Breaking News

In Bani 50


50……

_Antyna! People like you are rare a duniyan nan, thank you so much, and i dedicate this page to you, thank you ones again for taking care of me_

 

 

Shiryawa tayi tsaf cikin wani free gown na atampa red and black, color yay mata kyau sosai ajiki, batasa ko kwalli ba danji tayi gabaki daya tagaji da komi, fita tayi taje kitchen ta dauko broom tadawo ajiye broom din tayi akasa ta gyara gadon tsaf dabai wani baciba sanan tadau tsintsiyar tafara sharan dakin just to while away time dan dakin ba datti, baban zoben silver color dakenan kaman na azurfa data gani a tsakar dakin yasa ta tsugunna tana kallon zoben, daukan zobe tayi da hannu da sauri ta kalli zoben jin zoben da shegen nauyi a hannu kaman tadaga wani babban abu, hakan yasa tace “me Aadil yakeyi da wanan zoben mai nauyi haka” ajiye zoben tayi agaban madubi tana tunani dan bata taba ganin zobe a hannun Aadil ba, kodai bata lura da kyau bane, no babu zobe a hanun Aadil ko daya.

 

Share batun zoben tayi daga ranta tadau broom din tacigaba da sharan ta share ko ina na gidan ta turare gidan da turare sanan tadauko wayarta tazauna akan kujera tai yan danne danne ganin duk batajin dadin maganan Aadil sai zuwanmata yake arai yasa takoma bedroom ta dauro alwala tasa hijabi ta zauna tafara karatun Al’qurani har lokacin la’asar tayi ta ijiye tai salla tana idarwa ta daura karatun danko kadan bamatajin yunwa har magrib ta tashi ta shiga bayi ta dauro alwala, sallaman Mami dataji yasa tafita tana zura hijabi, murmushi Mami da idanunta sukai wani iri tayi tace “jekiyi sallan ki mun shigo muduba kine dama” gyadakai tayi taredayin murmushi tajuya takoma ciki, Big Mum tace “yarinyar badai hakuri ba, ga dauriya dudda abin na damunta she’s trying to hide it, muje muyi sallan muma” bude kofa sukayi suka fita daga dakin.
Sallan magrib tayi tacigaba da karatun har lokacin isha’i……

 

 

Wuraren takwas saura Abie yasake dawowa dakin ya kalli Aadil da tun safe yake kuka yaki shan daidai da ruwa agidan Abie hankalinshi duk yabi yatashi dan yasan yanajin yunwa kuma Aadil baison yunwa ko kadan nan da nan zakaga yanama kuka dazaran yaji yunwa, zama yayi gefenshi rike da bowl of fresh sliced fruits kaman zaiyi kuka yace “tashi to kasha saina kaika wurin Hamidan, idan bakasha ba bazan kaikaba” kallon Abie yayi da sauri yana tashi zaune yace “My Hamida?” gyadamai kai Abie yayi yay murmushi yace “yes but only if u have this fruits, you haven’t eaten since when we get here” fizge bowl din yayi ya debo fruits din da fork yakai baki yasha yana murmushin kuka Abie na binshi da kallo yanajin son dannashi na ratsashi, sau uku yasha yamika ma Abie yace “am okay” tsabagen yanda ya kosa yaga Hamidan, kallon fruits din Abie yayi dudda baiwani ci wani abuba but at least is something, yasashi yasa wani abu a cikinshi tundama dabaran tai aiki haka zai dingamai kullum yanamai wayau yanasashi yaci abinci, kayan dayakawo mai ya nunamai yace “tashi to kasa mutafi” jumping yayi from bed yanajin wani irin mugun ciwon kai yasaka kayan yay tsalle tareda murmushi yace “let’s go to My Hamida Abie” tashi Abie yayi yakama hanunshi suka fice daga dakin har zuwa compound yabude mota yasashi ciki sanan ya shiga gaba yaja motar suka fita daga gidan, tafiyan wurin minti talatin sukayi yay parking agaban gidan gonanshi dake wanan kyauyen, parking yayi yafito yabudema Aadil din fitowa Aadil yayi yana kallon gidan yace “My Hamida is here Abie?” yes Abie yace yakama hanunshi sukai ciki yaciro key yabude kofan ya shiga sitting room din dayay kura sosai kafin yayi hanyar dakin tsafinshi dashi, key yaciro yabude kofan yana rike da hanun Aadil suka shiga dakin dayay mugun duhu Abie yamaida kofan yarufe, rikeshi gam Aadil yayi yace “where’s My Hamidah Abie this place da duhu” sakata Abie yasaka nasama dana kasa yace “don’t worry u will see her now” yana rike da hanunshi yakarasa a duhun nan ya tsaya inda uniform dinshi suke yasaki hanun Aadil dake shirin yin kuka ya cire kayan jikinshi yasaka jan rigan tsaf sanan yana rike da hanun Aadil ya laluba yaciro ashana yay gaban dakin ya tsugunna ya kunna candles din wajen dake tare da gumaka da sunkai guda goma haske ya gauraye dakin, ihu Aadil yayi sosai ya rirrike Abie ganin mutane da sunkai guda goma shabiyar a tsaitsaye a dakin suna snye da jajayen kaya saikuma wani dake zaune gaban dakin fuskarshi kaman na biri idanunshi jajir dakaman jan wuta, runtse ido Aadil yayi gam ya rirrike Abie yace “Abie this is not My Hamida this is ojuju calaba, this is gorilla, am scared Abie” wani irin tsawa Ozo ya dakama Abie tareda buga karfen hanunshi akasa yace “kayi latti Tursoso sanan wayace kataho mana da wanan meeting iye” da sauri Abie yasa guwiwanshi akasa hakan yasa Aadil binshi, jikinshi narawa sosai yace “Great One Ozo tuba nake, tuba nake, inada dalilin kawoshi amma saika bani izini zan fadi” rike Abie Aadil yayi gam kanshi na juyawa idanunshi arufe, cikin murya mai kama data jarirai Ozo yace “fadi” ajiyan zuciya Abie yasauke yana addu’a Allah ya daurashi akan Ozo wanan karan kaman koda yaushe, ahankali cikin natsuwa yace “OZO na, Ozo mu, Ozo na kowa mai bamu kudade, Ozo mai bamu fame, Ozo the great one, zuciyata ta gaza natsuwa, zuciyata na cike da tsoron azaban ka dakuma hukuncinka, banzo koda da wasa nakara karyama doka ba dan banmanta abinda kaceba inhar na kara saba doka ban kiyaye sharadi ba bloodline must go dole saikunsha jini, saisa na shiryoshi takanas takano Ozo the great nazoma dashi, sonake ka shafemai gaba, sonake ka sideta ka shafeta tass ta yanda ko sha’awa bazaimaji ba balle harta mike yay kokarin saduwan, Ozo gashinan so nake ka shafeta dan kamashi nayi yana shirin saduwa da makirar yarinyar da aka auramai, Ozo inada matsalan jaraba kuma ina kyautata zaton yagado ni dan Aadil baisan komiba amma yana kebewa da mace gabanshi tafara mikewa, Ozo ka taimakamin nasan am asking too much nasan kuma you’ve always been granting my requests, Ozo kamin afuwa kataimaka min ka shafemin gabanshi ko hankalina ya kwanta nasan koshekara miliyan zaiyi da ita bazai taba karya dokaba dan baida gaban dazaiyi saduwan dashi, shikenan barata Ozo the the great” shiru dakin akayi kaman ba’ayi hallita awurin ba members duk kansu akasa ana jira aji abinda OZo zaiyi dan sosai sukejin haushin Abie, su Ozo baya daga musu kafa haka basu isa su karya dokaba sai Tursoso, babu dokan da Tursoso bai karyaba, duk ansha jinin yaransu na fari amma banda na Tursoso, wani irin tsawa Ozo yayi da saida dakin ya girgiza. “Tursoso!” zabura Abie yayi yamike tsaye Aadil kuma yasaki fitsari ya kankame Abie yana kuka. “Abie my Hamida” tureshi Abie yayi yana kallon Ozo, cikin fushi Ozo yace “Tursoso kan wanan yaron ne kaketa sabamin doka tun randa ka haifeshi ko, toyau zan zuke jininshi agabanka yamutu” ihu Abie yayi ya rungume Aadil tareda sakeyin kneeling cikin wani irin masifaffen tashin hankali yace “Ozo kayakuri natuba, natuba karka kashemin shi, to naji, naji basai ka shafe gaban nashiba, koda kashe yarinyar zanyi dandai nahanashi saduwa da ita zanyi Ozo the great kagafarceni karka tabamini Aadil dina Ozo” yanda yahaukace yana rokan Ozo yasa Ozo ya gyara zama yanamai wani irin kallon tsana yace “ina zobenka Tursoso?” da sauri Abie ya kalli yatsunshi ganin babu zoben dakemai aman kudi yasa yarude tsoro yamugun kamashi yace “Ozo, Ozo” yama rasa maizaice dan baisan inda ya jefar da zoben ba baitaba cire zoben daga yatsunshi ba koda da wasa cikin inda inda yace “Ozo hala nabarshi abayi danaje wanka ne amin afuwa” wani kallo Ozo yasake mai kafin cikin kakkausar murya yakira sunanshi azafafe. “Tursoso!” da sauri Abie yace “na’am Ozo da great one” “yarinyar nan tadamemu, tahanamu sukuni, tun jiya da daddare take konamu, kaje kafitar da ita daga gidan nan kanajina, kafitar da ita daga gidan nan da daddaren nan, i repeat kafitar da ita daga gidan nan inka sabamin zaka hadu da fushina dabaka taba ganin irinshi ba” cikin tsoro da fargaba Abie yace “to Ozo” wani jini Ozo ya mikomai a kwarya yace “ga sacrifice dinka jinin first born da ifufuwa” tashi yayi ya duka gaban Ozo ya karbi kwaryan yakafa abaki ya shanye jinin tass sanan ya ijiye kwaryan gaban wani gunki, Ozo yace “dau dandanka kuwuce kutafi kufitar da yarinyar nan daga gidan nan now, now, nowwwwww” yana fadin haka Ozo yabace daga dakin sauran yan dakinma haka, uniform din Abie ya chanza ya kashe candles din sanan yabude kofan yafita baima tsaya kulle kofan ba yanda Ozo yamai warning haka yasan abinda Hamidan tayi babba ne yafita da sauri yana rikeda Aadil da har lokacin idanunshi ke akulle mota yabude yasashi bude ido yayi sanan yasaki kuka sosai Abie baibi taka shi ba dan tashin hankalin dayake ciki yafi karfinshi ya shiga gaban mota yatada motar yaja dawani irin fitinannen gudu yabar wajen……..

 

 

Sai bayan ta idar da isha sanan tai shafa’i da wuturi ta tashi daga kan dadduma ta linke ta tube kayan jikinta ta linkesu dan basuyi dattiba ta maida wardrobe taciro rigan baccin dazata saka ta ijiye akan gadon tana tunanin Aadil, bathroom tabude ta shiga ahankali tana share kwallan daya zubomata, brush tafarayi sanan taja shower cap tasaka sanan tafara wanka da ruwan zafi sosau, tadan dade tana wankan sanan tafito tadau towel pink tadaura daya kusan kaimata guwiwa ta daura ta zare shower cap din daga kanta ta ijiye tana kallon fuskarta, share hawayen dasuka zubomata tayi danko kadan jitakeyi bataso tafita daga bathroom din batare dataga Aadil ba azaune kan gado yana washe mata baki ba, lallasan kanta tayi kafin tajuya tana tafiya kaman wacce kwai yafashewa aciki ta murda door handle tabude kofa tafito daga bathroom din tai gaban mirror ta tsaya tana tsane fuskarta da towel din, karan dataji na faduwan abu kwan yasa ta juya ta kalli kasa dan tasan bata taba komiba tome yafadi, zoben dazu tagani akasan dakin harzata dauke kai saitaga kaman zoben yakara girma fiye da dazu da sauri tasake kallon zoben tana ware manyan idanunta, gani tayi zoben yay girma kaman anhuramai iska da sauri ta dafe kirji tace “innalillahi wa innailaihi raji’un” kaman daga sama taga kwalliyan dake gaban zoben yakara girma saitaga ya dare yarabe biyu yabude baki yay katoo sosai, wani karamin paper tagani yafito daga bakin zoben yafadi akasan dakin saitaga paper yay wani irin girma shima taga yakoma kudi dubu daya sabuwa dal, wani irin faduwa gabanta yayi jikinta yafara rawa bakinta yafara rawa tana kokarin furta addu’a takasa, gani tayi bakin zoben yafara fiffito da kananun papers din dayawa suna zuba akasan dakin suna komawa yan 1, 1k note sababbi dal dal, wani irin ihu tabuga afirgice. “Mamaaaa!” tai wurin kofa da mugun gudu tabude kofan tafita kaman wacce ta zare tana ihu. “Mamaaa, Mamaa” ta kwalama Maman su kira ta kwasa da mugun gudu tai hanyar gate ta runtse idanunta gam dan zoben take gani a idanunta yana aman kudi zoben aljanu, bude gate tayi tafita dawani irin azababben gudu daidai kan wata mota Lexus ta danno yana shirin horn azo abudemai gate, ganin fuskar dabazai taba mantawa ba ko amafarki daure da towel kafafunta ba takalmi idanunta akulle dan gaban gidansu akwai manya manyan Street light bauuu sun haska ko ina yasa da sauri ya kashe motar yabude door yafito yana gyara zaman suit din jikinshi bude kofar gate dinsu yayi ganin babu kowa a compound yasa yawaiga da sauri ganin tana gudu yasa da sauri yabi bayanta, daidai tana shirin shiga titi yawani irin fizgo hanunta tadawo baya yariketa gam yana binta da kallo ganin idanunta a rufe ruf jikinta nawani irin rawa. “Mama Mama, Mamaaaaa! ” tasake kwalama mamansu kira yasa ya jijjigata tareda kiran sunanta. “Amatullah” ko kadan kwanyanta baya aiki a lokacin sai kiran Mama Mama mama take ta datse idanunta gam, da hannu daya yarike ta yacire black jacket din jikinshi dake kamshi sosai ya daura mata akan kafadarta ya jijjigata tareda kiran sunanta. “Amatullah look, look, hey relax is me, open your eyes menene?” jin murya kaman ta Aadil sama sama yasa ahankali tabude idanunta dasuka kankance jikinta na rawa, Sanye yake da farin long-sleeve shirt wuyanshi daure da nicktie gashin kanshi a kwance yay wani irin mugun kyau yana rike da ita gam gam yana kallonta ganin ba lafiya tattare da ita, fashewa tayi da kuka sosai tafada jikinshi ta rungumeshi tace “My Aadil you are back” cirota yayi daga jikinshi da sauri fuskarshi adaure yace “where are you running off to daure da towel batakalmi ba hula are you okay” rikeshi tayi gam jikinta ya dauki ruwa tana kokarin sake shigewa jikinshi yahanata tace “som….something in…a..dakin” luuuu tayi baya zata sume da sauri yariketa ya dauketa yay hanyar gida da ita, bude gate yayi mai gadi yafito mugun kallo ya watsamai yace “bakasan aikin kabako how can be our security idan baka taking note of who goes in and out of this house eh? Anyway banda time dinka call Mami for me kace ta taho da Dr” yay hanyar shashin su Hamida dauke da Hamidan, bude kofar dakin yayi wani hadadden kamshin turaren wuta yadaki hancinshi kwantar da ita yayi akan kujera yatashi yay hanyar dining dan daukan bottle water dayagani daidai lokacin Mami da big Mum dasu Baffa da Suleman suka shigo dan duk suna tare ana maganan Abie inda yakai Aadil Mai gadi yace suzo Hamida ba lafiya, da sauri Mami takaraso ciki da gudu tana kallon fuskar Hamidan tace “maiya sameta Aabid? Kafafunta butu butu haka, wat happen son?” bude bottle water yayi yace “i don’t know Mami dawowa na kenan naga tafito daga gate da gudu ahaka idanunta akulle i was trying to talk to her kuma saitai passing out” karban ruwan Mami tayi da sauri tana surutai. “na shiga uku wai meke faruwa ne ni Maryama” shafa ruwan tayi a fuskarta wani irin ajiyan zuciya Hamida tayi tabude ido tana kallon duka dakin, ahankali Mami tace “Hamida na kinajina?” kallon Mami tayi saikuma tajuya tana kallon duka yan dakin kafin idanunta ya sauka kan Aabid dayay folding hand akirji yana kallonta tashi tayi azubure tafashe da kuka tafada jikin Aabid tace “take me out of this place kaji My Aadil akwai wani abu adakin chan, akwai wani abu yanata girma am scared ka kaini wurin Mama dam Allah ku kaini wurim Maman mu da Kaka” takire Aabid gam, da sauri Suleman yace “to kodai tanada aljanu ne? ” komawa bayan Aabid tayi tarikeshi gamgam jikinta narawa tace “abun na dakina chan bedroom pls take me out of here, zai fito yakamani i carried it dazu” tafashe da kuka sosai da sauri Mami ta tashi zatai magana Baffa yadaga mata hannu bayan yagama nazarin Hamidan yace “kubarta yarinya mai natsuwa haka dole akwai abinda ya firgitata bakuga bata hayyacinta ba, Sulemanu kumuje muduba dakin mugani” da sauri Suleman yace “to Baba” big Mum tace “ku dauko adduna incase maciji ne ko kunama” hararanta Baffa yayi yace “babu reptiles agidan nan ana fumigation ai” sukai hanyar dakin harda su Mami Aabid zai bisu tasake fashewa da kuka tana rikeshi tace “don’t leave me kaji Aadil” juyowa yayi ya kalleta kafin ya dauke kai ganin she’s not okay, ihun su Big Mum dayaji dakuma salatin su Baffa kowa nakiran sunayen Allah yasa da sauri yay hanyar bedroom din yana rike da hanun Hamidan gudun karta kara fita, kutasawa yayi ta tsakakanan su Big Mum dayaga jukunansu narawa duk suna kallon dakin ya kutsa kai ya shiga dakin, chak ya tsaya kyam jinin jikinshi ya tsaya kyam, ganin abinda tunda yake aduniya baitaba ganiba, wani katoton huge zobe yagani akasan dakin yana aman kudi yan dubu daidai sababbin kudi nafita daga bakin zoben, kudin sun cika kasan dakin har wasu sun soma hawa kan gadon sunyi himm, daidainan Abie ya buga kofan falo ya shigo dakin rai abace Aadil biye dashi.

_hello lovelies, due to high demand na next page am introducing VIP readers, in bakison suspense kinason kiji next page always koda yaushe all you need to do is subscribe for VIP and be my VIP readers, for those interested all you need to do is pay 1k, for more enquiry 07012181461, chat me up and know more. I love you _

No comments