Breaking News

Kanwar Maza 45


 

Wani irin tausayinsa ne ya kama Aliyu, duk yadda adam ya so É“oye hawayensa kasawa yayi, ya barsu suka din ga zuba son ransu.

Da Æ™yar Aliyu ya É—an yi gyaran murya ya ce “Kamar yadda ka ce kai musulmi ne ka yarda da Æ™addara, to Yakamata a ga hakan a aikace, ka yi haÆ™uri in sha Allah sirikinka zai fuskance ka, Allah ya yi mata rahama”.

Mama ce ta yi sallama a É—akin tana faÉ—in “Aliyu ya tashi kuwa?”.

Ta tarar da su a zaune, mama ta ce “Alhamdilillah ala kulli halin, Allah mun gode maka, sannu ka ji?” Ya jinjina wa mama kai yana share hawaye.

“Ayi haÆ™uri, a fawallawa Allah, yaronka mahaifiyarka da sauran makusantanka suna buÆ™atar ka, ita tata ta Æ™are ta yi shahada sai fatan Allah ya karÉ“i shahadarta, ayi haÆ™uri, Aliyu je ka É—aki ka kawo ruwan shayi da abinci ya samu ya saka wani abu a cikin sa”.
Aliyu ya tashi ya fita, yana fita lokitan dare ya shigo, ya dudduba Adam aka bashi maganinsa na dare, likita ya jaddada masa ya kula da magani da dokokin da aka saka masa.
Sam Adam ba ya fahimtar abun da likitan yake faÉ—a, mama ta miÆ™a masa kofin shayi cikin kulawa ta ce “Daure ka sha, ka ga an baka magani, dole sai ka ci abinci” kallon mama kawai yake yi, wato duk in da uwa take uwa ce, yadda ta ke ta nuna kulawa a kansa sai ya ji daÉ—i, duk da tarin damuwar da yake ciki.
Duk da ba zai iya tantance manufar kulawar da mama take bashi ba, amma tun da ya taso kulawa É—aya ce yake gani ta zahiri, wato kulawar ammi ban da haka galibi masu yi masa murmushi suna yin sa ne da biyu.

Da ƙyar ya karɓi kofin shayin, ya ɗan sha kaɗan ya ajiye, mama ta yi ta masa nasiha, da rarrashi cikin siga ta dattaku da manyance.
Ya É—an murza zoben hannunsa ya ce “Da ke da iyalinki, babu abun da zan iya ce muku sai godiya, a rayuwata na daÉ—e ban ga mutane masu karamcinku ba. Amma dan Allah ku yi haÆ™uri da abun da zan faÉ—a, ina son zan karÉ“i yarona, dan Allah a rarrashi mamansa, na san zata tsaneni fiye da da, amma ni ba zan iya da rigimarta ba, a bata haÆ™uri zan É—au yaron nan zan tafi da shi wurin kakansa, sai hukuncin da ya yanke a kanmu”.

A take mama ta ji babu daɗi, domin ita kanta ta shaƙu da jaririn ba kaɗan ba, ya shiga ranta.

A zahiri ta ce “Babu laifi, Ubangiji Allah ya raya shi bisa tafarkin addinin musulunci, ya jiÆ™an mahaifiyarsa. Amma ina fatan ba zaka rabamu da shi gaba É—aya ba, dan a halin rumaisa bana jin za ta iya haÆ™ura”.

Yayi murmushi ga hawaye na zuba daga idonsa ya ce “Za ta saba in sha Allah, ba zata damu sosai ba amma yarona yana buÆ™atar kariya ta musamman, ba zan manta soyayyar da ta nunawa gudan jinina ba”

Jiki a sanyaye mama ta ce “Babu laifi, Allah ya jiÆ™an mahaifiyarsa, kai kuma ya baka lafiya” da haka mama ta yi musu sallama ta koma É—akin da rumaisa take. Ta kwanta tana facing É—in Sabir, tana ta baccinta, ta saka hannu ta riÆ™e masa nasa hannun suna bacci.

Tausayinsu ne ya kama mama, amma babu yadda ta iya, haka ta shiga harhaÉ—a wa sabir kayansa, a daren ta haÉ—a komai cif a wuri É—aya.
Suma ta haÉ—a musu nasu kayan, dan ta ji likitan yana cewa washegari zai sallami rumaisa, tun da ita ma ta warware sai abun da ba a rasa ba.

Sai da ta kammala, sannan ta yi alwala ta tayar da salla.

Da asubar fari, sabir ya tashi yana ‘yan koke-koke, mama ta É—auke shi ta yi masa wanka, ta bashi madararsa, ita kanta mama tana matuÆ™ar Æ™aunar yaron da tausayinsa, ta É—auke shi ta goya shi a bayanta, ta yi sallar asuba, ta tashi ruma ta yi salla sannan ta fita daga É—akin.
Harabar asibitin ta koma ta kira mai sunan baba, tana shiga ya É—aga, ya gaida mama, ta amsa masa sannan ta ce “Babana, dan Allah da gari yayi haske ka taho asibitin nan, yau za a sallami rumaisa, kuma yau za su karÉ“i É—an su, ka san halinta sarai, jiya da daddare babansa da ya farfaÉ—o ya ce zai karÉ“i É—an sa ya tafi da shi ya gabatar da shi a danginsa, sannan ya sanar da rasuwar uwar É—an”.

Mai sunan baba ya É—an yi shiru sannan ya ce b”Babu laifi, zan shigo in sha Allah, amma a bita a hankali dan Allah, ko a bari na zo tukuna”

Mama ta ce “ai shi ya sa na ce sai ka zo É—in”

Bayan sallar asuba, Adam ya karÉ“i wayarsa a hannun Aliyu, ya kira ammi, suka yi magana, ta ji daÉ—i sosai da jin muryarsa, tayi masa addu’a da fatan alkhairi.
Ya kira Bashir ma suka gaisa, tare da sanar da shi, ya je ya taho da Ammi.

Kiran jabir ne yake ta shigowa tun bayan da ya kunna wayar, kamar ya share sai kuma ya É—aga.

“Wai ina ka shiga haka baka É—aga wayata? Ya ake ciki ne akwai wani labari ne? Ko ka koma wurin yarinyar?”

“A’a ban koma ba, zan koma bacci yanzu zan zo gida in sameka anjima” bai ko tsaya saurarar mai jabir zai ce ba, ya kashe wayar ya ajiye, haryanzu ya kasa gazgata maganganun rumaisa, wai Aisha ta mutu, ganin abun yake kamar almara, sai yanzu ya gane ka rasa mutum ka ga gawarsa wata ni’ima ce, ba irin tunanin da bai zo masa a kan gawar Aisha ba.

Abun mamaki yau ruma taƙi komawa bacci, mama har tambayar ta ta yi ba zata koma bacci ba, ta ce ba ta ji.

Ta dubi in da mama ta haÉ—a kayansu ta ce “Mama wai tafiya zamu yi ne an sallame ni?”.

“Eh, in anjima za a sallame mu”

“Yeeee dama na gaji da zaman asibitin nan wallahi, yau sai gida, ga kayana ga na babyna nima na samu mai sunan babana, sai dai Allah ya sa kar yayi halin mai sunan kakanmu” tayi maganar da sigar tsokanar mama, amma mama ba ta tanka mata ba.

Har gari ya waye ruma idonta biyu, ta damu mama a kan ta bata sabir, amma mama ta hanata.

Wajen ƙarfe tara, Usman da mai sunan baba suka zo, ruma tana ta murna zata tafi gida, dan zumuɗi ta ce abincin ma sai ta je gida zata ci.

Usman ya din ga kwasar kayansu yana fitarwa, sai murna take yi yau ba kwanan asibiti, dan takardar sallama kawai suke jira daga likita.

Bashir ne ya shigo É—akin rumaisa, ya kalleta yayi murmushi ya ce “Yau sai gida uwar rikici”

Ta yi murmushi ta ce “ÆŠan uwanmu, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi, jin godiyar nake ma ta yi kaÉ—an a baki, amma zan din ga yi maka Addu’a idan na yi salla”..

Yayi murmushi ya ce “Kai masha Allah, amma na gode Æ™warai da gaske, sister na asiya ma tana gaishe ki, ita ma ba ta da lafiya ne. Amma kin je kin duba baban sabir kuwa?”

Ta É—an yi turus tana kallon mama, mama ta ce ‘Yanzu zan sakata a gaba mu je ta duba shi, sai mu tafi”.

Bashir ya ce “Yauwwa mama, dama ga ammi can ma ta zo sai ku yi sallama, ai bai kamata ku tafi babu sallama ba”.

“To ai yaya Aliyu ya ce bai mutu ba, har ya tashi”

“Haba rumaisa, idan da kara yakamata ki je ki duba shi, ko dan albarkacin sabir É—inki”.

Usman ya ce “Sai ka lallaÉ“ata ma, wuce mu je, kuma saura mu je ki yi rashin kan gadon naki, ya saka dogarai su saita miki zama”.

Suka ɗunguma zuwa ɗakin da takawa yake, suka tarar ammi na zaune a kusa da shi, ta riƙe hannunsa, tana share masa hawaye.

Ammi na ganinsu tayi murmushi ta ce “Kun fito? Yau ban Æ™araso mun gaisa ba rumaisa, hankalina ne a tashe”

Ruma ta durƙusa ta gaisheta, ta amsa mata cikin girmamawa.

Usman ya ce “Ki yi masa sannu mana”ta dubi Adam za ta yi masa magana, amma gabanta ya faÉ—i, ganin gaba É—aya idonsa ya koma baÆ™i, yana fitar da hayaÆ™i.

Mannewa ta yi bayan usman, tana leƙo shi, taga ita yake kallo, amma idonsa yana ta hayaƙi, kallonsu take yi, tana jiran ta ji wani yayi magana a kan idon takawa, amma ta ji babu wanda yayi magana da alama su ba sa gani.

“Ba zaki yi masa sannun ba?”

Ta sunkuyar da kanta Æ™asa ta É—an zuro kai ta ce “Sannu, Allah ya bada lada” tayi maganar a rikice dan a razane take, bata taÉ“a ganin idon mutum a haka ba.

Bashir ya ce “Ladan me kuma rumaisa, shi da ba shi da lafiya?”.

“Au ba lada ba, Allah ya warkar da shi”

Usman ya ce “Yau kuma meke damunki ne?”

Mama ce ta kwance Sabir daga bayanta, mai sunan baba ya karÉ“e shi,  ya Æ™arasa gaban gadon Adam ya ce “Allah ya Æ™ara lafiya, ya jiÆ™an mamansa, kamar yadda ka buÆ™ata ga yaronka, Allah ya raya shi, Allah ya biyaka É—awainiyar da ka yi da Æ™anwarmu”. Adam ya karÉ“i Sabir, yana Æ™oÆ™arin mayar da hawayen idonsa.

A rikice ruma ta ce “Ban gane ga É—an sa nan ba, da shi zan tafi ai, ni anty aisha ta bar wa shi” tayi maganar tana nufar Adam, amma mai sunan baba ya tare ta ya ce “Juya mu tafi” karo na farko da ta tsaya ta saka idonta a nasa ta ce “To ka karÉ“o mini É—ana”.

“Ni nake magana ki ke mayar mini?”.

“Haba mai sunan baba, ya za ayi a Æ™wace mini yarona, dama abun da aka shirya kenan? Mama ki saka baki” ta dubi Ammi ta ce “Dan Allah ku bani yarona, na sha wahala kan mu tsira tare, idan aka Æ™wace mini shi, mutuwa zan yi, wallahi ina son sa sosai, É—an uwanmu yaya bashir, dan Allah ka karÉ“o mini É—ana”
Gaba É—aya sai tausayin rumaisa ya kama su. Ammi ta ce “Kina ji ruma, ki kwantar da hankalinki, babu mai rabaki da yaronki, zamu je a kai shi cikin dangi ne, kuma in sha Allah za a din ga kawo miki shi ki ganshi”.

Rumaisa ta fashe da kuka ta ce “Da na san haka ne, gara na zauna mu mutu a dajin, da da wannan mutumin ya ce in tafi ba zan tafi ba, gara a harbeni, kwanana biyu ba ma bacci ni da sabir, saboda sanyi yana kuka, kwanana uku ina bulayin hanyar da zamu dawo, kuma a Æ™wace mini shi bayan mun sha da Æ™yar, ba anty aisha ba sabir É—ina. Dan an ga ni yarinya ce za a Æ™wace mini É—a” Mai saunan baba ya danÆ™i hannunta zai yi waje da ita, tana kuka tana miÆ™a hannu tana “Dan Allah ku bani sabir É—ina” tun da ruma ta fara kukan nan tana zuba, ko É—aga kai Adam bai yi ba ya sunkuyar da kansa Æ™asa.

Kuka sosai rumaisa take yi, tamkar an ce mata mama ta mutu, bashir ya rakosu yana ƙoƙarin rarrashinta, amma mai sunan baba ya ce ya rabu da ita, ya buɗe mota ya sakata, amma sai miƙa hannu take taka kuka.

“Ki rufewa mutane baki, idan an baki É—an ya zaki yi da shi, ke wace irin yarinya ce da ba a isa a gaya miki, ko ki rufe mini baki, ko na casaki a wurin nan” mai sunan baba yayi mata wata irin tsawa mai razanarwa.

A gigice ta ƙanƙame mama tana ƙoƙarin haɗiye kukanta, amma ta kusa ƙwarewa saboda kuka, ga hawaye ga majina har da yawu, saboda kuka.

Ammi na tsaye tana hango rumaisa yadda ake fama da ita, wani irin tausayinta ya kamata. Allah kenan ya karɓi uwar yaron, kuma ya sanya soyayyarsa mai tsanani a wata zuciyar.

A hankali ta juya ta koma É—akin da adam yake, yana rungume da jaririnsa.

Ammi ya dube shi ta ce “To me ka yanke? A ganina mu bari nan da ko kwanaki biyu ne ka gama warwarewa”.

Adam ya girgiza kai ya ce “Ammi, ba zan taÉ“a warkewa ba, barin lamarin ina sake jinkirta loka8, abubuwa caÉ“ewa za su cigaba da yi, daga nan gidan turaki zan wuce, zan je na sanar masa da laifina gaba É—aya duk hukuncin da ya yanke a kaina shikenan”.

Cikin damuwa Ammi ta ce “Kana ganin hakan shine mafita?”.

“Ammi dole ita kaÉ—ai ce mafita, na yi zaton aisha tana raye ne dama, shi ya sanya nake ta jinkirtawa, amma na yadda ta rasu yanzu, yanzu zan fara fuskantar mai girma turaki, daga baya kuma sai na fuskance Æ™alubale na gaba”.

Ammi ta É—an yi shiru yana kallon Æ™asa, daga bisani ta yi ajiyar zuciya ta ce “Shin, Ubangiji Allah ya yi mana jagora baki É—aya ”

Ya amsa da amin.
Bashir suka shigo tare da likita, likitan ya dubi adam da yake rungume da jariri ya ce “Allah sarki rumaisa, gaskiya ta shaÆ™u da yaron nan, ba ka kyauya ba da ka Æ™wace mata É—a” Adam ya sunkuyar da kai ba tare da ya iya yin magana ba.

“To Yanzu me yake damunka, zan rubuta maka teses na yi reviewing file É—in ka, na ga vitals É—in ka duk normal”.

“Sallama nake so” ya faÉ—a a taÆ™aice.

“Meyasa zamu sallameka? Dole mu riÆ™e ka zuwa gobe in Allah ya kaimu mu ga abun da hali zai yi”.

“Ba zaku hana Allah zartar da hukuncin sa ba, ku yi haÆ™uri tafiya zan yi ” duk yadda likitan nan ya so lallaÉ“a adam ya É—a zauna, amma yaÆ™i ammi ta ce ya basu sallama kawai, suna da issue a gida.

Haka kan likitan ya rubutawa adam sallama, da yayi tunanin ya kira jabir su tafi tare, sai ya ga babu wani amfani ma da jabir É—in zai yi masa a halin yanzu, dan haka kawai ya share suka tafi.

Suna tafe a mota, yana kalon sabir da yake ta ƙamshin turare, yana wasa da hannunsa, har da farar hoda da kwalli mama ta shafa masa, ba ayi masa aski ba, dan haka suma ta cika masa kai, ga ta a cike baƙa siɗik, har ta ƙasan hularsa ta fito, ga gashin girarsa a hankali yana tofowa.
Ƙasan zuciyar Adam yana ta fargaba da tunanin, yadda zai fuskanci turaki.

Har gidan turaki bashir ya kai su, sai dai shi ya tsaya a mota, su kuma suka shiga.

Da fari ta ƙofar turakar turaki ta harabar gidan, Adam ya shawarci Ammi su shiga, amma sai suka tarar da ita a rufe, dan haka dole suka bi ta cikin gida.

Falon ba kowa sai hadimai, suna ganin Ammi tare da Adam, cikin rawar jiki suka gaishe su, aka tafi nema musu iso wurin matar gidan.

Ba su jima a zaune ba sai ga mama ta fito cikin taÆ™ama, ta dubi Ammi ta yi murmushi ta ce “Giwa, yau ke ce a gidan namu?”

Ammi ta ce “Ni ce, kin san É—aurowa take a É—aure alÆ™ali, ya gida ya iyali?”

“Alhamdilillah, takawa magajin takawa, dan kujerar galadima ta yi maka Æ™anÆ™anta babbar kujera muke fata” tayi maganar tana kallon jaririn hannun Adam.

Ta sake cewa “Ina ku ka samo É—a?”

Adam ya ce “Dan Allah idan babu damuwa, muna neman iso wurin mai girma turaki idan yana nan”

Ta É—an jinjina kai ta ce “Yana nan, bari ayi masa magana”.

Ƙanwar Samha ce ta fito sumayya, ta gaida Ammi tare da takawa, ammi tambayeta ina samha, ta ce mata ta je abuja.

Mama ta fito ta ce “Bisimillah, ku shigo”

Ammi ta tashi, tana gaba adam na bin ta a baya, suka shiga falon turaki.

Yana zaune a falonsa, gefensa ga Alqur’ani a ajiye, da alama karatu ya idar.

Ya kallesu yayi murmushi ya ce “Maraba da manyan baÆ™i”.

Ammi ta risuna ta ce “Barkanmu da wannan lokaci”

“Barka dai, ya iyali ya kuma rayuwa”

Ammi ta amsa da Alhamdilillah, maimakon mama ta fita ta bar É—akin, sai ta nemi wuri ta zauna.

Turaki ya kalli Adam ya ce “Takawarka lafiya, ana lafiya?”
Adam ya jinjina kai kawai, amma bai yi magana ba.

Ammi ta gyara zaman ta ta ce “Allah ya baka nasara, wata muhimmiyar magana ce ke tafe da mu, amma kan in ce komai, zan fara da neman afuwa sannan a sassauta mana hukunci”

“Babu laifi, ku muke sauraro”.

Adam ya tashi a hankali, ya tafi gaban turaki ya durÆ™usa, ya É—ora masa Mahmud a kan cinyarsa”.

Turaki ya rungumi sabir ya ce “Masha Allah, ina na samu É—a, É—an kyakykyawa Masha Allah?”.

“ÆŠan wurin aisha ne” takawa ya faÉ—a jiki a sanyaye.

Turaki ya faÉ—aÉ—a fara’arsa ya ce “Ikon Allah, uwata yaushe ta haihu?, yaushe rabona da ita?”

“Allah ya baka yawan rai, haÆ™iÆ™a ni mai laifi ne, kuma a shirye nake da karÉ“ar hukuncin da duk ka zartar a kaina. Wannan jaririn É—an wurin aisha ne matata, kamar yadda aka kai ruwa rana da surutu a kan karatu da nace zata tafi. Duk ba wannan ba ma, maganar da nake maka, yanzu haka fulani ba ta duniya, ya rasu” Adam yayi maganar kansa a Æ™asa hawaye na gangaro masa.

Ayshercool.

paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, masu buÆ™atar vip ko special kuma, suna iya garzayawa arewabooks ku searching sunan littafin*

 

 

No comments