Breaking News

Ni da Almajirina 19


NI DA ALMAJIRINA
(Our Incomplete Story)

Episode 19

ASSALAMU ALAIKUM TEAM GAWASA, TEAM FALMATA DA TEAM HAJJAHKAKA INA MIKO DUBIN GODIYA GA MASOYAN WANNAN LITAFI
AT FIRST I WAS SCARED BAZA AMSHI LABARIN BA SAI GASHI KUN SAMACE NI DA SPIRIYENS KUNA BIN LABARIN HARMA DA BANI KWARIN GWIWA DA SHAWARWARI BA ABINDA ZANCE SAI GODIYA 殺

This page is dedicated to Yar baiwa tawa (SHAFAATUBAWA) 殺

Hold it there,i don’t wanto hear any trash coming from you. Ka matsamin na fita,ina gama fadin haka kawai na yanke jiki na fadi..

Bude idanuwa na dasu ka yimin nauyi na daura su kan Hajjahkaka dake hakkince zaune wheelchair .

Kokarin mikewa na ke son yi naji cikina ya murda na koma na kwanta.

Ina cewa karki mike saida kika mike ? So kike kija mana wani jagwal ?

Sai yanzu na hango cannular dake yatsa ta, na ga I’m on drip.

Bude kofar akayi ina kallon sa naji wani kahon tsanar sa ya cake ni. Nayi saurin cire idona daga kallon sa.

Baanaliye to Al hamdulillah ba wata tangarda ko ? Hajjahkaka tayi maganar tana kallon sa

Cikin taushin mirya yace eh Hajjahkaka, but we’ve to be cautious about it.

Wai Baanaliye ke zuba yaren nassara kai kace jakin kano ne ?wai yanzu duk me matsensa duwaiwai nan ya koya maku?ranan harda larabci naji kayi ?

Cike da jin haushin su nace Hajjahkaka don Allah kaina na ciwo kuma surutun ku na kara min ciwon kai .

Hajjahkaka tace sannu Falmata ko ?a ba lefin ki bane lefin mu ne da muka dinga sharba kuka daga ni harshi bame lalashin wani acikin mu,yanzu kin farfado shine zaki saka mana da tsiya?

To Hajjahkaka kice masa ya fita banso ganin sa, nayi maganar kamar zanyi kuka.

Jiya da kika bi dadi miji baki san baki son ganin sa ba ? Sai yanzu to ni a waye nike kuma ina da spiriyens ato ba zaki mayar dani wata Dodi minal Dodi ba ehe.

Baana yace Hajjahkaka bara mu bari ta kara hutawa by then ruwan ya kare, kince kina son cin soyayen zabi ko?

Hajjahkaka tace eh Baanaliye tayi maganar tana goge baki ta da gefen zani.

Hajjahkaka to mu koma dakin ki yayi maganar heading towards the door , Hajjahkaka ta kunna keken ta tabi bayan sa.

Suna fita na saka kuka,ina ma ace zan mutu yanzu dana fi kowa jin dadi,duniyar gaba daya ta isheni. Allah ka kubtar damu daga hannun wannan azulume mutane,Allah kayi mana maganin su,especially Almajirina.

Cikin Garin Maiduguri

Sojoji ne birjik kamar za aje yaki,idan kana tafiya a titi zaka checking points bila adadin, kowa yanzu A ankare suke..

Journalist Binta kam aiki ba dare ba rana, aiki biyu ta keyi yanzu , da aikin gwamnati da aikin dan barazana da ake mata da rayunwata.

Yau ta dawo daga aiki a gajiye ko zama ba tayi ba kiran Ya Amir ya shigo wayar ta, a firgice ta dauki wayar jiki na dari dari.

Zamu farmak wani makaranta mata, da zaran mubar wurin zamu bar miki shedar daukar rohotu, yana gama fadin haka ya yanke kira, hankali tashe ta fara salati , dan akwai yan uwanta da yawa da suke makaranta mata zallah,
Baci da ba tayi ba ranan kenan, wuni tayi tana kiran mijinta wanda ya kasance commissioner of police ne , amma sam be daga ba , tana rugume da ya’yanta biyu har garin Allah ya waye, tana ji tana gani amma ba bakin magana.

Wani shahararen makaranta gwamnati ne, wanda yau ya kasance “PRICE AND GIVING DAY ” Na makaranta iyaye da yaran su duk sun hallara wajan wannan taro, saide ko rabi da kwata na taron ba ayi ba, aka fara jin karan bindigogi, kamar kyabtarwa ido, gawawaki ne jibge a kasa, kuma sun diba na diba,sai bayan sun gama sojoji suka iso wurin,tare da Binta…

Ba abin da kake ji sai kururuwa da ambato yesu daga bakin iyayen yaran da akayi gaba dasu.

Cikin hanzari akai demacar ting wuri amma haka be hana Binta going live on TV.

Acikin iyayen yammata da akai gaba dasu ne, Binta ta samu damar tattaunawa da wani mahaifin daya daga ciki.

Baba ya sunan ka kuma me alakar ka da wannan makaranta ? Binta tayi maganar tana daura masa mic.

Ni sunana Thomas Garba, ni mahaifin ga Abigail ne kuma miji ga wannan matar ya nuna wata mata dake kwance cikin jini, yana kuka..

To Baba ko zaka iya gaya mana abin da ya faru?

Ni manomi kifi ne, gonar na beda nisa da makaranta, tun lokacin da Abigail ta zama budurwa na so na aurar da ita a bisa al ‘adar mu, amma Sairah ta dage wai sai yarmu ta samu karatun zamani, dan tana so yarta ta zama likita, sabida wannan daliline bana zuwa duk wani abu da ya shafe makaranta ta , har wannan abin ya faru , hade hannun sa biyu yayi yana kuka yace gwamnati kuyi kokari ku dawo mana da yaranmu Abigail kadai nake dashi.

Cike da tausayawa Binta tace in shaa yaranku zasu dawo cikin kwanciyar hankali, wannan gwamnati tana iyakaci bakin ta.

Kafin ka sanin the news is all over the world especially da aka ce girls school ne kuma mafi yawan su ba muslimai bane yakara jawo cecekuce a kasar kan cewa muslimai na son mayar da kasar ta zama ta muslimai.

Bayan sati biyu

Ya Amir ya saki video inda yake cewa aikin Allah su keyi kuma baza su dena ba.
Don haka arufe duk wani makarantu dake Nigeria ba abin da ake koyar a makarantu face boutan gumaka da iskanci, kuma yayi alkwarin muslintar da yammata da aka kwasa fisabilillah.
Yana gama fadin haka ya yanke video.

A ranan da aka deba yan makaranta first lady ta iso garin hankali tashe, tare da ita da wasu iyayen yaran suka dinga jimami.

A kankani lokaci gidan TV THE DAILY NEWS ta habka sabida sune no1 publishers masu kawo rohotu live and rubuce.

Fadar Ya Amir

Yanzu sam baya zuwa inda nake, dan da yazo na dinga kuka kenan,abinci na dena ci kamar da , ga yunwa ta adaba ta, amma taurin kaina ba ya bari na naci kamar yadda nake so , ni kawai fatan be wuce na mutu ba yanzu.

Hajjahkaka ce ta shigo dakin ta sama ko bude warmers din banyi ba .

Kai wannan yarinya da mugun hali kike,ki dubi yadda kika tsiyayye ki ka tsotse kamar a matse an tsotse lemo? yanzu dan mugun hali cikin naki kike ma mugunta? Hajjahkaka tayi maganar tana kallona?

Ni nagaji ni so nake na mutu.

Kwabe min baki Hajjahkaka tayi kafin tace , har yau de kanki ba spiriyens kina nan a Dodi minal Dodi, yanzu duk shawarwari da na baki akan yanda za muyi mubar wajen nan kiyin watsi dashi ?

Cikin kuka nace nifa bazan iya soyayyar karya da fasiki kuma kazami kamar wannan bakin ba .

Tabe baki Hajjahkaka tayi kafin tace to a gidan ubanwa Baanaliye ya zama fasiki? Ni tunda nake da Baanaliye ban taba jin yana warin gawasa ba, saida ya aure ki.

Rai bace nace da yake zuwa yana raping yara kin sani ne ?

Yaushe ya fara zuwa rafi kuma Falmata ? Kina numfi kin bude da har zaki kira kanti patarin ki da rafi?

Rai bace nace Hajjahkaka sauran yammata da ya bata nike nufi.

Kai wannan y’a akwai ki da bakin kishi, to Baanaliye be san wata ba sai ke, akan ki ya fara aikin manya idan baki sanin ba ki sanin yau waccan yarinya bashi yayi mata abin manya ba,.maza biyu ne suka murkushe ta,kin sansa da tausayi shine ya kawo ta na duba ta , to ke idan akace maki Baanaliye ne yayi wannan abin sai ki yarda?

Shiru nayi ina kallon ta kamar ina kokarin gano gaskiyar lamarin.

To kece de matar sa ta sunnah kuma ke daya ce kwal acikin ransa idan zaki dauki spiriyens na,da yanzu mun dade da barin wannan waje amma ke kinki bada hadin kai.

To zan gwada yin haka amma ya dena min magana da iko dani ba yarsa bace.

Ke wai Falmata baki jin tsoron wannan murdaden katon ne me kiran samudawa ? Kin ganki kuwa yar tsul a gaban sa? Dani ne ke shafa ma kaina lafiya zan yi mu rabu cikin lafiya, ke wannan me tsiyayyan duwaiwai yace zai miki dagaske walh ba zaki kai labari ba, dan de yana sonki ne ya shafa maki warin gawasa a hankalce.

Tunawa nayi da jinya da nayi ban san lokacin da nace a hakan Hajjahkaka ?

Kwarai dagaske kuwa Falmata aini har kin samace ni, ai ban taba zata ma zaki iya daukar wannan narkanka kato ba .

Hajjahkak zan ci pizza hut da meatballs.

Ware ido Hajjahkaka tayi kafin tace saide ki gaya me dani bama san me kike cewa ba, danna bell inta tayi sai gashi a dakin sai kallona ya keyi kamar ya hadiye ni.

Rai bace nace pizza and meatballs, inason oreo chocolate da pure milk.

Cikin murna yace is that all ?

Harara na watsa masa, kafin ya bar dakin.

Bude warmers Hajjahkaka tayi ta dibo soyayyen dankali turawa da kamoniya ta fara warfa tana ta zuba har tayi nak kafin tace to bara na koma can dan dauriya kawai nake yi, dan haryanzu ba dena warin gawasa kika dena ba.

Balla mata harara nayi.

Kin harari uban ki musa , nace kin harari wannan me tokobin hanci da burmamen baki Musa .

Rai bace nace goodnight .

Yar jaraba kawai, tudan akayi miki abin manya kika zama mara kunya, to ki kiyayeni kar nai miki baki kiyi cikin yan hudu walh, Hajjahkakka ta inda ta ke shiga bata nan take fita ba , har na gaji na sauko daga gadon zan nufa toilet.

Sakin baki Hajjahkaka tayi tace Falmata me zan gani haka? Nonuka kine suka koma luka luka dasu haka?

Turo baki nayi nace to baki san inza ga bakon watana haka suke komawa ba ?

To saka rigan mama idan bahaka ba walh yana ganin su a tsaye haka kamar zasu fasso daga riga da matsala Falmata ba barin su zeyi ba.

Uhmm ni ciwo suke min idan na saka nayi maganar ina shigewa toilet.

Chab to wannan yaro ba barin min jika zeyi ta sarara ba, to inama ze iya kallo ya kyale gasu luka luka dasu gashi tayi shadaudau da ita, to nide bazan jure warin gawasa ba tana cikin maganar Baana ya shigo.
Daure fuska tayi tana binsa da mugun kallo

Hajjahkaka lafiya?

To ka bita a hankali yarinya ce kuma bata da spiriyens bawai ka ta cin zalinta ba, tayi maganar tana kicin kicin da fuska.

Mika mata leda har biyu yayi, ta amsa ta bude ganin su kayan makulashe yasa ta saki ranta, ai idan ciki nan wanan watani ba abinda mace take so kamar dumin mijinta Baanaliye amma banda aikin manya ato nide ka ga tafiya ta.

Dariya Baana yayi yana girgiza kai.

Can na fito fuska daure, yana ganin na ya sauke kansa kasa
Hajjahna gashi,

Kwalin pizza family sizes guda hudu da sauran abubuwan dana bukata.

Zama nayi na fara cin abinda zanci, dana dago sai naga idonsa akaina nace maye sai ka cinye ni to .

Murmushi yayi yace how i wish i can dana cinye ki wanda ba me sake ganin ki sai ni,

Mtchews psychopath nayi maganar ina cigaba da cin abu na.

Ganin idonsa samar kirjina nace miye nayi maganar cikin tsawa..?

Babu kome Hajjahna ko zaki saka riga sanyi dan naga da sanyi sabida ruwan sama da akayi.

Idan ina jin sanyi kaine zaka fada min ?ina sha jikina ne ba naka ba ?don haka matsa min daga gani na.

Komawa gefe yayi yana ta kallona harna gama cin wanda zanci, bayan na huta na koma toilet na daurayo bakina na dawo na zauna
Kiramin Faruq ina so na ganshi.

To Hajjahna yayi maganar yana murmushi kafin ya ciro wayar sa, ya kira Faruq facetime,

Faruq na ganin kiran ya saka key a dakin sa, cike da murna yace my Uncle B good morning wheres Bigsis

Morning my chumchum she’s here yayi maganar yana mikamin wayar.

Sister Uncle B yace min soon zaki dawo kuma tare zaku dawo.

Murmushi nayi nace in shaa Allah baby , how is daddy ?

He’s doing fine amma yanzu ya dena damuwa coz yasan zaki dawo soon

Who told him that I’m coming soon?

He did, he promised to bring you back to us.

Cike da mamaki nake kallon sa kafin nace in shaa Allah baby, ka cigaba da zama good boy ok ?

In shaa Allah Sis, i love you

And i love you to the back and moon my pal .

Yace bye, nima nace bye kafin yayi ending call din, na juyo with a straight face nace who are you? Dawowa ta bayana ya zauna sannan yayi hugging ina hannun sa zagaye kan kirjina, buga hannun sa nayi, na juyo ina kallon sa nace WAYE KAI ?

Daura bakin sa gefen wiya ta yayi ba tare da yace kome ba yayi shuru, ya kara maido da hannun sa gun. Giving it a slightly massage.

Kokarin cire hannun nasa na fara yi, ganin yaki cirewa nace
Is it me you want or my body?

Jin tambaya yazo masa a bazata ya dakatar da abinda ya keyi, ya juyo dani fuskar mu na kallon juna.

Maimata tambayar ki, yayi maganar yana kallona, ba tare da shakkar sa ba na maimaita tambaya.

Idan da jikin nake so bazan taba auren ki, kuma da na dade da samun jikin ki, da so mutumin ne tabbas da sai ya maka ki a kotu na irin azabtar dani da kikeyi da soyayyar ki Hajjahna.

Ya mutse fuska nayi kafin na sake tamabayar sa a karo na biyu

“Waye KAI ?

 

 

Pharteema(DMK)
THANKS

No comments