Breaking News

Namijin Zuma 37

37….

 

Big hajiya ta kalli nabeelah wadda keta sadda Kai kasa ta tabe baki tace “ke daganin idanuwanki baki da gaskiya… Ina ganinki kmr ta kirki ashe ina…ohhh!” nabeelah ta


kuma sadda kanta kasa se taji wata kunyar ta kuma rufeta, ita yanzu batasanma da wata fuska zata kallesu ba, musammanma big hajiya, gabaki daya de Aeezad ne yaja mata wannan matsifar, dazata shigo falon ma kawai dakiya tayi ta shigo Allah kadai yasan ya takeji a zuciyarta. Aeezad ya kalli big hajiya da idanuwan rashin kunya yace “me tayi na rashin gaskiya? Karki kara ce mata mara gaskiya wlhi in kinasan zaman lafiyata dani…” Big hajiya ta taso masa “sannu ubana,tsinemin inbi duniya,,,ai kaine babban mara gaskiyar shege kayi da idanuwa kmr na yayan karuwai, gidan uban wa ka dauketa ka kaita? Kade ja mana abun kunya a dangi…” Aeezad ya amshe da “Da nayi me? A kan wata karuwar aka kamani nasa al’aurata?” Dukkaninsu seda sukaji kunyar abinda yace amma shi ko a jikinsa, big hajiya ta amshe Tana kara taso masa “to ita wannan ina ka kaita? Dan ubanka,. Har kanada bakin mgnr banza, Yarinya me tarbiya ka bata mata tarbiya, daman tin a jirgi naga wani al’amari, kawai kallonka nakeyi…wannan mgna dole a danganata da ubanka…” gaban nabeelah ya yanke ya fadi Jin abinda big hajiya ta fadi na karshe, har Zaks seda ya tsorata. Aunty hafsat ma haka sbda tasan karamin aikin big hajiya ne ta fallasa kowa yaji, daman kullum se mita takema Aunty hafsat kan wai Ina Aeezad yakai nabeelah , aunty hafsat tace bata sani ba itama, wuni big hajiya take Tana cancana maganar Tana cewa “gaskiya iskanci Aeezad yajeyi da nabeelah, sbda taga wani abu a jirgi…” shikam Aeezad abinda big hajiya tace ko a jikinsa ya daga kafad’a yace “Se akayi me Inkin fad’a ma daddy?” Ya karashe yana kuma tabe baki shi ko wa zata gaya mawa ta gaya mada. Aunty hafsat de Tana gefe tayi shiru. Big hajiya ta sake hayayyako masa “zakaci uwarka da ubanka ni kake gayama se akayi me? Kasa na hasala wlhi wannan mgna kmr a bakin Matarka da ubanka…” gaban nabeelah da aunty hafsat da Zaks ya kuma yankewa ya fadi ba kmr ma nabeelah seda ta hadiye wani azababben yawu. Aeezad dako a jikinsa ya bude baki zeyi mgna aunty hafsat ta rigasa dacewa “yanzu in kika fadi kice me big hajiya? Kidena irin wannan abun gaskiya…shaidar zirr haramun ne” big hajiya ta dawo kan aunty hafsat ta watso mata harara Hadi dacewa “SANNU kwankwasashiyar muna fuka, Yar shaidar zir din bura uba, kema kallanki nakeyi kawai nasan Kinsan komi,,,yaza ayi ace, namiji ya dauki mace tsawon sati daya, wannan kowa yaji ai yasan akwai lauje cikin nad’i, wannan ai fasikancine…” Aeezad ya amshe da “Aise ki nunamin inda nayi fasikanci, big hajiya sharrin Zina kikeso ki laqabamin kuma baze yuba sbda baki kamani Turmi Cikin tabarya ba…” aunty hafsat ta amshe da “Ai shine, gaskiya big hajiya kidinga shiru a abinda baki sani ba…” aunty hafsat ta dage tana kare Dan uwanta. big hajiya ta amshe da “Aise a hanani mgna bayan Allah ya tsagamin baki, munafukan banza, har Kai zakariyya tantirin munafuki ne kaine jagoran yan iska, shugaban fatsikai…” ta karashe Akalar maganarta da Kallan Zaks wanda yaketa kara makalewa a baya, Jin abinda big hajiya ta fadi ya karasa Zaks ya kara nokewa a baya duk mgnrsa yaki cewa komi. Big hajiya taci gaba dacewa “Kana ciwo ashe ciwon karya ne na munafunci na makirci tinda ka iya iskancin…” big hajiya tayi mgnr Tana karewa nabeelah kallo dashi uban gayyar datayi mgnr dashi Aeezad kenan. Ba tare da Aeezad yabi ta kan big hajiya ba yaja hannun nabeelah suka nufa dakin nabeelah, nan ya kuma bawa nabeelah kunya taji ina zatasa ranta Gashi da karfi yajata ba halin ta turje. Big hajiya ta kuma binsu da idanuwa hadi da Jan salati, ita fa abun ya fara daure mata Kai, se ynzu ta kuma lura da tafiyar nabeelah ma ta chanza, abinka da tsoffi tini ta fahimci wani abu, aunty hafsat ma data Bisu da idanuwa tini ta fahimci meya gudana, a ranta de adduah take tayi Allah yasa da Auren akayi, tasan ma tinda yace ya aureta to tabbas ya aureta din sbda shi baya karya, komi gaskiya yake fad’i duk d’acinta. “Tayaya akayi auren?” Itace tambayar da aunty hafsat ke yawaitama kanta. “Biri yayi kama da mutum, ohhh ni jikar ahmadu, yauni nashiga uku! Meke shirin faruwa a zuri’ah ta, amma wannan yaran d’an iska ne na gaske, wannan shine anyi amai an lashe, toh wlhi be isa ba, wlhi inde har ya lalata baiwar Allahnnan seya aureta , Kai daganin fuskarta kasan ba ruwanta ba a san ranta bane komi ya afku…wannan yaro shine zakka a zuriahta,, ni wannan shaani ya dauremin Kai ohhh!” aunty hafsat de tayi shiru dan ita bata sanar da big hajiya Cewar Aeezad yace ya auri nabeelah ba kmr yadda ya gargadeta. Big hajiya de Tana mita kuma Tana duba kayayyakin da aka shigo dasu, har tazo kan kayan ciye ciye ta bude wani chocolate tasha ta lumshe ido saboda dadih, Zaks ya kalleta suka hada ido da aunty hafsat sukayi murmushi. “Tsufa labari…” Cewar zaks. Big hajiya dake Shan chocolate dinta ta dago ta kalli zaks tace “Uwarka da ubanka ne tsoffi..” Zaks yace “godiya nake big hajiya, karde ki shanye chocolate din duka sbda kaf kayannan na mommy nabeelah ne…” “tinda uwarka da ubanka ne suka siya ba,,,naga de ai jikana ne ya siya, shege munafukai kuna ce mata mommy, mommyn karya kou? Makirai…” aunty hafsat ta kalli Zaks tace “Zaks kyaleta, karaso ka zauna…” Zaks ya karaso ya zauna kan kujerar 2ct. Big hajiya ta kalli aunty hafsat tace “munafuka …” aunty hafsat tace nagode. “Dake da Kaninki duk munafukai ne, duba kiga dan iska bayan ya dauketa na tsawon sati daya yanzu ya kuma binta cikin daki ko uwar da ubansa ze mata waya sani…” duk suka mata shiru ba wanda ya kuma bi ta kanta aunty hafsat ta zauna kan kujera, duk suka zuboma big hajiya idanuwa wadda ta tasa kayan ciye ciye se ci takeyi Kai kace ita aka kawo mawa. tanaci Tana ware laces din dataga sun mata, atamfofin dataga sun mata harda Abaya da hijjabs se fadi takeyi “wannan duk sunmin nawa ne, wancan kuma in kaima sirikata maryama matar Wannan d’an,,,,” gabaki daya big hajiya ta zabe rabin kayan.

Suna shiga dakin Aeezad ya mayar da kofar ya rufe yana shirin sa key ta rike masa hannu ya dago kwayoyin idanuwansa ya kallets ya narkar mata da idanuwansa, itama shidin take kallo yayinda suke daf-daf da junansu. “Wai meyasa baka gudun abun kunya ne Kai? Gabaki daya kasani a kunyar duniya kai kuma ko a jikinka…” Aeezad yakai hannu ya shafi duwawunta na gefen dama yaji Wani laushi ya lumshe idanuwa ya bude yace “Ke kikasan wata kunya ni ina ruwana da wata kunya…Nifa ba ruwana ko a gaban big hajiya da aunty hafsat in zaki bani gindi wlhi zan ciki a gabansu, to ai auranki nayi ba zaman dadiro nakeyi dake ba,,,nifa mommy wlhi ko zina nake dake Bazan Ji kunyar kowa ba a kanki, ni banajin kunya inde a kanki ne,,,wai ke Kinsan me naji newai danaci gindinki? Wlhi kin kuma rikitani na kuma sanki mommy, gindinki ya gama biyana bawanda ya isa ya rabani dake mommy…” nabeelah ta tsuresa da idanuwa, fuskarsa na tabbatar da kalaman bakinsa. “Ka gama Dani wlh, kajamin abun mgna a rayuwata ka zubarmin da mutumcina a idon mutane, kuma ka cinyemin budulci gaskiya ka cuceni…” ta karashe idanuwanta nayin narai-narai kmr zatai kuka, ta isa bakin gado ta zauna hadi da ajiye ledar wayar data shigo da ita kan bedside, ta sauke nishin gajiya a hnkli, sbda dukta gaji da tsayuwa tin a falon kafafuwanta sun mata nauyi, itade gabaki daya se a hnkli take jinta. ya karaso shima ya zauna gefen da take yana murmushi, dariya taso ta basa datace wai ya cinye mata budulci, irin shi kmr mayennan. ya rungumota ta baya ya daura kansa a kafadarta yace “Kiyi hkri tinda kince na zubar miki da mutunci again na dawo na cinye Miki budulci Duk ni kadai? to duk kiyi hkri, amma ki tuna auranki fa nayi, lada ma kika samu wlhi mommy, ke ai abin alfaharinki ne tinda kin kawo mutumcinki dakin mijinki naci nasa Albarka, gindin yaji maggi da gishiri wlhi sosai, ke knji wani abu kuwa a cikin gindinki me mugun ddh, gaskiya nide kin gamamin komi mommy, Mijinki nata sa miki albarka…” “Kaine Mijin nawa ?” ta fadi Tana daga kansa a kafadarta ta watso masa wani banzan kallo, ya kuma murmushi yace “bakinki ya bude kou sbda kin ganmu a gidan Aunty hafsat, kibini a hnkli sbda ni Kinsan ba kunyar idon duniya ce Dani ba,,,” “ naji tashi ka tafi pls…” ta fadi Tana kwanciya, ya matsa mata kafarta Daya, ya kawo bakinsa yayi kissing kafar Tata, ya tsure ma kafafuwanta idanuwa azabar kyau kafafuwanta ke masa ya dago ya kalleta yace “ni kike kora?koda kikaga kin dawo gidannan ba tsira kkyi ba a hannuna kike mommy,,,” Ta janye kafafuwanta da yake shafa da hannunsa me lafiya, ta hade rai ta rasa yaza tayi dashi ta huta, shi Sam be gudun abun kunya tace “ka fita a dakinnan pls kar aji shiru Asha wani abu mukeyi ka kara zubarmin da wani mutumcin…” murmushi Aeezad yayi yace “in ansha muna wani abun se me? Look mommy wlhi Ko daddy fa be isa ya hanani in kusanceki ba ko inyi wani abu dake , sbda ubangiji ya halattamin ke…” ya karashe yana kuma Kai hannunsa kan kafarta, ya kuma Kai baki yayi kissing yatsun kafafuwanta zata-zara masu azabar kyau. Nabeelah tayi shiru Tana kallansa kawai, zuwa yanzu ta maida komi kaddara, inta tuna yadda komi ya gudana ma kawai tasan aikin kaddara ne, kuma ita bata isa ta juya kaddarar taba, amma tabbas tasan wannan kaddarar Tata tana tattare da mummunar jarabawa karshen baze kyau ba, musammanma inta tuna da abinda big hajiya tace wai zata gayama daddy. “Dan Allah Aeezad karka bari big hajiya tagayama daddy wannan abun, Ina tsoro…bansan yazanyi da rayuwataba in akaji kwara kawai in tafi kasarmu kafin kowa yaji wannan mgnr, gidanmu kawai nakeso na tafi Aeezad, Dan Allah a maidani gidanmu…” tayi mgnr fuska dauke da alamar damuwa. Aeezad ya hade rai a duniya be kaunar yaji tace zata koma kasarsu. Fuska babu alamar wasa ya kalleta yace “Ina ruwanki in wani yaji? Lefinki ne ko nawa? Kuma in wani yaji kaina mgnr zata kare so ke ba ruwanki nine ke da ruwa da tsak’i nine uban gayyar kuma naji zan dauki komi babu wanda ya isa ya kalleki a kn wannan mgni, ni na miki alqawari, banga wata halittar data isa ta nuna miki yatsa ba in har Ina numfashi…” ta kuma narai-narai da idanuwa tana kallansa harya gama mgnrsa kana tace “Aah nide kawai zan koma kasarmu na hkra da zama a garinku,…” Aeezad ya kuma hade rai yace “wallahi wallahi mommy in kikayi kuskuren barin kasar nan ba izinina zakiga mummunan abinda zan miki, ke ko wajen compound kk fita sena bata miki Rai sosai,,,,” “wlhi sena fita,,,” nabeelah ta fadi cikin subutar baki a zuciya taso tayi mgnr amma seta subuce. Mikewa yayi rai hade sbda ta bata masa rai kuma yasan zata aikata duk abinda tace. “Okay shikenan kiyi wasa da rayuwata ki kasheni ki huta mommy…tinda baki kaunata baki kaunar me kaunata…kiyi duk abinda kkeso…wlhi in kk bar kasar Nan sede ki dawo kiga na mutu har lahira,,” yana gama fadar hknan yayi fice a dakin ta bishi da idanuwa kawai tana jinjina kkmnsa. Ya fito falon ya kalli aunty hafsat ya kalli big hajiya daketa Shan kayan ciye ciyen har yanzu, ta tasa komi gaba. ya kalli Zaks dake zaune, duk suma suka zubo masa idanuwa. Big hajiya ta tabe baki tace “Tabdijan! Ikon Allah , kiri-kiri ana aikata manyan zunubai…ohhh ni y’asu,,ohhh ni jikar mutum biyu, wannan fatsikanci har ina…” Aeezad bebi ta kan me big hajiya tace ba ya kalli Aunty hafsat Cikin tsare gida yace “Kar a bar mommy tadinga aikin komi gaskiya, sbda gaskiya ba yar aiki bace ita,,ko kofar waje kar a barta ta fita” aunty hafsat tace toh. Aeezad yana gama fadar hkn ya nufa kofar fita Zaks ta biyosa a baya. Big hajiya ta dauki sallallami tace “Tabdijan!” Ganin aeezad ze fice a falon big hajiya tace “wannan kayan nawa ne kou? Danni nariga na Zaba wadanda sukamin…” Aeezad ya Riga ya fice a falon dan haka Zaks ne ya juyo yace “Duka ki dauka an baki big hajiya, Ammade mgnr Aeezad da mommy ta zama sirri, da daddare ma zan dawo in kawo miki toshiyar baki…” big hajiya ta washe baki tace “Aiko wannan mgna bame jinta, kamar anyi ruwa an dauke,,ahhh kamar da kasa inji me ciwon Ido, wannan mgna wlhi bame jinta zakariyya, anjima kudi zaka kawomin kou?” Zaks yace “kudade masu yawa ma…sena dawo anjiman…” Zaks yama aunty hafsat sallahma kana ya fice a falon, big hajiya tashiga murna ta tashi ta kira masu aiki tace su kwashe komi sukai dakinta Aiko suka kwashe suka Kai dakinta big hajiya ta koma dakin ta zauna tanata kara dudduba kayan Tana murna, big hajiya nada tsananin San zuciya, Kai kace bata taba ganin kudi ba a rayuwarta, tanada mugun kwad’ayi ko kisan Kai akayi a gabanta inde aka bata kudi zatayi shiru.

Zaks yaja motar suka fice a gidan ya kalli Aeezad dake gaban motar yayi bending, duk jikinsa ya masa wani iri kewarta ta rufesa, Sam be iya fushi da ita komi zata masa, ji yakeyi kmr ya koma ya zauna gidan shima yayita kallanta, yariga yayi mugun sabo da ita a sati dayan dasukayi tare, ko zata dinga zaginsa Tana dukansa shi yana santa a haka kuma yanasan zama da ita. “ wani gida zamuje ?” Zaks ya tambayi Aeezad din, ba tare daya kallesa ba yace “Kaini gidana kawai, inaso doctor ya dubamin hannuna…” “zafi yake maka?” Zaks ya tambayesa “aah,,,ba Ayimin allurata ta safe ba ai…” Zaks yace “Okay inaga shiyasa doctor keta kirana se yanzu naga miss call…” ba tare da Aeezad ya kara cewa komi ba har suka isa gidansa, a packing space yaga motar naeema shi yana manta da ita se yanzu daya ga motar, tin randa tabar gidan taje gidan mommy sukaje gun boka a kan a musu aiki nabeelah tabar gidan boka yace an gama a bashi nan da 2weeks duk abinda ake ciki ze kirasu. Zaks nayin packing Aeezad ya fita a motar. Zaks ya karasa packing din motar ya fito yabi aeezad daya nufa falonsa,. “Ba abinda kake bukata inaso in tafi gida ne…” Zaks yayi mgnr da Aeezad bayan sun iso falon, shirin hayewa upstairs ma Aeezad yake, sbda so yakeyi yayi wanka ya kwanta ya huta. “Kaje ka dawo zuwa anjima after la’asar ko after magrib sbda zaka kaini inga mommy…” Aeezad yayi mgnr byn ya taka matattala hudu, ya juyo ya fuskanci Zaks din. Fuska dauke da mamaki Zaks yace “Wace mommy?” Aeezad ya watsa masa wani kallo yace “wacce kasani…” Zaks yace “naga yanzu muka dawo daga gurinta, ka barta ta huta pls aboki, kodan sbda big hajiya tasa ido…” “Ina ruwana da idon datasa ba abinda ya dameni ko hanci tasa wlhi bata isa ta hanani naje gun matata ba, Kai in duk duniya zasu taru basu iya su hanani zuwa ga mommy ba,,,” Cewar Aeezad. Zaks yaja bakinsa yayi shiru Aeezad ya haye matattakalar yana fadin “ka gayama doctor yazo ya jirani a falo, inyi wanka da sallah, se in fito yayimin allura…” Zaks yace toh, ya juya ya bar falon, ya nufa side din da doctor haphis yake ya isar da sako kana yaja motarsa yabar gidan. bajimawa Aeezad yayi wankan ya fito duk jikinsa ba ddh kmr an zare masa laka, ya shirya cikin kananun kaya marasa nauyi riga da wando iya guiwa kalar sky blue, yayi sallar azahar kana ya sakko falon kasa inda tini doctor ke jiransa hannunsa rike da charbi yana lazimi se zuba kamshi yakeyi, fuskannan tasa tayi fayau da ita. doctor ya gaidasa ya amsa, ya zauna kan kujerar 3ctr doctor ya duba hannun ya masa allura a baya ya koma ya kwanta kan kujerar 3ctr din idanuwansa na kan TV Amma zuciyarsa na kan mommy, da yanzu suna tare, tunawa yashiga jiya war haka yana tare da ita. “Ubangijine ya jarabceni da wannan azababben SON..” Aeezad ya fadi a ransa. doctor ya masa Allah sawake Sam be amsa ba sbda bejisaba, yanacan duniyar tunanin mommy. ftini doctor ya fice a falon da kayan aikinsa a hannu, a farfajiyar gidan yaga Hajiya naeema wadda ke tafe cikin isa sanye take da jallabiya nude color skin dinta na hutu se walwali yakeyi. Doctor haphis ya gaidata sbda yasan itace matar Aeezad din, sama sama ta amsa ta nufa part din Aeezad shi kuma doctor ya nufa part din da aka basa, yana tafe yana mamakin halin naeema tin tini in yana gaidata seta dinga amsawa da kyar, tin zuwansa gidan da 2days yaganta a gidan, wato ranar dasukaje gun bokan gidan hajiya mommy ta kwana har kwanaki biyu, tana gidan Alhaji sunusi ya gaya mata Aeezad ya kebance kansa sbda Yana bukatar hutu, Sam na’eema bata yadda da hutun da yaje yiba sbda baya daukar wayarta, Kuma gaskiya ba hk yake mata ba, ko a Wani hali yake yana daukar wayarta, daman ta tabajin kishin-kishin mijinta ya taba ajiye karuwa to Tasha gun karuwar yaje yanzu ma, Amma tayi shiru da bakinta seta tabbatar seta gayama hajiya mommy a dauki mataki, gabaki daya ma ya chanza mata, dace ada ne inya ganta jikinsa har rawa yakeyi yacita, Amma yanzu shiru,. Ta window dinta taga dawowarsa gidan yanzu.

Ayi hkri da typing error.

 

No comments