Breaking News

Ni da Almajirina 12


NI DA ALMAJIRINA
(Our Incomplete Story)

Episode 12

A yau zaki san ni waye ne, kuma da matsayina, yana gama fadin haka kawai ya dauke ni ya cilla ni samar bed, duk yadda nakai da kokarin kokowa niman kubta daga hanun sa,karshe de kuka da hakuri na dinga badawa amma yayi kamar baya jina, abin da yasa a gaba shi kawai yake kokarin..

Ban san lokacin da nafara rokon Allah da ya dauki rayuwa ta ba,dan bana taba tunanin zan iya rayuwa da wannan trauma indai hakan ta faru.

Baana kam toshe da rufe duk wani kofa na tausayin ta yayi, dan yana tunanin duk jiran da zeyi baza ta taba kallon sa a matsayin mijinta ba,wannan kadai zai sa ta yarda da iko da matsayin sa a kanta.

Tun ina iya babbanta fitar numfashi na da bugun zuciya ta har yakai da ban iyawa, amma nasan tabbas mutuwa zanyi, ga shi ban gana da mahaifina ba,zan bar duniyaa.
Idanuwa bude amma ina tunanin duk wani gabobi na jikina duk sun fita,bana tunanin ina da baki dan yin kuka da nema taimako..

Wani dogon numfashi naja kafin na fito dashi a hankali, a hankali nafara bude idanuwa na da suka min nauyi,a tunani na zan tsince kaina cikin kabari sai na gani cikin bahon wanka, kuma ga babban makiyi na tsaye gabana fuskar sa ba annuri..

Dukawa yayi kusa da bahon wanka, yana kare min kallo, can kuma yace ,’now you know who i’m to you.’
2days in coma kadai ya isa ki san matsayina ya fi karfin kazamin ALMAJIRIN KI.

Yana gama fadin haka ya karasa min wanka, ina ji ina ganin amma ba bakin magana, kamar yadda uwa zata shirya danta haka ya shirya ni, ya mayar dani daki. Sannan ya zubo min tea da kamoniya, da ido yayi instructing na, na bude bakina yana feeding na,ban da hawaye ba abin da na keyi harna gama cin abinci. Sannan ya banj pain reliever na sha.

Zaki iya rama salolin ki a zaune idan kina so,yayi maganar yana sanya min hijab. Ya gyara salaya ya ajiye ni akai.kafin ya koma gefen gado ya zauna,
Daukar waya yayi ya kara a kunnen sa.. Ya Amir barka da warhaka,asake min uzuri bazan samu zuwa taron, har yanzu bata da lafiya.

Ya Amir dake dayan bangare wayar yace, naga aiki na kokarin komawa baya sabida wannan yarinyar Auta?anya aikin zai yu a haka?

Baana yace Ya Amir da ta samu lafiya zan koma bakin aikina, sai nayi aikin fiye da wanda akayi a baya, please just this favor sir.

Duk da ainihin yaren kanuri su keyi hakan be hanani fahimta abinda suke cewa ba.

BAYAN SATI DAYA

Ina kwance in banda hawaye ba abin da nake yi tun lokacin da abin nan yafaru, i just can’t believe cewa shikenan nawa ta kare, ALMAJIRANA yayi min haka da gatana da kome?kamar kulum addua nake Allah da yabin min hakkna, dangi mahaifiyata sun cutar dani ta yadda ba abin da zance illa Allah ya isa. Daga shi harsu bazan taba yafe masu ba. Ina cikin haka ya shigo dakin da salama, daman tunda abinan ya faru ban bude baki nayi magana ba, haka zai ta magana shi daya.

Yau zan mayar dake dakin HajjahKaka sabiida zan yi tafiya sati daya. Yayi maganar yana kallona .

Ina jin ya fadi haka na mike daga kwance da nake, cikin mirya da baya fita nace Allah yasa in ka tafi can gawarka za adawo dashi a wulaqance, bama su maka sallah balle Allah ya yafe maka
Bazan daina addua nima hakkina gun Allah ba harsai ranan dana ga gawarka.

Murmushi yayi kafin yace ba abin da zai same ni matata indai kina a raye, do you know what?you’re the most sweetest thing that life could give in this duniya, ko na mutu ayau zan tafi da farin ciki cewa nayi ajiya a inda yafi kome tsada da mahammacin agare ni.

Yinkurin sake magana zanyi ya exlaiming lips na, ba karfin kokowa balle kwace kaina, sai da ya dauki 30mins yana abin da yake so kafin ya mike..

Hawayen bakin ciki kawai ke zuba daga idanuwa na.wai ALAMAJIRANA kemin wannan ba tare da ganin girma da kima na ?

Zaki canza kaya koko zaki je mata da warin Gawasa Baana yayi maganar yana me shu’umin murmushi.

Mayar da rigan nayi ina kokarin tsayar da hawaye na, dasu kasa tsayawa.

Cikin zolaya yace zaki iya tafiya ko na dauke ki?

A fusace na sauka daga gadon, na nufi hanyar fita, naji yace

Tsaya kar abin yayi wa HajjahKaka yawa, yayi maganar ya jamin zip riga hade da mikamin hijab.

Atare muka jera zuwa dakin HajjahKaka tana ganin mu tace

Alhamdulillah jikata tana raye, harda share kwalla na farincikin ganina.
Ya haka naga kinyi coko coko kina kallona? Ga warin gawasa duk ya cika min daki,can kuma ta tsaya tana kallona kamar me son gano wani abu, Yaushe kika samu tsokar baki Falmata? Ke da bakin ki kamar tsutsa,Kar de ace dukan ki ya keyi har ya kumbura miki baki? Ganin bance kome ba yasa tace to Tokareren kato me kayi wa jikata ta koma haka ?

Da saurin karfina na karasa wurinta a guje,sai yanzu na samu damar fashewa da kuka mai cin rai,inama Allah ya dauki raina yanzu HajjahKaka ?nayi maganar ina kuka kamar raina ze fita

Ke wai akan wannan bakinkirin kamar duwaiwai tojo shine kike kiran mutuwa? To munafiki ubanwa kake kallo haka? Can kuma ta mayar da hankalin ta kaina da nake fama kuka kamar wacce aka aiko da sakon mutuwar mahaifinta.

Ke mike na ganki da kyau, HajjahKaka tayi cikin matsifa, kamar yadda tace haka na mike , salati ta farayi tana kare min kallo kafin ta mayar da duban ta zuwa..

Pharteema(DMK)
THANKS

No comments