Breaking News

Waminal Hoob 21

ASMY#??
WM#??
Team#NooryAli forever#
[9/15, 6:11 PM] Asmy Mom Aydah??: da wani irin shock take kallonsa ,Haka lokaci daya take xare jikinta cikin nasa hawaye na xubar Mata tana girgixa masa Kai.cikin rawar


murya take fadin”karya Kuma ,karya kan Karya komai namu karyane meyasa?”ta fada da Dan daga Murya saurin rufe Mata Baki yyi Yana kallon kofa komawa yayi ya sakawa kofar key ya dawo ya riko hannunta ya xaunar daita gefen gado,shima ya xauna cikin sanyi Murya yake fadin”sabida farin cikin Ammah nayi Haka Nan da wata biyu insha Allahu xan samo solution din matsalar mu ki yarda Dani pls…..”!yayi maganar cikin raunin murya Yana jin shima kamar Bai kyautawa Noory din ba,inhar hakan xai saka Aliyu farin ciki da Kuma mahaifiyarsa A shirye take da tayi masu ma fiye da hakan,hannu ta saka tana dauke hawayen idonta ta kallesa gamida shagwabe fuska tana kama cikinta take fadin”baby xaici gwaiba,ta fada tana murmushi tana ware masa ido Bai San lokacin da ya saki murmushi ba.dama fuskar sa takeso ya saki, pillow ya dauka ya jefa Mata itama haka,haka suka fara xagaye dakin sai Daria suke cike da nishadi tamkar babu Abunda ke damunsu dukansu,Yana so ya rikota Taki basa damar hakan shammatar ta yayi ya damkota Yar Kara ta saki dukan su suka xube kan bed suna maida numfashi tana Jin yarda xuciyarsa ke bugawa.saurin dagasa tayi tana mirginawa gefe ,daga can gefe sukaji ana buga kofa da sauri Noory ta Mike tsaye tana xaro ido ,Dan murmushi yayi gamida gyara kwanciyarsa xuwa tayi ta bude kofar Ammah ce da Mai aeki a bayanta ,wata irin kunya ta kamata lokacin da Ammah ta shigo dakin tana bin koina da kallo yarda aka hargitsa komai ,da mmki take kallon Aliyu .Mai aikin ta ajey kular tsakiyar rug ta fice ,
Tsaye bakin kofa Nooriyah tayi cike da kunya,gaisheda Ammah yayi Yana kokarin Buda kular Ammah ta dakatar dashi tana fadin”me xakayi??”Ya dakune Fuska yana fadin Ban karya ba Ammah.”tace kaje dinning area akwai break fast wannan na Nooriyah ne.”suna hada ido tayi masa gwalo,Ammah ta kalli Nooriyah da har yau ke tsaye bakin kofa tace xo ki xauna ga alalen an gama,cikin sanyi jiki Nooriyah ta karaso ta xauna kan rug din tasa hannu ta bude kular alalar ciki sai tiriri takeyi ga manja Nan an xuba samanta,sai kamshin yajin tafarnuwa ke tashi .Aliyu waxeer ya dakune Fuska yana kallon Ammah yana fadin”Ammah kin manta bana cin wannan Abar,ya mike tsaye yana kokarin fiddo wayarsa dake famar Kara ya fiddo ganin Mai Kiran sai da gabansa ya Fadi.”saurin maida Wayar yyi cikin Aljihun wandonsa da mmki Ammah ke fadin”Ana Kiran ka a waya baxaka dauka ba,xan dauka Ammah ya fada Yana kallon Noory daita ma take kallonsa,
“xan dawo xuwa anjima.”Ya fada Yana kallonta daga masa Kai tayi ya juya yabar room din ,Ammah ta kalleta tana fadin”kici kar yayi sanyi bara naje na karasa aekina.”da haka itama tabar room din Yar ajiyar xuciya nooryn ta sauke .batasan Kuma sai xuwa Yaushe wannan karyar xata kare ba,,ta gaji ta gaji da wannan karyar.
(Omar Shagari mention)Shirin fita Yake yi daga gidan ko kadan baya son haduwarsa da Mami satin sa daya kenan da dawowa,sanin Mami sunje graduation dinsa na kammala masters yasa ya yarda yaxo yanxu din Haka Mami ko Yan gidansu Babu Wanda ya fada masa me Mami ke shiryawa ,sai da yaxo yaga lefen da Mami ta dankara Wai duk na xahra Axeez ne Nan da wata biyu aka sanya Auren su.”tun daga lokacin ya hau fushi da kowa a gidan ko Abincin gidan bayaci tun Mami na lallashi har itama ta daina lallashi dan acewarta tunda ba ubanta bane ta daina binsa ,Yasan dai hukuncin Wanda yaki bin umurnin uwarsa,knocking yaji anayi bakin kofar shigowa room dinsa yayi mugun hade Rai gamida harara kofar Yake fadin”Uban waye ke bugamin kofa!”yayi Maganar sounding so very Angry,dan duk a zaton sa Jamila Shagari ce wato autar mami wacce itake bin Farhaan, cikin fushi Mami ke fadin Uban Kane ke bugawa,baxaka xo ka budemin kofa ba sai na sassaba maka farhaan.”A fusace yaxo ya bude kofar yabata hanya ,ya dawo Cikin dakin ya dauki car key dinsa ya juya xai fita Mami ta bude ido da Baki tana kallon Rashin kunyar Farhaan din.”lallai kenan da na Bari ka Auro yarinyyar Nan shikenan na shiga ukku na lalace juyamin baya xakayi farhaan.”Mami tayi maganar da tsananin shock a muryarta ,Juyawa yayi Yana fadin”Mami fita xanyi da wani irin fushi Mami ke fadin biyoni a parlor tana fadin Haka tabar masa dakin a fusace tamkar xata tashi sama sabida masifa………Mami ta xauna ta xuba tagumi cike da Abubuwan da sukayi Mata yawa,duk Saboda farhaan Nafisa ta karaso cikin parlorn da mamaki take fadin Mami Baki same sa bane .”ko ya fita??tambayoyin da Nafisa ta jero Mata kenan,wallahi Nafisa jikina yayi sanyi Anya basai na shiga malammai Akan farhaan ba,yarinyyar Nan ba banxa tabarsa ba,kinga yarda nake fada Yana fada.” Nafisa ta girgixa Kai cike da takaici take fadin”bbu komai akan sa Mami iskanci ne kawai ke damunsa,idan an daura masu Auren ya saketa ranar,Mami komai rintsi karki Bari farhaan ya Auro matsiyaciyar yarinyyar Nan,Dan wlhi juya maki baya xaiyi.”Nafisa sai kace kin mantani ne aeko Bayan Raina farhaan ya Auri shegiyar yarinyyar Nan ban yafe masa ba dunia da lahira Haka Kuma baya taba ganin dai-dai cikin lamurrransa.”sai acikin kunnen farhaan Wanda ya Kara Shan jinin jikinsa kallonsa Mami kurum keyi,ya xauna Yana fadin”Mami ita wannan da xaki Auramin kin manta Yar iskace bin maxa takeyi.”!yayi Maganar da karaya a muryarsa,
Baki bude Mami ke kallonsa ta kalli Nafisa tana fadin”kin jisa da sharri kou.”Kai da idonka kaga katti na dannarta a dakin hotel,cike da takaici Yake fadin Mami waye baisan Zahra axeez ba har shaye-shaye take .”Mami dai kallonsa ta tsaya yi,kafin ta Mike tsaye tana fadawa Nafisa ta Miko Mata mayafinta a daki Mai shige da kayan jikinta ,sai ga Nafisa ta dawo dauke da mayafi ta mikawa mami.amsa Mami tayi ta saka,hannu ta Mika masa tana fadin ya Bata car key din hannunsa,Yana hade Rai yake fadin”Mami fita xanyi Aliyu na can na jirana akwai inda xamuje.”wani kallo da mamin tayi masa yasa ya Mika Mata car key din,wuce muje.”Mami ta fada tana nuna masa kofa, Mami ina xamuje na fada maki fita xamuyi…….”gidan ubanka xamuje farhaan!”tayi Maganar cikin daga Murya da bacin Rai,har Mami ta fara driving masifa take shi dai baice komai ba yayi shuru yana binta da kallo,
Ganin unguwar da suka shigo yasa ya juya Yana kallon mami,amma mamin Bata ko kallesa ba taci gaba da tukin ta .har suka kawo katon get din gidan su xahra Axeez,horn ta shiga dannawa maigadi ya leko,ganin Mami yasa ya wangale masu get.
Motar ma sai na fito da Kai.”Rai Abace ya fito daga cikin motar ya nufi Entrance din shiga gidan ma’aikatan gidan sai gashesu suke da ladabi ,Banda mugun kallo babu Abunda yake binsu dashi,da fara’a hajia Yasira ta tarbi Mami tana masu sannun da xuwa.”ta kalli farhaan tana fadin”sai yau kaga damar xuwa ,tun Yaushe kadawo??”shi dai baice komai ba sai Dan murmushin da ya kwakwalo na dole,
Xahra ce ta shigo parlorn tana Amsa waya,wata fitted gown
Ta atamfa ce ajikinta ta kamata sosai ,sai kanta da yasha kananun kalaba,tana da kyau sosai Dan farace sosai Haka tana da tsayi kiba daice Bata daita ko kadan,Amma tana da wani irin shape Mai daukar hankali ganin farhaan Shagari a gidan su tayi saurin katse wayar da gudu ta karaso cikin parlorn
Tana sakin murmushi take fadin”Yaushe kaxo??”kaga damar xuwa kenan…”Mami ta washe Baki ,hannunsa taja tana fadin”muje parlorn Baki,gaisheda Mami tayi cike da ladabi,suna shiga parlorn ya fisge hannunsa Yana binta da wani mugun kallo.
ta juya ido tana fadin wulakancin naka kenan Ya motsa.”xata tabasa ya fisge hannunsa Yana fadin”karki tabani da wannan kaxamin hannun.”!yayi Maganar da bacin Rai da wata irin tsanarta ,
Ta girgixa Kai tana sakin murmushi gamida dage gira daya take fadin”Ya Rabbi!””so much Anger!”yau kawai farhaan ,Kai kullum fada baka taba yimin magana Mai Dadi ba,
Ya harereta Yana fadin.”in har kina son kanki da arxiki ki fasa wannan Auren.”mexai faru idan Anki hakan ??”ta fada tana kallon cikin idanunsa,Aurenmu duka taimakon junane ,ni shegiya kai shege.”kowa sai yayi Rayuwarsa yarda yakeso ko Bayan Auren mune.'”ko ka xata Ban sanka ba farhaan!”ban San iya matan da kasani a Rayuwar bariki ba.haka Nima baxan iya kirga maka maxan da nasani ba,komai dai ya wuce yanxu tunda ina sonka baxan taba ganin illarka ba.”kallonta kurum Yake da idanunsa da suka fara canja kala,
Ta rungumesa sosai take fadin”Auren mu Alkhairi ne dukan mu farhaan Shagari babu takura acikin Auren mu kowa xaiyi Rayuwarsa yarda yakeso.”ya tureta daga jikinsa ya juya yabar gidan duka batareda sanin Mami ba xuciyarsa na tafasa……….sigari Yake kokarin kunnawa Aliyu waxeer ya dakatar dashi Yana dakune fuska Yake fadin”plz karka kunna kasan bana son warinta wlhi.”badan farhaan din yaso hakan ba ya mayar,ya kallesa da wani sabon bacin Rai Yake fadin”kasan me Mami tayi min kuwa??Aliyu na girgixa Kai Yake fadin”ya xaayi na sani sai ka fada,Nan ya fada masa Abunda Mami ke kokarin yi da Rayuwarsa ,cikin bacin Rai Yake fadin”Mami ta kusa kure hankurina da na Auri wannan yarinyyar karama duk Abunda Mami xatayi tayi bantaba ganin Haka ba Wai yiwa namiji Auren dole.”Ta rasa ma wacce xata hadani Aure daita sai karuwa wacce ta gama watsa duwawunta atiti.”Daria sosai Aliyu keyi Yana kallon farhaan ,Mami ta rantse ko Bayan ranta ban Isa na Auri Noory ba,plz kabani shawara ya xanyi da Mami.”Ya karasa Maganar da karaya a muryarsa,Aliyu ya lumshe ido na dan lokaci ya budesu akan farhaan din Yana fadin duka ka samu a matsala Farhaan Shagari ina da nasanin biye maka tun farko dama da Kai aka daura Wannan Auren kayi tafiar ka da Yarinyyar can kasar da kake karatu idan ka dawo sai ka fuskanci Fushin Mami .”Nima gashi yanxu kasani A matsalar Ammah.”Ya fada Yana basa labarin Abunda ya faru daren jia,dafe Kai Farhaan yayi Yana fadin”innalillahi aransa ,Ya kalli Aliyu Yana fadin matsalarka Mai sauki ne fiye da tawa ,wani kallo Aliyu keyi masa Yana fadin”Mai sauki fa kace Kasan babu Abunda Ammah ta tsana fiye da karya,
Kasan ciwonta har kake Kiran hakan da me sauki,ka samo Mana mafita wata biyu sukayi saura,ga Areefa mansoor tana ta kirana a gefe na turo magabata na mu
.”kasan me xai faru ??”Aliyu ya kalli farhaan Yana girgixa Kai,sakin Noory Mai sauki ne guduwa xanyi wlhi muje can muyi Auren mu Dana Auri xahra Axeez Kara na mutu.”shi dai Aliyu kallonsa kurum Yake da nashi tashin hankalin da Yake hangowa,kayi shuru ko baiyi ba??Aliyu ya girgixa Kai Yana fadin ban san me xance ba .”Kiran Areefa mansoor ne ya shigo a wayar farhaan shagari gabansa na bugawa ya kalli Aliyu da hankalin sa baya kansa Yana kan wayarsa ,saurin saka wayar silent yayi .Aliyu ya kallesa Yana fadin”ana Kiran ka a waya ko Mami ce.”Kafin yayi magana Kiran Areefa ya Kara shigo masa da sauri ya mike tsaye ya fice daga parlorn ,Yana dagawa Yake fadin”kina damuna dayawa Areefa kibarni naji da damuwata,muna tareda Aliyu Kuma.”Bashi ya dameni ba farhaan ciki ne ajikina.”ta fada da muryar shock.!”cike da mugun bacin Rai Yake fadin”dama ni kadai ke ganin duwawun naki.??”kinyi mugun Raina ni Areefa karki fara wasar da baxai yi Mana kyau ba pls.”Ya fada Yana kashe wayar duka da wani sabon tashin Hankali.”Yana Juyawa yaga Aliyu na nufosa ,
“Meya faru Kuma??Aliyu ya fada Yana karantar tashin hankalin dake kwance Akan fuskar farhaan,
Muyi waya bana Jin Dadi.”da mamaki Aliyu ke fadin ka fasa shiga wajen Ammah kenan??”Yana girgixa Kai Yake fadin xuwa gobe dai.”Kayi wani Abu cikin satin Nan Besty mu samarwa kanmu solution .Yana fadin Haka ya shige motarsa yyi Reverse ,shi dai Aliyu tsaye yayi Yana kallonsa har ya bar get din gidan hannunsa xube cikin Aljihun wandonsa,Yar ajiyar xuciya ya sauke dama ko kadan bai son Farhaan din ya hadu da Noory ,ya Kuma nemi dalilin hakan Ya rasa.A parlorn ya samu Ammah daga gefe masu decoration ne ke gyara parlorn da wani irin flowers masu kyan gaske ,ya xauna cikin soofas Yana kallon Ammah Yake fadin”duk wannan na menene??”Ammah na murmushi take danna wayar hannunta tana fadin”xan hada waleemar dare ne Yan gidane kurum xaa xo aci Abinci Ayi Addu’a Allah ya kawo Mana baby lfy,dinku nan ka na daki jeka duba Nooriyah din ma tana ciki itada Batool ya bude ido Yana fadin”ita kuma dake Makaranta meya kawota??”Ammah ta hareresa tana fadin”ina ruwanka ,girgixa kansa ya shigayi Al’amarin Ammah Yana karasa jikinsa yin wani sanyi,Yana tura kofar dakin Ammah sukayi ido biyu da Batool waxeer,
Ihun murna ta saki taxo ta wani rungumesa tana fadin”Yaya Mana.!””ina ka shiga inata nemanka,Yaya mun kusa samun baby !”kaji dadin da nake ji Ya jayeta daga jikinsa idonsa na kan Noory wacce take tsaye tana duba kayan da xai saka xuwa anjima.Batool ta kalli nooryn tana fadin kiyi sauri sistr inlaw xan tsaya parlor na jiraki lokaci na tafia da Haka ta fice daga room din,rufe kofar yayi ya jingina bayansa ga kofar ya harde hannayensa Akan kirjinsa Yana kallonta,karaso kaga wane xaka saka aciki yadin xaka saka ko shadda Ammah tace xuwa anjima Mai daukar hoto xaixo.”Kunyi magana da farhaan a waya?”Tambayar da yyi Mata kenan.”tana girgixa Kai take fadin”Bai kirani ba meya faru Kuma??”Nan ya fada Mata abunda farhaan keso Ayi.”ta dago manyyan idonta tana kallonsa,tayi murmushi xuciyarta na bugawa batasan meyasa duk lokacin da aka ambaci saki ba ,sai taji hankalinta Yana son barin jikinta dauriya kurum take ,
“Nifa baxan iya Auren Farhaan Shagari ba batareda ixinin mahaifiyarsa ba,Kuma ni ba jahila bace da xanbi namiji wani wurin A daura Mana Aure.”kuskure dukan mu munyi sa Amma wanna shawarar batayi ba gaskiyya.”Kai Kuma ka shirya raba Auren mu ina fatan ka shirya kalaman da xaka fadawa Ammah.”ta fada tana kallonsa ,karasowa yayi har gabanta Yana kallon cikin idanunta,
Jin tayi tana neman faduwa sabida yarda ya kura Mata ido saurin tarota yayi da wani irin yanayi yayi mata rumfa tana Jin yarda xuciyarsa ke bugawa da wani irin soyayyarta Wanda baisan ta inda ta fara ba,hade fuskarsa yayi da Tata saurin rintse idonta tayi xuciyarta na harbawa da Jin saukar numfashin sa,
Wani irin sonsa na Kara narke Mata xuciya.xatayi magana
Yayi saurin hade bakinsa da nata ido ta bude sosai tana karbar sakonsa,
Wani irin kiss Yake Mata Ahankali yaji xuciyarsa na saukowa daga bugawar da take ,sakinta yayi a hankali ya juya ya nufi kofa batare da ya Kara hada ido daita ba Yake fadamata ta xabar masa dinki da yafi dacewa dashi ta samesa a mota da kayan itada Batool xai sauke su wajen saloon.”da Haka ya fice daga dakin duka yabarta da kamshinsa,hawaye taji suna cika idonta meyasa kaddara xatayi Mata Haka,meyasa xata jefota awajen da Bai kamata taxo ba.farhaan Shagari ya cancaci tayiwa soyayyar Aure ba Aliyu waxeer ba….”
Hawaye kawai ke xubar Mata cike da bakin ciki da mugun kishi dake cin xuciyarta, Khaleel waxeer ya riketa sosae Yana fadin”ki dawo hankalinki pls laylah Wai meke damunki ne.”Yyi Maganar a Dan tsawace ,cikin ihu take fadin”tun da na aureka Ammah Bata farin ciki da Auren Nan ,Haka Bata Sona Bata kaunata Yaushe ma Aliyu yyi Aure da xata fara son matarsa har haka.komai na business dinta Noory ce kan gaba ,Akan me baxan damu ba.ta fada a haukace tana wani rike Khaleel gamida Fashewa da wani irin kuka,meye abun damuwa aciki duk da Haka bakin fi nooryn samun Albashi sosai ba,Kuma tarairayar da Kika ga Ammah nayi Mata cikine jikinta kin San burin Ammah taga ya’yan mu sai gashi Allah ya kawo,kema hnya abude take Idan kin shirya haihuwar ynxu sai ki daina Shan duk wasu pills na Hana daukar ciki.”wani kallo ta rika yimasa,duka -duka shekarar mu nawa da yin Auren kake Maganar ciki da Tara Ya’yah??”toh idan har hakane sai kibari a tarairayi wacce keda ciki,Kuma dole kije gidan Ammah xuwa anjima idan har bakije ba familyn waxeer xasu ga kamar kina bakin cikine ,da Haka Yabar Mata dakin tabisa da wani irin kallo.xama tayi akan gefen bed tana juya maganganun Khaleel waxeer,ya kamata tayi wani Abu xuwa daren nan.tana ta Kiran wayar Areefa Mansoor Bata xuwa ,Kuma tasan tana Abuja baifi sati biyu da gama karatun taba ,ta dawo gida duka……shiya kaisu wajen saloon haka ya jira suka gama ya maidosu gida,Batool kawai ce ya aje agida ,Yana fada Mata ta fadawa Ammah xuwa anjima xasu shigo.gidan su ya kaita wani irin farin ciki ya rufeta ,suna gama parking ta balle marfin motar ta fita da gudu batereda ta jira Aliyu ba,ganin ta kawai sukayi ta fado masu Adama na a tsakar gida tana wanke-wanke Baki Adama ta bude tana kallonta tana fadin”wana ke gani Anan??tamkar Nooriyah,duk da Nooriyah tayi haske tayi kiba Adama ta ganeta sai dai tana tababar itace ko baita bace,mikewa tsaye Adama tayi tana xagaye Nooriyah din da wani irin kamshin Yan gayu da Taji tanayi,Nooriyah ta wara ido gamida Rungumeta duka,Daria Adama tayi tana fadin”da gaske kece Nooriyah kinga yarda kika xama wata hajia ,
Daria Nooriyah tayi da sallama ya shigo cikin gidan Yara biye dashi dauke da Kaya suna saukewa,sannu da xuwa Adama ta shiga yiwa Aliyu tamkar xatayi Masa sujada,
da sauri ta nufi daki ta dauko tabarma ta shimfida masa,kallonsa Noory kawai takeyi da wani irin yanayi a fuskarta Wanda baxai fassaru ba,shima kallonta Yake da idanunsa ya wara ido Yana Mata tambaya da ido Menene???sai ta kwantar da Kai tana girgixa masa Kai,Adama ta dauko hijab tana fadin”Bari na karbo maku Ruwan Sha a bakin titi ,duka yaran basa Nan…….”da Haka ta fice daga gidan dukansu suka bita da kallo,Yan mintuna kalilan Adama ta shigo gidan dauke da bakar Leda ta aje agaban su Noory din tana fadin ga ruwa Nan susha,gorar Ruwan swan ne da Kuma lemun fanta.ruwan kawai Aliyu ya Sha ,ya kalli Adama Yana fadin”kawu ya fadamin baya gari Yana Kano.”Ehhh hakane ya tafi Kano xuwa jibi xai dawo da yardar Allah,Allah ya kawosa lfy.” Aliyu waxeer ya mike tsaye da bottle water A hannunsa,Yana fadawa Adama xasu koma sai an kwana biyu Kuma.Rafar dubu daya ya aje agabanta ta ,ya fice daga gidan Nooriyah ta kalli Adama cike da damuwa take fadin”ummah Safiyya fa tunda mukaxo ban ganta ba,kin San safiya Bata son xama wuri daya tun can dama. Ynxu haka tana gidan kawayenta.”mikewa Noory tayi tana fadin”ummah xamu koma insha Allahu xuwa jibi xan dawo idan kawu ya dawo ,da fara’a Adama ke fadin”toh Allah ya kaimu,Allah yay maki Albarka keda mijinki ya Baku xuri’a Mai Albarka a duk inda kuke,ya tsareku da Yan iska da shaidanu,
Har kofar gida Adama ta raka Nooriyah da Addu’a tamkar ta hadeta Dan so.”Nooriyah ta kawo sauyi Mai yawa acikin Rayuwarsu,ta kallesa da sauri tana fadin”gidan Ammah fa.ya kalleta yana fadin”gidan Ammah ne gidan Aurenki,
Muje malama ki Samar min lunch yunwa nakeji.”ko a kitchen din tsareta yayi duk inda ta wurga idonsa na kanta,a kitchen din yaci Abinci,har Kusan magrib suna tare sai ga Kiran Ammah ya shigo a wayarsa,Yana dauka Ammah ta fara fada,ya kawo Mata Noory Bata jira Mai xai fada ba ta kashe wayar,Koda suka Isa gidan Ammah ana Kiran sallar magrib anyi wani irin kawata parlorn Ammah,koina an axa pics din Aliyu da nooriyah wani pics duk na bikin sune,da sauri Batool waxeer taja hannunta suka wuce sama,shima Aliyu gudun haduwa da Ammah yasa ya juya ya nufi massallaci,Bayan ya fito massallaci sai ga motar farhaan Shagari na shigowa cikin gidan,tsayawa Aliyu yayi har yyi parking.Ya kalli farhaan din Wanda har ynxu kana karantar damuwa a fuskarsa,tare suka jera suka shiga gidan Aliyu,, hop yau xanga noory.”xaka ganta bara na shirya muje gidan Ammah ,da Haka ya nufi stairs xuciyarsa yaji tana yimasa nauyi,
Baa jimaba,sai gashi cikin farar shadda da Noory ta xabar masa.har suka karasa gidan Ammah a motar farhaan din bbu Mai magana,kowa da abun dake cin xuciyarsa.kusan tare suka shigo parlorn na Ammah ,kowa idonsa Akan Noory wacce ta hade cikin shigar English gown kalar Army green da mayafinta,tayi wani irin kyau acikin kayan.su Batool waxeer sun sakata tsakiyya sai daukar pics akeyi kida na tashi a hankali acikin parlorn,wasu na xaune wasu na tsaye suna rawa wasu Kuma Abinci suke ci.danna xuciyarsa kurum Yake ganin irin mayen kallon da farhaan kebin nooryn dashi Yana hade wasu irin yawu,Haka noor dinsa ta ciko ta xama macce lokaci daya.”Kai talauci balai ne jin ddi da hutu Kuma baiwa ne daga Allah.Farhaan ya russuna Yana gaisheda Ammah,
Batool waxeer taxo taja hannun Aliyu tana fadin Yaya Kai ake ta jira xaayi muna pics,
Haka ta hadasa da nooryn ana daukarsu pics sunyi wani irin kyau Haka sosai suka dace,kishi kamar farhaan xuciyarsa xata fito ganin yarda nooryn ta shige jikin Aliyu ana daukar su pics,duka hankalin su nakan farhaan din musamman nooryn da taga irin kallon da Yake yimata,duk Akan idon laylah waxeer wacce ta koma gefe ta harde kafa tana kallon farhaan din tana sakin murmushi a hankali,Batool ta xuba Abinci a plate ta damka masa a hannunsa tana fadin”Ammah tace kabata Abinci taci karta xauna da yunwa ,tana kula da Baki.”Amsar plate din Aliyu yyi tura Abinci Nooriyah kawai take hankalinta na kan farhaan,shima Aliyu ya lura da hakan duk yaji bbu ddi,muje ku gaisa da farhaan.har sun juya xasu nufi farhaan sukaji muryar Ammah na fadin”Ina Kuma xaku xo ku gaisa da ummah da matansu Nasir duka sunxo suna main parlor ba yarda suka iya suka juya suka bi Ammah,Haka ta shiga gaisawa dasu Batool nayi Mata bayanin su daya Bayan daya,kowa da kyautar gift’s dinsa,
Ummah ta kalli Aliyu cike da murmushi take fadin”Captain kyautar me xaka baiwa surukuta irin wannan big happiness da tabamu,dan Sosa kansa yyi Yana kwakwalo murmushi,
Aysha waxeer ta karaso gaban Nooriyah ta rufe fuskarta da farin kyalle,ta kalli Aliyu waxeer tana fadin Yaya dauketa muje ka Bata kyautar .”yin yayi tamkar baiji Aysha waxeer ba,sai da Batool waxeer ta fada da karfi tana fadin Yaya masu daukar pics suna jira ,
Daukarta yayi cak!xuwa compound din gidan aka bisu a baya ana sakin shewa Batool sai famar daukar su pics take,har gaban motar Aliyu ya Kai Noory,new model(BMW 7 series)baka wuluk sai sheki take wani irin ihu batool waxeer ke saki tayi hugging din Noory din,idanun farhaan yaji suna yawo akansu sai yaji duka ba ddi,dauriya kurum yake.ummah ce ta rungume Noory tana saka Mata key acikin hannunta,hawaye taji suna cika idanunta.bata san dame xata biya su ba kaunar da suke nuna Mata,ba xato taga Aliyu waxeer ya Jawota ajikinsa Yana subbatar goshinta da bakinta Yana fadin “thank you for d love and everything my wife.”pics aka shiga daukarsu,da Haka Aliyu yaja hannunta xuwa motarsa,ya bude Mata front side ta xauna ya rufe, wurin Ammah ya koma Yana fada mata xasu wuce gida kansa na masa ciwo , Ammah tayi murmushi tana fadin ka Sha magani.”Kuma ka kula da Nooriyah Naga itama da alamar akwai gajia a tare daita ,ya subbaci hannunta Yana fadin insha Allahu.”Nan ya juya Yana yima su ummah sai da safe,ummah ta kalli Ammah tana murmushi take fadin”bbu wani ciwon Kai shi dai Yana bukatar matarsa,itama Ammah murmushi kurum tayi.ganin motar Farhaan yyi acikin parking lot din gidan sa,shima parking yyi .Kusan tare suka fito motar tareda farhaan Wanda fuskarsa ko kadan bbu wani walwala ,gaban Nooriyah din yyi wani irin bugawa ganin farhaan din ,Bata daice komai ba farhaan ya karaso wurinsu Aliyu ya kallesa Yana fadin”mukarasa a parlor da Haka dukansu suka nufi Entrance din shiga gidan,Farhaan ya xauna acikin soofas,yyi crossing leg’s dinsa Yana Danna waya batare da yace komai ba,Aliyu da Noory na tsaye a wajen,dakyar Aliyu ya tattaro jarumtar sa Yana fadin xaije yyi wanka da haka ya juya da sassarfa xuciyar sa nayi masa wani irin nauyi ya nufi stairs,Jin tayi kafafun ta nayi Mata nauyi lokaci daya tabi Aliyun da kallo,kallonta farhaan yyi ganin inda take kallo ya mike tsaye ya wani fisgota ta fado kansa duka .matseta yyi cikin jikinsa yasa hannayen sa Yana xagaye kugunta dasu ,Aliyu Yana Juyawa ya hango nooryn cikin jikin Farhaan,wani irin ciwo Yake ji Akan kirjinsa da sauri ya juya ya shige master bedroom dinsa,cikin muryar rada Yake fadin”Ina son wannan kamshin naki my Noor,did you miss me??kamar yarda Nima nayi kewarki ba kadan ba,cikin rawar Murya take fadin”meya haka farhaan Dan Allah ka cikani.”ta fada tana kallon cikin idonsa da suka fara canja kala,Kara riketa yyi sosae.wannan karon ba riko Mai sauki yyi Mata ba har da mugunta ya hada Mata.”Meyasa xan cika ki,saboda Aliyu Yana kusa??ya fada da muryar kishi.”girgixa Kai tayi hawaye na tarar Mata take fadin”ba Saboda shi bane farhaan muna daukar xunubi ne,Akwae igiyoyin Aure akaina.”Cikin daga Murya da xafin Rai Yake fadin”sai me nace sai me??”kin manta only contract marriage,meyasa xaki wani damu.”Yarda Yake Mata ihu da tsawa jikinta yasa ya fara kadawa,ya Kara damko kugunta Yana fadin.”meyasa shi Idan ya tabaki bakya hanasa??”Ya fada Yana kallon cikin idanunta da Yake hango wani Abu acikinsu,ki Amsa min.”ta fisge kanta ta shiga Jada baya,shi Kuma Bai fasa binta ba,da mayyun idonsa .kokarin faduwa take yayi saurin tarota Yana fadin”karki Jima kanki ciwo,xuwa Nan da sati daya xan kawo karshen wannan Auren.”in har saboda wannan Auren kike Avoiding Dina.”da Haka ya saketa ya shafa kuncinta Yake fadin”Ina sonki a Koda Yaushe,da Haka ya fice daga parlorn xuciyarta na bugawa take binsa da kallo,
Da gudu ta nufi dakinta na barci batareda ta kalli dakin Aliyu ba……..Ya hargitsa dakin nasa Yana neman takarda da biro kurum lokaci yyi da xai Raba kansa da wannan Auren ko xuciyarsa xata samu sassauci,xama yyi ya Dora pen a takardar,lokaci daya yyi jifa dasu Yana dafe kansa dake neman rabe masa gida biyu ,wani irin Rawa jikinsa keyi jijiyoyin kansa lokaci daya suka mike idonsa ya kada yyi wani irin ja,are you fall in love with her Ali??”wata xuciyarsa ta shiga tambayarsa,da sauri ya dafe kansa cikin ihu Yake fadin”no I’m not fall in love with her.”I’m not!”ya shiga maimaita Kalmar hawaye na xubar masa Yana dafe kirjinsa da yakeji tamkar xaya cire,
Jin ihu a dakin Aliyu yasa ta fito nata dakin da gudu ta nufi nasa nakin,Koda ta tura dakin a bude Yake hango Aliyu tayi kan marbles ya dunkule wuri daya tamkar Mai Aljannu da gudu ta nufesa tana dagosa,
Da idonsa da suka fara yimasa nauyi ya dago Yana kallonta,
Lokaci daya hotosu itada Farhaan ya fado Masa,na rungumar da yayi Mata daxu.fisge kansa yyi lokaci daya Yana matsawa gefe Yake fadin”karki tabani karki tabani muguwa kawai !!”meyasa xaki Rungumesa da Ina da Ina ya taba ajikin ki.”Ya fada cikin ihun tsawa Yana dafe kirjinsa da Yake Jin tamkar bana sa ba, maganganu Yake xuba Mata cike da kishi ,pls go away !!”bana son ganinki.”Jin yyi numfashinsa na neman daukewa dakyar Maganar ke fitar masa,dafe kanta tayi hawaye na xubar Mata ta karaso ta rikesa take fadin”pls kayi shuru Dan Allah.”ta fada tana saka sa cikin jikinta duka tana Fashewa da wani irin kuka Mai cin rae,Jin tayi baya numfashi hankalinta yyi mugun tashi dagosa tayi tana Kiran sunan sa,Jin tayi baya numfashi ,da sauri ta ajesa dube-dube ta shigayi a dakin gaba daya ta rude wayarsa ta hango akan mirror dressing da dugu ta nufi wayar,Danna wayar ta shigayi sai dai akwai lambobin security ajikin wayar,aje wayar tayi ta nufi nata dakin da gudu ta dauko wayarta. Sai dai cikin Rashin sa’a Bata da caji Kuma saka wayar caji ma Bata lokaci ne hijab ta saka ta nufi masu tsaron dake gadin gidan ,fada masu ta shigayi hankali a tashe,su suka taimaka aka sakasa motarsa,
da gudu ta shiga motar ta jata da wani irin speed tana barin gidan, mention din Ammah ta nufa ,ko kashe motar batayi ba ta nufi cikin gidan da gudu sauran kadan suyi karo da Khaleel waxeer,yaja baya Yana kallonta xuciyarsa na bugawa.Ammah!””Ammmah.”Ta shiga kwalawa Ammah Kira,
Khaleel waxeer ya riketa Yana fadin”meya faru ??”jan numfashi ta shigayi takasa magana.xuciyar Khaleel waxeer na bugawa Yake fadin “kiyi numfashi Noory Ina Aliyu??”kofa ta shiga nuna masa tana fadin”mota!”da gudu Khaleel waxeer ya nufi kofa,Ammah ta riketa cike da sabon tashin Hankali take fadin”,”meya samu Aliyun.?”hawaye na xubar Mata ta wani rungume Ammah tana fadin”ban sani ba Ammah.baya numfashi.!””likitocine a kansa acikin Asibitin waxeer dakyar suka samu dai-daituwar numfashin sa ,sunyi Mai Allurar barci oxgyen ke rike da numfashin sa,Ammah da Noory suna xaune a wani daki na musamman kowace idonta ya kumbura saboda kuka,har washe gari Aliyu barci yakeyi Ummah ce ta kawo masu break fast karfe takwas na safe ,
Cikin Ammah da nooryn ba wacce ta kalli break fast din,
Dakyar da lallashi Ummah ta samu kowanen su ya Sha tea da ta hada masu,
Dr.Arhaam ne ya turo kofar da sallama A bakin sa da sauri Ammah ta amsa tana kallonsa,ya karaso cikin room din Yana gaisheda Ammah cike da girmamawa,ta Amsa tana kallonsa da alamar so take ya fada mata ya jikin Aliyu,xaiyi magana Khaleel waxeer ya shigo bayansa laylah waxeer ce wacce taci kwaliyya cikin wani uban less Wanda kudinsa xasuyi naira dubi dari da hamsin tana rike da basket,
Wanda kallo daya Ammah tayiwa basket din tasan A restaurant ya fito.. Khaleel waxeer ya karaso cikin room din Yana baiwa Dr.Hannu sukayi musabaha…

Littafin waminal Hoob na Kudi ne##500
Account Details
0004157137
Jaiz Bank
Asma’u Buhari Aliyu
Katin wayar MTN.ta wannan lambar#
09060259200
shaidar Biya ta wannan lambar#08086207764

ASMY#??
WM#??
Team#NooryAli forever#??
21/22 pg#

No comments