Breaking News

In Bani 59


Girgizamai kai Aabid yayi yana danne zuciyarshi dankar ya fahimci komi game dashi, ahankali yace “bakomi kaina keta ciwo last night saisa nai wani iri” kafeshi da ido Aadil yayi dan bai yarda da maganan shi ba ko kadan hakanan zuciyarshi taki natsuwa taki aminta da maganganun, ganin yanda Aadil din ke kallonshi yasa yatashi da sauri yay bathroom yana tafiya ahankali yace “lemme shower kaje ka shirya kaima” yabude kofar bathroom din ya shiga yarufe, binshi da kallo Aadil yayi dan yanda yayi yanzu yakara tabbatar mai da wani abune ke damunshi ba ciwon kaiba da sauri yatashi sabida yanda yaji zuciyarshi taki natsuwa ya shiga duba dakin, pillows din gadon ya daddaga amma baiga komiba, side drawer ya bubbude nanma baiga komiba, wayar Aabid din daya gani akan gado ya dauka yana budewa yaga ba password hakan yasa ya shiga dube duben wayan amma baiga komiba harzai ajiye wayan yaga watsapp message ya shigo daga Dr Sham “get well soon” da sauri ya shiga watsapp din yabude Dr Sham din, maganan Aabid ya gani kafin reply din Dr Sham ” _na am fine now Dr i took d drugs”_ da sauri ganin baida lafiya ne da gaske yasa yay scrolling sama dan yaga meke damunshi, idanunshi ne ya sauka akan maganan Dr yace _”you haven’t told me the problem, Hussain u are too young to be suffering from heart disease!”_ wani irin faduwa gabanshi yayi ganin heart disease da sauri ya zauna kan gadon yana dafe kirjinshi dake bugamai way too fast, ya shiga reading chat din ahankali daya bayan daya.
_”i used to be a bad boy Dr, inabin mata, ina shan alcohol sometimes su kadaine abinda nakeyi idan rage tunanin dan uwana barin ma idan yana tsaka da ciwo, kullum kuka nake in rasa kwanciya hankali sainaje nasha giya sanan zan manta, my brother, my twin brother is not okay almost every every month saiya kwanta a asibiti, my brother is my life ina sonshi sama da komi aduniyan nan idan kacire iyayen mu, wata rana a Lagos nahadu da yarinyar da i fell for her at a glance, My Jewel! My Amatullah!”_ chak Aadil ya tsayar da karatun jin sunan Amatullah ahankali ya furta sunan Amatullah, dan yaji su Mum sun kira yarinyar nan na dazu Amatullah, cigaba da karatun yayi..
_”my Hamida!”_ tsayawa Aadil yay chak kanshi yawani irin sara yana ganin flash din fuskar Hamida a idanunshi tanamai murmushi tana kiranshi “My Aadil, stop crying to” dafe kanshi yayi ganin yasoma tuna da yacigaba da karanta message din da kyar.
_”I saved her lokacin datai drowning a ruwa, Dr Sham i love her, i just fell for her naturally, inasonta sosai with all the fiber in my body with all my soul, i love Hamida with all my mind, my heart and soul, and right then bayan nakaita asibiti i confess my love for her cus i understood she was d one for me, mine, dudda she was afraid of me i get to understand that she’s a girl that hardly get comfortable around men lemme say mutane ma in general, bayan mun rabu, yan uwanta sunzo sun tafi da ita i was dreaming about her, babu randa zanyi barci na farka banyi mafarkin my Jewel ba, unfortunately my brother as well fell in love, he fell for her as well, funny right yanda twin brothers fell for mace daya, cikin ciwonshi bama tareda ya ganta ba tun amafarki yafara sonta”_ tsayar da karatun Aadil yayi kanshi na saramai komi na dawomai kadan kadan ya dafe kanshi dakemai zafi sosai kaman an kunna wuta.
_”maganan shi alokacin shine take me to she! She! Bid she! Ranan daya fara ganin Hamida was randa yafita shida Mami, dayaga Hamida saida yaja accident ahanya yafita yabita har gidansu har aka koresu ita da shi, atare mukazo muka gansu with the help of police dats d second time danake ganin Hamida, the way naga my brother hugged her touching her yana mata shagwaba playing with her saida yasa naji kaman an chakamin kibiya azuciyata, da kyar na iya na daure inata kallon Hamidan da at that instant nagane akwai strong connection and bond tsakanin ita da my twin dan she’s always free with him, bazaka tabajin maganan Hamida ba sai tana tareda Aadil, her smile her teeth saitana tare da Aadil, bakajin maganan ta tana surutu saitana tare dashi, we took them both home kasan ranan danai worst mistake?”_ ya tambayi Dr yacigaba
_”ranan danaga yana kokarin sama Jewel chocolate abaki yana mata all sort of things tanamai murmushi tana lallashin shi sosai zuciyata tai baki i was madly jealous, i don’t know Sanda nai raising hand dina on my brother inacemai yadena kiran Hamida his wife, banyi considering nashi ba banyi considering condition dinshiba namai duka sosai sabida kishi ina dukanshi yana kuka inajin zafin yanda nake dukanshi ajikina nima but i couldn’t help it, ranan i cried my life out for beating him najamai ciwo har saida akai admitting nashi a hospital, daganan from how things were going saina fara lallaba kaina ina lallashin kaina inason Hamida but my brother needs her more har akazo akasa ranan lallaba kaina nakeyi battling with depression dan i was seriously depressed ni kaina bansan lokacin danai ma Hamida wanan strong so dinba, banfadan ma kowa halin danake cikiba ranan daurin aure kasa daurewa nayi nabar garin straight to wurinka a hospital a Lagos sabida ciwon danakeyi harkai admitting dina bayan naji sauki na koma gidana a VGC nakira Vanessa nafara all sort of things just to stop thinking about Hamida, my brother’s happiness is everything to me Dr Sham, Hamida is blessing to his life saisa na daure, karka damu ciwo baya kisa saidai idan lokacin ne yayi i will be fine zan cigaba da shan magungunan daka rubutamin”_ yanda gaban Aadil ke bugawa kanshi na vibrating abin yadawo kaman ana tariyo mishi lokacin dayay haukan yana ganin komi daya faru yasa ya shiga dube duben dakin har ya jawo side drawer yaga wata yar box bude box din yayi nan yaga drugs din heart dayawa fashewa yayi da kuka sosai ya taushe baki komi nadawo mai yace “no no no, najama dan uwana ciwo” daidai lokacin Aabid yabude bayi yafito tsayawa yayi chak ganin Aadil idanunshi sunyi jajir yana rike da magungunan shi na ciwon zuciya yana kallonshi hawaye na zuba, da sauri yay wurin Aadil din yana rike da magungunan yanunamai magungunan cikin fushi yace “mesa kamin karya Bid why did you lie to me?” saukar da idanunshi Aabid yayi kasa yakasa magana chakumeshi Aadil yayi idanunshi sunyi jajir yace “you lie to me Bid, you are sick ka boyemin, you think i cannot take care of you? I can’t give you wat you want and i will judge you ko? Aabid!” yakira sunanshi kaman zaiyi kuka hakan yasa Aabid ya dago kanshi ya kallai, ahankali Aadil yace “you love Hamida! Nasan komi, Kanason Hamida tun ranan daka fara ganinta, kanason Hamida sosai kazaci bazan iya barma Hamida ba? Now i remember everything, natuna komi, Aabid i remember yanda kake kula dani, I remember yanda kake rike dani kana tareda ni tun ranan da aka fara sakamu a nursery school a UK, i remember yanda kake kuka koda faduwa nayi akasa, i remember yanda idan banda lafiya bazaka ci abinci ba ni ciwo kaima ciwo sabida ni haryau kana suffering from ulcer, i remember yanda kake amfani da rigan jikinka ka sharemin miyau danake dilalar wa, i remember yanda nakeda saurin fushi i will not talk to you but u will stick around kanamin murmushi harsai nadawo normal, i remember yanda kake sona nida kai were inseparables, Hussain i remember each and every single memory of my past, duk abinda kakeso aduniyan nan sainama shi you are all i have, kaine jinina, kanina, dan uwana, abokina, abokina rayuwata and komi nawa, zan iya sadaukar ma da komi aduniyan nan, am leaving Hamida for you, zan saki Hamida!” yafada hawaye na rolling down his cheeks yana kallon Aabid din dake kallonshi.

 

Good morning readers, like i said ni makarantana nakema rubutu and am at your service after all you guys paid for it.
Please vote da Aabid da Aadil wanne yafi dacewa da Hamida, wanne kuke so? This book is love o, romantic love story, so feel free kufadamin, thank you.
Aadil ☑
Aabid ♾

 

 

Wanan page din harda na jibi nahada muku, jibi bazanyi typing ba, love you殺 don’t forget to vote and lemme hear reasons dinku.

 

No comments