Breaking News

Ni da Almajirina 10


NI DA ALMAJIRINA
(Our Incomplete Story)

Episode 10

Don Allah Baana…. Maganar ya tsaya cak, gani yayo kaina, duk ilahirin jiki na ya fara rawa, tsabar tsorata da nayi da lamarin, gimtse idona nayi ina karanto addua da nema kariya daga gun sa.
Jin anyi shuru kuma ba a tabani ba yasa na bude idanuwana na gansa a sama na, hanayen sa ne kawai a samar gado kamar wanda zeyi press up.

Ganin yana matso da fuskar sa daf dana wa yasa nayi saurin rufe idona,numfashi sa sai yawo yake a fuska ta,mun dauki kusan minti biyu a haka kafin yace

Ya zanyi ki so ni?
Wacce hanya zan bi ki so ni?
Soyayyar ki tana illata ni Falmata, na rasa yan da zanyi da zuciya ta Falmata?

Tunawa da shawarar HajjahKaka yasa na bude baki cikin taushin mirya nace ban taba Soyayya ba kuma ban san ya akeyin ta ba,amma nasan da “So da Tsoro” basa tafiya gu daya, idan kana so na fara son ka, ka cire tsoron ka a zuciya ta. Nayi maganar ina fargaba abinda zai ce.

Janye jikin sa yayi kafin ya zauna a gefen gado rike da Kansa sai da ya dauki sakwani kafin ya dago da jajjayen idonsa ya daura su a fuska ta, nayi saurin sunkuyar da kaina zuciya ta na dukan uku uku.

Kin ci abinci? Yayi maganar yana kallona.

Idan na tuna da cewa NI DA ALMAJIRINA ne zaune haka yana min maganar da issa sai naji kamar na saka kuka dan bakin ciki, amma naga kamar shawarar HajjahKaka ze yi tasiri akan sa.

Je kiyi wanka ki zo ki ci abinci sai kisha magani yayi maganar sai kace wani ubana.

Jiki a sanyayye na mike ina tsoro nace ina ne toilet din sanan idan nayi wanka wani kaya zan saka? Nayi maganar ina satar kallon sa, shima kallo na ya keyi, can yace za a kawo miki, akwai duk wani abinda zaki bukata cikin toilet.

Kamar wacce kwai ta fashewa a ciki haka na dinga tafiya har na isa toilet din, abin mamaki well furnished toilet kome ya na ciki, wai ya akayi sukai gida nan? Su waye ma’aikatan da suka gina wannan gun? Dan structure gini sai kwararun architectures
Da wannan tunanin na fara wanka inayi ina tsoro har nagama, na bude wardrobe naga everything there is new pant and semitary pad na dauko na tofe da addua kafin na shirya, amma naki fito wa..

Bayan kamar minti biyar naji alamar za a shigo, na rikice nayi saurin dauka kayan dazun zan mayar dan towel ne a jikina.

Mi kamin kayan without looking at me kafin yana mikamin ya fice, jikina bari nayi addua kafin na saka kayan na fito idan na sama yana waya on speaker

Ya Amir yace na samu labarin cewa yau ka zama Namiji, gara da kabi umurni na, da ace ka bijire min da tuni na aikata barzahu, Baana yana gani na fito ya cire wayar a speaker kafin ya ba shi amsa da godiya nake Ya Amir. Umurni ka shine zabi na, kaine ubana kuma kaine uwata.
Dariyan manya Ya Amir yayi kafin yace shi yasa nafi son ka duk aciki, aci amarci lafiya sai na dawo, yana fadin haka ya yanke kiran..

Ki zo ki zauna ga abinci yayi maganar without looking at me.

HajjahKaka fa? Please I need her besides me.

Wani kallo yayi min da nayi saurin zuwa na zauna idan abinci yake, na soma ci banda ina jin dadin abinci ba.

Sai gobe zaki ga HajjahKaka yayi maganar da izza kamar wani sarkin gaske, kwanciya yayi sama gado fuskar sa na kallon sama

Ni duk na kosa ya saka kaya, ganin sa haka kade abin tsoro ne, amma shi ko a jikin sa.

“Idan kin gama ci ki zo nan.”

Cike da tsoro da abinda yace na cigaba da tura abinci a hankali hawaye na zuba, ganin ban da niyyar barin abinci yasa ya sauko kasa nayi saurin mikewa ina hawaye.

Duk taku dayan da yayi kara firgicewa na keyi,dan gani na keyi kamar wani mugun abu zai min, kawai ji na nayi kwance a kirjinsa basan ya hakan ya faru ba.

Don Allah Baana kayi hakuri kar ka cutar dani, nayi maganar ina kuka ganin gado muka nufa.

Baice dani kome ba harsai da ya kwantar dani samar gado kamar wata jaririya, ni tsoron sa ya hanani afanin da abinda HajjahKaka tace, hakan nan kawai ina matsifar tsoran sa.

Kwanciya yayi gefe na, hade da janyo ni zuwa jikin sa, ba abin da zuciya ta keyi sai pounding nasan shima kansa yana jin yadda zuciya ta keyi.

Daura bakin sa yayi samar kunne na kafin yace ki so ni don Allah ko zuciya ta zata samu sukuni ban san menene son iyaye ba Falmata, daga Ya Amir sai ku, ku ne gata na
Don Allah ki so ni. Yayi maganar kamar me kuka

Ni da tsoro ya hanani ko motsi sai sauke ajiyan zuciya na keyi, ganin ya dago da fuska ta, na sake runtse ido hawaye na sauka, daura bakin sa yayi samar nawa amma sam na kasa motsi kamar wata gawa haka na zama. Tunawa da cewa ALMAJIRANA ke min haka yasa nayi karfin halin janye jikina daga gare shi jikina na bari, amma hakan be hanani bude baki nace idan wannan abin shi ze sa na so ka? To bazan taba sonka ba. Jikina ya haramta a gareka kayi gaggawan barin daki nan na karasa maganar da tsawa.

Murmushi Baana yayi ganin the arrogance is still there. Ba tare da yace kome ba ya sake yinkurin kai ba kinsa

Ba tare da tabbacin zan iya marin sa na wanke fuskar da mari. Sannan nace matsayin ka ya nan a matsayin ALMAJIRANA don haka karka sake tabani nayi maganar cikin amon mirya.

Mamaki kamar ya kashe Baana amma kiran sa da Almajiri ya sa ya hassala,
Ko ki so ni ko karki so ni jikin ki ruhi ki nawa ne, da ina bin ki a hankali amma tunda haka kike so zan bi dake ta haka yana fadin haka ya danne ni samar gado,

Ganin da gaske wani abu zai min nayi saurin cewa kayi hakuri HajjahKaka tace na dinga yin maka haka zaka dena zuwa kusa dani duk da maganar can ciki ne amma yaji.

Saurin janye jikin sa yayi, yana me murmushi kafin yace HajjahKaka kenan, can ya mike ya nufa toilet

Sai mayar da numfashi na keyi ganin na tsira, da shikenan yau gawata za a dauka.
Ina zaune sai raraba idanu nake har barci barawo ya sace ni saide duk minti goma sai nafarka a firgice.

Baana yana gama wanka ya shirya ya fita gun jama’ar sa, bin ko wani point yayi to make sure kome na tafiya yadda kamata
Bayan ya gama za gaye ya nufa inda kame(prisoners) suke, carab idonsa ya sauka kan Ummu Altine dake fama rawan sanyi tsabar wahala da suka sha wajan tahowa a kafa da suka yi, kamar ance ta dago kawai tai ido hudu da Baana da farko ta dauka Zazzabi ne amma da ta sake kallon sa taga shine cikin miryan da baya fita tace

“Baana….?

Murmushi Baana yayi wanda shi ka dai yasan fassara murmushin sa.

Altine ta sake kiran sunan sa cike da mamakin ganin sa, Baana kaine koko gizau kake min?

Baana shiru yayi yana kallon ta kuma baida niyyar bata amsa

Can Altine tace nasan Baana ya dade da mutuwa a hatsarin mota, to kai waye?

Cikin daci Baana yace wannan dan shekara hudu da aka tura duniya kasancewa mahaifiyar sa ba ta raye shine yau tsaye gaban ki. Yana fadin haka ya juya zai tafi, yaji tace Baana daman kana raye? Ba tare da ya bata amsa ba yay wucewar sa. Idan akwai mutum da yake so ya fare kashewa da hannun sa to itace wannan matar.

Washe Gari
Sai shidan safe na farka a firgice ina lalube lalube, ganin ni daya ne yasa na mike da sauri na nufa idan toilet yake, nayi abin da zanyi na fito.

Ina zaune da misalin karfe takwas ya shigo dakin fuskar sa ba annuri sam, taso muje yana fadin haka ya juya nima na mike na bi bayan sa, wani daki muka nufa acikin gun,

Ganin HajjahKaka nayi tana zaune kasa ana shan kamoniya da Borno’s tea, tana hango mu tayi saurin ajiye abinci tana matse kwalla.

Da ace banyi masa bori ba nima na nuna masa ni jan wiya ce ai da bai kawo min ke ba,
To miye kika yi tsaye kina kallona ko anyi miki abin manya ne yasa kika wani tsaya kikam kina kallona, HajjahKaka tayi maganar tana goge bakin ta da zanin ta

A guje na karaso wurin ta, na rugume ta kamar wadda mukai shekara bamu ga juna ba.

Aah gaskiya bazan iya jure wannan warin gawasa da kike yi ba, dan haka kidan ja da baya kar abinda naci su dawo min, HajjahKaka tayi maganar tana kawar da fuska.

Dariyan da Baana be shirya yi ba shi yayi, can yace ki shirya nan da wata tara zaki ga jika.

Wani mugun kallo tabi sa dashi hade da kunduma masa ashar, uwar jika zan gani ba jika ba, kai Baana dan babu tsoron Allah a ranka kake fadin wannan zunubin a bakin ka..?

Murmushi Baana yayi kafin yace zuwa dare zan zo na dauki matata yana fadin haka ya fice.

Sakin baki da hanci tayi tana kallon sa har ya fice, can tace mike na ganki, HajjahKaka tayi maganar tana ya mutse fuska

Mikewa nayi ina kallon yadda take kallona kamar me kallo har hanji

Can tace yo hauka ma akeyi na yarda da yazo miki? Ai wannan tokareren kato ko matan da suka shahara a duniyanci yaje masu ai sai sunyi sati suna jinya balle ke da kamar a hura ta fadi, kin ga maza masu tsiyeyen duwawai abinsu yafi karfin yara irin ku,HajjahKaka tayi maganar tana bina da gefe ido.

HajjahKaka shawarar ki sam ba tayi aiki ba saura kadan da na mutu jiya,nan take na bata labarin abin da ya faru.

Yo ba dole ya kusa murkushe ki ba Falmata? In ban da abin ki wa ya ake ki dau hannun ki mare sa? Inda kin bi yadda nace da yanzu ba kya warin gawasan nan da kike yi, inhar kina so mu zauna gu daya dake maza kije kiyi wanka kuma ki shafa kwalachum sanan ki canza kaya.

To ni ina zan ga kaya balle wani turare eh? Nayi maganar ina turo baki

HajjahKaka kallon na take yi baki hangame can tace in baki dauki shawarar ta ba Allah sai kin yabawa aya zakin ta,kin ga maza masu tsiyeyen duwawai bindiga aikin su yafi karfin yara irin ku Walhi wannan yaron buju buju zeyi dake, kinga wannan bushashiyar cinyonyin ki kamar an soya cinyar fara, to sai sun noke sabida wannan tokareren dogon
Yanzu daman haka kika je kina masa daman? HajjahKaka tayi maganar tana rike da haba

Cikin jin haushi nace to me nayi kuma eh?

HajjahKaka tace uwarki kika yi, ke da nace ki zama jan wiya a gaban sa sai kije kina shagwaba? Yo dole ki zo min da warin Gawasa…..

 

Pharteema(DMK)
THANKS

No comments