raina ne,and maganar gaskiya I’ve much sha’awa on you”

Daura hannu aka tayi sannan tace Na shiga uku,na hadu da kwarto” duk zaton ta a sirrance tayi maganar ashe a bayyana ne.

“Ah Kar kiyi mun sharri ,nace miki bude mun tsuliyarki in tsotsa? Ko Na baki gindina nace kisha,daga nace kinada kyau?”

Wawwaige waige ta kamayi ko’ina a lullu6e da labule bamai iya ganinsu ,ga qaran kidin larabawa da ya cika motar Na tambarin gidan sarautar

“A’uzubillahi minash shaidanir rajim, Allah ya la’anci shedanin da ya hauro kanka yikeso ya sanya maka kallon lalata a matsayina Na matan dadynka”

“Haba wai ya kuke haka ne mata,Ana fa d’aukan haqqin oga shaid’an ,komai in akayi ace shaidan,no! Kawai maganar feelings ne,in kinyarda muyi abinmu cikin sirri zan tanajeki da kyakyawar masauki ,tamkar yanda kike me kyau”

Ca6e baki tayi batareda ta tamka sa ba ,lallai d ake cewa balaraben mutum yafi kowa shagala ashe da gaske ne

Hannunta ya kama ya fara murzawa a hankali

“Babae say something” a hassale ta dad’a d’aga hannu zata wankesa da mari,kurum sai sukaji tsayuwar motar su ,wancakali tayi da hannu wani hawaye Na cika mata kwamin Ido

Shikuwa da sauri ya dafe Kai alamar baiso aka kawo ba

Amma Allah ya kaimu dare zan bibiyi makwancinki,tabbas dole in dandani zumarki.

Qofarsa aka fara bude mai,saida ya gama zuba Mulki sannan ya fito ,tabbas sarauta ba qaryaa ba,a haka kamar Na Allah,amma a gefe guda tantiri ne
Cewar ummi da ta shiga rud’ani.

Itama wasu mata sukazo suka fiddo ta aka rankaya zuwa cikin tafkeken masarautar ,wanda duk dakiyar ummi er qauye ta Zama
“Shikuwa quliya me yake tsinta a Nigeria,da ya gwammace Zama a can da ya zauna a wannan gidan tattashin da tarin bayi da dukiya? Gabadaya matakalar qofar da zaikaika dakin sarauniya safiyya kuwa kwalliya akayi masa a dadda6e da zinare ,abun gwanin ban sheqi ,haka suka shiga anata lale da zuwansu har kowa ya zauna a mazauninsa ,quliya watsa idonsa yayi ya sauke akan ummi,aikuwa caraf idonsu ya sarqe,ta kuwa Galla masa harara
Matse gira yayi ,irin. Alamar tambaya lafiya dinnan
A maimakon tayi wani respond saita murguda masa baki.

Ai a fujajan yazo ya tashi Adnan dake kujeran daf da ita,ya zauna sannan ya rafka tagumi ya saka bakinsa cikin tafin hannunsa

“Zinariyata me nayi maki?”

Adnan ji yayi kamar ya shaqe quliya,don Allah ji wani son rai,gamu matasa masu jini a jika,muna buqata ku iyayenmu Ana rububida ku?…mtseww yayi tsaki a zahiri ya miqe

Hakan shi ya jawo attention din kowa Na wajen ,ciki harda quliya

“Son me ya faru ne kuma ? Banson wutan ciki?”

“Gajiya” ya bashi amsa gamida tsallake qafa yabar dakin da duk aka hadu za’aci abinci akuma tarbi su quliya ,tarba Na musamman.

D’an tsam yayi da rai kafin ya maze “zinariyata yadai ko gajiyar hanya ne?”

“Uhum kaina ke ciwo”

Gigice wa yayi nan take kamar wanda aka fada masa wani abun tsoro

Da sauri yakai hannunsa goshinta “ayyah ga zafi”

“Heyyy iynt ,ilal mustashfal aln” ya ya fito wata servant ,wai su wuce asibiti ynx

Tsam sophy ta taso tazo ta dafe kan ummi cikin kulawa “ma asa baha?”(what’s wrong with her?)

Kafin yayi magana tace “eyyah seems headache,sorry ladaina d’abib ,sa atiy huna bissur’a,l a takhaf”.

(Eyyah gayinan kamar ciwon kaine ma,bakomai ai muna da likita zai zo nan da sauri ,karka damu)

Ta kamo ummi suka miqe ta wuce da ita dakinta ,sosai quliya yaso a barsa da matarsa,amma Ina surukutan Hausa /Fulani ya shigesa bazai iya binsu dakin qanwarsa ba

A katafaren gadonta ta shimfideta ta rage mata kayan jikinsa,sannan ta kawo mata ruwa me sanyi da dan shayi me Zuma
Ta warware mata a.c
Da turanci tayi mata magana “ki Sha shayi kinji,sai kiyi wanka ,ki sa kaya matasa nauyi kafin likita yazo,allahu yashfik”(Allah ya baki lpy)

Gyada mata Kai kurum tayi don ba duk yaranta take jiba ,qalilan qalilan dai

A sanyaye ta kafa dan ficilin Kofin shayin na tangaram a bakinta,zuciyarta Na tuna mata Adnan da halayyarsa,mafarkanta dashi yina mata gizo ,ai unknowingly taji tashin ziciya

Da gudu ta dirka a gadon tana ware waren neman toilet

Zuwa tayi ta rungumeta

Me ya faru menene ?”

Ta kasa magana saboda aman da ya taho mata,da sauri ta rimtse bakinta tana mata isharan amai amai

Ai kafin sukai toilet ta fara kelaye amai ,kaf saida ta fidda madaran da Tasha a jirgi,haka take fidda numfashi sama sama tana kakari

Shafa mata baya ta shagayi bata damu da 6atata da tartsatsin aman da tayi ba

“Sannu matar yaya ,sannu kinji

Ruwa ta bata ta wanke baki ,sannan ta barta tayi wanka ,ta Kira hidimai suka gyara wajen ,nan danan ya dau qamshi kafin ma ummi ta fito wankan ,ai kwashe kayan ta da na sarauniya safiyya da ta 6ata, an bardasu gidan .wata sassauqar jallabiyya milk me jiki tattausa aka bata ta saka, ta fito da nufin ta kwanta,saidai kamshin turaren dakin Kansa tashuwar zuciya take ji

A take kanta ya buga “to meye haka daga zuwana qasan mutane zan qazantasu da laruran amai,wai ma me ya jawo min?

Falon ta ta fito da sauri ta bar bedroom din

Suna zaune da barorinta a gefenta tayi sauri ta taso ,ta kamo ta ta zo suka zauna a rungujejiyar 3 seater dinta da take ,tana Zama ta daura kanta akan cinyarta tana shafa kanta wani barci barci Na fizgarta me tsananin dad’i ,cikin abunda baifi 5 second ba kuwa barci ya sureta

Shigowar likita yasa quliya jin haqurinsa ya qare ,ganin shiru shiru basu fito ba ,yakuwa biyo bayan likitan

Yina hangen matarsa er d’agwas a cinyar qanwarsa ,tayi wani ru6u ru6u gwanin sha’awa ,tashin ta tayi ta hanyar dunga shafa mata kumatu tana kiran “kulthoom” a hankali ta bude Ido

Quliya yace “zinariyata ya jikinki”
Shiru tayi sannan tayi kwa6a kwa6a kamar zatayi kuka

“Ayyah yi haquri ga likita zai dubaki zakiji sauki ”

Kya6e fuska tayi cikin shagwa6a sannan ta gyada masa Kai alamar gamsuwa

Adnan dake dab da shigowa,dakatawa yayi yina kallon wannan abun ban haushin kurum da rufaffen Ido ya juya yabar wajen ba tareda sunga zuwarsa ba,zuciyarsa Na azalzalarsa da mugun sonta ,wanda ya kasa tantance menene ,shin sha’awa ce ko qaqa? Amma tabbas inajin tsananin kishin dady akan watannan er tsanan babyn…

No comments