Breaking News

Babban Yaya Book 2 Complete Hausa Novel

 

[11/2, 10:29 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*




*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA*


*37*

Ko da Mimi ta shigo ban saurare ta ba, ina tsaye bakin k'ofar dakin Ummanmu muna magana da ita.Simi-simi tazo ta shige dakinmu tana b'oye abu cikin mayafin ta, naji zuciyata bata yi min dad'i ba, futowa tayi ta tsaya kusa dani tare da fad'in "Shine kika tawo kika barni a hanya ko."? Umma tace" nima yanzu nake tambayar ki tace ta barki a hanya, amma kun Dade gaskiya sai da kwalliya ta biya kud'in sabulu tunda gashinan lallai yayi kyau sosai."

Mimi tace"wallahi kuwa Umma mun tadda ita tana yi wa wasu shiyasa." Tace" abuncin Ku na kicin."

Kicin din na wuce ba tare da na tsaya kallon Mimi ba, abuncin na dauko a kula nan rumfar Umma na zauna tare da bude food Fula's din ina k'okarin zubawa. Jiki a sanyaye Mimi ta k'araso inda nake zaune duk ta damu ganin yanda na share ta.Umma ta mike ta futa tsakar gida tana amsa sallamar da ake yi.

Mimi ta kalle ni bakinta na rawa tace"kin San me Asma'u. "? Nace" sai kin fad'a."
"Guy nan fa wayarsa ya bani had'addiya baki ganta ba, wai zai dinga kirana da ita.....gabana ne yayi wata irin fad'uwa!! Tuni naji abunci ya futa kaina na kalleta cikin dauriya tare da fadin" kin dace Mimi Allah ya kara k'auna" Mimi babu kunyar komai tace" ameen Ashe haka yake da saukin kai."? Nace"Hummm"? Hirarsa kawai take min takasa cin abuncin nace "Mimi so ya hanaki ki ci abunci ko? Ki dai yi a hankali." Dariya tasa cike da farin ciki, duk Wanda yasan Mimi a lokacin zai fahimci fara'ar ta da walwalarta ya k'aru.

*******
Kai tsaye Company nasa ya nufa Wanda ake aiki tuk'uru ma'aikata iri-iri sai kai kawo suke, insha Allah yau za'a gama komai sai abunda yayi saura  had'a wuta tare da fenti amma komai ya kammala kuma ma'aikata suna tsaye a kai. Yaji dad'i sosai da sosai ganin yanda sabon company shi ya koma tamkar Wanda aka dauko shi daga America aka dasa shi a gurin tsari da k'atuwar company ba'a cewa komai, nan ya zauna da tsofaffin ma'aikatan sa suka yi meeting akan yadda za'a tsaurara matakan tsaro a gurin, kuma dole za'a dibi sababbabin ma'aikata, Amana ya damk'awa Bashir Manager saboda yasan ya wuce chana gobe zuwa jini domin yaga wane irin cigaba a ka samu a can d'in.

Harabar gurin ya futo yana kewaya wa hannunsa goye a baya, tabbas zakaran da Allah ya nufa da chara ko ana muzu ana shaho sai yayi

Wani ma'aikacin gidan talavition ne ya k'araso gurinsa a nutse yace." Ranka ya Dade dama tun d'azu muke jiran futowar ka, mun dad'e a waccan rumfar muna zaman jiran ka."
Kallon gurin da yake nuna masa yayi sai ya gansu a zazzaune su kusan hud'u. Cike da mamaki yace." Me zaku yi min kuma."? Ma'aikacin yace." Ranka ya dad'e 'yan tambayoyi zamu yi maka a gurguje." Girgiza kansa yayi ya rasa me yasa suke bibbiyar sa, yace." Muje can d'in" wata k'atuwar rumfa suka nufa wacce take kewaye da wasu had'addan kujeru na silver gurin hutawa ne an kammala tsaf hatta da tayel an saka a gurin fenti ne kawai ya rage, kujera suka gyara masa ya zauna sannan kowa ya sai ta na'urarsa. Cikin nutsuwa d'aya daga cikin 'yan jaridun ya fara kwararo masa tambayoyi kamar haka."

*"Yallab'ai dama muna son Karin haske ne daga gurin a game da labarin da muka samu sati d'aya daya wuce shin da gaske bayan wannan company da ake aikin sa wai akwai wasu guda biyu a k'asashen waje? Yallab'ai muna buk'atar Karin haske akan wannan jita jita da jama'ar gari suke yi mussaman 'yan kasuwa."*

Murmushi yayi kawai yana girgiza kan sa ta tabbata kenan duk abunda yake idanun mutane a kansa yake, shidai a iya sanin sa babu da Wanda sukayi zan can cewa zai bude company a america da Ingila sai Anthony sai granny su kadai ne sukan wannan maganar.

Gyara zaman sa yayi sosai yayi gyaran murya alamun zai fara magana, duk suka matso da lasifik'an su, Yace." *K'warai kuwa ba jita-jita bace gaskiya ne maganar jama'ar gari tabbas ina shirye-shiryen bude company guda biyu d'aya a America daya a Ingila sati mai zuwa za'a gudanar da bukin budewar a can kamar yanda za'a gudanar anan, ina yi wa 'yan kasuwa albishir da cewar duk me sha'awar futa waje yayi odar kaya to ya je company mai suna A'A ABUL ABBAS MAI NASARA, babu shakka zai samu duk wani na'uin kayan idai ya ka sance Wanda d'an adam yake sanyawa a jikinsa ne, kamar kayan mu na hausawa k'ananun kaya suit da sauran su akwai b'angaran kayan mata ko wane iri ne, takalma na maza da na mata duk company zai kawo kan farashi me sauk'i , sannan duk abunda company na kasashen waje zai kawo a kwai shi a wannan company nawa*

D'an jaridar yace." Sai tambaya ta biyu Yallab'ai, ina fatan samun amsa a gurin ka, kamar yanda muka samu wannan amsa ta farko munji kuma mun gamsu."
"Shin Wai kana da aure Ku kuwa? Da yawa mutanan gari suna yi maka kallon Mai lyali Yallab'ai muna son mu samu wannan amsar daga bakin ki." Murmushi ne ya sub'uce masa, ya d'an Sosa kansa kamar yanda ya saba yace." A'a bani da aure a yanzu a sali ma ban shirya yin sa ba, tunda a halin yanzu bani da budurwa da na tsayar a matsayin wacce zan aura, to amma shi aure lokaci ne dashi idan yazo ko da matar a hannu ko babu A lokacin sai Allah ya kawo ta ayi ina fatan daku da jama'ar gari da duk wani me kaunta zaku taya ni da addu'a kan Allah ya zab'a min mace ta gari."

D'an jaridar yace." Insha Allahu Yallab'ai zamu taya ka da addu'ar Neman zab'in Allah ubangiji Allah ya baka mace ta gari tare da 'yaya masu albarka, mungode mutuka da bamu lokacin ka daka yi Allah ya kara maka suttura da daukaka ya kare ka daga sharrin masu sharri."

Hak'ika Amjadu yaji dadin addu'ar da Dan jaridar nan yayi masa, amsa da "Ameen suma ameen nagode K'warai da addu'a."
Nan suka had'a na'urorin su cike da murnar samun nasara yau sun same shi ba tare da sun kai ruwa rana ba."

Sai bayan sallah magariba ya bar company din hankalinsa kwance ganin komai ya kammala, tun a mota kira yake shigowa wayoyin sa, ko d'aya bai d'auka ba, draving din sa kawai yake yi saboda ya san dai bai wuce jama'ar sa ba masu son jin ta bakin sa, tunda ko wace kafar sadarwa ta jahar kano a labaran ta na yamma ta  sun sanyo jawabin sa, shine dalili kawai hatta da gidan television na NTA kano suma sun hasko shi cikin labaran su na k'arfe shida, yana ji a jikinsa kamar akwai wani babban al'amari da zai same shi anan gaba.
Kai tsaye gidan granny ya nufa domin yayi mata sallama.

*****

Governor ne da gaggan 'yan kasuwa wad'anda suka ci suka ts dakai marasa tausayin na k'asa dasu Wanda Kansu kawai suka sani. Masu bakin ciki ga duk wani Dan kasuwa da ya sauke farashin kayansa, a cewar su talaka ba abun tausayi bane. Su biyar ne a dakin meeting din gidan gomnati wato government house suna tattaunawa game da yanda zasu b'ulluwa Amjadu domin dukaninsu saurari jawabin sa, na yau, hankalin su yayi masifar tashi sosai jin wai har company biyu ya bude a kasashen waje bayan company shi nan Lallai ya zama dole su San yadda za'ayi su rusa shi.

Alhaji Sunusi mai leshi ne Yace. " Ni ina gani kawai mu  hada baki da ma'aikatan sa mu Sakar masu KUDI Sosai mu fada musu bukatar mu. Cewar muna so su sanya algus da mugunta a ko wace irin adduga da zasu sarrafa, a company ta inda duk kayan da za'a futar a company su zama marasa k'wari da karko kunga daga nan Jama'a zasu gane sai su fara guduwa."

Mai citta ya gyara zama hade da sakin murmushin mugunta yace." Wannan shawarar taka tayi kyau kuma itace abar d'auka dole zamu San yadda mukayi mu jone da ma'aikatan nasa idan muka jik'asu da kudi kome ye zasu yi ko ya kuka gani."?
Duk suka yi na'am da haka, nan taro ya watse ko wannen su cike da farin ciki.

*****
Tana zaune a parlor kamar ko da yaushe me aikin ta Iyami na zaune a gefanta tana bata labarin garin su, yayi sallama ya shigo parlor, Iyami dattijiwa mai kirki ta dinga yi masa sannu da zuwa had'e da tsokanar sa, zama yayi cikin kujera yana gaishe ta, ta amsa da fuska a sake, da sauri ta nufi kicin domin ta kawo masa abunci.

Granny ta kalle shi babu yabo babu fallasa tace"K'ato me k'irar damu dawa kana tafiya gotai-gotai da kai babu iyali kai ko kunya baka ji, ka kai munzali amma ka tsaya shirme."

B'ata fuskarsa yayi yace. " zan can kenan daga zuwa sai maganar aure wai a kanki nake ne." Granny tace." Yo ni in a kaina kake ai da tuni ka kashe ni. Dube ka don Allah kamar zaka ji babu jiki a murd'e ai kai kam matarka zata fad'awa 'yan garinsu."
Gyara zaman sa yayi yana dariya kasa-kasa yasan halin kakar tasa da sakin magana ko wace iri ce ita babu ruwan ta, kafin yace wani Abu yaji tace" ka fad'amin in baka da lafiya sai in baza ma nema maka magani ko kauyen su Iyami muka je nasan za'a samo maka maganin k'arfi, ina amfanin girman jiki da k'wanji babu fus!! Uhum? Irin Ku ne matayen Ku suke shan takaici a zahiri dai gaku maza a bad'ini kuwa sai takaici." Ta k'arashe maganar ta tsakanin ta da Allah.
Gyara zamansa yayi da k'awataccan murmushi a fuskar sa yace." E dama na kasa fad'a miki bani da lafiya don Allah ki shiga k'auyika ki nemo min maganin k'arfi kinji."!! Granny ta kalleshi da hankalinta a tashe tace"Yanzu kai k'ato da kana fama da wannan lalurar ka zauna sai dai kaci ka sha ka nemi kudi? Au! Ko da naji shiyasa ko wace mace aka kawo maka sai kace bata yi maka ba, tom yanzu yaya kake ji a jikinka shin kana sha'awar mace sa'i da lokaci ko A'a."!? Granny ta tsarashi da tambaya hankalinta duk ya tashi.
Kamar gaske yace." Kwata-kwata bana jin sha'awar mata, amma ina ganin a haka zanyi auran da kike so nayi." Tace" innalillahi u ni 'yasu! Amma yaron nan kaso kacuci kanta.....Iyami Iyami Iyami.!" Ta dinga kwala wa mai akinta kira.

Yace." Nifa ba cewa nayi kiyi min taron dangi ba, uhumm ke kad'ai na fad'awa damuwa ta." Hararasa tayi tace"Naji kana maganar zaka yi aure a haka Uwar me zaka tsinanawa matar taka, abunci da madara kawai zaka bata bukatar ta kuma waye zai biya mata."! Cike da tuhuma tayi masa tambayar." Dariya yake sosai yace." Ai Irina zan auro kinga bani da matsala ."
"To baka isa ba ehe! Nima ai ina son 'yan yara, a gaba, ni kawai zaka cuta.'!!! Tsakanin ta da Allah take maganar, Iyami ta shigo parlor da sauri take fadin" Hjy kira kike ko."? Granny tace"Iyami zama bai kama mu ba, k'ato babu lafiya." Iyami ta kalleshi cikin rawar baki tace"Mai gida babu lafiya Ashe? Allah ya kawo sauk'i.'"  Yace." Ameen Iyami ai tace"Zata shiga ta futa ta samo min magani."  Iyami tace"Hjy meye yake damun Shi ne." Granny tace"Iyami je ki cigaba da aikin ki zamuyi maganar idan anjima." Iyami ta mike da jiki a sanyaye. Kallo ya bita dashi yana kumshe dariya.
Ita kuwa granny surutai kawai take masa tare da yi masa fad'a ya zauna cuta yaci k'arfin sa,  saboda yana so ya zama lusarin namiji.
Aikuwa tana tsaka da fad'an ta taga an hasko shi a TV tashar CTV kano mutane kewaye dashi yana jawabi.
Tace." Duba ka gani k'ato dubi yanda Allah yayi maka kwarjini da daukaka ta jama'a kudi duk kana da su. OO ni! 'Yar nan Allah kar ka jarrabe mu da abunda baza mu iya ba." Granny ta fashe da kuka sosai! Cike da mamaki yake kallonta, ganin da gaske kukan take yasa ya rungume ta a jikinsa yana rarrashinta tayi shiru yasan ko ya fad'a mata da wasa yake ba yarda zata yi ba ganin yadda duk ta tada hankalinta yasa yace." Granny kiyi hakuri ki daina kuka don Allah zan yi aure in haihu, ina  ganin ma yanda nake jin k'arfi a jikina in dinga bada k'wayayen 'yan biyu ko uku , ki kwantar da hankalin kinji kiyi shiru kiji wani."Shiru granny tayi tana share hawaye tsakanin ta da Allah.
Wayarsa ya ciro daga aljuhu yace." Bari in kira miki ita Ku gaisa." Tace"wacece kuma"?
A hankali yace "My wifi mana."
"Meye wifi."? Ta tambaye shi dariya yasa yace." Matata mana."? Sakin fuska tayi tace" 'yar albarka ta yarda zata aure ka da lalurar ka ko.'? Gyad'a kansa yayi kamar gaske, yana laluban numbar Mimi, sai da ya kira sau uku ba a d'auka ba, shi da in yayi kira sau d'aya baya sake wa, yau gashi yayi uku, yana shirin yin na hud'u.

Mimi na band'aki a lokacin ta kuma b'oye wayar bayan katifar mu, ina shigo wa naji ringing din waya, dube-dube nake sam ban ganta ba, in da nafi jin karar tayi yawa nan na nufa na janye pillow da ta kare wayar dashi, ina dauka kiran yana katsewa, wayar na rik'e a hannuna ina dubawa cike da mamaki! Tabbas wayarsa ce, ga k'amshin sa nan jikin wayar domin hanci na ya Riga ya gama sanin k'amshin sa.
Wani kiran ne ya shigo  kamar kar in dauka sai kuma wata zuciyar tace"dauki kije abunda zai je da Mimi, dannawa nayi na bud'e  speaker sosai na aje ta kan kati far. Muryar sa naji yo yana fad'in"Ungo wayar gatanan Ku gaisa, kafin in an kara Naji muryar mace, macen ma ba yarinya ba, dattijuwa me kamali. Motsin Mimi naji a tsakar gida, da sauri na k'wala mata kira ina fadin"Mimi kizo an kira wayar ki."!!!!!!! Granny da shi kanshi uban gayyar suka yi sak! Yayi wa muryar ta farin sani saboda tana da saurin baki kuma bata kaurara murya tana da zaki don haka Ku cikin mata dubu ta shiga zai iya gane muryar ta.

Wani kiran na kara kwala wa Mimi tare da fad'in"Mimi wai ki ba kya ji ne, Habibin ki ne fa kiyi sauri kar ta katse........ Muryar matar Naji tana fad'in" D'iyar arziki sanun ki kinji Ubangiji Allah yayi miki albarka nagode mutuka zaki auri jikana duk da lalurar da take damun sa....ko da yake naji yace." Kema baki da lafiya, kuyi hakurin insha Allahu zamu shiga mu futa Dom......Kafin ta karasa naji yo muryar sa Yana fad'in"Nifa ba cewa nayi ki wani jawabi ba, cewa nayi Ku gaisa da My wife dina kin tsaya wani zance."!! Ji nayi tace" Matsa ka bani guri don Allah , ai wannan yarinyar ta isa a jinin na mata saboda tayi jahadi.... Dariyar shi na jiyo Yana fadin"Sai kiyi ai."" Ta cigaba da cewa"Allah yayi miki albarka kinji ko."  A hankali nace" Ameeen amma bani bace budurwar tashi tana band'aki ni Sunana Asma'u ita kuma Mimi in ta futo za'a..ban k'arasa ba Mimi ta shigo dakin. Nace." Yawwa ga Mimi nan. wayar na mik'a mata na futa daga d'akin.
Kwata_kwata ban fuskanci komai ba Dan gane da maganganun da matar take,cikin zuciyata dai nake cewa"K'ila sunyi wata hira ne shi da Mimi tace mishi bata da lafiya, tom ni dai a iya sanina Mimi bata da wata cuta wacce bamu San da ita ba, asalima Mimi bata fiye yin ciwo ba, sai shekara-shekara take zazzab'in nan Wanda ake fama dashi.
Cikin zuciyata Naji tausayin ta, kuma nayi alk'awarin sai na tambaye wane ciwo ne yake damunta Wanda har ta kasa fad'ar shi a gida ta tafi waje tana yad'awa... Tsintsaya na dauka na hau share-share dama Umma bata nan taje suna sai  mu kadai a gidan. Ta futo daga d'akin sai kace wata Mara gaskiya, kallonta nayi, ni yanzu tausayi take bani ganin yanda ta hada kanta da babban aiki. Sam yanzu na daina jin haushin ta, nace" Kun gama ne " zama tayi kusa dani tare da fadin "Eh, Ashe kakarsa ce wai take so mu gaisa shine ya kira ni." Cike da nazari nake kallonta nace"Mimi wane irin lalura ce dake da har kika kasa fad'ar ta a gida, kika fad'awa saurayi Wanda baki da tabbacin zai aure ki."? Yanda na tsare ta da ido ina tuhumar ta sai ka rantse da Allah uwarta ce ni ko yayarta.
Cike da mamaki take kallona tace." Ban gane abunda kike nufi ba."? K'wafa nayi cike da takaici nace"dama baza ki gane ba, naji wannan matar tana fad'in"Zata je ta nemo miki magani dake dashi kuma kinyi jahadi tunda zaki aure shi."
Ranta a d'an b'ace ta kalle ni tace"Kinga Asma'u ya zaki tasa ni a gaba kina min wata tambaya kamar wata uwata, ni babu wata magana da mukayi dashi. " Nace" Ok k'arya nayi kenan."!? Tab'e baki tayi tace"ke kika sani kuma" a hasale nace"To ki kiyaye wallahi duk inda kike tunanin wannan guy ya wuce gurin, naga soyayya ta rufe miki ido kina nema ki futa waje ki tona mana asirin gida, duk lalurar da ke damun ki nasan kika fad'awa Umma zata yi miki magani iya iyawar ta, ke da kanki Kin san kafin tayi min Abu tayi miki sau dubu me zai sa ki watsa mata k'asa a ido kije ki zauna kiyi tunani da kyau kafin kowa yasan abunda yake damun ki ita yafi kamata ta sani, amma..........Kinga Asma'u.!'" Mimi ta fada tare da D'aga min hannu a fusace ! Ta mik'e tsaye.
"Gwara ki nuna min cewar a gidanku nake zaune,Asma'u gwara kiyi min gori saboda ina zaune a karkashin inuwar Ku, amma ina so ki San wani Abu kin San dai nima ba daga sama na fad'o ba ina da Iyaye ina da dangi masu rufin asiri Ubana yana Raye a duniya sai dai kice ba a gari yake ba, tom insha Allah Allahu zan bar muku gida Asma'u kada wataran ki ce sai na biya Ku kud'in hidimar da iyayen ki suka yi min tun ina jaririya hakan ma na gode." Dugu ta shige dakinmu tana kuka!!! Jikina ne yayi sanyi Mimi daga magana zata yi min wata fassara ta daban, tunda muke da Mimi mu kwana mu tashi guri guda bamu tab'a fad'a na cacar baki ba,ko mu fadawa junanmu munanan kalamai, nice dama mafad'aciya in taga na hau sai ta sauko ko ta maida abun wasa,Mimi bata tab'a gaba dani idan inayi ma dariya take min, tayi min magana har in gaji in sauko.
Mik'ewa nayi na bita dakin namu na tsaya bakin k'ofar shiga, ina kallonta tana ta had'a kaya tana kuka,
Babu yabo babu fallasa nace" Mimi daga magana zaki yi min wata fassara ta daban, har kike had'a kayan ki, Mimi kina da wani gidan ne bayan wannan? Baki da Uwa da ta wuce Umma kuma baki da 'yan uwa sama damu, idan abunda na fad'a ya b'ata miki rai Allah ya baki hakuri." Nafada ina shigowa d'akin..... Akwatin da take had'a kayan na d'auke ina fad'in"So kike yau Yaya Aminu ya kusa kashe ni a gidanan kenan? Ko so kike Umma ta tsine min.? Kiyi hakuri bazan k'ara yi miki magana irin wannan ba."
Mimi mai saukin kai da saukin hali tace." Kin kasa fahimta ta ne Asma'u amma na fada miki babu wata magana da mukayi dashi wai bani da lafiya, idan bani da lafiya sai kin Riga kowa sani tunda tare dake muke kwana muke tashi a daki daya."
Domim a zauna lafiya nace"Nagane yanzu mybe shima yana tsokanar kakar tashi ne." Ta goge hawayen ta tare da fadin " ni ma nafi tunanin haka." Akwatin na d'auke na mai da ita inda take, nace"Tashi mu shiga kicin kar Umma ta dawo kin ga magariba ta kusa."
Mik'ewa tayi muka futa daga d'akin.

******

*Amjadu* tun lokacin da Granny ta mik'o masa wayarsa bayan sunyi sallama da Mimi yake tunani Muryar yarinyar da yaji ta tayar masa da wani azabbanan fleengs sosai daurewa kawai yake amma yau yana ganin  dole ya ragewa kansa damuwa saboda yadda yake jin mararasa na kullewa alamun sparm ya taru sosai. Lumshe idonsa yayi hade da Dan Mike k'afafun sa, jira yake gari yayi duhu a idar da sallahr Magariba yaje ya ragewa kansa damuwa.
Domin had'uwar su ta d'azu ta  tayar masa da sha'awa kausasan kalaman da tayi amfani dasu ne suka d'auke masa sha'awar ta a lokacin, tayi mugun b'ata masa rai.

Granny ta mike tana fadin"kar dai kayi bacci nan da lokaci k'ankani zaka ji kiran sallahr magariba, shiru yayi mata bai ce komai ba, ita kuma ta shige kicin..... Nan massalacin jikin gidan yayi sallahr shi a gurguje ya dawo gidan ko zama bai yi ba, yace." Zan tafi ni." Granny tace"ga abunci can Iyami tana jera maka a daining ya kamata kaje kaci tukkuna.
Girgiza kansa yayi yana d'an Sosa kunnen shi da key yace." Na koshi kinsa n bana cin Abu me nauyi da daddare damuna yake." Tab'e baki tayi, yace.' Gobe zan tafi chana kiyi min addu'a." Tace"Allah ya tsare min kai gaba da baya sai ka dawo."
"Ammen suma ameen si ba wani dad'ewa zanyi ba." Tace"To Allah ya tsare ya baka abunda kake nema."
"Ameen yace sannan ya futa da sauri!

Kai tsaye! Wani shararran hotal  ya nufa domin ba zai je nashi ba saboda idanun jama'a ,  yana mota yana tunanin wace yarinya zai nema,a halin yanzu shi kanshi addu'a yake Allah ya raba shi da wannan neme-neme Matan na jaraba da yake, tun bayan haduwar sa da yarinyar bai kara yin sex da wata mace ba bayan 'Yar gidan me citta, shifa ko a yanzu bai ce dole sai yayi sex ba romantic kawai ya ishe shi mutukar ya samu yarinyar da ta iya wasa, zuciyarsa ya ayyana ko ya kira Hibbah tunda yana da numbar ta.
Wayar sa ya d'auka da hannu guda d'aya hannun kuma yana driving dashi ya fara Neman numbar Hibbatu.......









*2/November/2019*
[11/3, 11:20 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*


*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*

*38*


Hibbah na zaune a bedroom dinta da wayarta a hannunta tana kallon wani blu film sai mutsu-mutsu take yi hankalinta yayi masifar tashi, a halin yanzu babu abunda take muradi in ba sex ba, lips dinta ta sanya a bakinta tana dan ciza, don jaraba taki ta daina kallon fim din, shigowar kira taji a wayar ta tana dubawa taga Amjadu ne, sai da wayar ta kusa fad'uwa k'asa don murna, da sauri ta danna tana saki wata ajiyar zuciya tare da langwab'e murya tace"My Amjad.. Ka tuna dani kenan. " ? Cikin yanayin maganar shi yace." Kina ina ne."? Murya a kashe tace ina gida ko kana nema na." ?
"Eh kizo *Shakira Hotal* yanzu ina jiran ki." Cike da murna tace" daga nan zuwa mintuna ashirin zaka ganni."
Yace." Ok" hade da kashe wayar.

Da gudu ta shiga toilet kamar. Wata mahaukaciya ta watsa ruwa ta futo a gurguje ta tsaya gaban mirror tayi b'arin turare a jikinta wasu mutsiyatan English wears ta dauko riga da siket masu bin jiki ta sanya a jikinta sai ta sanya after dressing akai mukullin motar ta dauka ta futa da sauri sai baza kamshi take.
Momy ta na zaune a parlor tana kallo tace"sai ina kuma"? Hibbah na tafiya take amsawa da cewar "Zan je gidan su Hanifa ne." Ba tare da dogon bunki ce ba Momyn tace"sai kin dawo ki gaida min da Momynta"
Hibbah tw fuce ba tare da ta amsa mata ba.
K'arfe 8:00 dai-dai Hibbah ta Isa Shakira Hotal, haske ko ina  samari da 'yan mata sai shige da fuce suke abun su, wasu na bakin swimming suna hutawa wasu na gefe a zaune kowa da abunda yake yi, wayar shi ta kira tana tambayar shi wane room yake.

Yana kwance kan wani had'addan bed daga shi sai gajeran wando idanunsa a lumshe suke shi kadai yasan abunda yake tunani.
Hibbah ta kwankwasa kofar. Cikin rashin k'warin jiki ya mike yaje ya bude mata.
Wani mayan kallo tabi shi dashi ta mayar da kofar ta rufe harda murza key. Idanunsa ta kalla taga sunyi jajawur dasu, da sauri ta kalli kasan shi, wani murmushi ta saki Wanda kana ganinsa kasan na farin ciki ne, rungume shi tayi hade da murza masa fatar bayan shi, tana yi masa magana cikin wani irin salo.
A take jikinshi ya fara rawa ya matse ta jikin kofar yana shinshina wuyan ta.
A hankali Hibbah ta zame after dressing dake cikin ta, ta fad'i k'asa ta d'ora hannunsa akan k'irjinta tana wani lumshe idonta
Damk'ar breast din yayi yana lugwigwita shi a hannusa,
Hibbah ta saki wata kakar dad'i tana gamtsaro masa kirji, cikin futar hayyaci ya d'auke ta caK bai dire ko ina ba sai bed, yayi mata rumfa hade da zuba mata jajaen idanunsa masu saukar mata da kasala.
Hannunta ta zura a gigice tana k'okarin cire masa gajeran wandon dake jikinsa. Hannun ya cire hade da matse su a nasa Hibbah ta gigice salon soyayyar guy tana nema ta kashe ta.
Kafarta guda ya d'aga sama ya sabule siket din jikinta.
Ya jefar dashi kasan gurin.da sauri ta mik'e zaune ta cire rigar ta manyan nonowan ta suka bayyana, kwanciya tayi plate kan bed din tana wata irin mik'a, ganin manya nonowan Hibbah ya gigita shi sosai ta inda ya kasa gane shin Hibbah ko Asma'u a gabansa, a gigice ya kai musu wawura yana sakin wani irin nishi.. Hibbah ta bude masa k'afafun ta shiga tsakanin ta hannunta tasanya ta rungume shi kam! Tana sakin ihun dad'i.
Ni dai nan na futo na bar su.
Ina wa *Amjadu* addu'ar Allah ya yaye masa wannan jarabar Neman Matan da yake.

Wani irin nishi! Nake jiyo wa, wata zuciyar tace." Maza Lek'a ki gani me yake faruwa.
Abunda na gani yayi mugun bani mamaki da haushi  Amjadu ne kan Hibbah d'are-d'are bananar shi a bakin ta tana tsotsa kamar wacce ta samu alawa me shegen zak'i, shi kuma sai sakin nishi! Yake hade da murza nonowan ta cikin futar hayyaci. Da sauri na koma da baya ina mamakin Amjadu. Na fi minti goma kafin in kuma lek'awa inda na hangosa ya sauka daga kanta yana zaune a gefen bed d'in ita kuma ta bayan shi, tana shafawa, alamun kuka naji na kasa kunne na sosai, sai naji tana fadin"don girma Allah kazo ka hau kaina wallahi ni idan ba shiga ta kayi ba. Bazan samu nutsuwa ba."
Muryar ta na rawa ta k'arashe maganar

D'an ture ta yayi yana k'okarin mik'ewa da sauri ta rik'e hannunsa tana murzawa magana take masa k'asa-k'asa.

Gani nayi ya fuzge hannun shi ya shiga toilet da sauri.! Hibbah ta kwanta kan bed din share-share ta ware k'afafun ta, hade da zura d'an ya tsanta guda a gurin tana wasa da gurin tare da sakin wani irin nishi tana lumshe idonta.

*Ko mawa nayi da baya ina tur da halayyar Amjadu da Hibbah gaskiya ko ni yau yayi mugun bani haushi wallahi*

Ko da futo ya ga halin da Hibbah ta ciki bai damu ba, kayansa ya sanya hade da d'aukar key d'insa ya tsaya kanta fuskarsa babu walwala yace." Zaki ji alert a wayar ki."
Hibbah ta kalle shi  Jan ido tana fad'in"Kai wannan ya dama, ni babban alert d'ina inji kana ci na shine damuwa ka tayar min da hankali kuma zaka tafi ka barni wallahi da nasan haka zaka yi min bazan zo ba."

Kafad'ar sa ya d'aga sama alamun abun be dame shi ba, ya sa kai ya fuce daga d'akin. Hibbah ta fashe da kuka tana matse cinyoyinta ji take kamar taje tayi masa dole, lallai guy nan ya cika tantari sai da ya bari tayi laga-laga sannan zai gudu ya barta bayan ita ta biya masa bukatar sa.Haka dai Hibbah ta dinga wasa da gabanta har ta samu ta rage wa kanta damuwa ta mike da ido jazur ko Wanka ba tayi ba ta zura kayanta hade da d'aukar Jakarta ta futa daga dakin ranta a mugun b'ace!

Shi ko Amjadu gida ya koma lokacin sai da ya kara Wanka ya futo daure da towol a jikinsa gefan gado ya zaune cikin dauriya domin bai gama zubar da sperm din nasa gaba ga daya ba, tun da suka had'u da yarinyar sha'awa take taso masa akai-akai yanzu haka mamar shi daure wa kawai take, Hibbah tayi masa wasa sosai yanda zai gamsu amma ji yake idan ba sex yayi ba zai samu nutsuwa ba, baya bukatar kowa a lokacin sai Yarinyar ko meye dalili oho.
Shine abunda yasa ya tsallake Hibbah ba tare da ya biya mata bukatar ta ba saboda baya cikin nutsuwar sa.
Stytem d'insa ce a kan cinyar sa, suna magana da Anthony, sai wajan k'arfe daya da rabi ya kwanta.

********
Da shiri zuwa karb'o din kunan mu muka tashi, amma sai mun fara zuwa gurin saloon tukkuna, ni da Mimi sama-sama muke yi domin har yanzu tak'i sakin jikinta nice ma mai k'okarin yi mata magana, tana amsawa babu yabo babu fallasa.

Ina zaune gefan katifar mu ina shafa mai Mimi na band'aki tana Wanka naji kakar wayar ta. Kallon wayar nayi ba tare da na dauka ba, abunda na gani an rubuta ya bani mamaki *My heart beat* da sauri na dauki wayar ina dubawa, gabana na fad'uwa numbar nake bi kamar ina karantawa kamar wata shashasha, tabbas shine, maganar ta sub'e min daga bakina, katsewa wayar tayi ko minti guda bai ba ya k'ara kira.
Naji kamar in dauka wata zuciyar tace min kar ki dauka babu ruwan ki. Ji nayi bazan iya hak'ura ba dannawa nayi tare da aje wayar kan katifa bayan na bude muryar.

Muryar shi naji mai cike da amo gami da sauti yayi sallama. Gabana ya tsananta fad'uwa
*"Hello momyna kina juna"* naji ya fada murya a lankwashe.. Kamar in kashe wayar sai dai na fasa,
Wannan murmushin nasa naji Yayi yace." Ku kuna tare da 'yar Uwar ki tayi miki kwarjini kin sa yin magana, domin na lura tsoron ta kike ji." Shiru babu amsa, yace." Ok Momy hope kin tashi lafiya domin itace babbar abun tambaya a gare ni. Yawwa bayan haka kuma INA son in fad'a miki zan je Chana yau insha Allah kiyi wa d'anki addu'a." Cikin taushin harshe yake maganar. " k'it!! Naji wayar ta tsinke, kura mata ido kawai nayi ina kallo Tare da tunanin maganganun da ya fada, Mimi lafiyar ta abun tambaya ce a gare shi, wato ya manta dani tunda ya gama latse ni ya San wacece ni, yanzu kuma Mimi yake so ya yaudara, Sam! Yanzu na dawo daga rakiyar guy nan.
Man shafawar na jefar kasa kwanciya nayi kan katifar wani irin Abu yazo ya tsaya min a mak'ogwaro na, lokaci guda Naji ruwan hawaye ya cika idona, k'okarin mai dasu nake inaaa!! Sai da suka zubo, hannu NASA na goge su da sauri domin kar ta shigo ta gani tunani nake yays za'ayi na hana Mimi kula shi, domin na lura tayi mugun nisa a gurin son shi.
Mimi ta shigo da sauri tana fad'in"Asma'u goma da rabi tayi kin ga har rana ta sauko k'asa.'' Nace" ni ai na gama ke nake jira." Kayan ta ta dauko tana sanyawa cikin sauri. Ni kuma na mik'e na futa daga d'akin.

Sai da mukaje saloon sannan muka karb'o d'in kunanmu sunyi bala'in kyau sosai sun matse ni dama haka nake so ko ina ya futo zam!zam! Dake Allah yayi min yalwar gashin kai bakikirin dashi, sai ya kara mik'ewa sosai da a ka gyara shi, abunda be dame ni ba kenan kwalliya da gashi amma gobe dole in tsula tsiyata son raina
Gidan aunt Hauwa muka wuce, muka tarar tayi bakuwa kawarta ce aunt Zainab tun ta k'uruciya nan muka zauna muna kallo muna hira aunt na soyo mana wainar fulawa wacce taji kwai da yaji me dad'i aikuwa na samu abunda nake so tuni na zage ina ci.

NTA HAUSA muna tsaka da kallon wani najeria film kawai suka katse tare da nuno *Amjadu* a filin jirgi lokacin yana k'okarin hawa matattakalar jirgi ya tsaya yana magana da wani d'an jarida, tsakanin ni da Mimi ban San Wanda yafi shiga d'imuwa ba, lokaci guda naji wainar da nake fi ta fuce min daga rai duk dadin ta kuwa.
Yana sanye da wasu uban suit blue and white hade da necktie d'insa  hannunsa daure da wani irin agogo na zallahr fata sai blue sai shek'i yake, k'afar sa sanye da takalmi rufaffafe black sai shaining yake, hannunsa rike da irin jakar nan ta matafiya.
Dan jarida bayan sun gama magana dashi sai ya juyo yana fuskantar TV din yace." *To masu kallon ga dai  Amjadu AbulAbbas Wanda kuka fi sani daYoung millionaire, zai tafi k'asashe biyu domin gudanar da harkokinsa na yau da kullum domin kawo wa k'asar shi cigaba muna yi masa fatan dawo wa k'asar shi lafiya tare da nasarori, duk wani me kaunar sa, sai ya raka shi da addu'a Allah ya bashi sa'a a dukanin abunda ya sanya a gaba.*
Yana gama maganar tashi
A ka d'auke shi, film din ya cigaba, aunt da kawarta suka dinga yi masa addu'a gami da fatan alkairi, Ni da Mimi kuwa babu Wanda yace." Uffan! Har yanzu ko wacce ita tasan halin da take ciki.
Aunt naji tana fadawa kawar ta abunda ya faru kwanakin baya, Zainab tace"Ko sonta yake ne."? Aunt tace " Nima nayi tunanin haka wallahi amma sai naga kwata-kwata bai nuna alama ba, Zainab tace"ke akwai dai abunda yake faruwa wallahi tunda nake ban tab'a jin ance ya dauki budurwa ya kai ta tayi shopping ba sai akan Asma'u ina ganin son ta yake."
Da sauri na kalli aunt Zainab nace"Bani yake so Aunt." Duk suka kalleni nace"Wallahi kuwa Mimi yake so." Mimi tayi saurin sunkuyar da kanta cike da kunya,
Aunt hauwa ta jawo ta jikinta tana dariya tare da fad'in"Kai Alhmdullahi kice wahalar mu ta kusa karewa dama nasan Mimi na ta shiga tsara ce babu namijin da bazai so ta ba farar mace alkyabar mata.. Wai!!!! Kice wata shekarar damu za'ayi aikin hajji.'"" Aunt Zainab dariya kawai take wa kawar tata ni kaina duk da halin da nake ciki sai da na dara ganin yanda aunt Hauwa duk ta gigice! Aunt Hauwa ba dai son kudi ba.

Nace"Aunt kinga ma wayar da ya bata." K'okarin dauko ta nake Mimi tana kwace jakar sai da na Ciro na mik'awa aunt ta karb'a tana dubawa hade da rik'e baki take fad'in"Mimi wannan wayar si tafi dubu Dari."" Lallai Juma'ar da zata yi kyau tunda ga laraba ake gane ta."
Aunt Zainab ta karb'i wayar tana dubawa itama jinjina kai tayi tare da fadin" har wani kamshi wayar take lallai abun na manya ne, Mimi Allah ya dubi maraicin ki, idan kika shiga gidan nan kar ki manta damu don Allah."
Cike da mamaki nake kallon su, ina mamakin son kud'in su lallai a duniya idan kayi kudi ka wuce komai Mimi tun kafin ta shiga gidan sun fara magiya.. Kallonsu kawai nake suna zolayar Mimi ita kuma tana wani sinne kai, cikin zuciyata nace "Kin had'u da aiki babba Mimi.

*********

K'arfe goma da kwata mun fito cikin shiri kamar wasu taurari Munnu nan tazo mu tafi tare, munyi bala'in kyau mussaman ma ni suffa da b'oyayyan kyau na yau sun futo a zahiri saboda abunda bana yi shi nayi wato kwalliyar fuska, kamar wata Queen haka na zama  muna sanye da material dinmu Wanda aka yi mana dinki duguwar Riga mai tattara daga baya daga gaba kuma yayi sama anyi masa wani irin yanke gege da gefe dogon hannu ne yayin da rigar ta kasan pitat gown ne   gaba d'aya rigar take tayi matse ni tam!! Nishi ma da k'yar nake, gani da manya breast da uban hifs  Sai da na sanya yari da sark'a na sannan na kalli mudubi, ni kaina nasan nayi kyau sosai, Munnu da Mimi suka saki baki suna kallona, nace" Meye wai!? Munnu tace." Anya baza ki cire kayan kuwa ba kinga yanda suka matse ki, ke gaki tubar kallah." Nace" lallai Munnu wallahi ko Umma yau baza ta hanani futa da kayan nan ba.Mimi tace" sai ki sanya hijabi idan muka je can ka cire,amma dai kin San gurin ya hada samari da 'yan mata duk budurwar da take da saurayi zata gayyace shi yazo gurin." Nace" Mimi ina ruwana wai don Allah Ku k'yaleni mana." Ganin raina ya b'aci ya sa suka k'yale ni. Umma na zaune s rumfa tana kule-kulen ta muka futo takalemu a tsanake tace "kunyi kyau tamkar wasu amare,amma ke Asma'u meye kika sanya hijabi."?
Nace" Umma dinkin ne ya matsani shine nace"idan na shiga cikin 'yan uwana mata sai in cire." Tace" haka yayi to Ku kula don Allah Ku tsare mutumcin Ku ana gama taro ku dawo gida kar Ku tsaya kad'e-kad'e da raye-raye." Muka ce insha Allahu."

Muna shirin futa daga gidan wayar Munnu tayi k'ara ts dauka a nutse tare da kashe muryar ta, kasa kunne nayi cike da mamaki jin tana ambatar sunan Shamsu. Ni da Mimi muka kalli juna. Ji mu kayi tana fadin"Eh ka shigo da motar yanzu zamu futo." Sukayi sallama, dukaninmu muka kalleta cike da mamaki nace"Munnu yaushe Shamsu ya dawo kuka kuma jone wa." Murmushi tayi tace" shekaran jiya ya dawo da k'arfin sa, Wallahi aurena zai yi domin aranar da ya dawo ma Baban shi yazo gurin Babanmu baku ga kayan da ya kawo mun ba, wannan hayaniyar da muke ciki ce ta hana ni fada muku."
Ni da Mimi muka Ce"Toum Allah ya sanya alkairi lallai alk'awarin Allah ya cika. " dariya Munnu tayi cike da farin ciki muka futa daga gidan. Samari na bakin titi suka bimu da kallo kamar wasu mayu.

Wata had'adadiyar mota na hango a fake gefan titi Shamsu na zaune a mazaunin dravar tare da wani Wanda ban gano fuskar shi na, suna sanye da wata masifaffaiyar shadda wagambari hade da hula damanga sunyi kyau har sun gaji. Ganin zuwan mu gurin yasa Shamsu futowa da sauri ya bude wa tauratowar shi motar yana fadin" Girman kujerar ki ne." Hararasa nayi tare da tab'e bakina nace"Haji Shamsu Ashe zaka dawo ai na dauka muma yaudarar tazo kanmu." Dariya yayi yace." Inaaa!! Baby Asma, Ai Munnubiya ta daban ce cikin mata, tab'e bakina nayi nace"Allah yasa da gaske kake."
Tunda na fara magana abokin Shamsu yake kallona ina kallonsa ta wutsiyar ido tsaki naja a fili na tsani kallo wallahi.
Munnu ta shiga ta zauna Mimi ta zauna nima nashiga sannan Shamsu ya koma gurin zaman shi hade da kunna motar muka tafi.
Shamsu sai janmu da hira yake yana fad'in"Ai duk naji labari lokacin da na tafi har daku ake cewa dama yaudarar Munnu nake yi humm yanzu Asma baby kina ganin zan aikata haka kuwa."
Nace"sosai ma kuwa Shamsu namiji ne fa kai hunm halin Ku sai Ku."Abokinshi ya juyo yana kallona tare da sakin murmushi yace." Baby Asma wasu mazan ne suka bata wasu amma abokina da gaske yake." Tab'e bakina nayi nace" muna da labarin fa duk 'yan Matan da ya yaudara sun kai goma. " Shamsu ya rike baki yana dariya tare da fadin" duk sharri ne wallahi, karya suke min." Mimi tace"Babu sharri nan gaskiya ce mu dai don Allah kar ka kara guduwa domin wancan karon sai da mukayi jiyyar ta" suka kwashe da dariya shi da abokinsa.
Munnu sai mintsina take wai in daina surutan da nake yi ina jinta na kiyin shiru.

****
Lokacin da muka Isa guri ya soma cika sosai aka kawata gurin gurin malamai daban da iyayen yara wajan dalibai daban, muma wajan mu daban wajan manyan baki daban .. Masu hotona da vedio baza su kirgu ba, saboda ko wacce da nata,muma mun dauki namu can muka tadda shi, MA kad'a sun fi su biyar suna gefe suna jiyar taro ya watse a fara shagali. Ko wane class da gruop d'insu da kuma irin kalar ankon su, ko wacce tana wace wannan.

Mai girma principal ya bude taro da addu'a  tare da yi mana nasiha sannan yayi wa 'yan matan da aka kusa bikinsu a cikinmu addu'ar zaman lafiya Wanda basu da mazaje Allah ya kawo musu, hakanan Wanda suke shirin cigaba da karatu Allah ya bada sa'a.

Haka Malamai suka dinga mik'ewa suna jawabi tare da addu'a, taro ya tashi guri ya hautsine kowa da ta wagar mutanan shi, da kawayen shi sai d'aukar hoto ake hade da vidio,

Ina gefe tare da jama'a ta domin wasu ma ranar na fara ganinsu duk ya wancin su maza ne, tuni na cire hijabina ina yawo yanda na gadama 'yan ajimu sai jana suke dole sai munyi hoto duk inda na sanya kafa abokin Shamsu nan yake sauke tasa ya zame min jele, haka na dinga shiga cikin abokan da samarin 'yan ajinmu muna hoto wasu nayi da waya wasu nayi da Camera man. Abun mamaki ni kadai jama'a suke ja lallai sai sunyi hoto dani, haka Alina ma duk gabar da muke da ita sai da tazo ta jani   cikin a bokanta maza da mata mukayi hoto wasu daga cikinsu na fiddo wayoyinsa nayi min.

Mimi ce tazo ta jawo ni da k'arfi tana fadin" meye haka kike yi don Allah ki daina ratsa maza kina shiga tsakiyar su baki San suba
Fuzge hannu nayi INA fadin "Kinga Mimi yau rana daya ce daga ita babu wata ki k'yaleni." Mimi ya rabu dani ta koma gurin Munnu da sauraynta

Duk ankon da mukayi sai da muka sanya su Shadda ce karshen sawa. Waiiiii!!! Fitina! Lokacin Dana futo cikin shadar  idanun jama'a kamar ya cinye ni, ni kaina sai  bayan na futo a haka Nazo ina da na sani dinkin fitat ne iya cibiya Sam rigar bata da hannu gashi ta matse ni, siket din yayi d'an, kwankwaso na kamar zasu yi magana  da kyar nake cire k'afa ta saboda yanda ya matse ni.
Tuni suka yo kaina suna ihu!!! Wani Dj ya saki wak'arnan ta *Hamusu brekar wato shimfidar fuska*  Filin na nufa sauran k'awayenmu suka rufa min baya, rawa sosai na dinga   *wakokin gwanja kamar ni na rera su* mussaman wak'ar shi ta *d'akin bak'uwa dudu bak'ar ashana* ai ina bala'in son wak'ar nan na zage ina rawa tare da sauran 'yan ajinmu Mimi ma da Munnu sun shigo filin ana yi da su.

Alina ce tazo ta ja hannuna wai inzo muyi sallama da abokanta, muka nufi bakin get, kamar walkiya naga gilmawar motar guy nan ta futa daga gurin. Abunda yasa na gane sunan shi dake bayan motar kuma na shiga cikin kusan sau biyu. Mamaki ne ya kama ni, mutumin da baya gari me ya kawo shi gurin nan.
Sama-sama mukayi sallama dasu na koma ciki ina tab'e bakina.

******
System d'in shi a kan cin yar shi yana dubawa Anthony na gefan shi yana waya cikin yaran na chana.
Sak'o ne ya shigo  yana dubawa yaga rambow ne, pictures ya fara gani kusan guda Dari suna shigowa,  da sauri ya bude yana dubawa, ji yayi zaman gurin ya gagare shi a sabili da abunda ya gani cikin loptop din shi, babu shiri ya mik'e da sauri ya shige wani had'addan bedroom  hade da sanyawa kofar key ya zauna gefen bed hannu na rawa yake duba hotonan  wani irin gum! Yana tsatstsafo masa a saman goshi










*3/NOVEMBER/2019*
[11/4, 11:56 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*39*


Yarinyar yake gani cikin maza ko ta ina, ga sassan jikinta a bud'e ko duk motsin da zata yi kana ganin saman breast dinta ga sunan a waje hankalinsa bai k'ara Tashi ba sai inda yaga ta shiga filin rawa tana juyi ana mata watsin kudi, wani uban ihu!! Ya kurma hade da jefar da loptop din ta fad'i kasa ta gangara can bakin kofa, mike wa yayi a zafafe! Ya kai wa bango duka da hannunshi!! "Ni wannan yarinyar zata tozar ta. ? Da k'arfi ya fad'i maganar, kaiwa yake yana kawo wa a dakin, a fusace! Yaje ya dauki wayar sa, yana lalubar Mimi, bugun duniya yayi tak'i shiga, jefar da wayar yayi ta fad'i kasa, dafe kansa yayi dake mugun sara masa, fuskar guy nan kawai yake hangowa Wanda yake nanikar yarinyar duk inda ta sanya gaba shine ya fi kowa zak'ewa, shifa idan ba idonshi ne yayi mishi gizo ba sai yace kamar yaga ya rungume ta, wani irin ihu ya kurma!!! Hade da sanya hannunsa biyun yana dukan katifar dake kam bed din sai kace wani mahaukaci, da sauri Anthony ya shigo domin yaji ihu!! Cin karo yayi da lopot bakin kofa a kife, cike da mamaki ya sunkuya ya dauko ta yana gyarawa, k'araso wa nan ma yaga wayar sa a jefe.. Ajiye loptp din yayi kusa dashi ya dauki wayar yana dubawa dake mai hade da batir ce kunna wayar yayi ta kama abunka da abu matsada nan take ta kama.
Zama yayi kusa dashi cikin harshen turanci yake tambayar sa." Dago kamshi Yayi yana kallonsa da idanunsa Wanda suka kad'a sukayi mugun ja!! Hannu ya mik'a masa alamun ya bashi wayar, da sauri Anthony ya mik'a masa wayar, Numbar Mimi ya kara kira is switch up, cikin sauri ya nemo numbar Rambo, bugun farko ya dauka, bai saurari maganar da yake masa ba, yace." A ina guy nan yake? I wiil kill you!!!." Rambo ya tsorata jin muryar Oban gidan shi, na wani irin rawa!! Yace. " Sir ban gan..........kafin ya karasa maganar ya katse shi cikin wata irin razananniyar tsawa yace." Rambo!! Ni kake fad'awa baka gane ba, Dan ubanka me ka turo min Yanzu."!!! Rambo yace." Sorry sir Wallahi ban San dai a ina yake ba, a tare dai suka zo gurin cikin mota.... Yace." Kafin safiya ka bunkito min a wani guri ya ke shi Dan gidan uban waye, sai na kashe shi."!!!!! Rambo yace." An gama sir insha Allah... Katse wayar yayi yana wani irin haki!

Shiko Anthony ya dauka irin mutanan sa Wanda suka sanyo shi a gaba wato abokan a dawar sa, sai ya dafa kafad'ar sa yana rarrashin sa da kalamai masu sanyi.
Gyad'a kansa kurrum yake yana tunanin irin hukuncin da zai dauka kan yarinyar da shi kanshi guy...wani irin rad'ad'i da zugi zuciyarsa take masa in da yake jin kamar ya Dora hannu aka yayi ta kurma ihu ko ya samu sassauci,, cikin maza don rashin nutsuwa ko wane namiji yazo ya jata kamar tinkiya ta bishi tana murguda masa mazaunai hade da gantsaro masa nonuwa duk Rabin nonuwan ta a waje da ta d'aga hannu hammata a waje
*Ya ilahi!!* abunda ya fada kenan da mugun k'arfi, Anthony ya mike da sauri gami da bude kofar dakin ya futa.
Minti biyu ya dawo hannusa rike da wata bak'alar kwalba wani Abu mai kyali a saman ta, bude wa yayi da sauri ya mik'a masa, cikin harshen turanci yake fadin "karb'i ka sha wannan zaka ji sassauci a zuciyar ka." Giya ce Anthony yake mik'a masa a zuciyarsa yace." Asma'u bata Isa ta sashi ya fara shan giyaba ko da zuciyarsa zata yi bundiga sai da ya mutu da bakin cikin ta. Kauda kansa yayi yak'i karb'a, Anthony ya aje kwalbar giyar da sauri ya Ciro kwalin sigari hade da leghtar ya kunna guda ya mik'a masa, aikuwa da sauri ya karb'a ya fara bata huta, duk guda zuk'a biyu yake mata ya shanye, tas!! Ya shanye kwali guda Anthony ya mike da sauri ya futa domin dauka masa wata, shi zufa kawai yake lokaci guda yaji wani irin sanyi-sanyi a jikinshi alamun zazzab'i ya kama shi. Kwanciya yayi rigingine kan bed din yana sak'e-sak'e cikin zuciyarsa

*********
Kwata-kwataKwata-kwata ma ni mantawa nayi da naga Rambo cikin jama'a na koma muka cigaba da sabgar mu, har lokacin da taro ya watse.
Ana kiran sallahr Magariba muka shiga gida, nida Mimi Yaya Aminu da Umma na tsaye da alama magana suke, kafin in an kara naji duka ko ta ina!! Ihu! Na kurma ina fadin "Yaya Aminu me nayi maka kake dukana." Fad'i yake "Asma'u gwara in kashe kan inga abun kunyar da kike k'okarin jawo mana banje gurin party Ku ba, amma ina da labarin dukanin abunda ya faru so kike ki futa zakka a jikinmu Asma'u Ashe 'yar iska ce ke ban sani ba,."!!! Ya k'arashe maganar cikin tsananin b'acin rai!

Umma naga tayi shigewar ta daki ranta a bace babu abunda tace kan irin dukan da yake min, kuka na fashe dashi INA fadin" wallahi Allah ba zai barka ba sai ya saka mi... Wani irin mari ya galla min tare da fadin" a gidan uwarki sai ya hau dukana da kafafunsa ina karewa tare da fashe wa da kuka.
Mimi na tsaye tana kallonmu daman abunda take guda kenan shiyasa tun farko ta hanani, ganin yanda yaya Aminu yake dukana ne yasa Mimi shahada taje ta rungume ni sosai itama tana kuka tana tayani bashi hakuri, amma saboda rashin imani na Aminu ko kallonmu baiyi ba ya dinga duka yana fadin "Ai dama bakinku daya, wato ke mai tausayi ko? Asma'u zata Kai ki ta baro.!!! Sai da yayi mana lilis sannan ya kyalemu.

Da Jan jiki muka shiga dakinmu ko wacce tana shararar hawaye Mimi tace" Tun farko abunda na hango kenan, amma da yake kedin me taurin kan tsiyace kika ji, kika dinga shiga cikin maza saboda rashin kamun kai, wallahi Kiyi wa kanki fad.... Katse ta nayi a fusace.! Nace"Mimi kiyi min shiru ki k'yaleni inji da guda d'aya mana.""" Itama a fusace! Tace"bazan k'yale ki ba Wallahi ai dama gaskiya ce bakya so sai kije kiyi tayi." Mik'ewa tayi ranta a bace ta fara cire kayan jikinta.

Ni ko zama nayi ina duba jikina inda Ya Aminu ya FASA min wani gurin ma har fatar ta kwailaye gefan bakina ya fashe hannu na  NASA na shafo jinin , a fili nace " Allah ya Isa Wallahi bazan tab'a YAFE wa, duk abunda nayi ai ba akaina farau ba, ballanta na ma banyi komai ba tunda dai ba kamani a kayi gidan karuwai ba ina zina ko ina cacah,tsabar mugunta da rashin tsoron Allah yayi mutum yawo aikin banza da wofi"!! Da k'arfi na karasa maganar domin ya Aminu yaji na dauka yana gidan, Umma ce ta d'aga labulen dakin tace" Yayi miki kyau! Asma'u wuyan ki ya Isa yanka kiyi ba dai-dai ba kice baza'ayi miki fada ba, lallai kin cika, kuma kin kai munzali Yanzu kin kara tabbatar min da cewar aure kike so bari gobe tayi da kaina zai wanke kafafuna naje gidan Kawun Ku Yunusa muyi magana gwara in aurar dake tun kafin ki jawo min abun kunya."
Da sauri na mike na Isa gurin hade da rike mata kakafu ina kuka tare da bata hakuri ina fadin"Umma wai me akace muku nayi a gurun party nan ne, Umma ki lura dani wallahi bazan tab'a zubar da mutumci na ba da kima ta ta 'ya mace, Umma ki yafe min kina kallon yanda Ya Aminu yake duka na kamar zai kashe ni." Umma ta fuzge k'afafunta ta futa daga dakin ba tare da tace komai ba

Bakin kofar na zauna ina kuka Mimi tazo ta tsaya a kaina tare da fadin "Bani waya ta,aikin kawai kin karar min da chaji a banza da hotunan ki, kin San ba wuta ake kawo wa ba"Wani irin kallo nayi mata ina gyad'a kai cike da takaici nace" Ki duba wayar ki cikin jakata gata can a tsakar gida. " tsallake ni tayi ta futa, daga dakin.
Chaji taje ta kai domin bai zama lallai su kawo mana wuta ba,
Ranar ko abuncin dare hanci ba, haka na kwana da cikina  tsabar bakin ciki ya hanani bacci sai juyi nake.

*****
Kamar yanda ta kwana tana juyi to shima haka ya kwana yana murk'ususu zuciyarsa Sam! Babu dad'i ga uban zazzab'i da ya kwana dashi, ko da asubah ma a daddafe yayi sallah Yana jira   gari ya waye musu a can , time din ko wace k'asa daban yake
K'arfe Biyar na asubah mun tashi Ya Aminu ne ya tsaya a kanmu har sai da yaga ko wacce ta mike tsaye sannan ya nufi massalaci, motsin Umma Naji a tsakar gida tana alwala da sauri na koma na zauna, domin bana son na futa mu had'u. Mimi ta futa ta barni,, ko minti biyu ba ayi ba kira ya shigo wayar Mimi, daga inda nake  in hangowa *Heart beat* sunan da nagi kenan, cikin zafin zuciya na dauki wayar na kashe! A fili nace"Aikin banza da wofi asubar fari za'a damu mutane. " wani kiran ne ya kara shigowa na kashe da sauri,, A'a wani kiran ya kara shigowa na kashe, sai da ya kira sau bakwai ina kashewa, yana kiran na takwas din ne kawai na kashe wayar gaba d'aya.
Nashi b'angaran sakato yayi da wayar a hannu lokacin da ya kira suka fad'a masa cewar an kashe wayar ma gaba d'aya, tunani ya shiga yi anya Mimi zata kashe masa waya kuwa? Why!!! Me yake faruwa ne.? Jefar da wayar yayi kan bed ya yunk'ura ya tashi zaune kwalin sigari ya dauko ya bata wuta ya fara fesawa cikinsa hayak'i da sanyi safiyar na, da sauri kuma ya dauko wayar tare da nemo numbar rambow bugu guda tayi ya dauka baki na rawa yace."good morning sir." Bai amsa ba yace." Meye labari ina fatan ka yi aikin da na sanya ka."? Rambow yace." Yes sir Ashe ma ba d'an gari bane yazo bak'unta ne dan barno ne wato mai duguri." Da babbar murya yace."kaje Sanar dashi cewar inji ya bar garin nan kafin in k'araso idan ba haka ba sai da uwarsa ta haifi wani Wallahi. "!!!! Rambo ya tsorata jin furucin oban gidan nasa, ta yaya zai iya zuwa ya fad'awa mutumi haka, amma duk Dan a zauna lafiya yace." Insha Allahu zani yanzu." Kashe wayar yayi yana huci!!!

Mimi ta shigo a tsanake ta shimfid'a dadduma ta tayar da sallah, futa nayi daga dakin nima domin dauro alwala. Bayan ta idar Da sallahr ne sai ta dauki wayar kawai ta ganta a kashe alhalin a kunne ta bar ta. Kunnawa tayi tana zargin Asma'u cewar ita ce zata kashe mata waya.
Aikuwa ko minti biyar ba ayi ba, kira ya shigo wayar tana dubawa taga *Heartbeat* wani murmushi ta saki had'e da kwanciya kan katifar tana lumshe ido ta d'aga wayar. Tare Da fad'in"Assalamu alaikum."
Sama-sama ya amsa murya a kaurare! Yace." Had'a ni da wannan yarinyar." Dai-dai lokacin dana shigo dakin kenan ina jin komai tunda a hands free wayar take.. Cikin tsawa yace." Ko ba kyaji ne."!! Mimi ta tsorata mutuka, muryar ta na rawa tace"Wace yarinyar."? Kai tsaye yace." Asma'u. " jin ya anbaci sunana yasa na zabga tsaki da k'arfi don yaji, aikuwa yaji lokacin da tayi tsaki! Sai ya mike da sauri jikinsa na wata irin tsuma! Kamar Wanda ya sha tsumin 'yan bori ya kwatsawa Mimi tsawa tare Da fad'in "Bata wayar naji ta a kusa dake."!!
Ganin yanda yake kurma wata irin tsawa ne yasa na fasa tada sallahr raina a mutukar b'ace na karb'i wayar da take Mik'o min murya sama-sama nace" ta bani wayar meye."!! Tsaye ya mik'e da sauri cikin hargagi yace." Budurwar 'yan daudu yarinya mai aji da kamun kai!! Budurwa me lasisi a jahar kano, duk naga abunda kikayi jiya, ki sani kamar a gabana komai ya faru! Wallahi-wallahi ki kiyayi haduwar mu dake sai kinyi mugun raina kanki!! Ni zaki zubar wa da mutumci...... Katse shi nayi kafin ya k'arasa maganar tashi nima cikin hayaniya nace" Kai!!!! Malam wai me ka dauki kanka ne? Meye ya shafe ka dani? Meye alakar ka dani da kake wannan ihun! To bari kaji naji dad'i da ka gani ka sani jikina ba irin na ko wane lusarin namiji bane irin ka mai aikata sab'on Allah yanzu nayi maka nisa! Kuma tab'a min jiki da kayi kwanakin baya na barka da Allah ehe!!! Ita ma Mimi addu'a nake mata Allah ya tsare ta daga sharrin k........."ShautUp Your dirty mouth."! A zafafe! Tsorata nayi amma saboda taurin kai yasa nace" Ank'iyin shiru d'in duk abunda na fad'a gaskiya ne ai Mtssss." Na buga wani irin tsaki had'e da jefawa Mimi wayar a cinyar ta. Ji nayi yana fad'i" Ok zamu had'u ne zaki San Wanda kike wannan rashin kunya wallahi sai kin maimata min duk abunda kika fad'a kuma, kiyi gaggawar korar wannan mummunar saurayin naki bak'i me kamar alade irin ki, idan ya sake Nazo sai na b'adda shi a duniyar nan."!!
Mimi tayi sakato da waya a hannu bayan ya kashe nu kuwa tada sallah ta nayi raina a mugun b'ace!
Wani irin tunani take a zuciyar ta, wannan tashin hankali da guy nan yake yi na lafiya ne kuwa? Anya ba son Asma'u yake ba? Take tambayar kanta, in kuwa hakane babu shakka rayuwar ta tana cikin garari domin baza ta iya had'a miji da Asama ba, gashi duk duniyar nan babu namijin da take so kamar sa, tana ganin sai da ta mutu babu aure.

Wayar ra dauka tana neman numbar sa, bugu guda ya dauki wayar, cikin siriryar muryar ta tace"My kayi hak'uri don girman Allah nasan ranka yanzu a b'ace yake, babu shakka Asma'u bata kyauta ba."
Ajiyar zuciya ya sauke a kashi d'ari na damuwar sa kashi casa'in ya ragu , yaji dadin maganar Mimi yace." Momyna 'yar uwarki bata da kirki wallahi kanta rawa yake yi, ki rink'a yi mata fad'a kinji ko."

Mimi tace"Kullum kuwa cikin fad'a muke yi da ita Sam! Asma'u bata son San gaskiya, wallahi." Ina ji ina sallahr lallai Mimi har sunyi sabon da  zata dinga kai suka ta a gurin shi.sauri nake in idar muyi wacce zamu yi da ita.

Ina jinsa yace." Kar ki biye mata da duk abunda zata yi miki na rashin mutum ci domin na lura tashan balaga take, idan tayi ba dai-dai ba ki yi mata fad'a koda zakuyi doke-doke da ita kuwa."
Mimi tace." Insha Allahu kar ka damu." Yace." Zan dawo gobe ko jibi kiyi min kwalliya me kyau sannan ki turo min pictures dinki ta whatsp zan gani." Cike da kunya tace" shikkenan ka bude data zan turo maka." Sallama sukayi Mimi tana saki murmushi daga ni tana cike da farin ciki.

Ina idar da sallah ko addu'a banyi ba nayi kan Mimi da masifa nace "Mimi kin Dade baki kai suka ta gurin sa, ba ki fad'i abunda ya fi haka a gurin shi ba damuwa ta bace, kece yake gaban ki da har idonki ya rufe a kansa kika kasa fari da bak'i aikin banza aikin hofi ina kara dai tunasar dake cewar kiyi hattara ki kula idan ba haka ba ke zai kai ya Baro....Wannan karon Mimi bata k'yale ni ba, itama a fusace ! Tayo kaina tare da fad'in" duk abunda zaki fada ki fada ke ya shafa kowa rai yayi wa dad'i ba kamar me shi ba ne Asma'u kije kiyi abunda kike so kuma wallahi kar ki sake ki kara zagina domin uba bai fi uba ba. " Kanta nayi zuciya ta namin zafi nace" Sai nayi RAYUWAR ki ce ko tawa dake dashi da Yaya Aminu kusa tsinken tsire ku tsikare n......Ban k'arasa ba naji saukar Mari! Da sauri na dafe fuskata ina kallon Wanda yayi min haka, Umma ce tsaye tsakiyar dakin ranta a mugun bace tace" Tsokane mata ido zakiyi ne Mara kunya."? Shuru nayi hade da sunkuyar da kaina kasa ta cigaba da cewa." Duk rashin mutumcin da kikayi ina jinki, ina ce Mimi ta girme ki da har kike tsaye kanta kina nuna ta da d'an yatsa kan ta fada miki gaskiya." Mimi tace"Umma kiyi hakuri don Allah." Tace" ke zan bawa hakuri Mimi da kike k'okarin nusar min da ita, duk da rashin mutumcin da take miki." Mimi tace"Umma wannan duk abunda ya shafe mu ne, dama mun saba fad'a haka." Cike da tausayi take kallon Mimin ta rasa wace irin zuciyace da ita, tace." Ba irin wannan fad'an kuka saba ba. Ke kam zuciyar ki tana da sanyi ina addu'ar kar Allah ya kai gidan me mata ki sha wuya domin kishiyoyin ki zasu raina ki wallahi." Shiru Mimi tayi. Ita kuma Umma ta kama hanyar futa,
D'an juyo wa tayi tana kallon katifar mu, waya ta gani tamfatsetsiya cike da mamaki tace"Wannan wayar waye a cikin Ku."? Shiru mukayi dukanin mu.Cike da zargi da tuhuma tace." Ba tambayar Ku nake ba."?
Baki na rawa Mimi tace"Tawa ce Ummah." Cikin mamaki tace "Mimi yaushe kikayi magana babu labari." Yanda Umma ta fad'i maganar kai tsaye ya tabbatar mana da cewar Hankalin ta ya tashi. Da sauri tace"Mik'omin wayar nan." Hannu na rawa Mimi ta mik'a mata, ta karb'a had'e da fucewa daga d'akin.
Shuru muka yi dukanin mu, yanzu na daina jin taikacin komai nayi kwanciya kawai a zuciya ta nace"Ke ma abunda ake min a gidanan yazo kanki sai kiji in da dad'i baya na juya mata ina lumshe idona babu abunda ya dame ni,   injita ta kwanta itama jikinta duk yayi sanyi.

K'arfe takwas dai-dai naji hayaniyar Ya Aminu a kaina rumtse idona nayi da k'arfi ina fadin"Ya Aminu Dan bala'i ne wallahi.

"Ke Mimi tashe ta kuzo rumfar Umma ina Neman Ku." Yafad'a cikin daga murya. Futa yayi ita kuma tafara tashi na, tsaki ns buga ina kara gyara kwanciya ta, tace"Nasan dai kina ji tom Ya Aminu ne kin san dai halinsa.
Nace"Kije ke ni kam babu inda zani." Mik'ewa tayi tana fadin "Taurin kanki ne yake jawo miki komai.

Ina jinta ta futa, minti biyu na mike nima domin tsoro ne ya shige nasan halin Ya Aminu bai k'i ya shigo ya dake ni da sanyi safiyar nan ba.

Ina shiga dakin Umma na yadda Aunt Hauwa har tazo suna ta mai da magana, zama nayi gefan ta muka gaisa hannun Islam na jawo INA fadin " Baki je makaranta ba yau."? Aunt ta kalle ni tana nazari tace"Ke kuma waye ya fasa miki gefan fuska." Kwallah ce ta taru a idona nayi shiru hade da sunkuyar da kaina.

Yaya Aminu yace." Nine nan! Na fasa mata idan kuma tayi min gaddams kan abunda zan tambaye ta yanzu to bakinta zan fasa mata har sai hakori ya  futa." Kallonsa nayi cike da rashin tsoro, cikin tsawa yace." Ki fada min a ina kika samo wannan tafkekiyar wayar me uban tsada kin San kuwa kud'inta,? Nasan wayar taki ce, Mimi ta rufa miki asiri ne kawai kamar yanda ta saba." Mimi na kalla dake wasa da hannunwan ta  nace"Abunda kike zo kika CE musu kenan."? Da Jan ido ta kalle ni, nace"Kiji tsoron Allah Mimi." Murya na rawa tace"Umma me nace tunda Nazo gurin nan." Umma tace"Baki ce komai ba zargi take." Ya Aminu na kalla fuska a hade nace" Waya ta Mimi ce don haka ita zaka tuhuma bani ba, yanda ka ganta nima haka na ganta. "








*4/November/2019*
[11/4, 5:49 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*

*40*


Yaya Aminu ya kalli Mimi cike da mamaki domin bai tab'a tsammanin faruwan hakan daga gurin ta ba, a nutse yace." Hakane Mimi."? Gyda kanta tayi tana k'ara sunkuyar da kai kasa, aunt Hauwa tayi karaf tana fad'in"dama baku San da wayar a hannunta ba."? Umma tace"Bamu sani ba Wallahi sai yau" aunt tace"To ai ko lokacin da suka je gidana da wayar a hannunta yau kwanansu Uku kenan." Umma ts tsare Mimi da kallon tuhuma tana fad'in" Ki fada min gaskiya Mimi wannan wayar ta wacece tsakanin ke da Asma'u. "Mimi tace" Wallahi Umma tawa Ce." Tace" waye ya baki ita." Shiru tayi, da k'arfi Ya Aminu yace." Ba tambayar ki ake ba."

Cikin inda-inda tace"Amjadu ne." Dukaninsu jikinsu yayi sanyi Mussaman Aminu Umma tace"Kina nufin yaron nan mai company ko me."? Aunt tace"K'warai kuwa Umma wai sonta yake yi shine ya bata waya." Umma tace" Ni abunda na kasa fahimta a nan shine, shin da ke da ita Asma'u wa yake so a cikin Ku? Ke ya baki waya mai tsada ita kuma ya bata KUDI da kaya dukanin Ku akwai alamun tambaya a tare daku."

Aunt tace"Shine maganar wallahi nima kaina ya kulle sosai." Hannu Ya Aminu ya mik'a tare da fad'in"Bani wayar." Mimi ta mik'a masa wayar jikinta a sanyaye . tashi yayi ya futa ranshi a mugun b'ace!

*********
Yinin ranan haka yayi shi babu dad'i ko da suka futa da Anthony ma shi kad'ai ya dinga zurga-zurgar sa, sai sa komai ya kammala sannan suka dawo gida.

Wanka kwai yayi ya futo parlor inda Anthony yake zaune yana aiki da loptol firji ya nufa ya dauko ruwa na gora ma sanyi tsiya yazo ya zauna kan kujera hade da bud'e ruwan ya fara tuttulawa cikinsa.
[11/4, 5:34 PM] .: Ko da wasa bai kara kallon pictures din nan ba, yana ganin idan ya k'ara kallonsu zai iya had'iyar zuciya ya mutu. Wayar shi ya bude hade da bude data ya shiga whatsp yana dubawa, Alina ya ga ta turo masa da pictures, domin kwana biyu baya d'aukar wayarta ko ta kira, ko wancan karon ma da yaje birthday din ta cin sa'a tayi.
Yana bude wa gaban shi Yayi wani irin bugawa ganin da yayi Asma'u tsakiyar 'yan iskan abokan Alina sunyi hoto*innalillahi wa'inna ilahi rajun*  shine abunda ya furta ya mik'a zaune sosai zufa!! Na keto masa hotonan yake dubawa sosai lallai yarinyar tayi nisa, shi a ganinshi kamar jarabar ta ce ta sanya take shiga cikin maza ko zata rage wa kanta damuwa amma idan ba haka ba mace d'iyar Hausa Fulani tayi irin wannan d'inki Wanda dashi babu maraba da tsirara ta dinga keta maza, lokaci guda yaji zuciyarsa tana wani zafi tare da muguwar tsanar yarinyar, gani yake shine ya cuci kansa kwanaki baya da ta kawo masa kanta har gida, da ya sani ya biyawa kansa bukata tunda ita bata tausayin kanta.

Pictures da Mimi ta turo masa yake dubawa, du Rabin su ita da Asma'u ne sai wannan budurwar da ya tab'a ganinsu tare wato Munnu, kayansu iri d'aya haka ma Dinkin su iri daya to wai me yasa d'inki a jikin Asma'u yafi nuna tsaraci. Shi kadai yake WANNAN tunanin, wata zuciyar tace masa ai duk tafi su ciki ta ko wane fanni.. Fuskarta yake kallo kamar zai lashe ta, har kara zomming din pic din yayi dai-dai ita yana kare mata kallo, ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin"Zaki gane Baki D's wayo yarinya, wani pic din ya bude ,sai da wayar ta kusa fad'uwa daga hannunsa, ganin guy nan shi da ita suna kallon juna kamar masu kallon love. Ji yayi duk duniyar tayi masa zafi, ya kalli Anthony da jan ido cikin turanci yace." Gobe zan wuce najeria Tunda komai ya kammala anan."
Anthony ya gyad'a kansa gami da cigaba da aikinsa

Mik'ewa yayi da sassarafa ya shige bedroom din, kan wata duguwar kujera ya zube hade da dafe kanshi, yana cije lips din sa tunani kawai yake wane irin hukunci ya kamata yayi wa yarinyar nan.
[11/4, 5:47 PM: *****
Kwanan bakin ciki da damuwa yayi a ranar, washe gari  kuwa da wuri ya gama sallamar duk Wanda ya dace, ya bar amanar komai a hannun Anthony ya nufi k'asar sa ta gado wato Najeria.

Sha biyu dai-dai jirgin su ya sauka a filin jirgi na Malam Aminu kano, su Rambo na gefa suna ganin saukowar sa suka k'araso da sauri Rambo ya karb'i wayoyinsa shi kuma doh-doh ya karb'i 'yar jakar sa. Suka nufi mota.

Satar kallon fuskar sa suke ganin fuskar ogan nasu kamar Wanda aka aikowa masa da mutuwar iyayensa, Tunda ya shiga motar babu Wanda ya kula a cikinsu har suka isa gida. Get Man yana ta d'aga masa hannu tare da fatan alkairi ko kallonsa bai yi ba Doh-doh na gyara parking ya bude motar ya futo ba tare da ya jira rambo ya bude masa ba.

Kai tsaye ciki ya nufa suka rufa masa baya, nan parlor suka aje masa wayoyin shi hade da jakar shi, suka futa da sauri.
Yana shiga bedroom dinshi ya fada toilet Wanka yayi ya futo ko mai bai shafa ba, parlor ya futo masifa na cin sa, zama yayi hade da kiran Rambo a waya domin yaji meye labarin guy nan yana ganin ta kanshi zai fara.




*4/November/2019*
[11/5, 11:28 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*


*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*41*


Rambo ya shigo cike da Ladabi yace. " Sir g... Gurin zama ya nuna masa Rambo ya zauna jikinsa a sanyaye saboda yanayin da ya ga ogan nasu ya bashi tsoro. Cikin dakakkiyar murya yace." Wannan guy ya bar garin nan ko kuwa."? Rambo yace." E to jiya da na ga gilmarsu a mota shida abokina sun wuce can Titin rimin gata, ina kyauta ta zaton can masaukin sa, yake." Mik'ewa tsaye yayi hade da goya hannunsa a baya, ya kalli Rbow da jajayen idonsa yace." Kaje kazo min dashi, nan." Rambo ya mik'e jiki na rawa ya futa daga d'akin. Shi kuma ya cigaba da kaiwa da kawo wa cikin parlor
Rambo da doh-doh sun jima a tsaye suna tattauna maganar kafin Rambo ya shiga mota ya tafi, yanda suka tsara shine baza su biyewa Ogansu ba, zasu yi masa dabara ne kawai saboda suna ganin a yanda yake kan dokin zuciya zai iya kashe guy nan kamar yanda ya fad'a.
*Amjad* yafi a wa guda a tsaye a parlor sai kace wani soja, bedroom dinshi ya nufa wayar shi ya dauko ya dawo parlor ya zauna numbar Mimi ya kira yaji wayar a kashe, ranshi a bace ya aje wayar yana tunanin ta yarda zaiyi ya gansu. Minti ashirin a tsakani ya k'ara kiran wayar kamar da wasa aka dauki wayar, Muryar Namiji yaji yana sallama.Amsawa yayi Tare da gyara zaman sa, Ya Aminu a nashi b'angaran ya gane muryar Amjadu da sauri ya gaishe shi, ya amsa babu yabo babu fallasa, yace." Yallab'ai Ashe dai yaran nan da gaske suke yi." Amjadu yace." Menene ? Aminu yayi masa bayanin yadda suka tada hankalinsu ganin wayar a hannunsu. Murmushi yayi yace." Nine na bata domin mu dunga gaisawa, Ya Aminu yace." Allah ya saka da alkairi gaskiya akwai alamun tambaya anan Yallab'ai idan banyi rashin kunya ina so in San cikinsu wacece tayi dace da samun gwarzo miji irin ka."
Kai tsaye yace." Dukaninsu nake so zan aura lokaci guda idan zaku bani." Aminu yaji gabansa ya fad'i yace." Yallab'ai a yi haka kuma."?
Murmushi yayi yace." Anyi an gama ni dai a gurina saboda haka ina so ka sanar da manya kafin in turo magaba tana a tsai da magana domin baza a ja lokaci me tsayi ba."

Yaya Aminu yace." Insha Allahu Yanda kace haka za'ayi mungode sosai da wannan karamcin." Sallama sukayi hade da kashe wayar.

********

Yaya Aminu ya dad'e zaune a gurin da yake kafin ya mike ya shiga gida jikinsa a mutukar sanyaye, ya samu Umma na d'aurin sikari a rumfa zama yayi kusa da ita tare da fadin "Umma kinji gagarimun abunda mutumin nan ya dauko mana kuwa." Umma tace"Wane mutumin ?
"Amjadu" Aminu ya fada jikinsa babu k'wari, tace "A ina kangan shi kai."
"Yanzu muka gama waya dashi, Wai yana son ya auri Asma'u da Mimi lokaci guda." Umma ta saki ledar da take hannunta tana kallon Aminu cike da mamaki tace"Wannan wace irin magana CE."? Yace." Wallahi haka yace" Shiru tayi tana nazarin maganar  daga bisani tace"Mimi da Asma'u Anya hadin yayi kuwa gaskiya Indai Yana so sai da ya zab'i d'aya a cikinsu." Aminu yace"Umma mutum me girma kamar wannan ko mata hudu yace." Zai aura a lokaci guda za'iya ya tsallake gidaje sama da miliyan yazo nan bamu  aje ba bamu bawa wani ajiya ba, gaskiya ni bazan iya fada masa haka ba."
Umma tace "Zaman kishi tsakanin Asma'u da Mimi akwai kwara Mimi sanyi hali Asma'u wayo da rashin kunya gata itace k'arama bana son abunda zai tab'a zumumcin su." Aminu yace." Sai dai idan sune suka so haka amma in sun hade Kansu babu wata matsala. Umma tace" Shikkenan zanyi magana dasu." Ya Aminu ya mike ya futa jikinsa babu kuzari.

Mimi na daki a kwance ni kuma ina bakin rijiya ina wanki Umma ta kwala mana kira, aje sabulan hannuna nayi na amsa hade da cewa "Gani nan zuwa Umma.

Ina zama Mimi ta shigo salo-salo Umma tace." Kun San abunda yake faruwa kuwa."? Girgiza kaina nayi, tace" A cikin Ku Wa ya tab'a furtawa Kalmar so." Nace"Umma waye." ? Hararata tayi tace"Wanda kuka sani mana." Kaina sai ya daure kawai domin ban fuskanci abunda take nufi ba."

Tace"Ke ya baki KUDI hade da yi miki shopping ke kuma ya baki waya, shine nake tambayar wacece a cikin Ku ya taba cewa wance ina son ki,saboda yau ya bujoro mana da bukatar son ya aure Ku duk Ku biyun."

Das!das! Haka gababa ya dinga fad'uwa, baki na rawa nace"Umma ban...ban fahimce ki ba." Mimi ta kalla tare da fadin"Ke dai nasan kin fahimce ni ko."? Mimi ta gyad'a kanta tare da fadin"Na fahimce ki Umma a gaskiya ni dai Kalmar so bata tab'a hadani dashi ba sai da ko ita Asma'u. " harara na banka mata nace"Ki fad'i gaskiya dai ko kinyi maganar aure dashi amma ni meye shafe ni da har zai ce zai aure mu ni dake, babu wata kyakyawar alaka mybe ma duk abunda yayi min saboda kene, Umma ni kam babu abunda ya shiga tsakanina dashi Mimi yake so." Na fada raina a bace. "
Umma tace"Yanzu dai ya turo Aminu da sako saboda haka sai kuje Ku sasanta kanku."
[11/5, 7:40 AM] .: Tab'e bakina nayi na mike hade da barin gurin. Wankina na cigaba da yi ina tunanin al'amarin lallai ma, wai yana so ya aure mu ni da Mimi kiji sai kace Wanda aka ce masa mun rasa majin aure aiko sama da kasa zata hade bazan aure shi ba, Mimi taje ta aure shi, ni gani nake ma kamar da wata manufa ya shirya hakan

Ina kallon Mimi ta futo salo-salo ta shiga dakinmu kallo na bita dashi ina tab'e bakina nace"Kin had'u da aiki babba a rayuwar ki, Ya Aminu ne naga ya shigo cikin gidan da sauri hannunshi rike da wayar Mimi ya nufi dakinmu, babu wayar ya futo, da alama shi yake kiranta. Zuciyata naji babu dad'i naji ina son inji wace hira suke dashi, daurewa kawai nayi na cigaba da wankina, ina jiyo muryar Mimi k'asa-kasa tana magana...... Kwafa! Kawai nayi cikin zuciyata nace"wannan guy shigowar shi cikin al'amari mu ba k'aramin hatsari bane domin zai iya wargatsa mana zumuncin mu." Sai da na gama tsaf! Sannan na shiga dakinmu ina k'okarin cire kayan jikina Mimi ta kalleni baki na rawa tace." Asma'u kin San meye."? Kai tsaye nace"sai kin fada."
A hankali tace"Wai Amjadu ne zai zo bayan sallahr Isha'i zai kawo mana tsarabar mu." Ba tare da na kalleta ba nace"zai kawo miki tsaraba dai." Har da ke ai." Girgiza kai nayi nace" ni kam bana son komai nashi, ban sani ba ko sai kunyi aure sannan zan daina jin haushin sa." Tace"Waye ya fada miki zan aure shi." Cike da mamaki nake kallonta na kasa cewa komai ma, na cigaba da saka kayansma tace" bazan Iya hada miji dake ba Asma'u, gwara in hak'ura in bar miki shi." Muryar ta na rawa ta k'arashe maganar.
Sai ta bani tausayi mutuka nace"Mimi zaki iya hakuri da ruhin ki Ashe? Zuciyar ki tana mutukar kaunar mutumin nan, idan kikayi haka to zaki jefa kanki a halaka, wallahi in har don ni zakiyi haka, to bari kiji wallahi zan iya sadauakar miki da komai na rayuwata domin ki samu farin ciki, ballanta d'a namiji ki kwantar da hankalin ki, ni ba bakuwar zafi bace, Sam Amjadu baya gabana, a yanzu na bar miki shi zan cigaba da yi miki fatan alkairi har karshen rayuwar ki."

Kuka tq fashe dashi hade da rungume ni sosai take kuka nima sai na tsinci kaina da share hawaye tace"Asma'u kin San Allah sai dai in mutu da sonshi mutukar kika ce baza ki aure shi nima na hak'ura gwara soyayyar shi ta zama ajalina."

Yanda take fad'ar maganar tana shashshekar kuka hade da wani irin Abu yasa hankalina yayi mugun tashi Mimi kuka take wiwi tana dukan k'irjinta hade da fadin"Me yasa zuciyata zakiyi min haka.? Meyasa kullum kike azabtar dani akan son mutumin nan, Asmau da nasan inda zanje in jefar da zuciya ta da najefar na huta da masifa" tana wani irin kuka ta k'arashe maganar.
Hankali a tashe nace"Mimi meye haka? Mai yayi zafi? Kina so ki kashe kanki ne? Kike dukan kirjinki." Cikin kuka tace" Asma'u gwara in mutu akan i n rayu a duniyar nan, kwata-kwata zuciyata ba tayi min adalci ba, Asma'u na san ke Amjadu yake so amma saboda sharrin zuciya kullum sai take fada min karya ne, ni yake so, kinga kuwa wannan zuciyar bata da amfani a gare ni, Tunda tana kokarin sanya min abunda bazan samu ba." Cike da tausayin ta nace" Mimi yaya zaki ce baza ki samu ba, kinga na farko dai mutumin nan ya fad'i kirkin ki da kyawun halin ki kyawun zuciyar ki, ko wannan ma amsa ce ta ki gane cewar yana sonki, ki saka a ranki baki da Miji sai Amjadu insha Allahu zan iya bakin kokarina gurin ganin tabbatuwar auran Ku." Hawaye ne kawai yake zubo mata na sanya gefan zanina INA share mata, da kyar na samu tayi shiru dadin da naji ma Umma ba taji ba yara sun cika gidan suna siyyaya.

*********
K'arfe shida dai-dai ya futo cikin kyakyawan shiri yau, shigar manyan kaya yayi  wata lafiyayyir galila ce a jikinshi skyblue dinkin babbar Riga da 'yar ciki taji lafiyayyan sirfani na masu hannu da shuni yau mutumin Ku ya sanya hula inda ta kara futo masa da ainihin kyawun sa hade da kwarjinsa, hannunsa daure da agogo shi mai tsada sai zabbuna na azirfa guda uku a ya tsunsa masu wani irin ado hade da stons kana ganinsu kasan zasu ja kudi, takalmi me gidan ya tsa ne a k'afafun shi kamfanin Gucci Dan Asali yayi kyau har ya gaji inda kasan wani ango, *Ni ko nace ba dole ba za'a tafi neman aure* fuskarsa babu yabo babu fallasa ya futa, bodyguard d'insa suka mike da sauri, hannu kawai ya daga musu ya karb'i key hannun Doh-doh da kanshi ya futo da motar daga inda take mai gadi ya bude masa gate ya futa daga gidan suna daga masa hannu Kai tsaye gidan granny ya nufa, bai shiga gidan ba sai da ya gabatar da sallahr magariba a massalacin dake manne da gidan sannan ya shiga.
Kamilar Dattijuwa na zaune kan dadduma da carbi a hannunta tana lazimi da alama ta idar da sallahr ne, zama yayi a kujera Yana jiran ta kammala, minti goma a tsakani ta shafa addu'ar ta, ta kalle shi bayan ta aje carbi tace"Babban mutum." Kallonta yayi cike da mamaki! Tace"Yau dole in kira ka da wannan suna
Wannan kwalliyar ta burge ni sosai don har na fara kishin ka tun kafin kaje inda zaka je." Dariya ya sanya tare da fad'in"Ai kuwa sai da kiyi domin babu abunda zai hanani tafiya Neman aure, auran ma na mata biyu kece ta ukun. Kafin in cika so ta hudun.
Hararsa tayi tare da fadin"Mace biyu ai bata kama ce ka ba kaji da guda daya, ta Isa." Yace." Ba kin ce zaki shiga kauyika ki samo min maganin k'arfi ba."? Zama ta gyara tana kallonsa tace"K'warai kuwa yau a can muka yini nida Iyami ga wani sassak'e can na karb'o maka Wanda za'a dafa shi da jar kanwa ya zama shine ruwan shanka, insha Allahu mai maganin yace zaka koma kamar zaki gurin k'arfi."
Dariya ya kyalkyale da ita Sam! Ya manta da b'acin ran da yake ciki yace." Toum kinga sai in fara Neman aurena da hujja." Mik'ewa tayi tsakanin ta da Allah take fad'in"Ai mutukar zaka diman ci shan maganin matar ka baza tayi takaici ba." Cikin dariya yace." To kawo min na fara sha yanzu ya bi jikina nasan dai already kin had'a min." Tace"Yanzu kuwa a i mikewar da nayi zan dauko maka ne, NASA Iyami ta k'ukkula maka shi a farar Leda kullum ka dinga shan d'aya." Yace" maza ki kawo min uwargina." Bedroom dinta ta nufa, tana tafiya tana kara tisa maganar.

Shi kuwa bayan shigewar ta dariya ya kama yana mamaki wai shi Granny zata bawa maganin k'arfi hummm! Yana zaune ta futo dashi cikin Leda viva sabuwa dal, dauru kusan ashirin ya karb'a yana dubawa, dauri daya ya dauko yana sansanawa, cikin haushi da takaici tace"Meye haka kuma zaka haramtashi fa." Cikin dariya yace." In na haramanta ma ai ni nawa ne kuma ni zan sha." Tace" To fasa dauri daya kasha a gabana." Aikuwa ya fasa hade da zukewa yace." Idan cikina yayi ciwo kece kin yadda." Tace"Na yarda wannan maganin bazai saka ciwon ciki ba sai dai ma ya gyara ka." Yace." Naji to zauna muyi magana dake."
Granny ta zauna kusa dashi.
Yace." Neman aure zanje fa."
Granny tace." Alhamdullahi yau Allah ya kawo ni wannan lokacin. "
Gyad'a kansa yayi yace." Mata biyu zan aura ya kika gani. "
Shiru tayi tana nazari daga bisani tace"Ai Matsalar Ka ce abun ji." Murmushi yayi yace." Kar kiji komai duk zan iya dasu.
B'ata fuska tayi tace"to naji  amma dai ta biyun Hafsa ce ko."?
Yace."Wacece Hafsa kuma."? Tsaki taja tace"Kamanta kenan kana so ka hadani da Innar ka kenan? Dama suna cewa sai abunda nace dakai kake yi baka zumunci dasu dukiyarka baka Mora musu sai dai su ji a gari."
Shiru yayi kawai domin shi kanshi ya San baya kyautawa Sam baya ziyartar dangin mahaifiyar sa, sun gani da korafin sun hak'ura dole yanzu ya gyara ko don kada duniya ta zage shi, Granny ya kalla yace." Yanzu yaya kike so ayi. "? Zama ta gyara tare da fadin" Kaje ka nemi auran Hafsa yarinyar na da kirki kuma tana sonka." Ya mutsa fuskar sa yayi wannan bukatar ta granny baza ta yi wu ba, yace." Kiyi hakuri Granny bana so ayi Abu daga baya azo ana da an sani kin fi kowa sanin halina bana rufa-rufa yarinyar bata yi min ba, zan dai yi kokari gurin ganin naje mun gaisa dasu kuma zanyi musu alkairi sosai."
Ajiyar zuciya ta sauke tare da fadin "Shikkenan to Ubangiji Allah yayi maka zab'i na alkairi "
"Ameen yace yana kallon agogon dake daure a hannunsa.
Mik'ewa yayi  yace." Insha Allahu komai ya dai-dai ta zamu je ki ga kawayen naki ko kuma in ce kishiyoyin naki." Tace",Allah ya kaimu yanzu ma ace dasu ina gaishe su."

Har ya futa ta bishi a bays hannuta rike da ledar magani tace." Ka manta kuma." Shiru yayi yana nazari,hannu ya mik'a ya karb'a sukayi sallama ta koma gida

Mota ya bude ya zura ledar maganin kusa dashi ya zauna sosai hade da kunna motar mai gadi ne ya mik'e da sauri ya bude masa Gate ya futa daga gidan.

Kai tsaye,....... Gidansu Asma'u ya nufa.






*5/November/2019*
[11/6, 5:13 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*


*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*42*


Yana tafe cikin mota yana sauraron wak'ar Joy mutumin shi, gyada kansa yake da alamun Yana jin dadin wak'ar, sai da ya kusa shiga unguwar tasu ne ya kira Mimi a waya, lokacin muna zaune a tsakar gida bayan mun gama cin abunci muna ta fama da wasu shegun cinna ku da suka addabe mu, dama duk lokacin damuna haka suke futowa a gidan ta cikin ramuka suyi ta cizon mu. Wani ne ya cije ni a hannuna ina ta faman sosawa hade da haska gurin da toch din wayar Mimi neman sa nake in kashe, kira naga ya shigo wayar *Heartbeat* abunda na gani kenan, siririn tsaki naja hade da mik'a mata wayar ta karba hade da tashi daga gurin, Umma ta bita da kallo tana girgiza kanta. Minti uku sai ga ta ta futo da wayar a hannu tana sink'e kai Umma tace "Waye ya kira ki harda barin gurin."?
A hankali tace" Amajad ne, yazo Umma." Sakin fuska tayi tace" To masha Allahu, alamu sun nuna ke yake so, tunda gashi ya kira ki a waya yazo zance maza je ki shirya Ubangiji Allah ya sanya alkairi." Umma ta  k'arashe maganar cike da murna da farin ciki.

Mimi ko kunya ta shiga dakinmu da sauri, sai abun ya bani mamaki ganin d'azu take kuka tana cewa ta hak'ura dashi ta barmin amma dubi yanda take rawar kafa saboda zuwan sa. Ni dai shiru nayi kawai, har ta futo Cikin shiri sai zabga kamshi take. Tace"Umma sai na dawo." Umma tace." Ki gaishe shi da kyau kuma ki iya ladabi da biyyaya." Tace"To tana k'okarin futa sai farin ciki take.
Hira muke da Umma sama-sama nake jin ta domin a lokacin bana cikin hayyacina wani irin lami bakina yayi sai kace mace mai yaron ciki haka nake jin wata irin kasala da sagewar gwiwa jiki babu k'wari na shige dakinmu hade da fadawa kan katifa ruf da ciki rumtse idona nayi sam zuciya ta babu dad'i ni kadai nasan abunda yake damuna.

Parking yayi bakin hanya hade da kunna Fitilar wayar sa, unguwar duhu dumd'um!! Sai hasken masu ababen siyarwa dake kan hanya, masu charge masu wanki da guga, masu provision da sauran su,  yaji dadin haka domin baya son ya futo har jama'a suka gane shi, wayar Mimi ya kira hade da fada mata gashinan ya iso. Lokacin tana kan hanya. Inda ya Saba parking ta nufa cikin yanayin tafiyar ta tsallaka titi tayi ta isa kusa da motar hade da d'an kwankwasa wa, a hankali ya bude motar tare da haske fuskar ta da wayar hannunshi, sakin Fuska yayi yace." Momy na tafi ta kowa." Mimi tayi wani fari da ido. Yace." Shigo ciki mana." Cike da kunya ta shiga motar ya mai da murfin ya rufe. Kashe ta yake da kallonsa na goggun 'yan duniya, sunkuyar da kanta take tana fadin"Sonka zai iya kashe ni." Cikin zuciyar ta tayi maganar
Yace." Bamu gaisa ba Momyna kunyar ki na bani mamaki tana d'aya daga cikin abunda yasa naji kin kwanta min a raina"
Mimi tayi murmushi yace." Ok ni ne yafi kamata na gaishe ki tunda nine danki. Kinga kuwa dole in nemi albarka." 'Yar dariya tayi sai kace sokuwa, tace"Ina wuni"?

Cikin sangarta yace." Umum!! Nine zan fara gaishe ki." Mimi taji kamar tana yawo kan gaji mare don shauki gaskiya guy nan ya iya love.

Yace." Ya jin dadin ki Monyna hope komai lafiya Lou."
"Alhmdullahi wallahi."
Tafad'a fuskarta dauke da murmushi
"Ina *Asma'u?*
ya tambaye ta kai tsaye!!! Wata irin fad'uwar gaba taji jin ya baci sunan Asma'u.
Bakinta na rawa tace" Tana gida."
"Owk d'azu mun Dade da yayan Ku a waya ina fatan duk kunji sak'ona ni Amajadu zan aure ku dake da 'yar uwarki Asma'u."
Gyada kanta tayi tace"Ya fada ma Umma."
"Masha Allah." Ya fada da murmushi a fuskar sa, shiru na minti biyu sannan yayi gyaran murya tare da fadin" Shikkenan kije gida sai munyi waya, sai ki kira min *Asma'u* itama muyi zance kamar yanda mukayi dake."
Jiki babu k'wari Mimi ta bude mota ta futa, ya bita da kallo had'e da fadin "Kar ki manta fa ki kashe wayar ki, kafin in kwanta ina son jin muryar ki." Mimi taji wani sanyi ya tsirga mata a zuciyarta murmushi ta saki tare da fadin"Insha Allah."
Hannu ya d'aga mata ta tsallaka titi kana ta shiga layin su.
Umma na zaune a inda take tace"Har ya tafi."? Mimi tace"A'a Asma'u yace." A kira masa." Umma tayi shiru cike da mamaki tace." Asma'u Kuma. " daga Kai Mimi tayi.
Ina kwance a dakin ina jinsu sama-sama, domin bacci ya soma hawa kaina.
Ina jin sanda Umma take fadin "Sai kije ki kira ta tana daki."
Mimi ta shigo dakin hade da tsayawa a kaina tana kiran sunana.
Banza nayi mata.
Tace" nasan dai kina ji don yanzu ba lokacin baccin ki bane, kije Amjadu yana kiran ki."
Mik'ewa zaune nayi nace"Uwar me zanyi masa."
Tace"Idan kinje sai kiji."
Yanda ta fad'i maganar na gane taji zafin zagin da nayi.
Tsaki nayi na koma na kwanta.
Tace.don Allah ki tashi kije babu kyau wulakanci."
Ina daga kwance nace"Kin San Allah Mimi babu inda zanje domin ban ga tsiyar da zan masa ba.
Futa tayi daga dakin.
Can naji Umma na kwala min kira.
Mik'ewa nayi da sauri na futo tsakar gidan INA amsawa
Fuskarta a hade tace "kije kiran da ake miki ko ranki ya b'aci."
Shiru nayi raina a bace
Cikin tsawa tace." Ko bakya ji ne."
Nace" Tom Umma" dakin mu na koma na zurmo hijabina na sallah na futo silafas na zura a kafata na futa.
Tsayuwa nayi a waje ina tunanin ko in lab'e a wani gurin ne. ?
Wata zuciyar tace" kije ki kare masa rashin mutumci tunda yazo unguwar Ku.
Aikuwa tafiya nayi inda nasan zan ganshi
Can na hango motar shi kasancewar ya kunna futular motar.
Ina zuwa gurin na buga motar da k'arfi. Budewa yayi hade da haske fuskata da hasken wayar shi, kalon-kalon muka fara ni dashi. Gani nayi ya kauda kansa yana dariya
Haushi da takaici suka kama ni, sai kace mahaukaciya ya tasa ni a gaba yana dariya. Cike da takaici naja tsaki hade da juyawa da niyyar tafiya, ji nayi an fuzgo min hijabi da k'arfi na fada cikin motar.
Jikinshi ya kwanto kaina ya rufe motar hade da sanya mata security, kallonshi nake a tsorace! Naga fuskarsa a mutukar murtuke Yayi bala'in shan kunu irin Wanda bai tab'a yin irinsa ba,
Ya hasko fuskata sosai da wayar shi, Yana kallona tare da ya mutse fuskar sa.
Kauda kaina nake ganin yadda ya dallare min ido.
Hannunsa guda ya sanya ya shak'o wuyana dake cikin hijabi, Murya k'asa-k'asa yace." Maimata irin zagin da kikayi min a waya jiya." Kifkifta idona kawai nake, ya k'ara shak'e min wuyana hade da d'aga kaina sama sosai, yace"Ko bakya ji ne."?
Da kyar na samu na kakaro magana nace"Sakar mun wuya kar ka kashe ni."
Kin saki yayi sai ma kara damk'e wuyan yayi, hannuna guda na sa ina kokarin b'anb'are hannunsa daga jikin wuyana, ko motsi ya kiyi, wuyana yayi bala'in sagewa, nace"Ka Sakar min wuyan....... Ka tsani Yayi ta hanyar fad'in" Ki maimata irin zagin da kikayi min jiya Zan sake ki."
Babu wasa a cikin maganar sa.
Hawaye na ziraro min nace"Wane irin zagi nayi maka, duk abunda na fada maka gaskiya na fada ciki babu sharri ko kashe ni zakayi sai dai ka kashe ni."

"Very good."!! Ya fad'a yana k'ara bank'are min wuyana sama, cike da mugunta, yace." Na lura da abunda kike so in yi miki ni kuma bazan yi ba, na daina hora ki da abun domin na lura yana miki dad'i shiyasa kike bukatar haduwar mu, Yanzu zanyi miki horo ne irin na gidan prison. " Kasa magana nayi saboda yadda naji mak'o gwarona ya bushe,
Hannu ya sanya ya cire hijab din jikina, na rintse idona saboda nasan babu rigar arziki a jikina wata vest ce mai kama jiki sosai kuma iya kacin ta cibiya ta, domin nayi shirin bacci Mimi ta tashe ni shine kawai na zura hijab din a kai.

Miskilin murmushi ya saki tare da cije lips d'insa yace" Surprise!" Wato dama  kin tawo da shirin ki kenan ko."? Shiru nayi masa wasu zafafan hawaye na zubo min a Kumatuna.
Murmushi yayi had'e da shafa sajan shi yace."Wannan karon baza ki samu abunda kike so ba, domin na fara nisanta kaina dake, sai  kije gurin wannan saurayin naki mai kama da alade,sai Yayi miki wasa dasu."

Shashshekar kukana ce ta fara futowa fili ina mugun Jin ciwon rashin mutumcin da yake min.

Muryarsa a kaurare! Yace." Wancan karon kin min lafi nace ki bani hakuri kink'i OK wannan karon ki bani hakuri ko kuma in dauki mata ki nag gaba a kanki."

Cikin shashashekar kuka nace"Babu hakurin da zan baka tunda banga laifin da nayi maka, ba, kuma bak'i mai kama da alade da kake magana a kansa gwara min shi sau dubu a kanka, Allah ne ya hallice shi a haka. "
Gyada kansa yayi tare da fad'in"Wannan ke yake damu, kiyi abunda na umarce ki kafin in Riga goma." Cikin daga murya ya fad'i maganar.

Jin nayi shiru ne yasa ya damk'i gashin kaina hade da ja da mugun k'arfi !! Ihu! Na kurma ina fad'in"Zan y......Fuzgar gashin Yayi da k'arfi yace." Oya! Ce ne *Amjadu* kayi hakuri sau goma sha biyu nake so ki fada."
Rintse idona nayi ina cije bakina na fara fad'ar *Amjadu kayi hakuri bazan k'ara ba.!"* sai fa na fad'i haka sau goma sha biyu kamar yanda ya umarce ni.

Babu sauk'i a muryarsa yace." Duk naga shirme da kika rafka naga irin rashin mutumcin da kika tsula a gurin party ku , to ki sani ma Sam! Bakiyi wani kyau ba, kullum kina kiran kanki da Me aji mace mai daraja to duk baki amsa wannan sunan ba, *Momyna* ita za'a kira da wannan sunan."
Shiru yayi na minti biyu ya cigaba da cewa "Momyna ita yafi dacewar na aura a tsakanin Ku, to kuma sai d'azu wanki Aminu yake rokona kan in hada in aure Ku gaba d'aya, cewar kin tayar da hankalin ki, ke ni kadai kike so, hake ko ba haka bane."? Kallonsa nayi cike da mamaki anya Ya Aminu zai fada masa haka.? Wata zuciyar tace" Tsaf Ya Aminu zai iya fada masa haka saboda daman ba shiri kuke dashi ba."

A d'age na kalleshi ina ya mutse fuskata nace"Sai dai Mimi don da ita kuka fi dacewa amma ni ko maza sun k'are bana jin zan aure ka gwara in k'are rayuwata a haka."

Miskilin murmushi yayi bai ce komai ba ya sake ni, hijabina na dauka ina kokarin sanyawa naga ya tada motar nace"Ina zaka kaini."? Ko kallo ban ishe shi ba, ya figi motar da gudu.!

Da sauri na sanya  hannu guda na rike sitiyarin motar murya ta na rawa nace"Ka mayar dani gida don girman Allah." Ko kallona bai yi ba, ya cigaba da fafura gudu, kuka sosai na sanya tsoro ya shige ni ganin fuskarsa murtuk!! Nace"Wai me nayi maka ne kake kokarin wulakantani ? Ita Mimi meya sa baka yi mata abunda kake min. " Shiru babu Amsa, yanzu tsoron gida nake da tsoron dukan da Yaya Aminu zai yi min.

Hannunsa na rike tamau! Ina rokanshi motar ta fara gargada! A fusace! Ya fuzge hannuna had'e da yarfa min mari." Cike da mamaki na dafe kuncina ina kallonsa... Da Jan ido ya kalle ni tare da fad'in"Ki shiga hankalin ki."
Shiru nayi tsoro yana shigata.
Gudu yake sosai kan kwalta, naga mun wuce Jambulo wajan gidan shi ya mik'e titin BUK bakina na rawa nace"Kayi hakuri." Hankalinsa na kan driving ki kallona bai yi ba.

Rimin Gata muka shiga sosai, yayi parking dai-dai wani k'aton gidan mai
Haske ko ina jama'a na ta shiga da motocin su Suna shan mai.

Da sauri naga wani mai aikacin  ya nufo mu jikinsa sanye da Uniporm orange da tambarin sunan mai gidan mai yana k'araso wa na ga jikinsa rigarsa an sanya *A&A Amjadu Mai nasara feturolium* nace Ashe har gidan mai ne dashi, cikin turanci naji suna maganar Sam ban fuskanci komai ba na dai ga mutumin ya juya ya tafi da sauri!
Minti biyar sai ga mutumin shida wani, sai da suka k'araso sannan naso na gane wanene. Gaba na ne ya fad'i ganin Abokin Shamsu wato Abba gana, yayi tsuru-tsuru,
Bude kofar motar Yayi hade da umar tarsa ya shiga
Abba gana ya shiga motar ba tare da  gaddama ba. Shi kuma ma'aikacin ya koma gurin akinshi

Juyo wa yayi yana kallonsa, muryarsa babu wasa yace." Malam meye sunan ka? Kuma meye ya kawo ka wannan jahar."?

Abba yace." Sunana Abba Gana ni mutumin mai duguri ne, yau sati na biyu a jahar kano, Nazo Neman kudi."

Gyada kansa yayi murya a cunkushe yace." Kasan wannan yarinyar."?
Naji gabana ya buga damm!!!
Shiru Abbah yayi, tsawa ya buga masa tare da fadin" Answer me." Baki na rawa Abba yace." Banga fuskarta ba Yallab'ai."
Cikin wata irin kyara da hantara yace." Ki juya masa fuskar ki ya kalle ki."!!!!
Da sauri na juya muka hada ido da Abbah Wanda tun ranar party mu bamu sake had'uwa dashi ba.
Da sauri Abba yace." Na Santa sosai Yallab'ai. "
"Good."!
Yafad'a yana jin jina kansa. Bakina na rawa nace" A ina ka sanni da har kake cewa kayi min farin San.....ban k'arasa ba, ya gwab'e min bakina da gwiwar hannusa. Dafe bakina nayi ina kallonsa hawaye na zubo min.
Kallona yake shima fuskar sa babu sauk'i.
Minfi minti biyu a haka sannan ya juya da kaurarriyar murya yace." Abba kana son ta ko."?
Abba yace." K'warai kuwa Yallab'ai. "
Gyada kansa yayi yace."Zaka aure ta ni zan tsaya maka a kan komai zan baka gida akin yi da duk abun bukata."
Abba ya dinga godiya tsakanin sa da Allah, yace." Kana iya tafiya"Abba ya fara kokarin bude motar sai kuma ya daka ta tare da juyo wa Cikin sauri yace." Yallab'ai nagode k'warai da wannan karamcin naka, hak'ika idan ana samun mutane irin Ku to da talakwa sunji dadin su, amma ka yafe min hak'ika yanzu na kara tabbatar da cewar Asma'u matar manya CE, nagode da karamcin ka, Asma'u da kai ta dace Yallab'ai. "
Wani kallo Amjadu ya watsa masa yace." Bayan kun gama wasan soyayyar da ita zaka ce dani ta dace. Tab'e bakinsa yayi yana girgiza kansa yace." Ni nafi k'arfin socond hand, kawai idan baka so in bawa wani."
Abbah yayi shiru yana tunani daga bisani yace." To Yallab'ai duk yanda kayi dai-dai ne."
'Yar dariya yayi yace." Yanzu kayi magana guy kaje kawai ka fara shiri."
Simi-simi Abbah ya bar gurin yana mamakin meye manufar sa kan haka, yarinyar da yayi-yayi ta bashi numbar waya tak'i yau ita za a bashi, shi ba Yaro bane yana kallon tsantsar so hade da kishi a idon sa, addu'a yake Allah yasa kar ya auna shi garinsu dama jarabar fad'an da ake ne yasa ya biyo Shamsu tunda dukanin su iyayen su sun mutu.
Kunna motar yayi muka fara tafiya. Da gefan ido ya kalleni tare da fad'in"Ko kiyi min shiru ko kuma in sauke ki anan."
Cikin kuka nace"Allah kad'ai na mik'a masa kuka na akan ka, ka zame min bala'i ka shiga rayuwa ta, me na tsare maka a duniyar nan, da kake kokarin tozar ta ni." Cikin zafin zuciya yace." Kika tozarta kanki dai! Ni gata nake so nayi miki saboda na lura da yanda bagalar ki take, kar ki dauko abun kunya domin baki da juriya, nace zan rufa miki asiri in aure ki kin ce bakya so, tom naje gurin sauranyin naki da Kuka gama rungume-rumgume dashi zan taimake Ku, shine kike min kuka harda hada ni da Allah, me kike so ayi miki."?
Murya ta a shak'e nace"Idan na dauko abun kunya meye damuwar ka? Na farko dai dani da kai bamu had'a dangartakar komai ba, babu wata alak'a a tsakanimu,saboda haka baka da damuwa da wannan....ka tse ni yayi ta hanyar fadin"Sai kace ba musulumi ba, wato kina so Allah ya kama ni kenan ? Idan kika je kika dauko zunubi dole ya shafe ni tunda Allah ya nuna min ko wacece ke, kuma kina maganar dan gantaka a tsakanimu idan yanzu babu ita tom nan da kwanaki kad'an zata samu, bana so duniya ta dinga kallon ki a matsayin k'anwar matata wacce ta dauko abun kunya......Ihu!!!! Na kurma da k'arfin gaske ina zuciya ta kamar zata tsage, dukan shi na kama yi  kamar wata sabuwar mahaukaciya ina Kuka ina fadin "Allah ya Isa na."!!!! Motar ya tsayar da sauri ganin tana kokarin sauka daga kan titi.
Bakina ya matse da k'arfi!!! Muka fara kallon kallo dashi, babu alamun sassauci a fuskarsa yace." Duk abunda na fada gaskiya ne, ga zahiri ne nan na gani, saboda na saba tab'a jikin ki in muka had'u shine kika sanyo k'aramar riga don in gani inyi sha'awa, tab'e bakinsa yayi ya cigaba da cewa"Ko tsirara zakiyi a yanzu bazan sha'awar komai naki ba, saboda kin gama rabawa gayu a titi yanzu sunan ki sorry."!! Ya k'arashe maganar sa hade da Sakar min bakina da ya matse yana shegen murmushin sa da ya saba.

Fad'ar tsananin b'acin ran da nake ciki a lokacin b'ata wa ne,raina yayi min bak'ik'ikirin ta inda naji duk a fadin duniyar nan bani da babban makiyi sama da guy nan, tunda nake a rayuta ba a tab'ai min tozarcin irin na yau ba, lallai na yarda ko wane namiji akwai sharrin shi don shi wannan guy ma na rasa a ina zan aje shi, duk inda kake zaton sa ya wuce nan........







*6/November/2019*
[11/7, 11:04 AM] BintuUmarAbbale: [11/6, 10:37 PM] .: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*

*43*



Wani irin gudu yake da motar kan kwalta, tsoro duk ya kama ni burina kawai in ganni a gida, tun lokacin da yace nayi shiru na rufe bakina domin ina jin tsoron kar ya tsoro da wata futunar. Dai-dai tal'udu yayi parking din motar hade da futa kallonsa nayi ina cikin motar naga ya dauko glass cikin aljihunsa ya sanya a fuskar sa, tsallaka titi yayi ya nufi  had'addan gurin abincin nan wato *Mai takobi* ina nan zaune mintuna goma na hango shi,
Saurin kauda kaina nayi cikin zuciya nake fadin"Mutum har mutum amma babu kyawun hali
Hannunsa rike da ledoji ya shigo motar kujerar baya ya aje ya kunna motar muka tafi
Bacci ne ya fara daukata kamar daga sama naji muryar shi yana fadin
"Kar ki sake kiyi min bacci a mota"
Zumbur na bude idona
Da suka fara yin ja.Kauda kansa yayi yana ya mutse fuska.
Nima ban sake kallonshi ba,
Har yanzu fuskata a hade take tamau! Nayi alk'awarin har in sauka daga motar bazan kara kula shi ba duk abunda yayi min na barshi da Allah.
Wayar shi ce tayi kara a lamun ana kira,  a hankali ya sanya hannunsa ya dauki wayar da take kusa dani.
Ji nayi tsigar jikina ta mike jin hannunshi na tab'a gefan cinya ta.
Addu'a ns fara yi a zuciyata ta neman rinjaye.
Cikin wani irin voice naji yana fadin"Hibbah!! Wai sau nawa zan fad'a miki ki rabu dani ."! Ban ji abunda tace ba,  sai naji ya ja tsaki yana fad'in"Ki jik'a ki sha kayan ki, kwanan nan zanyi aure in huta da bala'in Ku, ko wace 'yar iska ita dai a cita."
Kallonsa nayi a fakaice ina mamakinsa cikin zuciyata nace"Zaka aikata abunda yafi haka.
Ina jin budurwar tashi tana kaskantar da kanta hade da yi masa magiya, takaici ya she ni, cikin zuciyata nake fadin"Mata yanzu sun koma bin maza har da magiya akan ya so ta wallahi abunda bazan taba iya wa ba kenan.
Tsaki ya ja ya kashe mata waya
Draving dinshi ya cigaba da hannu daya daya hannun kuma da wayar a hannunsa yana dubawa.
K'arfe goma shaura na dare,
Aje wayar yayi gefe na, saurin matsawa nayi jin hannunshi ya tab'a ni
Haka muka isa unguwar mu, masu sana'oin dake kan layinmu duk sun fara tashi unguwar tsitt!! Gashi duhu dumd'um muna Matsalar wutar NEPA.
Parking yayi hade da juyo wa yana kallona.
Dauke kaina nayi da sauri!
Yace."Kina iya tafiya." Hannu nasa ina kokarin bude kofar
Taki bud'ewa, hannunshi ya d'ora kan nawa cikin wani irin salo ya shafa sannan ya bude min kofar
Jikina a sanyaye na futa daga motar ina wurga ido domin akwai ni da bala'in tsoro ga unguwar mu da karnukan tsiya gari yayi tsitt ga duhu. Leda guda ya mik'o min cikin ledojin nan yace."_Karb'i ki kaiwa my Wifi bayan haka kice ta kunna wayar ta ina son muyi hira."
Share shi nayi ina kokarin tsallaka titi.
Sunana naji ya ambata *Asma'u* kin ji yuwa nayi na wuce da sauri!
Wani kare ne yayo kaina da gudu, yana haushi.
Ihu!! Na sanya na dawo da baya ina haki!
Dariya yayi ya bude motar ya  futo
Karan ya kara haushi da k'arfi!
A hankali yace." Wannan bakin hijab din na jikin ki shiyasa yake miki haushi.
Cikin tsoro na kalle shi, nasan bala'in karan nan bashi da sabo.
Yace." Ni zan tafi ki San yanda kika yi kika wuce gida,ko kuma ki kira saurayin ki.
Muryata na rawa nace"Motar ai zata shiga lugun don Allah in shiga ka kai ni
Girgiza kansa yayi hade da bude murfin motar ya shiga.
Shahada nayi na kara yunk'urin tsallaka titin a karo na biyu
Cikin  fusata karan yayo kaina.
Da sauri na koma baya kamar wata zarrariya na dunga dukan motar ina fadin bude min don Allah.

Sauke glass din motar yayi yace." Meye wai! Kiyi tafiyar ki ki k'yale ni." Hawaye suka zubo min nace." Nasan wancan karan bashi da mutumci kuma bashi da sabo Wallahi zai iya cizo na, kwanaki da ya ciji wani sai mutuwa yayi don dafi ya zuba masa "
Cikin k'osawa yace."Tom yanzu ya kike so ayi."?
"Ka taimake ni, wani in ya ganni anan ba zai min kyakyawar fahimta ba."
Wani kallo ya watsa min tare da fadin"Au ke kina jira jama'ar gari suyi miki kyakyawar fahimta. "
Shiru nayi
Yace." Ki cire wannan a ran ki."
Kunna motar yayi zai tafi, da sauri na bude na shiga ciki
Kallona yake cike da mamaki yace." Meye haka? Kin damu in kawo gida na kawo ki, kin hanani tafiya."
Karyar da kaina nayi cike da tausayin kaina nace"Ka taimake ni." Hannunshi na kama na rike gam!! B'ata fuska yayi tare da fadin "Wane irin taimako zan miki. Kai tsaye! Nace" Ka raka ni gida wallahi karan can bazai Bari in wuce ba."
Tausayi ta bashi amma bai nuna ba yace."gaskiya bazan iya shiga lokon can ba, kawai kiyi tafiyar ki,ko kuma ki cire hijab din jikin ki ki yar.
Nasan saboda hijan din ya Hana ki wuce wa, da zaki gane ma kawai ki daina sanyawa domin mugun muni yake saki."

Wani irin. Kallon nayi masa nace"In cire hijab dina fa kace."
Gyada kansa yayi tare da kanne min ido daya yace." Meye a ciki to bayan babu kowa a unguwar idan ma da mutane ai abun ba sabo bane a gurin su, tunda duk kin raba musu.
Naji ciwon maganar sa, amma dake taimakon sa nake nema ban tanka masa nayi Shiru hake da sunkuyar da kaina har yanzu hannunsa na rike da nawa gam!!! Murya k'asa-k'asa yace." Sakar min hannu." Sakin sa nayi  ya fara kokarin cire babbar rigar jikinsa,
Mik'o min Yayi yace. " cire hijab din ki sanya wannan."
Cike da mamaki nake kallonshi
Yace." Kin ce in taimake ki kuma kin tsaya kina kallona.
A hankali na karb'i rigar kamshi turaran shi sai tashi yake
Yace. " Cire hijab din ki lullub'e jikin ki."
Nace"Matsalar Idan naje da rigar gida."
Katse ni yayi da sauri yana fadin" wannan kuma damuwar ki CE, kina bata min lokaci."
Da sauri na cire hijab din na fara kokarin kare jikina da babbar rigar tashi
Ina kallonsa yana min wane mayen kallo hankalin shi duk yana k'irjina, ni kuma sai kare wa nake.
Hannunsa ya sanya Wai zai gyara min.
Cikin dubara naji ya shafo nonuwana, Ni dashi ban San Wanda ya fi shiga d'imuwa ba.
Rigar ya tattato a hannunsa dai-dai k'irjina ya kama hannuna hade da Dora gurin, murya a harhade yace." Ki rike nan da kyau."
Shiru nayi ban amsa ba.
Ya bude motar ya futa
Futowa nayi jikina babu k'wari
Tsalla titin mukayi a nutse sai naga karan ya koma gefe ya zauna ya daina haushin.
Sai da muka shiga layin mu sosai sannan ya juya ba tare da yace min komai ba.
Nace"Rigar ka fa."
Yana tafiya yace." Ki jefar da ita ana.
Shiru nayi  ina kallonshi har ya tsallaka titin ya shiga motar sa hade da barin gur Rigar na rike sosai ina sakin ajiyar zuciya, cikin sauri na tsallake kwatar dake kusa dani na nufi gida, daga nesa na hango Aminu tsaye a waje hankalina ya tashi nan na tuna hijab dina Dana barshi a motarsa Cikin zuciyata nace"Dana dauko shi sai in jire rigar jikina nasan dole Aminu sai yayi magana
Ina k'araso wa ya bini da kallo
Simi simi Nazo na wuce cikin gidan ya biyo ni a baya yana zabga tsaki
Sakata ya zura sannan ya shiga
Umma na tsaye tsakar gida na shigo kallona tayi tace"Sai yanzu ya tafi. "?
Gyada kaina nayi jikina tabi da kallo cike da mamaki.
Da sauri nace" Wannan masiffafn karan ne ya hanani shigowa layin nan, shine ya bani babbar rigar shi na sanya.
Ya Aminu yace." Dole yayi miki haushi dama an hana ki sanya bakin hijabi kink'iji sai kinje wata rana ya cije ki.
Girgiza kai Umma tayi ta shige daki.
Nima dakin mu na wuce jiki babu k'wari
Mimi sarkin bacci har tayi bacci
Rigar na cire na zaune gefan gado ina sauke ajiyar zuciya
Tunanin rashin mutumcin da guy nan yayi min nake, hanyar da zanbi in rama nake nema
Wani shashe na zuciyata yake fada min kull kika ce zaki rama domin duk WANNAN abunda kuke dashi baki tab'a samun galaba a kansa ba,
Duk abunda yayi ado ne a garunshi ke Kuma zubewa mutumci ki rabu dashi kurrum
Rigar shi na dauka ina shashanawa lumshe idona nayi hade da kwanciya rigingine tsigar jikina ta fara mik'ewa abunda na Dade ban ji shi ba yau shi naji, muguwar sha'awar sa kawai nake, nipple d'ina suka fara k'aik'ayi kasa na ta soma motsi, rike rigar nayi da k'arfi ina cije bakina,  matse jikina nake sosai tare da rungume rigar shi ji nake kamar shi na rungume a jikina. Karar waya naji Mimi na can tana bacci da sauri ns dauki wayar saboda lokacin ji nayi ina son in kara jin muryarsa ko zan samu sassauci
Kasa&kasa nayi sallama,
Bashi b'angaran ya fahimci muryat ta ce, Kai tsaye yace." Ina Momyna bata wayar zamuyi hira. " muryata a shake nace"Tayi bacci."
"Ok ke me ya hana ki yin baccin."? Ya fada Kai tsaye... Nace" Ban sani ba nima.
Sai da na fad'i haka kuma na fara Dana sani.
Shiru yayi na minti biyu yace." Ko dai Jarabar ki ce ra hanaki bacci don na lura da halin da kike ciki d'azu.Shiru nayi idanuna a lumshe, shine yake abun shi don ba jinsa nake sosai ba, ina can duniyar shauki jin muryarsa ji nake kamar yana kusa dani ga k'amshin sa a jikina motsi kawai nake ina lumshe idona wayar ma saura kad'an ta fad'i, yace." Ko bakya ji ne."? S hankali nace "Uhmum."!! Nashi bangar yaji tsigar jikinsa ta tashi yanayin yanda tayi maganar ya tada masa da sha'awa, lumshe idonsa yayi hade da gyara kwanciyar sa, yace." Shikkenan tunda kina so nayi hira dake, yanzu ki fada min wane shawara kika yanke a kan auranmu ki zab'i guda ni ko Saurayin ki."

Shiru nayi ban ce komai ba
A hankali naji ya ambaci Sunana *Asma'u* wani iri naji a jikina ya iya fad'ar sunana.
"Uhum."!! Abunda nace kenan.
Yace" Malama ki bude baki kiyi min magana ko in kashe wayata meye wani Uhumm.!? Nace "Me kace to? Nifa ban ji abunda kace ba."
Tsaki yaja  yace." Baza ki ji ba dama fitinanniya kawai."
Kitt!! Ya kashe wayarsa
A hankali na aje wayar ina tab'e bakina ko banza na samu sassaucin abunda nake ji.
Mimi sahorama tana can tana bacci ko motsi ta kasa yi

Amjadu yana sane ya kashe wayar shima saboda yanda ya fara jin  Jikinsa ya sauya joystick dinshi ta mike sosai wata irin sha'awa ta bujoro masa, yasan haka zai kwana cikin mawuyacin hali.

Haka suka kwana suna juye-juye sai dab da asubah bacci ya dauke su, cike da mafarkin jununsu.

********
Umma da Wuri ta futa Unguwa don abun kari ma mu muka Dora ni da Mimi
Kowa sabgar gabansa yake yanzu dukanmu mun rage sakewa da jununmu.
Tare muka karya da muna hira sama-sama  Mimi ta kalli gurin kwanciyata taga rigar Amjadu.
Tace"Asma'u waccan kamar.... Kafin ta karasa nace"Eh rigarsa ce ya bani na kare jikina da ita jiya dare yayi kafin in shigo gida ga shegen karanan yayi ta yi mun haushi. "
Fuskarta ta sauya tare da dauke kanta tace"Har nayi bacci ina sauraron shigowar ki."
Ina sane nace "E Wallahi unguwa na raka shi.
Kallonta tayi fuskarta a hade ta tab'e bakinta.. Nace." Jiya kina bacci ya kira wayar ki."
"Meya sa baki tashe ni ba."?
Nace" Shine yace"A k'yale ki ki huta, shine mukayi hira sai kusan k'arfe daya na dare na kwanta.
Wani irin kishi ya bujoro wa Mimi mik'ewa tayi taje ta kwanta kan katifar ta
Kallon ta nayi cike da Mamaki nace"Mimi kishi kike dani ko."?Cikin wayancewa tace"Wane irin kishi zanyi dake Asma'u. "?
Nace" Gashinan daga magana kin je kin kwanta ko abincin ma kin kasa ci."
Murmushi tayi tace"Ji nayi bakina babu dad'i tunda naji kin ambaci Amjad gabana yake fad'uwa.wani irin nauyi k'irjina yake min."

Nace."Mimi ya zama Dole fa ki ragewa kanki damuwa soyayyar da kike nunawa. Mutumin nan fa akwai matsala domin zata ita kai ki ta baro kuma duk sanda ya fahimci son da kike masa wulakanta ki zai yi, Sam! Ba'ayi wa Namiji haka."
Lumshe ido tayi tace"Asma'u wani irin nauyi nake ji cikin zuciyata da ina iya hak'ura da guy nan da na hak'ura na bar miki shi Wallahi saboda na fahimci kamar yafi sonki dani."
Nace"Ki barmin shi ko in bar miki shi, Amjadu Mijin ki ne ki kwantar da hankalin ki." Shuru tayi ba ta sake cewa komai ba.
Minti goma tsakani wayarta tayi kara dauka tayi tana lumshe ido na na tabbatar da cewar shine ya kira ta, mik'ewa nayi na fuce daga dakin domin bana son inji hirar da zasuyi ballantana i n shiga damuwa.

Sai bayan Sallah la'asar Umma ta dawo gidan, jikinta duk babu k'wari tace" Asmau Zuba min ruwa inyi Alwala a hanya la'asar tayi min."
Da sauri na zuba mata na mik'a mata ina nazarin ta, har ta shige band'aki

Dakinmu na shiga jikina a sanyaye a zuciyata nace Akwai matsala gaskiya tunda naga Umma ta shigo gidan nan jikinta babu k'wari.

Kusan Rabin awa da shigowar ta ta kwala mana kira. Ni da Mimi muka amsa a nutse muka Isa Rumfar, tana zaune da carbi a hannunta tace"Duk Ku zauna muyi magana."
Zama mukayi ko wacce da Abunda take saka wa.

Carbin ta aje ta kallemu tare da fadin "Babban al'amari ne yake tunkaro mu dani da Ku, ina so kuyi min adalci kuyiwa kanku a adalci bana son zumuncin Ku ya lalace saboda duk inda akace kishi to sai anyi shi ko ciki daya kuka futo
Yanzu daga gidan Yunusa nake Wannan yaron da yake Neman Ku da aure tun safe ya turo magabatan sa, da kud'in aure harda sadaki yace." Nan da wata guda yake so, ayi komai a gama. Kawu Yunusa ya amsa musu hade da karb'ar dukiyar auran, kafin in futo daga gidan Aminu yaje da maganar shi ta cewar yana son auran ki." Tafad'a tana nuna Mimi da hannu, a cewar sa tun kina yarinya yake sonki ya ki fada ne kawai saboda yana ganin baza ki fi k'arfin sa ba, sai Kuma gashi lokaci guda wanki hula na Neman ya kaishi dare.
Kawu Yunusa yace magana ta wuce tunda har ya bari aka karb'i kud'in auran ki. Sai dai yayi hakuri kawai. Yanzu halin da ake ciki yana babban asibiti na Malam Aminu domin fad'uwa yayi a gurin har na tawo bai dawo dai-dai ba."
Umma ta k'arashe maganar ta zuciyar ta babu dad'i.
Nace"Umma me yasa Ya Aminu bai yi magana da wuri ba har sai da ya bari aka karb'i kud'in auran ta, to ai itama Mimin. Zata shiga wani hali
Kuma jiya mun gama magana da Amjadu cewar ya janye aurena saboda rashin dacewar haka, Mimi zai aura kuma daga baya azo ana kace nace."
Umma tayi shiru fuskarta cike da alhini.
A hankali Mimi tace." Umma ki kwantar da hankalin ki, Indai akan sona Yaya Aminu ya suma har ta kaishi ga kwanciya a asibiti insha Allahu ni zan share miki hawaye
Dama nike son Amjadu bashi ba Asma'u yake so tuntuni zuciyata takasa yardar min da haka, Umma zan auri Ya Aminu ki kwantar da hankalin ki."
Umma ta share hawayen ta, tace"A'a Mimi bazan miki dole ba bayan an kawo kud'in auran ki saboda son kaina ince ban yarda ba ga Wanda nake so ki aura duniya sai ta zage ni mutanan gari su dinga fadin"Don bani na haife ki ba shiyasa nake miki bakin cikin shiga cikin daula bayan haka kuma zuciyar ki tana son Amjadu idan nayi haka ban miki adalci ba, dole Aminu shine zai janye kudurinsa."

Kuka Mimi ta sanya hade da rungume Umma tana fadin "Wallahi Umma da gaske nake babu abunda zaki nema a duniyar nan ban yi miki ba, mutukar ina dashi, Na hak'ura da Amjadu zan auri Ya Aminu."
Cikin kuka ta k'arashe maganar.

Rungume ta Umma tayi tana kuka, nima naji k'walla ta cika min ido nace"Umma yaushe zamu je asubitin ."? Je ki d'aura abunci da sauri ana idar da sallahr magariba sai muje."
Mik'ewa nayi na nufi kicin.








*7/November/2019*
[11/8, 11:36 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

Mallakar_BINTA UMAR

LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.




44

A gurguje na kammala dafa abunci shinkafa da faduka nayi wacce taji allayyahu da albasa, Bayan mun idar da sallahr magariba ne muna shirye-shiryen tafiya sai muka ji sallama Umma ta futo da sauri Yaya Aminu ne da Musa da Kawu Yunusa suka shigo, Umma tace"Kaddai an sallame shi."
Kawu Musa yace." Gashinan kina gani dama nace Zai farfad'o Suma yayi."
Ya Aminu ya zauna kan tabarma hade da dafe kansa.
Nida Mimi muka futo muka tsaitsaya
Dariya nake wa Ya Aminu ganin yadda ya fyad'e lokaci guda.
Sallama Kawu Yunusa yayi suka tafi ni da Musa kuwa babu Wanda ya kula kowa.
Umma tace"Maza je ki kawo masa abunci."
Kicin na nufa da saurina.
Mimi ta zauna gefansa tana yi masa ya jiki.
Abunci na kawo na aje gabanshi
Naje na dauko ruwa pure watar babu sanyi,yace." Kije ki siyo min me sanyi."
Umma ta mik'o min ashirin tare da fadin"Ki siyo guda hudu.

Hijab din Umma na zura na futa daga gidan da sauri

Ya Aminu bai ci abincin sosai ba ya aje cokalin ya mike ya bar gurin.
Duk muka bishi da kallo. Umma tace"Cuta ta samu manya ." murmushi nayi kawai
Mimi kuwa tashi tayi simi-simi ta shige dakinmu
Nida Umma bamuyi hirar arziki ba muka tashi
Ina shiga dakinmu na tadda Mimi ta juya baya tana Kuka harda shashsheka.
Cikin mamaki nace"Mimi kuka kike yi."?
Banza tayi min
Da sauri naje na birkitota sai naga idonta yayi mugun ja sai ajiyar zuciya take.
Zama nayi kusa da ita hade da rike hannunta nace"Mimi nasan kin amsawa Umma ne domin ki kwantar mata da hankali.
Nasan bakya son Ya Aminu Amjadu kike so Mimi me zai sa baza kiyi wa kanki  gata ba zaki jefa kanki cikin mummunan hali. Kinsan bakya son Ya Aminu me yasa kika amsawa Umma."
Hannuna ta rike tamau! Naji jikinta sai karkarwa yake
Tace." Asma'u na rasa yanda zanyi da zuciyata nayi-nayi incere son Amjadu abun yaci tura ji nake kamar zan mutu Mimi zuciyata tana azabtar dani kan abunda bazan samu ba, don girman Allah ki taya ni da addu'a zuciya tabar cutar dani, soyayyar da nakewa  Amjadu Allah ya cire min ta gaba daya ta koma kan Ya Aminu."

Kuka nasa saboda tausayin ta tabbas so bala'i ne hannunta NA rike dake yin wani irin karkarwa nace"Mimi zan sanya ki a adduata in sha Allahu, kinga na farko ke kika cuci kanki d'azu da Umma tayi miki maganar Aminu sai ki nuna rashin amincewar ki, tom kinga daga baya baza kije mata da wata magana ba.
Zan cigaba da taya ki addu'a Ubangiji Allah ya yaye miki ya zab'a miki mafi alkairi."
Sosai take kuka ina rarrashinta
Sai kuma naji ta fara wani irin tari!! Na mike da sauri na dauko mata ruwa
D'ago ta nayi na fara bata,
Tana shan ruwan tana tari da idonta yayi jazur
Cire ledar ruwan nayi na bugun bayan ta.
Tare da yi mata sannu.
Dana ga tarin yak'i sauk'i futa nayi da sauri na dauko gishiri a kicin na zo na Dan gwala mata a baki.
Tafi minti goma tanayi sannan ya lafa.
Sai haki! Take.
Ruwan na mike mata ta karba ta sha kadan.
Nace "ki kwanta kiyi bacci zakiji sassauci.
Kwanciya tayi tana lumshe idonta
Sai dana ga bacci ya dauke ta sannan nima na kwanta ina sak'e-sak'e Cikin zuciyata.
Bacci ya soma fuzgata naji kiran waya
*haetbeat* tsaki naja na dauki wayar na kashe gaba d'ayan ta domin shi nake mutukar jin haushi a ganina duk shine ya jawo mana wannan masifar.
Tun farko da bai nunawa Mimi yana sonta ba, ina ganin duk haka baza ta faru ba.
Da tune-tune bacci b'arawo ya kwashe ni.

******
B'angaran Amjadu kuwa, tun bayan da Wakilansa suka zo suka Sanar masa da cewar An bashi guda cikin 'yan Matan da yake so ya aura sai gaban shi ya fad'i ya tunini ko Mimi ce, shine dalilin da yasa ya tambaye su kud'in wacce a ka karb'a a cikinsu nan Kawunsa yace." *Asma'u* yaji dadin haka don haka kafin su tafi sai da yayi musu kyauta ta mussaman.

Shirye-shiryen bude company ya kammala yau saura kwana biyu gari ya dauka kafufin yad'a labarai in ka bude zancan kenan *Ranar Juma'a Biyu ga watan bakwai za'a bude shaharrarn company nan wato AmjaduAbulAbbas materials* za'ayi bononza a ranar abun dubu daya Dari biya abun dubu goma dubi biyar. Mutanan gari sun kunzige kudinsu suna jiran ranar domin su je su kwaso garab'asa.

***
Washe gari muka tashi da jiki a sanyaye Mimi ta rame lokaci guda, shi ko Ya Aminu dama tunda Kawu Yunusa ya Sanar dashi cewar an fasa karb'ar kud'in Mimi ya watsake ko da ya tashi da safe tamkar Wanda bai yi ciwo ba, yanzu Mimi CE abun tausayi so ya tasa ta a gaba.

Da kyar na rarrashe ta ta Karya kummalo
Umma ta tsaya bakin kofar mu tana fadin "Menene wai naji kuna takkadama."?
Zuciyata tace kawai ki fadawa Umma ko menene ko Allah zai sanya ta fahimta."
Kaina a kasa nace"Umma ina ganin wa....Shiru nayi na kasa magana.
Umma tace." Meye kika yi shiru."?
Bakina na rawa nace"Umma don Allah Ya Aminu ya janye kudirin sa a kan Mimi akwai cutar wa a ciki, ya kamata Mimi a bata zabin zuciyarta Ya Aminu Namiji ne shi zai iya jure komai kinga Mimi ko yarinya ce mai karanci shekaru gata kuma mace."
Shiru Umma tayi tana nazarin magana ta.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali tace"Kin yi gaskiya Asma'u ni ma zuciyata batayi na'am da haka ba, saboda ina gudun zagin jama'ar gari tunda duk sun San komai Da Aminu da ke da Mimi duk daya kuke a gurina babu Wanda zan ce nafi so, amma kina ji da bakin ki tace ta amunce da Aminu kuma ko jiya Kawun Ku ya maimata min maganar babu gudu babu ja da baya tunda sunyi magana da mahaifin ta a waya yace ya bashi wuka da nama, Babansu Munnu ma har dashi cikin maganar kin ga bani da ta cewa."

Nace "Umma kina da ta cewa mana don Allah ki sanya Ya Aminu ya janye magana.....kafin in karasa naji saukar Mari a kuncina Ya Aminu ne tsaye a kaina yana wani irin huci! Yace." Kina so naci ubanki Asma'u, wato kina zu ga Umma kina zuga Mimi kan su bujirewa Bukatata ko me? Ni kinsan halin da Zan shiga idan na rasa ta, ko kinsan irin son da nake mata, mutukar ina Raye a duniyar nan bani da mata sai Mimi, dake da ita kuje kuyi abunda zakuyi akin gama ya Riga ya gama."
Yana gama maganar shi ya fuce daga gidan a fusace!
Umma barin gurin tayi ni da Mimi mukayi shuru muna sak'e-sak'e
A hankali naji tace"Asma'u don Allah kar ki kara wata magana kan al'amarin nan, kinji tunda dai kince zaki taya ni addu'a tom na gode miki.".
Murya na rawa take maganar
Nima naji zuciyata ta karye nace"Mimi sai dai idan gani nayi am d'aura muku aure da Aminu shine zan daina magana domin nasan ki nayi a banza ne, bakin alkami ya bushe, amma magana kan al'amarin yanzu na fara."
Shiru tayi tans kallona.
Mik'ewa nayi na futa daga dakin zuciya nayi min zafi!

*RANA BATA KARYA*

Manyan attajirai da manya manyan 'yan boko 'yan siyasa masu mak'ami daban-daban Sarkin Kano sarkin Zazzau Sarki Katsina Jama'ar gari tsakunsu da kwarkatar su, sun hallara a wannan guri.

Hayaniya ce ta tsananta tare Da jiniya wannan ya tabbatar min da cewa me girma governor ne ya iso bani kadai ba, duk wani Wanda yasan da akwai dabi tsakanin *Amjadu* da me girma *Governor* sai da yayi mamaki, tuni jama'ar gari suka fara ihu!! Suna fadin abunda ransu yake so ga me girma governor.

Ko kunya babu me girma governor ya futo daga mota tare da jamarsa ya dinga ratsa jama'a Yana daga musu hannu hade da washe musu baki wai shi lallai ga governor tsagerun matasa masu goyon bayan Amjadu suka sanya ihu!! Da dariya suna fadin abun da yayi musu kan governor din, wasu na fadin"Ba mayi!!!! Sai da 'yan sanda suka tsawa tar sannan hayaniyar ta lafafa, can gurin da aka  tanadar wa manyan baki governor ya nufa, police na biye dashi a baya domin sun tsorata da irin ihun da jama'ar gari sukeyi,
Sai da suka ga ya zauna sannan suka koma gefe suka tsaya da bundigun su a hannu.
Can na hango Mai citta shida abokanan shi, sai zare ido suke.
Limamin babban massalacin jama'a na garin kano ne ya tashi ya bude taro da addu'a yayi karatun alkur'ani me girma sannan daya baya daya manya baki suka fara jawabi kowa yana yaba kwazo da jajircewa irin ta Amajdu
'Yan jarida a gurin baza su kirgu ba, domin wasu jamar gari na gida kowa na gaban TV Wanda bashi dashi kuma kunne shi mak'ale da waya ko redio yana saurara.

Lokacin da Amjadu ya futo zai yi Jawabi Ihu!! Jama'ar gari suka sanya tare da fadin"Sai kayi fari me farar aniya ka iya ka huta *AmjaduAbulAbas* muna biye da kai insha Allahu *2004* taka ce sai ka zama shugabanmu." Ihu! Kawai suke, sun hana aji bayanin da yake, da kyar jami'an tsaro suka shawo Kansu suka yi shiru.
*Amjadu* yayi jawabi me gamsarwa jawabin da ya ratsa zukatan al'umma Su Kansu manyan gurin sun jinjina masa kuma sunyi masa fatan alkairi.mai Martaba Sarki yaji dad'i sosai da samun hazikin Yaro a garin shi yana mutukar alfahiri da shi.

K'arfe goma sha biyu da rabi taro ya watse saboda ranar juma'a ce za'a tafi massalaci, nan Amjadu ya bada sanarwar cewa jamar gari suje massalaci su dawo bayan an idar da sallahr za'a bude company daga nan har zuwa goma na dare.

Haka akayi kuwa bayan an sakko jama'a sukayi ta tururwa company suna kwasar garabasa.Sai k'arfe daya na dare sannan aka samu saukin Jama'a.

*****

Duk abunda yake faruwa a gari muna da labarin shi munji a redio Kuma mun gani a TV dake ranar sun bar mana wuta, abun mamaki Mimi yini tayi tana farin ciki.
Amjadu ya sha addu'a gurin Umma, aunty Hauwa ma ba abar ta a baya ba, kusan a dai-dai ta sahu guda tayo da kayan da bata koma gidan ta ba sai bayan sallahr Isha'i.
Ni ko tunda nayi masa kallon farko a TV ban sake kallonsa ba daga k'arshe ma tashi nayi na bar gurin naje na tsiri ninkin kaya ina tunin yanda Allah ya dauka kashi a duniya 'yan da yake da kyauta da son talaka da yanda yake da farin jinin jama'a, yanda yake da ibada, amma yana aikata sabon Allah domin zina mugun aikine Wanda Allah ya hana shi, kawai sai na tsinci kaina da yi masa addu'ar shiriya naji wani irin tausayin shi, babu uwa babu uba ga makiya da d'umbun masoya gaba da baya, Allah ne kadai yasan abunda zai zama nan gaba, a fili nace"Ubangiji Allah ya kare ka daga sharrin ma su sharri Allah ya shirye ka shirin addinin musulunci yasa ka daina aikata zina."

******
Yau sati guda kenan da faruwar al'amarin Wanda yayi dai-dai da kwanaki goma da afkuwar al'amarin Auran mu komai ya dai-dai ta, tun ranar da ya kira wayar Mimi na kashe ban kara kunnawa ba sai yau, sun kawo wuta na jona ta a chaji.
Mimi ta shigo dakin jikinta babu k'wari ta zube kan katifa.
Binta nayi da kallo. Nace"Mimi kinga yanda kika rame kuwa."?
Shuru tayi min
Nace"Wallahi Ki yiwa kanki fada ni yanzu kin daina bani tausayi haushi kike bani wallahi, wai Amjadu shi kadai ne namiji a duniyar nan."
Shiru dai tayi min bata ce min komai ba.
Tsaki naja na futa daga dakin.

***
Tun lokacin da ya kira wayar yaji an kashe bai Kara kira ba yasan Mimi baza ta kashe masa waya ba.
Tabbas Asma'u ce shiyasa bai kara kira ba.
Yana zaune gefan bed da wayar a hannunsa  numbar ya kira sai yaji ta shiga har ta katse ba a dauka ba, kira ya kara yi a karo na biyu nan ma ta katse ba a dauka ba, a je wayar yayi hade da Jan tsaki a fili yace." Mata masu aji kenan." Mik'ewa yayi ya futa parlor.

Mimi na kwance a dakin lokacin da yake kiran wayar tarin da take ne ya hanata d'aukar wayar har ta katse.
Cikin wani irin mugun tari da galabaita ta mike zaune hade da dafe k'irjinta tana cigaba da tarin sosai wa
[11/8, 6:21 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*


*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*

*45*

Ni da Umma muka shigo dakin da sauri!
Mimi na durkushe ta rike k'irjinta tana ta tari.
Da sauri Umma taje ta rike ta ni kuma ns dauko ruwa hade da fasawa na dago kanta ina bata, k'arfin tarin ya hanata ta karb'i ruwan.
Umma tace"Maza kije ki dauko gishiri a kicin.
Cikin tashin hankali na nufi kicin din na dauko ledar gishiri
Umma ta dangwala a hannuta ta sanyawa Mimi a baki tana Dan bubbuga bayanta hade da yi mata sannu.
Mimi idonta ya rufe sosai take tari! Da haki tare da hawaye.
Ni da Umma duk mun shiga tashin hankali.
Nace"Wallahi Umma jiya da daddare haka ta dinga yi da kyar tayi bacci."
Umma tace"Ikon Allah watak'ila busawar sanyin nan ne,.
Nace"Ina jin hakane " cikin ikon Allah tarin ya lafa sai dai haki da take yi.
Umma ta rungume ta a jikinta tana yi mata sannu
Ya Aminu ne ya shigo dakin ya tsaya bakin kofa fuskarsa s daure yake tambayar menene?
Umma tace"Mimi ce babu Lafiya in anjima ka siyo mata maganin tare saboda dare."
Wani irin kallo yake wa Mimi daga bisani kuma ya tab'e bakinsa Yace. " Umma ki rabu dasu duk karya ne,nasan wannan'yar iskar ce take zugata."
Umma ta bata fuska tare da fadin"bana son wannan halin naka Aminu ina ruwan Asma'u anan.?
Futa yayi daga dakin ransa a bace.
Nace"Umma shifa bazai taba ganewa ba tunda ya samu ya kubuta Mimi CE abun tausayi.'
Shiru Umma tayi min, sai da taga Mimi tayi bacci sannan ta gyara mata kwanciya ta futa daga dakin jikinta duk babu k'wari.
Kallon Mimi nake gwanin tausayi duk ta rame tayi Dan wuya k'irjinta sai sama yake yana kasa alamun tana jin jiki.

Jikina babu k'wari na kwanta kusa da ita ina tunani
Ringing din wayar naji wacce take jone a chaji na mike da sauri hade da dauka
Babu sauk'i a murya ta nayi sallama

Ajiyar zuciyarsa naji a hankali yace." Ya kike mata masu aji."!! Sama nayi da murya ta nace." Ina nan kallo kamar tsumma a randa, amma kasan da cewar  zuciyar da ka yaudara da sunan so kake azabtar da ita tana cikin gararin rayuwa tana cikin halin ha'ulai kullum bata da sukun hawayen idonta ya kasa daina zuba....... Katse ni yayi kafin in karasa magana ta yace." Wannan wace irin banzar magana kike min kina yi kina daga murya kamar kina yi da sa'an ki, kiyi min magana yanda zan fahimci me kike nufi ."

Haushi maganar shi ta bani saboda haka nace "Da Hausa nake maka magana ba da harshe nasara ba, nace" D'aya zuciyar daka yaudara tana cikin halin ha'ulai da damuwa saboda haka in ta shiga mugun hali to kai ne sila."
Lokaci guda ya fahimci inda maganar ta ta dosa.
Babu ya bo babu fallasa yace." Bani Momyna mu gaisa. "
A hasale nace"Ya ina yi maka magana daban kana yi min wata maganar, Mimi dai na bacci Wanda muka samu ya dauke ta da kyar don haka bazan tashe ta."
Na k'arashe maganar tawa a kufule!
Wannan karon akwai sassauci a muryarsa yace." Nace kiyi min bayani dallah-dallah yanda zan fahimta ni har yanzu ban gane abunda kike nufi ba."

Nace"Mimi na kwance babu lafiya tana jin jiki saboda sonka shine Abunda nake nufi. Ina jinsa yayi murmushi cikin nutsuwa yace." To waye mai laifi tsakanin ni da ita da iyayen Ku."?
Da sauri nace "Kar ka sake ka zage mu ko kafad'i bak'ar magana kan iyayen mu."
'Yar dariya naji Yayi yace." 'Yan matana kenan, dags magana zan zage iyayen Ku cewa nayi waye mai laifi sai ki bani amsa ta."

A fusace! Nace "Kai kasani."
Yace."OK naji bani Momyna muyi magana. "
"Kasan Allah bazan tashe ta ba wai me ma zaka fada mata ne bayan ka yaudare ta."
'Yar dariya yayi tare da fadin"Ina ruwan ki? Ke dai nace ki bani ita." Shiru yayi sai kuma ya cigaba da cewa"Kina maganar na yaudare ta, nifa ita nace s kawo wa kud'in aure akayi mistake aka kawo miki, bayan nan Kuma maganar Aminu ta futo, ai ni ne ma zan ce an yaudare ni an bani wacce bana ra'ayi."
Tsaki! Naja na kashe wayar ganin yana nema ya Mai da mutane mahaukata.

Ganin magariba ta kusa ne yasa na tashi Mimi domin baccin magariba babu kyau.
Lokacin Ya Aminu har ya kawo magunguna dasu Lemo da ayaba sai kai wa yake yana kawo wa, in muka hada ido ya buga min harara.

Muna idar da sallah na sanya Mimi a gaba taci abunci sannan na bata magunguna sai ta kwanta.
Nida Umma muna addu'ar Allah yasa kar tarin ya kara sark'e ta.

K'arfe Tara dai-dai naji ringing waya tsaki nayi Dan nasan wanene. Dauka nayi hade da sallama ba tare da ya amsa min ba yace." Ki futo yanzu ina jiran ki."
Ya kashe wayarsa.
Umma na kalla naga tana kallona nasan wayar handsfree ne taji komai
Tace "Ki tashi kije su manya mutane basa son jira."
Nace"Umma wane irin zance ne wannan k'arfe Tara na dare."
Umma tace"Sai kinyi surutun dai ko ki tashi kije Kuma kar ki sake ki futa da wannan kayan na jikin ki, masu kaurin hayak'i Dan dare yayi ma da sai kinyi wanka, ki gyara fuskar ki duk ki goge wannan maikon na fuskar ki,  don nasan bs hankaline dake ba sai ki futa haka.

Mik'ewa nayi na shiga dakinmu wallahi dai dai Umma tace in sanja kaya amma da bazan sanja ba, material dinmu na anko na dauko na tusa a cikina ina nishi na fesa turare na me saukin kudi goge fuska ta kawai nayi da abun goge hoda na yafa mayafi karami. Takalmi plate na sanya a kafata na futo
Umma ta bini da kallo cikin zuciyar ta tana tunanin kayan jikina domin sun futo da sassan jikina,
Shiru kawai tayi nace"Umma na tafi."
"To ki nutsu dai banda kaifin harshe nasan halin ki."
Raina babu dad'i na futa daga gidan ina mamakin kallon da Mimi take Min tunda taga na futo.

Dake dare ne kuma babu wuta a gari yasa bansha kallon gurin Samarin layinmu ba.
Na karasa har inda motar tasa take fake.
Sabuwar mota ce yazo da ita, fara tas! Daga yau ya fara shigar ta sai walwali take motar tayi kyau kuma daga ni zata ja kudi sosai.
Cikin zuciyata nace"Kaji dadinka yanda ka samu duniya Allah ya baka lahira."
Dake motar bata da duhu yana hangota sosai yake kallonta har ta k'araso ya bude motar tare da fadin"Bisimillah.." Kin shiga nayi na jinga jikin motar tare da fadin"Yau kam bazan shiga motar ka ba, domin bansan inda zaka kaini ba, in ka damu ka futo waje sai ka fada min abunda ya kawo ka."







*8/November/2019*
[11/9, 8:14 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*46*

Nafi minti goma da magana banji motsin sa ba, nace"Zan tafi tunda dai baza ka futo ni kam na daina shiga motar ka."
Daga ciki naji muryar shi a hankali yace." Ki shigo ciki shi yafi arziki ko kin manta da yanda nake cikin jama'a ? Yanzu zaki zama abun kallo, bayan haka kuma ga sauro a gurin , bana kaunar cizon sauro."
Nayi mamakin yanda yayi min magana Cikin kyakyawan lafazi nace" kayi alk'awarin baza ka kaini ko ina ba."?
Kai tsaye yace." Eh nayi alk'awari."
Motar na shiga wani irin sanyi da k'amshin sa suka cika min hanci.
Ina kokarin rufe motar ne ya ziro hannunsa ya rufe jikinmu ya had'u gurin haka.
Nace"Ka gani ko."?
Kallona Yayi tare da fadin"Me kuma nayi."? Shiru nayi masa ina dauke kaina.
Yace." Duk kin sanya sauro ya cika min mota dole a kaita car wash gobe. "
Ni dai bance masa komai ba.
Gyaran murya yayi tare da fadin"Babu gaisuwa ne."?
A hankali nace "Ina wuni."?
" Lafiya Lou ya halin ki."?
Ya fada yana min wani irin kallo.
Kauda kaina nayi zuciya ta tana wani irin bugawa bana son in kalleshi ballanta in rasa kuzari na shiyasa nake kiyayewa yana sanye da kananun kaya As'usuel ya kyau kamar ka sace ka gudu.

"Ya jikin Momyna."? Yafad'a idanunsa tsaye a kaina."
Nace"Da sauk'i dai."
"D'azu kina min magana ban fahimta ba, me yake damunta."?
Kai tsaye nace " Ciwon so."?
'Yar dariya yayi hade da Sosa kansa yace." Allah ya bata lafiya, 'yan mata da dama suna fama da wannan lalurar a kaina."
Kallonsa hade da bata fuska nace "Naga dariya kake yi kamar babu abunda ya dame ka, kasan kuwa Mimi tana jin jiki."
Girgiza kansa yayi yace." Ban sani ba, amma yanzu zan sani muje ki rakani in siyo mata kayan dubiya sai kiyi min jagora gidan naku."
Nace." Indai Lemo da ayaba ne kayan dubiyar bakin layinmu ma ana siyarwa."
"Ba irinsu zan siyo mata ba."
Yafad'a yana wani lumshe min ido tsabar munafurci.
Nace"Ni kam babu inda zani in ka shiga ka duba ta haka babu Wanda zai ce maka don me."
Siririn sajansa ya shafa hade da yin kasa da murya yace." Momyna tafi k'arfin haka a gurina ke dai kice baza ki rakani bane."
Shiru nayi masa kawai
Tsira min ido yayi yana kallona.
Ta wutsiyar idona nake kallonsa, sai na tsargu na fara kare jikina ina motsu-motsu."
Hannunsa ya sanya yana Jan k'aramin mayafina tare da fadin"Wannan gyalen dashi gwara babu domin babu abunda bana gani na jikin ki."
Da sauri na buge hannunsa INA hararasa.
Bai yi zuciya ba ya kara Jan gyale tare da fadin "Ai danni kikayi kwalliyar sai ki bari in duba da kyau."!
Baki na rawa nace" Kayan alk'awari cikawa."
Cikin wata 'yar iskar murya yace." Wane alk'awari nayi miki."?
Shiru nayi masa ina kara takure jikina jikin motar.
Gyaran murya yayi kamar wani munafuki yace." Dan kin samu ma nayi sha'awar kwalliyar ki, 'yan mata nawa ne suke so nayi sha'awar su basa gabana."
Tab'e bakina nayi nace." Wannan abunda ya shefe ka ne bai shafe ni ba."
Mayafin nawa ya kara ja a karo na uku yace." Kema ya shafe ki, tunda dai zaki aure ni dole kiyi hakuri dasu."
Hannuna nasa naja mayafin hade da bata fuskata nace"Abunda kake yi haramun ne, bana so idan ka saba taba jikin 'yan mata to ni ba irinsu bace, bari kaji wani Abu da baka sani ba, Wallahi Sam bana sha'awar auran namiji mazina ci."
Kallona Yayi da rai a bace!
Nayi saurin kauda kaina
Yace." Kawai don nayi niyyar ganin kwaliyyar ki zaki kirani da wannan kalamar."
Ban tanka masa ba, ya cigaba da cewa"Kar in kara jin wannan mummunar Kalmar ta futo daga bakin ki, idan zina nake baza kimin addu'a ba?  Ta inda Momyna tafi kenan ta iya lafazi da lallami da kalaman soyayya ke ko babu abunda kika iya sai hauka!!." Ya fada a harzuke.!
Naji haushin abunda Yace. Nima na kaurara murya ta sosai nace"Ai ba karya nayi maka ba, nima sau nawa kana auna ni, kuma ranar nan a gabana naji kuna waya da budurwar ka, kana yi mata zancan 'yan iska." Yace." To ina ruwan ki da 'yan mata na."?
Shiru nayi sai da na fad'i maganar nake da nasani nima kar ya dauka ko sonshi nake.
Da sauri nace"Babu ruwana dasu gaskiya ce na fada maka."
Shuru yayi min hade da zuba min ido kamar wani tsohon maye.
Babu zato naji ya fuzge min mayafi na ya jefa shi kujerar baya.
Da sauri na kare k'irjina sanin da nayi duk sun bullutsu ta saman rigata.
Matsowa yayi sosai hade da kashe hasken motar tayi duhu sosai. Matseni yayi jikin kujera hade da Dora hannunsa saman k'irjina yana shafawa,
A tare muka sauke ajiyar zuciya
Cikin wata kasalalliyar murya Yace. " Wannan dai nawa ne ni nasan ni zan iya dasu, ko na aure ki ko ban aure ki, baza ki taba jin dadin wani da namiji ba idan bani ba, saboda haka kin jawowa kanki ma zanyi abunda ban yi niyya ba."
Ture kanshi nake daga wuyana hankalina a tashe, hannunshi naji ya zura bayana yana laluben zif din rigar ta, kafin in Ankara naji ya zuge shi, k'arfi na na sanya ina tire shi hade da fadin"Wallahi idan baka dagani ba zan maka ihu!!!."" Kwantar da kujerar yayi na ji ni akwace da sauri ya rufe fa gagan jikinsa hade da cusa fuskarsa tsakanin wuyana yana sakin wani irin nishi!
Kafin in Ankara naji harshen shi a fatar wuyana yana lasa,cikin wani irin Dan iskan salo, tuni na kusa zaucewa na fara sakin nishi, hannunsa ya zura cikin briziyya ta ya damko breast dina guda yana mulmulawa.
Duk wani karsashi da jarumta na nemi shi na rasa sai na tsinci kaina da rungume kanshi dake saman k'irjina yayi laga-laga a kaina sai lasa ta yake.
Ina sakin nuffashi na manta a ina nake..................Daga ni yayi ya koma mazaunin shi.
Idona na bude ina kallon bayan shi, shi kuma yana kallona ta mirror fuskarsa dauke da wani miskilin murmushi.

Jikina nake dubawa babu Riga sai brez itama da ita gwara babu tunda duk ga breast dina nan a waje, siket dina duk ya tattare cinyoyina a waje.
Zuciyata nayi min wani irin zafi na mike zaune hade da d'aukar rigata ina sanyawa.
Naji yace." Yanzu ni dake waye d'an iska? Kawai daga tab'a ki kin wani lanjare har kina rungume ni kina kara bude min jikin ki ummmm!. Ki bani amsa ta."
Fad'ar halin bakin cikin da nake ciki a bata lokaci ne, rigar ta na sanya na dauki dankwalina na d'aura hade da gyara siket dina na soma kokarin bude kofar motar
Wani guri naga ya danna jikin kujerar sai ta mike zaune dani na zauna kusa dashi.
Har yanzu da murmushi a fuskarsa yace." Kinyi shiru baki bani amsa ba."

Muryata na rawa nace"Bude min kofa in futa Allah zai saka min."
Dariya yasa yana nuna ni da hannunsa yace." Allah zai saka miki kika ce.? Hummmm Asma'u manya mata."
Shiru nayi masa ina dauke Kaina.
Yace." Ki Bari lokaci nan zuwa da zan tsotse ki na shanye ki tasss!!!!! Lokacin da ya fad'i maganar wani irin fleenges ne ya zo min lumshe idona nayi gabana na fad'uwa Yace." Muje ki rakani in duba Momyna in wuce ina da gurin zuwa yanzu. "
Kallonsa na danyi nayi saurin kauda kaina zuciyata na raya min kila zai tafi gurin karuwarsa ne ya biyawa  kansa bukata.

Rai a bace nace"Kaji tsoron Allah a duk inda kake."
Babu yabo babu fallasa Yace." Tom Malama ta nagode da wa'azi." Kofar motar ya  bude na futa, shima ya futo Idonsa sakaye da glass mai duhu, naji yana fadin"Wannan unguwar taku banda dalilin Ku ban tab'a shigowa cikin ta ba."
Banza nayi dashi na tsallaka titi ya biyo bayana Cikin yanayin tafiyarshi ta jarumai yazo ya wuce ni

Da sauri na bi bayansa domin kar ya wuce gidan.
Tsayuwa nayi kofar gidanmu har ya k'araso ya tsaya muna kallon junanmu nace"Sai ka Bari in Sanar da Masu gidan."
"Owk" yace yana bin gidan da kallo, shiga nayi na barshi tsaye a gurin.
Mamaki yake sosai yanzu dama acikin wannan gidan Asma'u take rayuwa? Duka girman gidan bai kai b'angaran mai gadin gidan shi girma ba, gyada kansa yake yana duba 'yan gujub-gujub din gidajen dake layin namu a cikin zuciyarsa yake fadin talaka na ganin rayuwa me zai hana baza'ayi zazzab'in maleria ba kwataci duk sun bi hanya sauro da kudaje da bola ko ina.

Tsaye na ganshi jikin bango hannunsa nan nade a k'irjinsa nace"Shigo to"
Gaba nayi yana bina a baya

Umma na zaune gefen sabuwar tabarmar da ta shimfid'a masa tana sanye da farin hijab  fuska a sake take amsa sallamarsa.
Cikin ladabi naga ya tsaya bakin kofar ya cire hadd'adan takalimsa karfashi sanye da wata lafiyayyar safa ya karasa kan tabarmar .

Umma fad'i take"Sannu da zuwa yaron arziki Mara ba lale.
Zama yayi kanshi a kasa yace." Barka da yamma Umma na same Ku Lafiya."?
Umma tace"Lafiya Lou Alhmdullahi ya kokarin ka da fama da jama'a. "?
Yace." Alhmdullahi wallahi ya me jiki kuma."?.Tace" Jiki yayi sauk'i ai bs wani tsanani Yayi ba Asma'u ta ta soka." Murmushi yayi tare da fadin"Dama yau nayi niyar in shigo mu gaisa sai kuma take fadamin Momyna babu lafiya."
Umma tace"Wallahi kuwa tari take amma da sauk'i dai tunda Aminu ya siyo mata magani Tasha ta samu tayi bacci."
Yace." Tou Alhamdullahi Allah ya kara sauk'i. "
Yanda suke hira da Umma sai abun ya bani mamaki kamar Wanda suka shekara da sanin juna Umma sai shi masa albarka take da fadin"Muna ganin taimakon talakawa da kake yi a garinan muna jin dad'i Ubangiji Allah ya tsare ka ya kare ka daga sharrin masu sharri. " yaji dadin adduoin da Umma take masa ga yanayin yanda yake amsawa

Mimi dake kwance a daki tana bacci kamar a mafarkin taji muryar shi firgigt ta tashi ta zauna k'irjinta yayi mata nauyi sosai rarrafowa tayi ta futo tsakar gida tana dafa bango
Nice na fara ganinta ganin kamar tana kokarin fad'uwa ya sanya naje da sauri na rike ta muka karasa kusa dasu Umma
Tace." Yauwa ai gata nan ma ta tashi sannu Mimi."
Zaunar da ita nayi kusa da shi, na matsa gefe
Amjad mamaki ramar Mimi yake duk da yake dare ne kuma tsakar gidan babu wadataccan haske sai da ya fahimci tana jin jiki.
A hankali yace." Momyna ya jikin ki? Ashe haka Abu yayi tsanani. "
Cikin sanyayyr murya tace." Jiki da sauk'i ." gyada kansa yayi tare da kallon Umma yace." Kunje asibiti da ita kuwa."?
Kafin Umma tace Wani Abu Yaya Aminu ya shigo gidan.
Gabansa ne ya fad'i ganin Mutumin dake zaune ga gidan jininsa Mimi kenan a zaune a kusa dashi, lokaci guda ya b'ata fuskarsa hade da yin kicin-kicin da ita sama-sama suka gaisa dashi Yana mamakin me ya kawo shi, zama yayi gefen rijiya yana sauraran maganar da suke yi da Umma.
[11/9, 6:44 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*46*

Nafi minti goma da magana banji motsin sa ba, nace"Zan tafi tunda dai baza ka futo ni kam na daina shiga motar ka."
Daga ciki naji muryar shi a hankali yace." Ki shigo ciki shi yafi arziki ko kin manta da yanda nake cikin jama'a ? Yanzu zaki zama abun kallo, bayan haka kuma ga sauro a gurin , bana kaunar cizon sauro."
Nayi mamakin yanda yayi min magana Cikin kyakyawan lafazi nace" kayi alk'awarin baza ka kaini ko ina ba."?
Kai tsaye yace." Eh nayi alk'awari."
Motar na shiga wani irin sanyi da k'amshin sa suka cika min hanci.
Ina kokarin rufe motar ne ya ziro hannunsa ya rufe jikinmu ya had'u gurin haka.
Nace"Ka gani ko."?
Kallona Yayi tare da fadin"Me kuma nayi."? Shiru nayi masa ina dauke kaina.
Yace." Duk kin sanya sauro ya cika min mota dole a kaita car wash gobe. "
Ni dai bance masa komai ba.
Gyaran murya yayi tare da fadin"Babu gaisuwa ne."?
A hankali nace "Ina wuni."?
" Lafiya Lou ya halin ki."?
Ya fada yana min wani irin kallo.
Kauda kaina nayi zuciya ta tana wani irin bugawa bana son in kalleshi ballanta in rasa kuzari na shiyasa nake kiyayewa yana sanye da kananun kaya As'usuel ya kyau kamar ka sace ka gudu.

"Ya jikin Momyna."? Yafad'a idanunsa tsaye a kaina."
Nace"Da sauk'i dai."
"D'azu kina min magana ban fahimta ba, me yake damunta."?
Kai tsaye nace " Ciwon so."?
'Yar dariya yayi hade da Sosa kansa yace." Allah ya bata lafiya, 'yan mata da dama suna fama da wannan lalurar a kaina."
Kallonsa hade da bata fuska nace "Naga dariya kake yi kamar babu abunda ya dame ka, kasan kuwa Mimi tana jin jiki."
Girgiza kansa yayi yace." Ban sani ba, amma yanzu zan sani muje ki rakani in siyo mata kayan dubiya sai kiyi min jagora gidan naku."
Nace." Indai Lemo da ayaba ne kayan dubiyar bakin layinmu ma ana siyarwa."
"Ba irinsu zan siyo mata ba."
Yafad'a yana wani lumshe min ido tsabar munafurci.
Nace"Ni kam babu inda zani in ka shiga ka duba ta haka babu Wanda zai ce maka don me."
Siririn sajansa ya shafa hade da yin kasa da murya yace." Momyna tafi k'arfin haka a gurina ke dai kice baza ki rakani bane."
Shiru nayi masa kawai
Tsira min ido yayi yana kallona.
Ta wutsiyar idona nake kallonsa, sai na tsargu na fara kare jikina ina motsu-motsu."
Hannunsa ya sanya yana Jan k'aramin mayafina tare da fadin"Wannan gyalen dashi gwara babu domin babu abunda bana gani na jikin ki."
Da sauri na buge hannunsa INA hararasa.
Bai yi zuciya ba ya kara Jan gyale tare da fadin "Ai danni kikayi kwalliyar sai ki bari in duba da kyau."!
Baki na rawa nace" Kayan alk'awari cikawa."
Cikin wata 'yar iskar murya yace." Wane alk'awari nayi miki."?
Shiru nayi masa ina kara takure jikina jikin motar.
Gyaran murya yayi kamar wani munafuki yace." Dan kin samu ma nayi sha'awar kwalliyar ki, 'yan mata nawa ne suke so nayi sha'awar su basa gabana."
Tab'e bakina nayi nace." Wannan abunda ya shefe ka ne bai shafe ni ba."
Mayafin nawa ya kara ja a karo na uku yace." Kema ya shafe ki, tunda dai zaki aure ni dole kiyi hakuri dasu."
Hannuna nasa naja mayafin hade da bata fuskata nace"Abunda kake yi haramun ne, bana so idan ka saba taba jikin 'yan mata to ni ba irinsu bace, bari kaji wani Abu da baka sani ba, Wallahi Sam bana sha'awar auran namiji mazina ci."
Kallona Yayi da rai a bace!
Nayi saurin kauda kaina
Yace." Kawai don nayi niyyar ganin kwaliyyar ki zaki kirani da wannan kalamar."
Ban tanka masa ba, ya cigaba da cewa"Kar in kara jin wannan mummunar Kalmar ta futo daga bakin ki, idan zina nake baza kimin addu'a ba?  Ta inda Momyna tafi kenan ta iya lafazi da lallami da kalaman soyayya ke ko babu abunda kika iya sai hauka!!." Ya fada a harzuke.!
Naji haushin abunda Yace. Nima na kaurara murya ta sosai nace"Ai ba karya nayi maka ba, nima sau nawa kana auna ni, kuma ranar nan a gabana naji kuna waya da budurwar ka, kana yi mata zancan 'yan iska." Yace." To ina ruwan ki da 'yan mata na."?
Shiru nayi sai da na fad'i maganar nake da nasani nima kar ya dauka ko sonshi nake.
Da sauri nace"Babu ruwana dasu gaskiya ce na fada maka."
Shuru yayi min hade da zuba min ido kamar wani tsohon maye.
Babu zato naji ya fuzge min mayafi na ya jefa shi kujerar baya.
Da sauri na kare k'irjina sanin da nayi duk sun bullutsu ta saman rigata.
Matsowa yayi sosai hade da kashe hasken motar tayi duhu sosai. Matseni yayi jikin kujera hade da Dora hannunsa saman k'irjina yana shafawa,
A tare muka sauke ajiyar zuciya
Cikin wata kasalalliyar murya Yace. " Wannan dai nawa ne ni nasan ni zan iya dasu, ko na aure ki ko ban aure ki, baza ki taba jin dadin wani da namiji ba idan bani ba, saboda haka kin jawowa kanki ma zanyi abunda ban yi niyya ba."
Ture kanshi nake daga wuyana hankalina a tashe, hannunshi naji ya zura bayana yana laluben zif din rigar ta, kafin in Ankara naji ya zuge shi, k'arfi na na sanya ina tire shi hade da fadin"Wallahi idan baka dagani ba zan maka ihu!!!."" Kwantar da kujerar yayi na ji ni akwace da sauri ya rufe fa gagan jikinsa hade da cusa fuskarsa tsakanin wuyana yana sakin wani irin nishi!
Kafin in Ankara naji harshen shi a fatar wuyana yana lasa,cikin wani irin Dan iskan salo, tuni na kusa zaucewa na fara sakin nishi, hannunsa ya zura cikin briziyya ta ya damko breast dina guda yana mulmulawa.
Duk wani karsashi da jarumta na nemi shi na rasa sai na tsinci kaina da rungume kanshi dake saman k'irjina yayi laga-laga a kaina sai lasa ta yake.
Ina sakin nuffashi na manta a ina nake..................Daga ni yayi ya koma mazaunin shi.
Idona na bude ina kallon bayan shi, shi kuma yana kallona ta mirror fuskarsa dauke da wani miskilin murmushi.

Jikina nake dubawa babu Riga sai brez itama da ita gwara babu tunda duk ga breast dina nan a waje, siket dina duk ya tattare cinyoyina a waje.
Zuciyata nayi min wani irin zafi na mike zaune hade da d'aukar rigata ina sanyawa.
Naji yace." Yanzu ni dake waye d'an iska? Kawai daga tab'a ki kin wani lanjare har kina rungume ni kina kara bude min jikin ki ummmm!. Ki bani amsa ta."
Fad'ar halin bakin cikin da nake ciki a bata lokaci ne, rigar ta na sanya na dauki dankwalina na d'aura hade da gyara siket dina na soma kokarin bude kofar motar
Wani guri naga ya danna jikin kujerar sai ta mike zaune dani na zauna kusa dashi.
Har yanzu da murmushi a fuskarsa yace." Kinyi shiru baki bani amsa ba."

Muryata na rawa nace"Bude min kofa in futa Allah zai saka min."
Dariya yasa yana nuna ni da hannunsa yace." Allah zai saka miki kika ce.? Hummmm Asma'u manya mata."
Shiru nayi masa ina dauke Kaina.
Yace." Ki Bari lokaci nan zuwa da zan tsotse ki na shanye ki tasss!!!!! Lokacin da ya fad'i maganar wani irin fleenges ne ya zo min lumshe idona nayi gabana na fad'uwa Yace." Muje ki rakani in duba Momyna in wuce ina da gurin zuwa yanzu. "
Kallonsa na danyi nayi saurin kauda kaina zuciyata na raya min kila zai tafi gurin karuwarsa ne ya biyawa  kansa bukata.

Rai a bace nace"Kaji tsoron Allah a duk inda kake."
Babu yabo babu fallasa Yace." Tom Malama ta nagode da wa'azi." Kofar motar ya  bude na futa, shima ya futo Idonsa sakaye da glass mai duhu, naji yana fadin"Wannan unguwar taku banda dalilin Ku ban tab'a shigowa cikin ta ba."
Banza nayi dashi na tsallaka titi ya biyo bayana Cikin yanayin tafiyarshi ta jarumai yazo ya wuce ni

Da sauri na bi bayansa domin kar ya wuce gidan.
Tsayuwa nayi kofar gidanmu har ya k'araso ya tsaya muna kallon junanmu nace"Sai ka Bari in Sanar da Masu gidan."
"Owk" yace yana bin gidan da kallo, shiga nayi na barshi tsaye a gurin.
Mamaki yake sosai yanzu dama acikin wannan gidan Asma'u take rayuwa? Duka girman gidan bai kai b'angaran mai gadin gidan shi girma ba, gyada kansa yake yana duba 'yan gujub-gujub din gidajen dake layin namu a cikin zuciyarsa yake fadin talaka na ganin rayuwa me zai hana baza'ayi zazzab'in maleria ba kwataci duk sun bi hanya sauro da kudaje da bola ko ina.

Tsaye na ganshi jikin bango hannunsa nan nade a k'irjinsa nace"Shigo to"
Gaba nayi yana bina a baya

Umma na zaune gefen sabuwar tabarmar da ta shimfid'a masa tana sanye da farin hijab  fuska a sake take amsa sallamarsa.
Cikin ladabi naga ya tsaya bakin kofar ya cire hadd'adan takalimsa karfashi sanye da wata lafiyayyar safa ya karasa kan tabarmar .

Umma fad'i take"Sannu da zuwa yaron arziki Mara ba lale.
Zama yayi kanshi a kasa yace." Barka da yamma Umma na same Ku Lafiya."?
Umma tace"Lafiya Lou Alhmdullahi ya kokarin ka da fama da jama'a. "?
Yace." Alhmdullahi wallahi ya me jiki kuma."?.Tace" Jiki yayi sauk'i ai bs wani tsanani Yayi ba Asma'u ta ta soka." Murmushi yayi tare da fadin"Dama yau nayi niyar in shigo mu gaisa sai kuma take fadamin Momyna babu lafiya."
Umma tace"Wallahi kuwa tari take amma da sauk'i dai tunda Aminu ya siyo mata magani Tasha ta samu tayi bacci."
Yace." Tou Alhamdullahi Allah ya kara sauk'i. "
Yanda suke hira da Umma sai abun ya bani mamaki kamar Wanda suka shekara da sanin juna Umma sai shi masa albarka take da fadin"Muna ganin taimakon talakawa da kake yi a garinan muna jin dad'i Ubangiji Allah ya tsare ka ya kare ka daga sharrin masu sharri. " yaji dadin adduoin da Umma take masa ga yanayin yanda yake amsawa

Mimi dake kwance a daki tana bacci kamar a mafarkin taji muryar shi firgigt ta tashi ta zauna k'irjinta yayi mata nauyi sosai rarrafowa tayi ta futo tsakar gida tana dafa bango
Nice na fara ganinta ganin kamar tana kokarin fad'uwa ya sanya naje da sauri na rike ta muka karasa kusa dasu Umma
Tace." Yauwa ai gata nan ma ta tashi sannu Mimi."
Zaunar da ita nayi kusa da shi, na matsa gefe
Amjad mamaki ramar Mimi yake duk da yake dare ne kuma tsakar gidan babu wadataccan haske sai da ya fahimci tana jin jiki.
A hankali yace." Momyna ya jikin ki? Ashe haka Abu yayi tsanani. "
Cikin sanyayyr murya tace." Jiki da sauk'i ." gyada kansa yayi tare da kallon Umma yace." Kunje asibiti da ita kuwa."?
Kafin Umma tace Wani Abu Yaya Aminu ya shigo gidan.
Gabansa ne ya fad'i ganin Mutumin dake zaune ga gidan jininsa Mimi kenan a zaune a kusa dashi, lokaci guda ya b'ata fuskarsa hade da yin kicin-kicin da ita sama-sama suka gaisa dashi Yana mamakin me ya kawo shi, zama yayi gefen rijiya yana sauraran maganar da suke yi da Umma.

Umma tace." Ba muje asibiti ba amma dai gobe in Allah ya kaimu za muje a duba ta sosai."
Gyada kansa yayi shiru na minti biyu yace." Gobe idan Allah ya kaimu zan turo dravar sai a kaita asibtin malam Aminu a duba ba ta sosai."

Umma tace"Allah yayi albarka ai da ka bari ma, sai muje asibitin Murtala ." Hannu ya zura aljihu ya futo da kudi masu yawa ya zube gaban Umma ya mike tare da fadin" Zan wuce Allah ya bata Lafiya ."
Umma tace"Harda wahala kuma ai da ka barshi."
Shiru yayi ya mik'awa Aminu hannu suyi sallama.
Rai babu dad'i Aminu ya mik'a masa nasa hannun sukayi musabaha.
Takalmin shi ya sanya Umma sai godiya take masa futa yayi cikin sauri Umma ta kalleni tare da fadin" Kije ki raka shi mana kinye tsaye."
Bayansa nabi da sauri..
Yayi nisa sosai don Haka sai da na k'ara sauri.
Na tadda shi.
Yana kokarin bude mota na same shi
Yace." Amma nayi mamakin ramar Mimi,Abunda kika fada gaskiya ne."?
'K'warai kuwa Mimi na sonka sosai kai kuma kana yaudarar ta."
Shiru yayi yana tunani tabbas abunda Asma'u ta fada gaskiya ne baya jin dai-dai da kwayar zarrah na son Mimi a zuciyar sa, yana yi mata so ne kawai irin na musulunci sai kuma sunan mahaifiyar sa da take dashi.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin"Allah ya bata Lafiya, Nasan ni babu laifina anan gaskiyar magana ko Yanzu aka ce an bani ita zan aure ta darajar son da data ke min."
[11/10, 8:25 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*Mallakar_BINTA UMAR*
*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*47*

Shiru nayi masa domin na rasa abunda zance dashi ni kaina al'amarin Mimi yana bani tsoro Mota ya bude ya shiga tare da fadin"Ni zan tafi zan kira waya insha Allahu. "
Matsawa nayi daga jikin motar ba tare da nace masa komai ba ya ja ya tafi na lura jikinsa duk yayi sanyi.
Ina koma wa gida na tarar da Ya Aminu ya tasa Umma a gaba sai faman bala'i yake mata
Ina shiga ya hau d'ura min ashar wai me yasa na gayyato Amjadu gida wallahi komai kulafucin sa ba zai bar mishi Mimi ba.
Masifa yake kamar zai dake ni Umma tace"Kar ka sake ka doke ta Aminu Sam Asma'u bata da laifi Kaine dai idonka ya rufe, ka ke ganin da laifin ta anan.".
Kan Mimi ya dawo cikin hargowa yace." Wallahi Mimi ko mutuwa zaki baza ki aure shi ba sai dai idan ki Mutu ni dashi mu rasa amma ina ji ina gani bazan bar masa ke ba."
Yana gama maganar shi ya fuce daga gidan a fusace.!
Mimi ta fashe da kuka tari ya sark'e ta, aikuwa ta dinga yi bubu ji babu gani,
Umma ta jawo ta jikinta ta rungume ta sosai tana danne mata kirjinta hankalinta duk ya tashi
Da sauri tace"Asma'u d'ebo ta murhu a shafa mata ko Allah zai sanya ya Tsaya tari.
Da gudu na nufi kicin na d'ebo toka Umma ta bude rigar Mimi ta shafa mata.
Kamar kara ingizata ake ta cigaba da tari!!! Nace." Ina maganin a dauko a kara bata."
Da kyar Umma tace"Dauko a daki." Dakin na shiga da sauri na dauko maganin, abunda na gani yayi mutukar gigita ni da bani tsoro wani irin jini bak'ikkirin na gani daga bakin Mimi yana zubowa jikin Umma,
Da sauri na jefar da kwalbar maganin nayi kanta INA salati.
Umma kuwa kuka ta fashe dashi tana tare jinin da hannunta.
Baki na rawa nace"Umma jini ne ko."? Tace." Asma'u maza duba waje ki gani Aminu nan ki kirashi mu tafi asibiti abun ya zama babba."
Da gudu na futa ko talkami babu.
Mimi ta galabaita iya galabaita tari take sosai jini na zuba daga bakinta idanunta sunyi jajazur dashi sai daga hannu take.
Ni da Aminu muka shigo gidan hankalumu ya tashe.
Yana ganin Abunda yake faruwa ya gigice tare da fadin"Innalillahi wainnailahi raji'un. " futa yayi da sauri ya dauko mota.
D'aukar ta yayi kacokan ya futa da ita da saurin
Nida Muka rufa masa baya zuwa yanzu na fara kuka tukuru ganin yanda Nuffashin Mimi yake hawa da sauka.
A dai-dai sahu har kofar gidanmu don haka muna futa muka shiga saboda idanun Jama'a Umma ta rungume Mimi a jikinta hankalinta duk ya tashi mai a dai-dai ya ja mu katafi shi ma hankalinsa ya tashi da ganin abunda yake faruwa ya tausayawa Mimi sosai.
Murya a sanyaye Umma tace" Ka kira aunty Ku a waya ka fada mata halin da ake ciki, sannan ka kira Kawunta wato Babansu Munnu."
Wayarsa ya futo da ita da sauri.

Kai tsaye!! Asibitin zana d'an a dai-dai ta ya sauke mu, Aminu ya sallame shi mu kuma muka taitayi Mimi muka shiga da ita ciki.
Har yanzu tarin take idanunta a rufe gaban rigarta duk ya b'aci da jini
Wani ma'aikacin gurin ne ya k'araso gurunmu da sauri da wani keke dama mun San ka'idar asubitin Mimi muka Dora kan keken ya ja ta da sauri ya shiga ciki da ita.
Tsayuwa muka yi bakin kofa duk jikinmu a sanyaye.
Umma tace"WANNAN kukan da kike bashi ne zai bata lafiya ba, addu'a zakiyi mata kawai."
Nace"Umma Mimi na bani tausayi haka kurrum zata jawo mana abunda baza mu iya ba."
Tace"Itama ba ita ta dorawa kanta ba Allah ne saboda haka sai dai mu bar masa.
Yaya Aminu kuwa kai wa yake yana kawowa a filin asibitin idan ka kalli fuskarsa sai ka rantse da bai taba dariya ba tunda uwarshi ta haife shi, shi a ganinsa zuwan guy gidan ne ya dawo da Mimi ciwon ta sabo ta inda har ya tsananta ta fara zubar fa jini dole ya mike tsaye a kan al'amarin domin yana ganin Ana so ayi masa tsakiyar da babu ruwa wani irin haushin guy yake ji da tsanar sa a cikin zuciyarsa

K'arfe goma saura sai ga aunt Hauwa ta shigo asubitin hankalinta a tashe take tambayar abunda ya sami Mimi Umma ta dinga fada mata tun farkon al'amarin
Jama'ar gidansu Motar Babansu Munnu ce ta shigo asubitin Aminu ya karasa da sauri ya bude masa motar
Ya futo tare da Ummansu Munnu da ita Munnu duk babu nutsuwa a tartare dasu.
Su k'araso kusa da mu suna gaisawa da Umma jiki duk babu nutsuwa
Yace." Ina Aishatu take." ? Dake da haka yake kiranta
Umma tace." Tana ciki tun d'azu dector yana dubata."
Jin Gina yayi jikin bango yana sauke ajiyar zuciya Mahaifin yarinyar ya tuno da yanda yake kaunarta da irin amanar da ya bashi kafin ya tafi Wanda har yanzu ba a San a wace duniyar yake ba, tun bayan rasuwar mahaifiyar Mimi din yaji duniyar ta isheshi ya hada ina sa ina sa, yayi sallama da 'yan cewar ya tafi Neman kudi tunda ga ranar har yanzu basu sake ganinsa ba amma labari na zuwan musu cewar yana cikin koshin Lafiya, kuma bashi da zance dai na d'iyarsa Aishatu.
[11/10, 6:49 AM] Binta U Abbale: Umma da Ummansu Munna zancan suke yi cikin jimami ni da Munnu kuwa babu abunda muke yi sai aukin kuka

Kusan awar Mimi daya a ciki sannan wata narse ta futo tace"Waye mahaifin yarinyar nan da aka wo ta yanzu emergency. " Kawu yace." Ganinan." Juyawa tayi tana fadin"Muje dector yana son ganinka ".
Dukaninmu sai mukaji kamar mu bi Kawu muji me dector zai ce masa.

Kawu da dector ne a ofis a hankali Dr ya cire farin gilashin dake idonsa ya kalli Kawu suka gaisa a mutumce yace." Kaine mahaifin yarinyar nan ko."?
Jiki a sanyaye Kawu yace." Nine Dr Allah yasa naji alkairi."
Dr ya gyada kansa tare da fadin " I'm sorry to say yarinyar ka tana cikin garari rayuwa domun zuciyar ta ta Riga ta tab'u sakamakon tunani da damuwa da ta sanya a ranta bayan haka kuma da akwai a Abunda take mutukar so Wanda aka hanata shi shine mussababbin ciwon nata idan ba 'ayi gaggawar kwantar mata da hankalin ba, to ana iya rasa ta a ko wane lokaci."

Kawu ya share zufa da take tsatstsafo masa a goshi yace." Dr yanzu wane irin taimako za'ayi mana."?
Dr ya gyada kansa cikin nazari yace." Taimakon da zan fara yi shine, kuje gida Ku rarrasheta sosai Ku lallame ta tayi kokarin fada muku abunda take so Wanda ta sanya a ranta ya dame ta, idan kun San abun to sai kuyi gaggawar bata shi domin samun zaman lafiya da d'orewar lafiyar ta, bayan haka kuma zan d'aura ta a kan magani insha Allahu mutukar aka bi doka zata samu lafiya, yanzu dai mun dakatar da zubar jinin insha allahu babu matsala."

Kawu yace." Insha Allahu komai zai zo cikin sauk'i zamu bi doka zamu kuma zauna da yarinyar domin mu tuntube ta muji meye Matsalar.

Dr ya gyda kansa tare da fadin"all right."  rubuce-rubece yayi jikin wata takarda ya mik'a masa tare da fadin idan ka futa zaka ga pharmacy sai ka shiga ka siyo wad'annan magungunan insha Allahu, amma ba yau zamu sallame ta ba sai zuwa gobe dole zamu ga dai-dai tuwar numffashinta."
Kawu ya karb'i takardar da sauri ya futa.

Yana futowa muka mike da sauri dukaninmu tambayar sa muke jikin Mimi
"Da sauk'i yake cewa kawai ya nufi dakin magani Aminu ya bishi a baya.
Ofis din Dr suka nufa har Aminu Dr Ya kalli Aminu tare da Kawu yace." Wannan fa."?
Kawu yace." Shine Wanda zai aure ta." Dr yace." Zauna muyi magana da Kai. "
Aminu ya zauna kan kujera jikinsa sanyi k'alau!
Dr yace." Kaine kafi kusanci da sosai Kaine zaka fi sanin abunda yake damunta domin sai ta fada maka abunda yake damunta bata fadawa Iyayenta ba, saboda haka Kayi kokarin rarrashinta ta Sanar da kai meye matsalarta domin magance ta kada ka rasa kyakyawar matarka Cikin lokaci kankani."Ya Aminu yayi shiru yana sauraran Dr da abunda yake fada
Ba sai yayi masa dogon sharhi ba, yasan kome ye yake damun Mimi bai wuce soyayyar Amjadu ba, Wanda yake ganin a kan ya sadaukar masa da ita gwara Mimi ta mutu in yaso kowa ma yayi asara.
Shiru kawai yayi har Dr ya gama maganar shi suka mike da niyyar futa Aminu ya tsaya tare da fadin" Dr babu halin ganinta a yanzu."? Dr ya gyda kansa tare da fadin" ta samu bacci yanzu sai dai gobe insha Allahu da safe sai Ku shiga Ku ganta kafin a sallame Ku."
Jiki babu k'wari ya futa daga ofis din.
Fuskarsa na kalla naga yayi kucin-kicin gabana ya fad'i nayi saurin kallon Fuskar Kawu nan ma naga babu sauk'i tuni kukana ya tsananta nace"Ku fada mana ko menene k'afafun Babansu Munnu na rike ina kuka.
Ummansu Munnu ta janye ni tana rarrashinna ni a lokacin sai nake ganin kamar zasu ce Mimi ta mutu ne Sabuda yanda muka kawo ta a sibitin ta futa daga hayyacin ta.

Can gefe guda suka tsaya suna magana. Kawu yace." Aminu ni a iya fahimta ta nafi tunanin Mimi ta sanya soyayyar wannan Yaro da zai auri Asma'u a cikin ranta ne Wanda yake kokarin haifar mata da WANNAN gagarumar Matsalar shine Abunda nake tunani."

Aminu ya gyara tsayuwarsa babu sassauci a muryarsa yace." Dama ni tun kafin muzo gaban likita ya fada mana meye na gane komai, a gaskiya Baba babu mahalukin da zan iya barwa Mimi domin nima idan nayi haka zan iya shiga cikin tashin hankali watak'ila ma nawa yafi nata tunda kowa ya shaida nafi sonta ita bata sona saboda haka ni ina gani kawai daga nan zuwa jini a d'aura mana aure da ita ba sai an jira lokacin da aka sanya ba, idan taji labarin haka nasan dole zata hak'ura ta fawwala Allah kasan dama ance kiyyayyar 'ya mace bata tasiri ina ganin Mimi zata hak'ura ta zauna dani."!

Kawu ya gyada kansa yana Nazarin maganar Aminu Yaro Yaro ne, murmushi yayi yace." Aminu kenan, kamar ka manta abunda Dr yace akan Aishatu, Jin labarin d'aurin auranku zai iya sanyawa zucuyarta ta buga gaba daya ta mutu lokaci guda, kaga kuwa wannan sha'awar taka ba abun dubawa bace."

Aminu ranshi ya b'aci da jin abunda Kawu yake fada murysrshi a kaurare yace." Kai ya kake ganin za'ayi."
Kawu ya kalleshi cike da mamaki jin yana yi masa magana kazar-kazar babu Wani ladabi.
Yace." Abunda za'ayi shine mu samawa Aishatu abunda take so domun samun ta da tabbatuwar lafiyar ta.

Aminu ya watsa masa wani kallo tare da fadin"Kawu in na fahimce ka anan shine kana so kace min in hak'ura da Mimi in yaso Ku bats Wanda take so kome."?

Kai tsaye..... Kawu yace." Shine abunda nake Nufi."
Aminu ya guda kansa yana murmushi me ciwo yace." Impossible, bazai tab'a yiwu wa ba Kawu Mimi 'yar kace nima inda kara d'an ka ne nasan baza ka bawa Mimi bare ba gani a zaune, ina so saboda haka yanda aka karb'i kud'in aure na da Mimi to babu mahalukin da ya Isa ya hana tabbatuwar auramu idan ba Wanda ya hallice mu ba."
Cike da d'umbun mamaki Kawu yake kallon Aminu ganin yanda yake wani irin huci!! Yace." Aminu ka fahimce ni mana ba wai ina k'in ka ban......... Kafin ya karasa Aminu ya daga masa hannu a fusace.!!! Yace." Kawu ga magana nan ta futo kanunamin bakai ka haife ni b.... Cike da b'acin rai Kawu yace." Rashin kunya zakayi min Aminu. "
Daga kafad'a yayi tare da fadin "Babu maganar rashin kunya anan Kawu gaskiya ce ni nayi rantsuwar babu Wanda ya Isa ya hanani auran Mimi."

Ganin tsageran cin da Aminu yake masa ne yasa ya fusata shima yace." Aminu indai nine waliyin Aishatu to baza ka aure ta ba."
Aikuwa sai ya ingiza Aminu ta inda ya shiga sirfa masa rashin kunya wanda ya jawo hankalimu Kansu dukanimu mu k'araso gurin tare da tambayar ba'asi
Abunda Aminu yake yi yayi bala'in konawa Umma rai ta cire hannunta ta zabga masa mari cikin tsawa tace"Na kara jin bakinka a gurinan Aminu sai na tsine maka, a tunanin ka wannan tsagerancin da rashin kunyar da kake yi shine zai sanya a baka auran Mimi ko meye."?

Kawu yace." Kyaleshi ya zage ni son ransa lokacin sa ne."
Wuce mu yayi tafi can bakin get ya zauna tare da masu gadi

Fada sosai Umma take wa Aminu Tace" Haka ake soyayya da hauka Aminu ka futo da son zuciyarka a fili kana ganin mawuyacin halin da yarinyar nan take ciki shine zakaje gwara ta mutu a kan ka janye kudirin ka a kanta, me yasa ita lokacin da ka fad'i har ka kwanta a asibiti tace"Zata aure ka alhalin ga Wanda zuciyar ta take so Mimi yarinya ce me ladabi da gudun b'acin rain wani ta so ta faranta maka ta faran wa zuciyata  ba tare da ta damu da nata farin cikin ba, shine yanzu tana cikin halin rai da rayuwa kake mummunan magana a kanta Aminu wannan ba soyayya bace."!!!!
Umma ta karasa maganar ta tana haki! Kana ganinta zaka fahimci tana cikin tsananin b'acin rai da damuwa
Cikin kuka na futar hayyaci nace"Wallahi tallahi Umma mutukar Ya Aminu bai janye kudirinsa ba nima bazan aure shi ba, sai dai mu zauna a haka, kawai a aura mata Wanda zuciyarta take so ta huta da wannan azabar da take sha."
Umma tace." Ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Mimi bata da Miji sai Amjadu dole a bawa zuciyarta hakuri abata abunda take so."
Ya Aminu ya kalleni ya kalli Umma zuciyarsa nayi masa wani irin ciwo yace." Umma don bani da kudi bani da aikin yi bani da mota bani da babur bani da keken hawa kana bani da kudi a banki kuke mun haka,? Meye laifi na meye? Aibuna anan Zan kula da Mimi zan tsare mutumcin ta zan sanya ta farin ciki! Umma kar Ku kware min baya akan Mimi Ku duba halin da zan shiga a kanta soyayyar ta tana iya kashe ni!!!!! Umma ni danki ne baza ki so wani bayan ni ba, Umma ki dube ni da idanun rahama!! Ki tuna so da kaunar da kike min Umma ki bani Mimi domin itace farin cikin rayuwata."!!!!!!!! Ya k'arashe maganar sa hawaye na zubowa daga idanunsa

Umma ta zube a gurin Tare da dafe k'irjinta tana salati aunt Hauwa da Ummansu Munnu suka rike ta hawaye ne ya fara zirarawo daga idanunta muryarta na rawa tace"Ya Allah ka ije mun wannan masifa da ta tun karo ni, Allah ka sanyaya min kasa kawo karshen wannan badak'ala!! Sai hawaye sharrrrrrrr-sharrrrrrrr suka fara zuba a kuncinta.
Duk taurin zuciya irin ta aunt Hauwa hawaye ta fara sharewa ganin Umma tana kuka abunda zai sanya Umma kuka ba Karami bane hakuri kurum suke bata

Ni ko da sauri na bar gurin bayan na warce wayar Munnu dake tsaye, wani d'an korido na nufa dake Cikin asibitin na fara Neman numbar sa, sai da tayi ringing sai uku ba a dauka ba,

Sai ana hudu ne ya dauka muryarsa da yanayin bacci yayi sallamsa da sauri nace." Kanwa ta kar tsami! Kwarna fi ya kwanta. "!!!! Jin muryar yarinyar ya sashi mik'ewa zaune da sauri hade da yaye blanket din jikinshi na ci gaba da cewa " Yanzu haka muna babban asibiti na zana Mimi a kwance rai a hannun Allah bayan tafiyar ka, jini ya tsinke mata ta baki ta hanci!!!! Ta galabaita mutuka duk ta dalilin ka!!! Ina kara fada maka duk abunda ya same ta Kaine sila Kaine! Mujaza!! Mahaifiyar mu ta zubar da hawaye akan haka, mun zubar da hawaye a kan haka, duk wani mai imani ya kalli Halin da Mimi ta shiga a yanzu sai ya tausaya mata, insha Allahu duk wani sharrinka sai ya koma kanka ka cuce mu, ka yaudare mu, Ka azabatar da zuciyar Mimi akan sonka kullum kana fada cewar zaka aure ta, alhalin karya kake!!! Wallahi mutukar ka bari Mimi ta mutu baka yi Wani Abu akai ba nima sai na kashe ka."!!!!!!!!!!! Kamar wata mahaukaciya haka na k'arashe maganar..... Wata irin zufa ce ta keto masa duk da cewar akwai AC a dakin Muryarshi sanyi k'alau yace." Asma'u.!!! " saurin kashe wayar  nayi na zube a gurin hade da fashewa da kuka mai cin rai.

Mik'ewa yayi da sauri ya duro daga bed din toilet ya nufa ya dauro alwala ya futo yana kallon agogo bango uku shaura na dare,
Jallabiya ce a jikinsa sai garan wando ya dauki wata rigar sanyi sa mai hula ya sanya kai a gogonsa ya d'aura ya dauki key ya futa da sauri.

Rbow suka ji ana kokarin tada mota hankali a tashe suka futo daga gurinsu, suna tambayar sa yace." Su koma kawai shima yanzu zai dawo jikinsu duk babu k'wari suka tsaya a gurin har sai da suka ga futar shi Daga gidan.

Kai tsaye......Asibitin Zana ya nufa zuciyarsa kwata-kwata babu dad'i abun yana mutukar bashi mamaki shi dai yasan babu wata Kalmar so da ya tab'a fadawa Mimi wacce har suke zargin sa da ya yaudara ta, maganar auran ta kuwa ya fada ne saboda son da take masa gami da  ganin yanda suka shak'u da Asma'u yana ganin ko ya aure su su biyu ba za a samu matsala ba, yanayin dabi'un Mimi da nutsuwar ta gami da kunyar ta suna bashi sha'awa amma zallah so gangariya babu Wanda yake wa sai Asma'u duk cikin 'yan matansa babu wacce ta samu wannan matsayin kamar ta hak'ika Asma tana da babban matsayi a zuciyarsa.

Da wannan tunane-tunanen ya Isa asubitin, Madi suka bude masa kofar ya shigo cikin sauri suka biyo motar da gudu  yana parking suka bude masa kofa suna yi masa barka da zuwa.
Amsa musu yayi babu yabo babu fallasa, ya wuce ciki.
Suka tsaya suna binshi da kallo tare da tunani wane dalili ne ya kawo shi asibitin ? Suna zargin yau ya zagayo su ne duba marasa lafiya da. da bada tallafi kamar yanda ya saba, murna suke sosai yau zasu cika aljihunansu.

Wayarsa ya futo da ita yana laluben numbar da ta kira shi da ita yanzu....






*10/November/2019*
[11/11, 9:19 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*


*Mallakar_BINTA UMAR*


*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.*


*48*


Ringing d'in wayar ne ya dawo dani cikin hankalina wayar na duba sai naga numbar sa, da kamar kar in dauka wata zuciyar tace"Dauki kiji me zai ce miki.
Jin alamun ta daga wayar ne yasa yace." Gani cikin hospital din ki futo kiyi min jagora har inda kuke."
Bai saurari Abunda zata ce ba ya kashe wayar sa.
Futowa nayi daga gurin da nake.
Har yanzu suna tsaye kan Umma sun yi mata rumfa Aminu sai fiffita yake mata.
Aunt Hauwa ta kalle ni tare da fadin"Da ina kika shiga tun d'azu. "
Cikin wayan cewa nace"Futsari naje nayi."
Raba ido nake yi a gurin ko Allah zai sanya I n hango shi
Da yanayin tafiyar shi na gane shi.
Shiru nayi har ya k'araso gurin.
Cike da mamaki suke kallonsa.
Ya mik'awa Aminu Hannu su gaisa.
Da kyar ya mik'a masa nasa hannun kamar yanda yayi masa jiya.
Umma ya kalla yace." Umma Ashe bayan tafiya ta jiki ya rike CE."
Umma ta gyara zamanta hade da gyara mayafin ta tace"Wallahi kuwa aman jini take sosai."
Gaban shi ya fadin jin abunda Umma tace, Yace." Bari in ga dector babu matsala insha Allahu komai zai zo da sauki."
Binsa mukayi da kallo har ya shige ciki abun mamaki babu Wanda ya hana shi shiga cikin ma'aikatan sai ma da d'a gyara masa hanyar wuce da suka yi.

  Kamar yanda dector ya yiwa Kawu Baya ni haka yayi Amjadu baya ni Wanda ya gamsar dashi kuma shima ya gane kan ciwon Mimi kamar yanda Asma'u take fada cewar ciwon sonsa ne yake damunta.

Yace." Doctor yanzu kun gama komai ko."? Gyada kai Dr yayi tare da fadin"Mun gama komai dasu domin har sunje sun karb'o magani a pharmacy kuma yanzu na sanya nurse ta bata maganin  babu matsala insha Allahu mutukar an bi doka."

     "Yanzu sauransu biyan kudi domin yanzu nake cewa Narse ta zo mik'a musu rasit." Yace." Kar ka damu insha Allah ka bani numbar accont din Ku na hospital din sai a turo maku hakkin Ku.

   Da sauri Dr ya dauki 'yar k'aramar ta karfa da biro ya rubuta masa hade da mik'a masa, ya San ba iya kacin kud'in su zai tura musu ba Dole sai yayi musu kari, tunda dama ya saba kawo musu ziyara a sibitin.

     Har ya mike zai futa sai kuma ya tsaya tare da fadin"Yanzu babu halin a ga yarinyar. " ? Dr ya mike da sauri yana fad'in"A'a Yallab'ai kai zaka iya shiga ka ganta."

    Tare suka shiga room d'in da Mimi take kwance bacci take sosai sai dai har yanzu nuffashin ta bai gama dawo wa normal ba. Dr ya futa hade da jawo masa kofar , ido ya tsura mata sosai yake kallonta mace har mace tana Neman ta jefa rayuwar ta a wahala.

    Domin shi a ganinshi wahala ce,kaso Wanda bai San kana yi ba, bai tab'a tunanin son da Mimi take masa ya kai haka a zuciyar ta, sai yaji zuciyar sa tana ce masa da ma wannan Soyayyar daga gurin Asma'u ka same ta daka ji dad'i. Amjad mutum ne mai mutukar son a dunga tattashin sa da rarrashin sa kulawa da soyayya, shiyasa yake addu'ar Allah ya bashi mace wacce take da wannan azanci domin matan ma suna suka tara.

     Yafi minti goma a tsaye a kanta yana kallonta, kokari yake yaji wani abu wanda ya shafi so ya darsu a zuciyarsa a game da ita, bai ji komai ba sai dai tausayin da taye mata da kuma kaunar da yake mata saboda sunan Maman shi, Wanda ba ita kadai yake wa wannan kulawar ba, mutukar A kace kina da suna Aisha to zaki samu kulawa sosai a gurin shi.

    A gogon dake daure a hannunsa ya kalla hud'u shaura na Asubah. Gyad'a kansa yayi ya bude kofar dakin a hankali ya futa, har yanzu suna zaune a inda suke sai dai sun matso cikin wata rumfar kwano dake gurin saboda sanyin asubah. Sosai suka bashi tausayi mussaman Asma'u da ya ganta tayi wujuga-wujuga da ita ga idanunta sun kode. daga nesa ya tsaya tare da fadin "Umma ni zan wuce Allah ya bata lafiya."

    Umma tace"Ameeen suma ameen mun Gode k'warai da kulawa." Kallona naga yayi a fakaice sai kuma ya kalli Aminu dake dauke dauken kai ya mik'a masa hannu domin suyi sallama.

    Da kyar Aminu ya bashi hannunsa, Amjadu ya wuce yana mamakin abunda Aminu yake yi sai kace jahili in banda dalili ya kai dalili Aminu ya Isa yaga inuwar shi ma ballanta ya hada hannu dashi, duk sanadin Asma'u ne.

    Sai da ya shiga motar sannan ya kira ta a waya, ina jin wayar na ringing naki dauka Munnu ta karba daga hannuna tana dubawa. Mik'a min tayi tare da fadin"Shine." Aunt Hauwa tace" Sai ki tashi kije mybe akwai abunda zai ce miki."

    Kallon da Umma tayi min ne yasa na mike da sauri na bi hanyar da naga ya bi.Na gane motar shi tunda duk inda suke basa b'uya bayan haka kuma gurin da haske.

   Kallonta yake yana daga cikin motar har ta k'araso. Ajiyar zuciya ya sauke babu wasa a tartare dashi ya bude motar tare da fadin"Shigo muyi magana dake ta fahimta."

    K'in shiga nayi na tsaya ina kallonshi. Shima ya kalle ni babu fara'a yace." Time d'in sallah ya kusa ki shigo muyi abunda zamuyi in tafi gida Ok."

    A hankali na shiga motar na zauna ina kauda fuskata. Ya kalle ni na minti uku, kana yace." Wannan kukan da kike yi Sam! Ba zai miki maganin komai ba sai dai ma ya kara sanya miki damuwa da ciwon kai, Yanzu shawara zamu yanke dake idan kin amince ni mai sauki ne."

     Kallonshi nayi ina d'an ya mutsa fuskata nace"Ina jinka." Shiru na minti biyu bai ce komai ba yana kallona, na dago kaina hade da watsa masa harara nace"Kace lokacin sallah ya kusa amma kuma ka sanya ni a gaba kana kallo kamar tv."

     Ajiyar zuciya ya sauke hade da lumshe idonsa, k'asa-k'asa naji yace." Asma'u Allah ne kadai yasan ita a dadin kaunar da nake miki a cikin wannan zuciyar tawa, tun da nake a rayuwata ban tab'a furta wa mace WANNAN Kalmar ba sai ke, duk da cewar nayi rayuwa da 'yan mata iri-iri masu kyau da kudi Asali nasaba da wayewa amma babu wacce ta samu wannan Kalmar sai ke."
Shiru nayi  sauraron shi. Ya cigaba da cewa "Ina da kudi sosai Wanda ban San iya a dadin su ba kuma kullum karuwa suke yi ina zakka da duk wani Abu da Allah yace kayi da dukiyar da ya baka amana, Abu guda ya rage min mata, kuma na samu insha Allah." Shuru Yayi na minti biyu ya cigaba da cewa "Mimi ta bani tausayi mutuka nasan illar so, tabbas tana so na, Wanda naji a zuciyata dama kece kike min irin son da take min da babu namijin da ya kaini dacewa a duniyar nan."
Kallonshi nayi jin abunda yake fada.

Dauke kaina nayi hade da d'an ya mutse fuskata nace"Me yasa ka yaudari Mimi kasan baka son ta."

Shiru yayi yana nazarin magana ta can naji yace." Da farko da wasa nake yi, amma daga baya na d'aura niyyar auranku tare domin in cuzguna miki dalilin yin haka kuwa shine Rashin mutumcin da kika je kikayi gurin pary Ku ya bani haushi shiyasa na yanke wannan shawarar."

    Murmushi nayi me ciwo nace"Idan domin ka bani haushi kace zaka auri Mimi a lokacin wallahi da baka wahalar da kanka,saboda kasan shi so sai ana kishin mutum ake yin sa, Mimi tana sonka tana kishin wani ya rab'e ka ciki kuwa har da ni, Mimi ita yafi da cewa ka aura bani ba."

      Fuskarsa ya Dan hade yana kallona tare da k'ankantar da idanunsa yace." Gashi ni kuma ba Mimi nake so ba ke nake so, sai dai idan kin yarda in hada ku, Ku biyu in aura amma duk abunda ya biyo baya kar kiyi kuka dani."

      Ba tare da tunanin komai ba nace"Ni dama akan wannan k'adami nake, Ya Aminu dole ya janye maganar auran Mimi idan yak'i janjewa nima nace bazan aure ka ba, sai dai duk mu hak'ura dama ni ban damu ba, itace abar damuwa."

     Gabanshi ya fad'i jin abunda take cewa, tana nufin idan Aminu bai janye maganar auran Mimi ba itama baza ta aure shi ba? Lallai a kwai badakala anan gaba, idan Aminu yak'i janje maganar shima ya kusa fadawa chakwakiya kenan, yanzu zai canza salo domin ya risinar da zuciyarta iya zaman shi da ita ya fahimci yarinya ce me mugun taurin kai da kafiya.Dole ya nema wa kansa mafuta domin bai San abunda zai je ya dawo ba nan gaba.
Shiru motar tayi bayan na gama magana ta. Yace." An sanya wata uku na auranmu ina ganin za'a kara sauko da lokacin k'asa saboda gudun wata masifar, ki San yanda zakiyi a gida ki ga Aminu ya janye kudirin sa daga kan Mimi ni kuma zan aure Ku ga ba d'aya."

   Motar nake kokarin bud'ewa ina fadin"Kai kake damun kanka da lallai sai ka aure ni, nifa idan Ka aure duk d'aya idan baka aure ni ba ma duk d'aya ne, mutukar ka aure Mimi da ka sanya ta fad'a komar ka shikkenan bukata ta tabiya domin likita yace zuciyarta daf take da ta buga."
Ina gama magana ta na bude motar hade da fucewa a fusace.!! Kallo ya bita dashi cike da mamakin gaud'ancin ta yarinya mai baud'andan ra'ayi shi a yanzu ma ya rasa in da ta dosa. Jikinsa babu kuzari yaja motar ya tafi zuciyarsa na masa wani irin ciwo idan ya tuno kalaman ta wai bata son sa, wannan kalma ta nayi masa mugun ciwo ya za'ayi ya auri macan da zata dinga gasa masa magana ko wace iri CE, da Alama Asma'u baza ta kula dashi. Mimi ita ke son sa sosai da sauran 'yan matansa tabbas a gurin su zai samu irin kulawar da yake buk'ata.

     Bayan munyi sallah gari yayi haske sai ga Babansu Munnu ya shigo a sibitin cikin motar sa, dama jiya gida ya koma saboda b'acin ran Aminu.
Da sauri muka mike ni da Munnu muka karasa gurin da yayi parking din ya futo muka gaishe shi hade da karb'ar kayan dake hannunshi, k'aton Fula's din tea ne sai wata Leda babba cike da bread da kayan shayi dangin su madara da Milo gaba yayi muka bishi a baya.

     Cikin mutum ci suka gaisa da Umma aunt Hauwa ta gaida shi Aminu baya nan domin ana idar da sallahr ya tafi gida, kai tsaye..... Ciki ya shiga gurin dector

     Ni da Munnu ne muka had'a wa kowa tae d'in shi ga manya manyan bread nan kowa ya dauki Wanda yake so, Ni kam tea din kawai nake kurb'a bakina babu dad'i fargabar rashin lafiyar Mimi da tunanin maganganun Amjadu na d'azu, nayi mamakin yanda yake k'aryar min da kai da sanyayyar murya yake fadin Yana sona, mutum me kudi kyau mukami izza da ginshera duk ya na dasu, amma d'azu duk ya aje su gefe, gaskiya na gazgata maganar shi, tab'e bakina nayi  kawai na cigaba da kurbar tae din amma lokaci zuwa lokaci  sai in ji gabana ya fad'i tsigar jikina ta mike idan na tuna shi.
K'arfe Takwas dai-dai wata nursa ta futo tace"An futa da Mara lafiyar yanzu zaku iya shiga Ku ganta duk da cewar ma yanzu za'a baku sallama." Da sauri muka mike dukaninmu muka fara turereniyar shiga duba Mimi.

    Tana zaune kan gado tayi wani firgai-firgai da ita fuskarta ta kode ta kara wani ufan haske Mimi da ma ba jikin arziki ba tayi wata irin rama lokaci guda. Umma na ganin ta sai hawayen ta ya dawo ta zauna kusa da ita hade da iri hannunta tana fadin"Mimi ke ce kika dawo haka lokaci guda." Ganin Umma na zubar da hawaye Mimi ma ta fashe da kuka kamar zararriya ta hau dukan k'irjinta tana fadin"Umma k'irjina ciwo da nauyi na rasa wace irin masifa ce wannan? Umma na rasa me yake damuna gwara in mutu in hutaa!!!!! Aunt Hauwa ta buga mata tsawa Cikin jin haushin ta tace"Don Allah ki daina wannan kukan da kike yi kiyi tawakkali mana ita rayuwar ai duk hakuri ake yi, kina kuka kina bugun k'irji dole hankali Umma ya tashi, ko me kike ji a zuciyar ki sai ki dinga fadin "Innalillahi Allah zai miki magani."

     Leb'anta na rawa tace"Aunt Hauwa baza ki gane ba ne, bana fata Allah ya dora wa wani masoyina abunda nake ji a zuciya ta, gwara in mutu da wannan rayuwar."

Hankalina ya kai k'oluluwar tashi jin abunda Mimi take fad'a  ban tsaya naji Abunda Ummansu Munnu take cewa ba na futa daga d'akin. ba tare da sun ganni ba.

    Diri-diri nake harabar a sibitin kamar wata sabuwar mahaukaciya nayi waje da sauri na, bakin titi na tsya na tari a dai-dai ta sahu, na fad'a mishi idan zai kaini. Har kofar gidan Kawu Yunusa ya aje ni, nace"Bari in shiga ciki in karb'o maka kudinka." Kallo kawai d'an a dai-dai ta ya bita dashi.

     Ina shiga soron gidan naci karo da Musa zai futa yaci kwalliya cikin shaddar sa, gaishe shi nayi ya amsa yana was he min baki, tare da fadin "Husna kece a gidan nan da Safiya." ? Nace"E h Musa ga mai s dai-dai ta can bashi kudinsa don Allah."  Da sauri ya futa ni kuma na shige gidan.


     Muka gaisa da Baba Mariya a muntunce sai tsokana ta take da amarya amarya ni dai nayi mata shiru, tace"Na ganki duk a furgice ." nace"Kawu yanan ko."? D'aga kanta tayi tare da fadin yana sama tare da d'aya Kawun naki Idiris nasan maganar auran ki suke yi." Mik'ewa nayi ina fadin"Yawwa dama gurinsu Nazo."
Babu yabo babu fallasa nayi sallama dakin Kawun namu Wanda ya zame mana waliyi, daga ciki naji muryar shi yana fad'in "Shigo ko waye." Na shiga cikin mamaki suka Bini da kallo shi da Kawu Idiris na zauna muna gaisawa . Kawu Idiris yace." Daga ina kike da sassafe nan." ? Nace"Daga asibiti. " Kawu Yunusa yace."Waye babu lafiya."? Kuka na fashe musu dashi nace"Mimi ce ."  Kawu Idiris yace."Mai ya same ta kiyi shiru kiyi mana bayani yanda zamu gamsu."


    Cikin kuka nace"Aman jini take sosai da kyar likitoci suka shawo kan Matsalar kuma sun ce lallai a bata abunda take so idan ba haka ba zuciyar ta zata buga da ko wane lokaci."

    Kawu Yunusa yace." To mu wannan ai bs hurumin mu bane zaki zo ki tayar mana da hankali da sanyi safiyar nan." Kawu Yunusa yace." Nima abunda na gani kenan kije ki Sanar da kanin mahaifin ta shine magana."

    Kallonsu nake cike da mamaki dama halinsu ne rashin zumunci da rashin taimako Sam 'yan uwan Babanmu basu da kara basu da kawaici kowa kansa ya sani da iyalinsa, mun sha wahala sosai bayan mutuwar mahaifinmu shiyasa nake jinjinawa aunt Hauwa ta ko wane fanni domin ta taka muhimmiyar rawa a gare mu, kafin Umma ta tsaya da k'afafunta.

     Nace." Kawu Wallahi nayi rantsuwa da Allah mutukar baku sanya Ya Aminu ya janye maganar auransa da Mimi ba to nima dole Ku warware nawa Ku mai da wa da Amjadu kudinsa, na aure da kuka karb'a, Mimi ba son Aminu Amjadu take so saboda haka yace. Zai auremu ni da ita Ya Aminu dole ya hak'ura tunda shi namiji ne idan yak'i hak'ura kuma to nima bazan aure shi ba."



    Jikinsu ne yayi sanyi jin abunda yarinyar take cewa, Suna murna arziki ya shigo musu gida ai ba za su Bari wannan dama ta kubce musu ba shiyasa suka yi ruwa suka yi tsaki kan al'amari idan banda rashin hankalin Asmau da kanta ta zo nema wa kanta kishiya. Babu ruwan su su dai burinsu suga tabbatuwar auran ta da Amjadu ko banza zai kira su Waliyyanta Kuma zai dunga tunawa dasu, duk abunda zai biyo baya babu ruwan su."


     Kawu Yunusa yace." Wannan ce matsalar taki."? Gyada kaina nayi ina share hawaye na, Yace." Kar ki damu zan samu Aminu in rarrashi shi tunda kinji kin gani shikkenan Allah ya sanya alkairi." Ameen nace na mike hade da yi musu sallama.


      Tana futa suka cigaba da maganar cike da mamaki sukan ba damuwar su bace hakan burinsu tabbatuwar auran kawai.

    Ko da na koma asubitin tashin hankali na tarar domin  Ya Aminu ya dawo ya tadda Surutun da Mimi take yi tamkar me motsuwar kwakwalwa take sambatu tare da fad'in sunan Amjadu , fad'uwa yayi a gurin hankalinsa a tashe, yana dafe k'irjinsa haki! Yake sosai, likitoci suka shigo dakin suka dinga fada sosai suka yi kora waje, nan suka dauki Aminu da bai San a wace duniyar yake ba, cikin tashin hankali suka yi wani daki dashi ganin yanda yake jawo numfahi da kyar oxygen suka sanya masa.

     Mimi jikin ya kara rike wa likitan ta kamar ya mammari su Umma haka yake ji ya dinga fada sosai da sosai itama Oxygen din aka sanya mata Dr din yana addu'ar Allah yasa kar jinin ya dawo mutukar jinin ya dawo da zubah to babu shakka  sakamakon su ya nuna masa cewar zuciyarta zata iya daina aiki.









*11/November/2019*
[11/12, 11:13 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*



*Mallakar_BINTA UMAR*



*LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA*


*49*


Hankalin Umma ya kai k'oluluwar tashi inda ta dinga wata irin zufa!! Gabanta yana wata irin fad'uwa su biyu kawai iyayen su suka Haifa ita da k'anwar ta, Aisha maihaifyar Mimi kenan tabbas idan ta rasa Mimi bata da wani Abu da ya dangaci k'anwar ta, Mimi take kallo a matsayin Aisha k'anwar ta, Aminu danta ne dole zata iya sarrafa shi ya hak'ura da Mimi a bata zabin ranta, ko da kuwa Shi Aminu zai rasa tasa rayuwar wannan hukuncin ta yanke, ba tare da bata lokaci ba ta sanya aunt Hauwa ta kira mata Kawu a waya yace gasu nan zuwa asibitin.

    Sunzo sun tadda badakalar da take faruwa Umma tace Ita ta Riga ta gama yanke hukunci Aminu ya janye auran sa a kan Mimi dole a aura mata Wanda take so.

   Kawu Yunusa yace." Muma maganar da take tafe damu kenan domin Asma'u taje har gida ta Sanar mana saboda haka tunda taga zata iya shikkenan dama kuma shi yaron Neman auran mutum biyu yazo ita da Mimi saboda haka kan Aminu baza mu bari a rusa wannan auran ba domin mu abun alfarin mu ne, hada jini da Amjadu saboda haka zamu tattashi Aminu."

Wannan shawarar ita ce matsaya Babansu Munnu na tsaye bai ce komai ba sai da suka gama magana yace."Idan babu damuwa Aminu yazo ga Munnubiya na bashi sai a d'aura auran rana daya.

    Kawu Idiris yace." Mungode da wannan karamci zamu jira ya dawo hayyacinsa muji ta bakinsa.

   4:35 Aminu ya farka masha Allah nuffashin sa ya dawo dai-dai budar bakinsa "Ina Mimi take kar kice min ta mutu Innalillahi wa'ina ilahi raji'un."
Ya fada yana yunk'urin tashi zaune

    Dr Yayi saurin mai dashi ya kwantar yana rarrashin sa fafur Aminu yak'i zama dole sai an kaishi gurin Mimi, Dr da kansa ya Dora shi keke saboda jikinsa babu k'wari kai tsaye dakin da Mimi take ya nufa da shi.

    Mimi na kwance sambal hancin ta sakale da oxygen idanunta a rufe Aminu ya tsura mata ido zuciyarsa nayi masa zafi wai yanzu shi Mimi take gudu tafi son bare dashi, hak'ika Allah ya jarrabe shi da kaunar ta tun tana 'yar jaririyar ta, Ashe zan Ga wannan ranar ta bakin ciki, wasu zafafan hawaye ya share cikin zuciyar sa yace ."Ya zama Dole in hak'ura dake Mimi domin ko ns aure ki zuciyar ki na can gurin wani bazan samu kulawar da nake so ba."

Wasa-wasa har k'arfe goma na dare Mimi bata farfado ba, likita ya duba ta sosai ya tabbatar tana Raye kawai tayi dogon suma ne, nan ya rarrashin Aminu da ya tada hankalinsa a kan hakan.

   Da kyar Aminu ya futo daga d'akin sai yaji duk ya samu sauki ma domin halin da yaga Mimi a ciki ya tsora tashi babu shakka zai iya SADAUKAR da soyayyarsa a kanta domin ta rayu. Wannan shine sahihin so.da wannan tunanin ya futo.

   Ya Tarar da tashin hankali a waje Inda Umma ta kasa nutsuwa ta tare wata narse tana share hawaye tana rokonta wai ta fada mata idan Mimi ta mutu shikkenan sai su hak'ura saboda d'azu da Dr ya futo Lokacin su Kawu Yunusa nan yake tambayar sa,lafiyar Aminu yace masa ya dawo dai-dai Ita Mimin ce bata dawo normal ba shine hankalin ta ya tashi .

   Aminu yazo ya rike ta zuciyarsa nayi masa rad'ad'i da zugi ga wani irin jiri yana d'ibar muryarsa a shake yace." Kiyi hakuri Mimi lafiyar lau bata mutu ba, yanzu daga gurin ta nake." Umma ta rike hannunsa tana kallonsa cike da tausayi ta bude baki zata yi magana ya katse ta ta hanyar fadin "Umma na hak'ura da Mimi idan shine samun kwanciyar hankalinta na hak'ura ta auri Wanda take so. Umma ta rungume shi tana share hawayen ta tace." Aminu Allah yayi maka albarka Ubangiji Allah ya zab'a maka mafi alkairi a rayuwar ka, nagode da wannan karmanci da kayi min yarona ka fidda ni daga zargin mutane."

   Rungume ta yayi tare da tausar zuciyar ta, Ni da aunt Hauwa muka kama ta muka zaunar da ita jikinta sai bari yake. A hankali Ya Aminu yace." Ni zan je gida in kwanta in huta jiri nake ji." Aunt Hauwa tace." Idan kana ganin babu matsala shikkenan. " gyada kansa yayi kawai ya bar gurin yanda yake tafiya zaka San ba shi da cikkakiyar Lafiya.

   Tun lokacin da Ya Aminu ya fad'i cewar ya janye maganar auran sa da Mimi naji wani irin sanyi a zuciyata tayi wasai duk wani bacin rai da fargabar da nake ciki naji babu shi. Umma ma na lura ta sauya ta saki jikinta

   Munanan zaune har sha biyu babu Wanda yake kokarin kwanciya ko gyangyadi muna sauraren futaw Dr wata narse ce ta futo daga d'akin da Mimi take Fuskata babu yabo babu fallasa tace." Wacece "Asma'u a cikin Ku."? Da sauri nace" Nice." Tace." Kizo maralafiyar nan da kuka kawo na Neman ki. Hamdala Umma tayi tare da fadin"Ta farfado kenan." ? Narse tace "Eh kusan awa biyu da farfadowar ta shine Yanzu tace." Wai a kira mata Asma'u." Umma tace." Maza jeki kiji kome ye ko kara kwantar mata da hankali." Da sauri na bi bayan nurse din.

    Mimi na zaune ta jingina da jikin gado kanta a kasa tana wasa da hannunta kamar wata sokuwa ko kuma sabon shigar hauka duk ta sauya, cike da tausayin ta na zauna kusa da ita tare da fadin"Mimi gani menene."?
D'ago kanta tayi hawaye na bin kuncin ta, ta rike hannunwa tamau!! Bakinta na rawa tace." Habbity ya zanyi da rayuwa ta ne."!!!!? Ba kasaifai take kira na da wannan sunan ba, sai muna cikin damuwa da ni da ita.

    Hannunta na rike sosai nace." Mimi ba dai *Amjadu* ba."? Shiru tayi min hawaye na zuba a idonta. Murmushi nayi me ciwo nace." Kamar kin aure shi kin gama an gama komai manya ma sun shiga maganar Ya Aminu kuma ya janye maganar auran ki, Yace ki auri Wanda kike so." Na k'arashe maganar fuskata dauke da murmushi na karfin hali.

   Hannuna dake damk'e da nata ta matsaye sosai tana gyda kanta,bata CE min komai ba, minti biyu tsakani nace." Kuma d'azu  yazo duba ki lokacin kina bacci ya dad'e ma tare da dr duk wasu hidima shine yayi, nima na amunce ya aure mu tare ki kwantar da hankalin ki."

    Cikin nauyin baki tace"Nagode Habibty 'yar uwata ta kaina hak'ika kin cika 'yar halak Nagode Asma'u na rasa wata irin zuciya ce dani narasa wace iri ce ni, ki yafe min zuciya ta tafi karfina bazan iya sarrafa ta ba."

   Murmushi nayi hade da rike hannunta nace "Ba laifin ki bane Mimi sharrin so ne kawai kowa ma haka tana iya faruwa dashi, kuma kinsan kowa da irin zuciyarsa wani yana da dauriya wani kuma bashi da ita, hakanan wani yana iya sarrafa zuciyar sa, wani kuma zuciyarsa tafi k'arfi sa, kamar ke kenan, hummm!! Yanzu dai magana ta wuce insha Allahu baki da miji sai Amjadu zakiyi rayuwa inuwa guda dashi."


   Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tare da sakin wani irin murmushi Wanda dashi gwara kuka tace." Asma'u na Dade da sanin cewar  *Jad* baya sona nice nake haukana a kanshi, ke yake so inda ke kuma baya gaban ki!! Ki bani shawarar Ya za'ayi na jawo hankalin sa kaina. "

   Murmushi nayi ina mamakin Mimi da so ya rufewa ido ashe har suna ta sanya masa wai *Jad* humm!! Sunan kuwa yayi min dad'i. Domin in kara kwantar mata da hankali nace" Mimi ke kike abunki kar ki damu ni nasan da an d'aura aure zai so ki kamar ya mutu zai so ki fiye da yanda Ya Aminu yake son ki, Mimi kina da kyau kina da kira mai d'aukar hankali  gaki fara alkyabar mata, babu namjin da zai kauda kansa daga kanki ki kwantar da hankalin ke dai."

    Murmushi tayi hade da sunkuyar da kanta har yanzu hannuna guda na rike da nata.nace "Kinga wayar ki ma a hannuna Bari in kira miki shi Ku gaisa ko."?

Bata ce min komai ba, na fara kiran numbar shi, bugu daya ya dauka muryar shi da alamun bacci yace."
*HUSNAH."!* Sai da naji wani irin yarrrr! A jikina jin yanda ya ambaci sunana da ba kowa ne yake kira na dashi ba,  ga muryar tayi low sosai kamar me mura. Ajiyar zuciya na sauke babu yabo babu fallasa nace"Ga Mimi za kuyi magana. "

   Shiru naji yayi nace ."Hello." Gyaran muryar shi na ji yace." Owk bata wayar." Mimi na mik'awa wayar da murmushi a fuskata, hannunta na rawa ta karb'i wayar tayi sallama da dusashashiyar muryar ta.

      Ina jinsa yana amsa mata a sake, yace." Ya jikin naki Momyna."? Tace." Jiki da sauki." Yace." Alhmdullahi ki kwantar da hankalin ki kinji ko duk abunda kike tunanin bazai yi wu ba to zai yi yuwu da izinin Allah idan Allah ya kaddara ke din matata ce Sai ki ga munyi aure, ki daina tashin hankalin ki, Tare da yardar 'yar Uwar ki ni na amunce zan aure Ku a tare ina fatan alkairi a kan haka, daga k'arshe nake ce wa dake ki godewa 'yar Uwar ki, domin tabbas ta sadaukar da nata farin cikin a kanki da samun fi gaban ki hade da lafiyar ki. Momyna hak'ika kin sa'ar 'yar uwa me kyawun zuciya."
Ya karasa maganar tasa cikin nutsuwa.

    Ba Mimi ba ni kaina kalaman sa sun yi min dadi kuma naji dadin yabon da yayi min abunda bai tab'a faruwa ba ni dashi, bai tab'a fad'ar alkairina ba sai yau.

    Murmushi naga tana yi kunne na kasa sosai ko zan ji abunda yake fada mata Wanda yake sata sakin wannan kayataccan murmushi, babu abunda nake ji daga b'angaran sa saboda ya k'ara yin kasa da muryar sa sosai, ita kanta Mimi sai ta kasa kunne sosai sannan zata ji abunda yake fad'a.


     Ji nayi zuciyata nayi min wani irin zafi nayi saurin kauda kaina  tare da ambatar innalillahi cikin zuciyata domin ji nayi take wani kunci ya ziyarce ta, zuciyar tawa sai take raya min kamar da akwai wani munafurci a ciki don me yasa zai dinga magana a waya kamar munafuki wannan bayi bane ni a ganina. Maganar da Mimi tayi ce ta dawo dani hayyacina , wayar take mik'o min tare da fadin"Yace." A baki wayar ku yi sallama."

    D'aga murya nayi domin yaji nace"Mimi kashe wayar nan don Allah bacci nake ji, tunda dai kun gaisa dashi shikkenan dama haka nake so in sanya zuciyar ki farin ciki, kashe wayar mu kwanta Wallahi nayi bala'in gajiya."

     Ga mamaki na sai naga Mimi ta kashe wayar kamar yanda na umarce ta ta aje wayar gefan kamar ba ita ta saki fuska sosai tana yi min hira. Mamakin ta kawai nake, nace ta kashe waya ta kashe babu kara bare tayi min magiya kan in karb'i wayar kamar yanda ya bukata, lokotan baya idan taga ina mishi wulakanci haushi take ji amma banda yanzu. Kwanciya nayi gefan ta ina lumshe idona sama-sama naji muryar narse na shigo tana tashina, na bude idona Wanda suke cike da bacci ina kokarin mik'ewa zaune.

   Mimi tace" Ki k'yaleta mu kwana tare domin ko a gidama a tare muke kwana." Nurse ta futa bata kara magana, sama-sama muke yin hira da Mimi bacci yaci karfina ban San sanda ya kwashe ni ba.

     Shida shaura na Safiya na tashi lokacin har masu bada magani sun shigo dakin sun bawa Mimi wacce take zaune dungurgur taki yin bacci saboda tsabar farin ciki, mik'ewa nayi ina hamma idona cike da bacci nace." Mimi shine baki tashe ni ba ko? Kinga na rasa sallah asubah."

    Murmushi tayi tare da fadin "Asma'u naga a gajiye kike gashi kince bacci kike ji shiyasa na kyaleki kiyi hakuri." K'wafa nayi kawai na sauka daga gado toilet din dake cikin dakin na shiga.


     K'arfe takwas dai-dai likita ya shigo ya gama  aune-aunen sa kan Mimi kuma yaji dad'i da ya duba yaga yanda ta kwantar da hankalin ta, nan ya rubuta sallama hade da kara tausar Mimi sosai kan ta kiyaye ta daina saka damuwa a ranta. Nima kuma yace." Mu dinga sanya ido ankata sosai muna guje b'acin ranta.


    9:00 am mun futo daga asibiti da bamu shigo da kaya komai ba amma zamu futa dasu niki-niki a hannu muna futa harabar asibitin wata shirgegiyar motar *Siyana* mai dauke da tambarin *A&A mai nasara*  sabuwa dal! Ta shigo gurin, Dravar shi ne ya futo da sauri muka hada ido dashi. Saurin kauda kaina nayi daga kansa

    Ya k'araso gurimu hade da zubewa gaban Umma yana gaishe ta ta amsa a sake, Ummansu Munnu ma ta amsa ita da aunty Hauwa, sai ya mike hankalinsa na kaina yace." Ranki ya Dade oga ne yace in zo in kaiku gida."

    Cikin zuciyata nace shi kuma ko wa ya fada masa anyi sallama oho! Shiru nayi masa, aunt hauwa naji tana fadin"Aikuwa mungode dama yanzu muke tunanin a dai-dai ta nawa zamuyi damu da kayan mu." Na muka nufi motar kowa na fadin albarka cin bakinsa.



     Duk yawan mu damu da kayanmu motar sai da ta dauke mu, hat guri Yayi saura doh-doh yaja motar muka tafi gida, Mimi ta sake sosai ina jinsu suna hira da Munnu ban tanka musu ba.


    Goma shaura muka Isa gida Har ya danyi kura saboda rashin mutane a gidan kwana biyu kawai, ni da Aunt Hauwa muka fara aiki Ummi da Mimi kuwa na rumfa daga inda muke muna jin yanda Umma take rarrashin Mimi da kalamai Masu dad'i da kwantar da hankali.



******

Yau Kwana ki biyar kenan da bud'e sabon company me zaman kansa a jahar kano company *A&A mainasara* ya amsa sunansa  sosai ya samu daukaka domin an fara gudanar da harkoki yanda ya kamata kullum a cike yake da baki daga garuruwa daban-daban sun shigo d'aukar kaya.
Hakanan Sauran company sa na waje suma komai ya kammala harkoki ake sosai da sosai Allah ya shiga al'amarin.

Sanye yake da wani yadi mai masifaffan kyau da tsada ni kam sai ince ma a jikinsa na tab'a ganinsa milk coulor ne mai sharashara anyi masa dinki boda yayi amfani da singlet black kana ganin shatin ta, bai sanya hula ba taje lafiyayyar sumar sa yayi wace take bakkirin sai shek'i take, ya gyara sajan sa kamar ko da yaushe ya feshe jikinsa da turaran shi na ko da yaushe,  takalmi mai gidan ya tsa ya sanya a fararen k'afafun shi, blck ne sunyi masa kyau ba kad'an ba, hannunsa daure da agogon shi, na zallar fata fad'ar kudin shi ma b'ata wa ne, komai na Amjadu colour ne domin bai fiye amfani da Abu gama gari ba.

   A nutse ya futo hannunshi rike da wayoyin shi, kana kallonsa zaka fuskanci akwai damuwa a tattare dashi Dan dai jarumin namiji ne me b'oye damuwar sa. Harabar gidan ya futa, Doh-doh da Rambow suna tsaye kamar dogarai suna ganinshi ya futo Rambo ya nufi inda yake shi kuma doh-doh ya fara kokarin futo da mota.

    Wayoyinsa ya karb'a yana yi masa barka fa futowa a dakile ya amsa masa ya wuce shi kuma ya bi bayan sa, motar ya bude masa ya shiga ya zauna shi kuma ya zaga ya gurin zaman shi, motar ta futa daga gidan.

   Sai da sukayi nisa sosai Doh-doh yace." Oga ina muka nufa."? Zaman shi ya gyara tare da Dan ya mutse fuskarsa yace." Muje gidan granny ko." Doh-doh yace." Angama sir."

      Wayarsa guda ya karb'a gurin Rambo ya fara laluben numbar jiya yaji mugun haushi abunda tayi masa ta sanya Mimi ta kashe masa wayar wato bata buk'atar tayi magana dashi abunda yarinyar take ya soma b'ata masa rai, Sam bai saba ganin wannan shariyar ba a gurin 'yan matan da suke son shi, amma yana ganin dole zai rage zak'ewa a kanta ko zata gane muhumamcin sa.


    Cikin ikon Allah da ya kira wayar itace ta dauka muryarsa shi a cunkushe ya amsa mata sallama minti biyu tsakani yace." Kina jina ko."?
"Umm." Abunda tace kenan. Yace." Munyi waya da dector d'azu an baku sallama shine na turo Doh-doh ya dauke ku a mota babu wata matsala ko."?
"Ummm."! Nace.  Haushin yanda take masa yaji Umm da Umm sai kace wata kurma, k'aramin tsaki yaja yace." Yanzu zanje in dauko granny zata zo ta duba Momyna."
Sama-sama nace"Sai tazo." Kafin na an kara ya kashe wayar a fusace.! Tab'e bakina nayi nace "Kai ka sani kuma.

     Umma na fad'awa zuwan kakar shi ta tashi ya fara shiri aunt Hauwa na shirin tafiya gida Umma ta hana ta wai ta tsaya su tab'i bak'uwa sosai a ka gyara gidan duk a ka kauda kayayyakin sana'ar Umma dasu ke rumfar tamu kamar su kalazinr galan din mai robibin magi da su d'aurikan busassan kayan miya rumfar tayi tas da ita Umma ta shimfid'a tabarma ta zauna jiran zuwan su.

Wani irin kamshi ne ya bugi hancin mu kafin muji muryar dattijiwar matar cike da nutsuwa da kamala tayi sallama.
Umma ta amsa mata tare da fadin"Sannu da zuwa maraba lale shigo ciki Hajiya."

Granny ta shiga ta zauna kan tabarma fuskarta cike da farin ciki da annushuwa, suka gaisa da Umma cikin mutumci, aunt Hauwa ta gaishe ta hade da dauko mata Lemo mai sanyi hade da ruwan roba Wanda aka siyo mata shi mussaman, Granny ta bude ruwan tasha tayi hamdala, sannan ta kalli Umma cikin barkwanci tace. " Nazo duba kishiyoyina ne, kafin a Kai min su mu fafata da juna."

    Dariya Umma tayi tace." Aikuwa dai, dole suyi miki ladabi domin shi kanshi uban gayyar da bazar ki yake taka rawa ba a raba hanta da jini kuma da tsohuwar Zuma ake magani."

   Dariya Granny ta sanya tace." Ai ya juya min baya kwana biyu baya ta tawa kullum bashi da zance sai na kishiyoyina kin ga kuwa dole inyi kishinsu." Umma tace"In ya gama d'akinsa ai dolen sa ya dawo gurin ki." Dariya suka yi a tare aunt Hauwa ta mike tare da fadin "Bari a kira miki su Ku gaisa wai kunyar ki suke ji."

   Granny tace." Wane irin kunya? Suna jin dai tsoron su hada ido dani tun kafin su shiga humm zasu aure min miji ai dole su b'oye je ki kira wo mun su." Aunt Hauwa ta futa tana Dariya tare da mamakin halin grnay kamar sun saba mata Mai fuska da fara'a gaskiya tana da kirki.

    Tun lokacin da naji sallamar matar gabana yake fad'uwa har yanzu narasa ko ta menene aunt ta shigo tare da fadin "Sai kuzo Ku gaisa da ita ko." Mimi tayi s'aurin mikewa tana gyara hijab dinta ko jira na bata yi ba tabi bayan aunt Hauwa cike da mamaki nake bin ta da kallo ina mugun mamakin azarb'ab'inta da rashin kawaici lallai Allah mai mutane sai ga mutum yana Abu shi a ganinsa ba komai bane.

     Muryar Umma naji tana k'wala min kira na amsa da sauri na dauki zurmemam hijabi na sanya na futa da sauri Mimi na zaune kusa da ita sai faman sunkuyar da kanta take tana murmushi nayi sallama granny ta daga kanta tana kallon Asma'u fuskar ka a sake tace" Zo nan kema ki zauna mu fahimci juna daku domin bana don Ku kwace min mijina."

    Babu yabo babu fallasa naje na zauna kusa Da ita kaina a kasa na gaishe ta, ta shafa kaina tana fadin"Sannu Asma'u d'iyar arziki Allah yayi muku albarka gaba ki d'ayan Ku, Allah ya baku hakuri. Zama da juna kuyi ta hakuri da Mijinku domin wani irin mutum ne shi muskili kuyi hakuri da dabiun shi, gaku 'yan gida daya nasan baza a samu wata Matsalar ba ta fannin kishi tunda 'yan uwan junane Ku, Ku rike junanku da amana kunji ko Allah yayi muku albarka."







*12/November/2019*
[11/13, 7:59 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*50*

Umma tace." Ameen suma ameen Hajiya ki kwantar da hankalin ki insha Allahu babu wata b'araka da taza faru a tsakaninsu zasu zauna lafiya tunda Allah yasa sun hada miji gasu kuma 'yan juna, komai zai zo da sauki. "

   Granny tace." Masha Allahu to Allah ya tabbatar mana da alkairinsa, hira tsakanin Umma da granny ta mik'a sosai ba tare da sun gane ba, ni bar dakin cike da kunya, Sai ga Mimi ta biyo bayana kwanciya tayi kusa dani hade da lumshe idonta, murmushi nayi ina kallonta cikin tsokana nace." Mimi amaryar Amjadu Alherin Allah."

  Bude idonta tayi tana kallonta fuskarta dauke da murmushi nace." Ko ba haka bane."? Girgiza kanta tayi tare da fadin." Ni amarya ke kuma Uwar gida ko."? Nace." A ina na zama Uwar gida ke amarya kuma ke Uwar gida. " mik'ewa zaune tayi ta rike hannuna tare da fadin "Yanzu kakarshi take fada cewar k'arfe biyar zai dawo ya dauke ta, wane irin Abu zamu tanadar masa."?

   Nace." Mimi duk abunda kikayi NIYYA ki bashi domin ki faranta masa kuma kinyi dabara hakan zai k'ara jawo hankalinsa gare ki."  Tace." Me zan bashi yanzu."? Dariya na sanya hade da fad'in "Idan baki da abunda zaki bashi in yazo to ki bashi labari mai dad'i da wannan sanyayyar muryar taki." Dariya tayi hade da bani hannu muka tafa, haka dai na dinga biye wa Mimi da duk abunda zata ce min akan Amjadu kuma bana bata shawarar banza.

   K'arfe shida shaura kira ya shigo wayar tata lokacin tana band'aki tana wanka, Kin dauka nayi don na duba naga shine, motsin ta naji bakin rijiya nace"Mimi yi sauri kizo ana kiran waya. " aikuwa sai gata ta shigo da sauri hannunta na digar ruwa ta karb'i wayar daga hannuna. Kallo na bita dashi. Wata irin murya da ban Santa da ita ba naji tace." Hello." Daga bashi bangaran naji muryar shi sama-sama yace."Momyna kuna ina ina ta kiran waya kusan sau biyar babu wacce ta dauka a cikin Ku." Muryar ta a sanyaye tace." Ni ina wanka ne."
"Asma'u fah."! Yafad'a babu sauki a muryar shi,kallonta tayi sai kuma naji tace." Gatanan. "   yace." Ok kina nufin kice min tana ganin kirana taki d'aukar wayar."? Mimi shiru tayi taki bashi amsa. Shurun da Mimi tayi shi ya tabbatar masa da abunda yake zargi. Tsaki! Yaja yace." Ok ki fad'awa granny gani Nazo ta futo mu tafi OK." Kafin Mimi tace Wani Abu ya kashe wayarsa. Jikinta a sanyaye take kallona nima ita nake kallo nace"Dole ki koyi hakuri fa, kuma kiyi hakuri da halin shi tunda aure zakuyi ." zama tayi kusa dani tare da fadin"Wai sai ki dinga cewa aure zamuyi eh aure zamuyi har dake a ciki ai,ko" mik'ewa nayi ina dariya nace." Har dani mana, ni ai farin cikin ki ne nawa kar ki damu dani." Futa nayi daga dakin ba tare da na saurari abunda zata ce ba."
Cikin sauri Mimi ta shirya ta futo tana ta zabga kamshi ina zaune kofar kicin ina gyara kayan miya na bita da kallo sakin fuskata nayi tare da fadin "Kinyi kyau sosai Mimi." Mirmushi tayi ta shiga Rumfar inda naji grnnay tana sallama da Umma, suka futo a tare Umma sai godiya take mata, sun kuyar da kaina nayi kasa na cigaba da aikina har tazo kusa dani ta tsaya da sakskkiyar fuska tace." To ke zan tafi naga sai wani b'uya kike yi ko tsorona kike ji tun kafin ki shigo kinga 'yar Uwar ki ta saki jikinta mun saba da ita."

Murmushi nayi nace." Ki gaida gida mun gode." 'Yar dariya tayi tare da fad'in"Na ga alama gudun angon naki kike yi 'yar uwarki tafi ki sonshi." Ni dai ban ce komai ba har suka fuce ita da Mimi da aunty Hauwa har soro Umma ta raka ta sannan ta dawo cikin gidan.

Yana zaune cikin mota ya hango zuwan su, Mimi yake kallo tun daga nesa taci Uwar kwalliya abun ya bashi mamaki sosai, yarinyar Da jiya I Yanzu take kwance magashiyan rai a hannun Allah, amma dubi kamar ba ita ba, abunda bai sani ba shine tunda Mimi taji labarin auransu zai yi wu dashi da ita ta watsake tamkar bata tab'a cuta ba, har suka k'araso gurinsa yana mamakin wannan abu .

Murmushi mai k'ayatar wa take sakar masa, Wanda Sam hankalinsa baya kanta yana can gurin Granny wacce take kokarin shiga mota sai mita take masa, yace." Idan zaman gidan ne bai ishe ki ba sai ki koma ai ban ce miki dole ba." Tana daga cikin motar take fadin"Wallahi karshen zamana a wancan gidan yazo domin baza ka aje ni ba sai kace mayya ni daya gida kullum kana gidin matan ka, nima gidan naka Zan dawo ." dariya yasa yana kokarin futowa daga motar yace." Sa ido ne zai kawo ki gidana bana Neman ki." Bude motar yayi ya futa yana jinta tana surutai ya shareta

Fuskarshi  dauke da murmushi yake kallon Mimi yace." Momyna jiki yayi kyau gashi har anyi min kwalliya mai kyau da burgewa." Mimi ta rufe fuskarta cike da kunya, yace." Kinyi kyau sosai zan so in ta kallon fuskar ki, sai dai Dole zan bar gurin nan saboda idon Jama'a ina fata babu wata matsala ko."? Cike da shauki Mimi tace." Babu wata matsala dama ji nayi zuciyata baza ta iya nutsuwa ba dole sai ta ganka." Murmushi yayi hade da Sosa kansa yace." Momyna kenan nagode sosai da wannan kaunar ina alfahari dake."

Mimi ta dinga jin dad'i a zuciyarta yau gata ga masoyinta Amjadu Sam bata so yayi mata sallama ba, taso suyi ta tsayuwa a gurin tana kallon kyakyawar fuskar shi.

Sai dai motar tayi nisa  har ta daina ganinta sannan ta bar gurin cike da nishadi.

*****

Labarin auran *Amjadu Young millionaire* ya baza garin kano da ka bude redio zan can kenan Young millionaire zai yi aure a Sati biyu masu zuwa inda zai auri 'yan gida daya ya da k'anwa jama'ar gari na mamakin wannan Abu, masu bin kwakwkwafi kuwa sai da suka bunkito ko su waye 'yan matan da zai aura hade da bunkice 'yayan wane mai kud'in ne ko kuma mai mulki a jahar kano da sauran garuruwa.
Abun mamaki surutun jama'ar gari sai ya karu wannan gayawa wannan 'yan matan da *Amjadu Young millionaire* yake nema da aure 'yayan talakawa ne tilis d'aya ubanta ma ba'asan inda yake ba tun tana jaririya ya gudu ya barta ana zargin ma 'yar shege ce bayan yayi cikin ta ya gudu daga gari, ita kuma d'ayan ubanta ma'aikacin company ne na madara dake Sharada ya mutu bashi da ko kwabo bashi da famsho balle garatuti ya mutu bashi da gidan kansa,sai a company da yayi wa aiki ne suka bar mishi gidan da suka bashi a ro saboda iyalinsa, Duk ana zargin'yan matan da zai aura 'yayan mace ne." Duk cikin jarida ta gaskiya dokin k'arfe Amjadu ya karanta wannan labarin. Zufa ce kawai take keto masa ko ta Ina, wani irin kira ya kwalawa Rambo sai gashi ya shigo farlor da sauri. Jaridar ya mik'a masa muryar shi a sama yace."Kuna ina haka ta faru. "!! ? Rambo ya karb'i Jaridar yana dubawa hannunshi sai rawa yake yi, shima abunda ya gani ya tsorata shi, yasan makiyan sa ne suka shirya wannan Abu domin su tozarta shi, Yace." Sir ka kwantar da hankslinka wannan duk sharrin jama'a ne kar ka manta kana tare da mahassada ko su zasu aikata maka wannan Abu."

Mik'ewa yayi yana kai wa da kawo wa a farlor yace." Kaje ka tsaurara bunkice ka gano gaskiyar abun shin abunda na karanta jikin jaridar nan hakane Mimi Bata da uba shegiya ce kamar yanda suka fad'a shin hakane wannan gida dasu ke ciki na company ne kaje ka tsaurara bunkice ka gano wane company mahaifin Asma'u yayi a aiki a sharada."
Rambo yace." Insha Allahu Sir ka kwantar da hankalinka duk sharrine domin da d'aga maka hankali kuma a tozarta ka a don duniya. " Wayar shi tayi kara Rambo ya mik'o masa da sauri, kunnenshi ya kara wayar a dake yace." Salamu alaikum. " Kawu Yunsu Ya amsa cike da tashin hankali yace." Yaro mai halin manya na bugo ne in kwantar maka da hankali kan abunda jama'ar gari da kafafan yad'a labarai suke shela a kai, ina so in tabbatar maka da cewar mu 'yar mu Asma'u tsarkakkiya ce da Ubanta kuma muna da nasaba me kyau duk fadin koki da cikarta babu Wanda bai san mahaifinmu  Malam Sulaiman mai ishiriniya ba, idan kana so kattabar da haka ka sanya ayi maka bunkice."" Muryar shi a sama yace." Babu bunkice da zan sanya ayi min akan Asma'u na yadda da ita Dari bisa Dari, kokwantona yanzu akan Mimi yake shin da gaske ne mahaifin ta ya gudu ya barta ko kuwa."?

Kawu Yunusa yace." Hakane tun bayan haihuwar ta ya gud .....  Katse shi kafin ya karasa yace." Tabbata kenan abunda nake zargi." Kawu Yunusa har yayi niyyar cewa gaskiya ne sai kuma ya fasa tunowa da yayi da maganar Asma'u inda take fadin bata har indai Mimi bata aure shi ba itama baza ta aure shi ba, yayi saurin cewa." Yarinyar 'yar sunna ce sai dai ubanta ya hofintar da ita ne shine mahaifiyar Asma'u ta dauke ta ta raine ta.

Amjadu ya sauke ajiyar zuciya tare da fadin"Yau saura kwana nawa d'aurin aure."? Kawu yace." Kwana shida ne." Shiru na minti biyu sannan yace." Yau muna laraba ko."? Kawu yace.'k'warai kuwa" Yace. "Idan Allah ya kaimu jibi d'aurin aure insha Allahu Ku zauna cikin shiri daga yanzu a fara shiri duk wani Abu da ake bukata kayi min magana kar ka samu damuwa.
Kawu yaji wani irin sanyin dad'i ya shiga ransa yace."Insha Allahu komai za a yi kamar yanda kake so Allah ya kara arziki da wadata." Amjad yace." Ameen suma Ameen ina so in zauna da Waliyin ita Mimi domin akwai wasu muhiman tambayoyi da zanyi mishi." Kawu yace." Ai babu damuwa yana aiki ne a babbar makarantar ta PCE nan kofar famfo." Gyada kansa yayi yace." Insha Allah zan same shi a ofis din." Nan suka yi sallama da juna.

Wanka ya shiga a gurguje ya kimtsa jikinsa ya futo sai zabga kamshi yake kamar ko da yaushe , fuskar sa a daure ya futa, abun mamaki da daure kai can ya hango 'yan jarida suna rigima da masu gadi gurin wai lallai sai sun shigo Estate din."

Mota ya nufa zuciyarsa nayi masa suya wato yanzu za a sanya shi a bakin duniya kenan Saboda ana zargin zai auri Shegiya mata uba, shi yarinyar da suke maganar ta ba su San ba sonta yake ba, kaddara ce kawai auran su, da ita zasu sashi a duniya duk Wanda yayi masa tunon asiri nan bai kyauta masa ba.

Ganin shi ya futo yasa suka dinga kokawar shiga cike da b'acin rai yace." Doh doh kayi kamar zaka bi takan 'yan iska da mota." Aikuwa Doh_ doh ya fafuri motar da guda! Lokaci guda suka watse amma duk da haka wasu daga cikinsu sai da suka dinga d'aukar motar tashi hoto masu vedio ma nayi kamar bala'i suka bi motar da gudu suna fadin"Yallab'ai me zaka ce a game da jita-jitar da jama'ar gari suke a kanka wai zaka auri shegiya Mara Uba shin hakane ko karya ne, Yallab'ai muna so mu ji ta bakin ka."

Ko kallonsu bai yi ballanta su saka ran zai amsa musu motar ta b'acewa ganinsu. Sai da sukayi nisa sosai sannan yace." Doh ka kaini makarantar  FCE Yanzu." Doh yace." OK Sir.  motar na shiga makarantar samari da 'yan mata suka yi mata Caa! Da ido kasamcewar duk inda motar shi take an Santa saboda tambarin da yake bayanta. Doh.. Yayi parking inda aka tana da kana ya futo da sauri ya bude masa kofar motar.

A hankali yace." Ka shiga ciki makarantar ka bunkita min ofis din Muktar Inuwa Gyaranya." Shine ai nihin sunan Kawun Mimi wato Baban su Munnu kenan. Nan da nan doh-doh ya tafi cika umarnin da aka bashi

*****

Muna cikin tsananin tashin hankali da rud'u tun lokacin da Umma taji labarin abunda jama'ar gari suke fada a kan Mimi take kuka ta tana fadin"Yarinyar sinna ake shigantawa ni Mariya Innalillahi kuka take sosai tun muna daurewa har muma muka fara taya ta, Ya Aminu ya shigo gidan shima ranshi a bace domin yaga sai Wani irin kallo jama'ar gari suke masa sai kace Wanda yayi sata ko maita Mimi ya kalle ranshi a mutukar bace yace." Kukan karya kike yi Mimi, ko kin dauka auran Wanda ya shahara a duniya wasa ne? Kin dauka in kin auri Young millionaire zaki samu irin kwanciyar hankalin da kike so, to bari kiji auran irin su Sai kayi ta fuskantar kalubale kinga ishara yanzu da Uwar ki da ubanki jama'ar gari suna kiran ki da shegiya, tom me zakice game da wannan zargin da suke miki, ku sani ga 'yan jarida can a waje suna kokarin shigowa cikin gidan nan nine na hana su na rufe kofar gidan da sakata. "

Mimi kukan ta ya tsananta ta inda ta fara karkarwa tari ya sark'e ta har tana kokarin kifawa k'irjinta ta rike tam da hannu biyu sai tari take ga hawaye na zuba daga idonta. Hankali a tashe nayi kanta ina kuka wurjajan ina ji kamar in tashi in gaggaura Aminu mari, murya ta a sama nace." Ya Aminu ka k'yaleta mana baka ga tari ya sark'e ta ba."!!!! Ko kallona baiyi ba ya futa daga rumfar a fusace,!! Ni da Umma muka rike ta sosai muna dukan bayan ta duk mun gigice.!

Wata irin zufa ce take keto wa Baban su Munnu bayan ya gama sauran maganar da Amjadu yaje masa da ita, to son ya San meye dalilin da yasa Uban Mimi ya gudu ya barta ko zancan da jama'ar gari suke yi gaskiya ne.". Hankali a tashe Baban su Munnu ya fara magana kamar haka.
"Hak'ika Aishatu yar halak ce mahaifin ta Dan uwana ne cikin mu daya, mu 'yan kano ne gaba da baya yan Asalin unguwar Gyaranya dake k'aramar hukumar Dala, tun bayan rasuwar Matar shi wato Aisha mahaifiyar Mimi kenan ya ji zaman garin ya ishe shi bayan sadakar ar'abain ya tafi Neman kudi a cewar sa, yau shekara goma sha shida kenan, ban sanya shi a idona ba sai dai labarin sa yana zuwar mana sa'i da lokaci kuma kullum yar shi tana ranshi yana yi mata ake akai akai, Mariya yar mahaifiyar ta Itace ta dauke ta shayar da ita nonota lokacin tana goyon 'yar ta Asma'u sai ta had'a ta shayar dasu tare babu abunda zamu ce da Mariya domin ta cika jajurtacciyar macace. Wannan shine ainihin abunda yake faruwa." Kawu ya k'arashe maganar sa yana goge zufa.!!

Shima Nashi b'angaran wani irin faragaba da fad'uwar gaba ne ya riske shi lokacin da ya gama jin abunda Babansu munnu yake fada, hannunshi na rawa ya Ciro hankici daga aljuhunsa ya fara tsane gumin dake saman goshinsa, minti goma babu Wanda yayi magana a cikinsu, da kyar ya bude baki yace." Kana so ka fada mun cewar *Asma'u da Mimi* sun sha nono d'aya kenan."? Kawun su Munnu ya gyada kansa tare da fadin"k'warai kuwa."
Amjad ya sauke gwaron numffashi  yace." Aurena da Mimi ya haramta idan Asma'u zan aura idan kuma Mimi zan aura aurena da Asma'u ya haramta.!!!!!!!  Babansu Munnu ya tsinci kansa da shiga rud'u da fargaba Sam!! Ya manta da wannan k'aulin *Innalillahi wa innailahi raji'un*


*K'ak'a k'ara k'ak'a tsara*





*13/November/2019*
[11/14, 7:52 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*51*

Cikin yanayin damuwa Babansu Munnu yace." Wannan abu akwai rikita-rikita a cikinsa akwai daure kai, tunda ake wannan sabgar ban tab'a tunanin wannan alak'ar ba, Babbar magana ce wannan, tsarin na addini islama babu aure a tsakanin mutum biyu sai dai ka dauki daya ka bar d'aya, sun Riga sun tsotsi nono d'aya mutukar ba d'aya ce ta mutu a cikinsu ba, to baka da damar auran 'yar uwarta har abada, amma kasan ko wane ijma'in malamai da nasu k'aulin, Allah ne dai masani."
Babansu Munnu ya kare maganar sa cike da tararrabi yanzu idan Amjadu ya zab'i Asma'u ya bar Mimi wand irin hali zata shiga? Watak'ila ma karshen rayuwar ta yazo."

Amjadu jikinsa yayi wani irin sanyi tunda yake bai tab'a shiga rud'u da fargaba ba irin na yau, ko mutuwar iyayen sa bai shiga wannan halin ba duk da cewar mutuwar ta girgiza shi sosai wannan yasan dole ce ko wa sai ya d'and'ane ta.

Kusan mintuna goma babu Wanda yayi magana a tsakaninsu dukaninsu suna tunanin ya za'ayi su warware Matsalar, Mik'ewa yayi hade da mik'awa Baban su Munnu hannu sukayi sallama,  ba tare da yace masa komai ba ya futa daga ofis din.

    Yana shiga mota ya fara kiran wayar Kawu Yunusa buga daya ya dauka hade da yin sallama kamar zai masa sujjada, saboda kwantar da murya. Yace."Aure tsakanina da Mimi ya haramta saboda sun sha nono d'aya da Asma'u tun farko Asma'u ce zab'i na saboda haka na janye Neman auran Mimi ina rokon Allah ya fe min kuskurana, ita kuma Allah ya bata miji nagari."

    Kawu Yunusa ya share gumin fuskarsa shima sai yanzu ya tuna da wannan alak'ar mamaki yake sosai me ya hana su tuno da haka sai da magana tayi nisa, idan hakane Ashe Aminu duk abunda yake akan yarinyr babu aure a tsakanin su."
"Kawu Yunusa yayi gyaran murya  tare da fad'in "Idan ban da ka tsaurara bunkice a kan al'amarin da sai dai muyi ta tafiya a haka domun idanun mu sun rufe akan al'amarin ta inda muka mance da wannan alak'ar saboda haka yanzu zab'i na gare ka, Kaine zaka zab'awa kan ka matar aure cikin su biyun."

   Ranshi babu dad'i yace." Matar aure tuntuni na zab'e ta Kawu Asma'u ita na zab'a Insha Allahu ina fatan ta zama Uwar 'yayana." Kamar yanda Kawu yayi tsammanin haka daga gareshi hakane ya tabbata hamdala yayi a fili yace." Insha Allahu baza kayi nadamar auran d'iyar mu ba Allah ya sanya alkairi.." Ameen suma ameen Yanzu dole kaje ka Sanar da Umma halin da ake ciki na janye auran Mimi tunda bai hallasta ba." Kawu yace." Yanzu kuwa zan bar kasuwa inje in Sanar da ita, kuma maganar d'aurin aure tanan jibi insha Allahu." Sallama suka yi da juna, Amjad ya kashe wayar zuciyar sa na sak'a masa abubuwa da dama jikinshi na bashi kamar akwai wani Gagarimin al'amari da zai faru nan gaba.

   Kai tsaye gidan Granny ya wuce domin ko ya koma gida yanzu yasan mutane baza su bar shi ya huta ba, to zancan kenan itama Granny fad'a tayi ta yi tana fadin dama Ashe basu da Asali yaran haka kawai zai jawo wa kansa zuvewar mutum ci to itama ba ta yadda da wannan auran ba, yana kwance cikin kujera yana jinta bai ce mata komai ba, duk abun duniya ya dame shi, daga zarar ya tuni Asma'u sai yaji faduwar gaba, abunda bai ta faruwa dashi ba.

******
*Innalilhi wa inna ilahi raji'un* shine abunda Umma take nanatawa lokacin da ta gama sauraron maganar da Kawu Yunusa yake tafe da ita, tashin hankalin ta sai ya ninka na da tana fargar bar Mimi taji wannan mummunan labari tsakanin ta da Amjadu babu aure tunda dai ya zab'i Asma'u a cikin su, ga jikinta ya rikice tun d'azu take kuka an kasa shawo kanta. Cikin yanayin damuwa da tashin hankali Tace." Kawu wannan k'addara Allah ya ije mana ita naso yaron nan ya zab'i Mimi domin ceto ranta, rai shine abun dubawa Mimi marainiya ce kuma tana dauke da ciwo mai mutukar hadari kuma kaga ta dalilin sa ta Sam......... Bata k'arasa ba Kawu Yunusa yayo kanta da bala'i yace." Baki Isa ba Mariya wallahi tallahi baki Isa ba!!! Arziki yana neman mu kina korarsa awwo!! Bakin ciki kike mana? Ko kuma bakin halin ki zaki nuna mana wanda kika saba, 'yarinya dai 'yarmu ce muna da ikon mu aura mata duk Wanda muke so ke!! Baki Isa ki hana mu ba 'yar bakin ciki kawai." Tsakanin Kawu da Umma dama ba a shiri tun Asali, basa jituwa a cewar sa itace take zuga Babanmu lokacin in ya dauki albashi baya taimaka wa mahaifiyar su lokacin tana Raye.Umma ta fusata! Ranta ya b'aci sosai wato har Yunusa yana da bakin magana akan 'yayan ta, mutanan da suka wofin tar da ita bayan mutuwar mijinta suka watsar da zuri'ar shi, wahalar duniya babu wacce bata sha ba, akan 'yayan ta, sai yanzu da suka ga sun zama mutane shine zasu yi wata magana har da gadara cewar 'yayan su saboda kwadayin abun duniya to har indai itace ta haifi Asma'u zata nuna masa iko a kanta. Ranta a mutukar bace tace." Yunusa ni kake d'agawa murya har kana kokarin kai min duka akan 'yaya na, Yanzu kai kana da bakin magana akan Asma'u wacce baka San cin ta ba baka San shan ta ba, sutturarta karatun ta duk baka San wannan ba, sai yanzu daka ga ta zama mutum sannan zaka yi wata magana akanta."? Ta k'arashe maganar cike da mamaki, Kawu Yunusa ya mike tsaye a fusace! Yana a matsayin wan mijinta take kiran sunan sa kai tsaye, ransa ya b'aci sosai yace." An fad'a miki nace na fad'a miki magana Mariya kiyi abunda zakiyi dama ai baki da kunya nasan halin ki d'an uwana yayi hakuri zama dake, kina maganar suttura da sauran su, ki fad'i kud'in wahalar da kikayi sai a biya ki, wacce bata gaji arziki ba, mu bama haihuwar 'yayan banza d'an uwana ya iya haihuwa koma komai abunki sai anyi wannan auran."!!!

   Umma ta fashe da kuka Wanda yasa na futo wuf!! Daga cikin dakinmu Allah yasa na samu Mimi tayi bacci duk irin tujarar da Kawu yake wa Umma a kunne na kuma duk naji zancen da suke yi, rai na a b'ace na futo INA kallon Kawu dake tsaye kan Umma yana ta surfa mata masifa! "Ita yarinyar da kike so ya aura yace. Ba yaso saboda rashin galihu ya fi son 'yar Asali me cikkakiyar nasaba, bayan wannan kuma sun sha nono d'aya babu yadda za'ayi ya aure su duk su biyun, in banda kidahumanci irin naki Mariya 'yar ki zata auri mai kudi Wanda duniya ta San dashi ke kanki kin bar kangin talauci ki nuna ba kya so Allah yayi wadaran ki Mariya."! Ya k'arashe maganar sa a harzuke.

   Kuka na fashe dashi jin irin cin mutumcin da Kawu yake wa Umma tana kuka ko tausayin ta baya ji, idanuna sun rufe ta inda nake  ganin girman shi ya zube a gurina, tunda nasan da me yake wannan tashin hankali, duk dan kudi da soye-soyen rayuwa yau da talaka ne Amjad Kawu bazai tako cikin gidan mun ba  ko dan kar ace yayi kayan daki, amma yanzu dubi yadda yake tada hak'arkari da jijiyar wuya.

   Ina kuka nace." Kawu wannan ba dai-dai bane kar ka manta da cewar har gidan ka naje munyi magana dakai cewar mutukar Amjadu bai auri Mimi ba nima bazan aure shi, to yanzu duk naji abunda kuke magana akai ni da Mimi mun sha nono d'aya, Amjadu ya zab'e ni a matsayin matar auran sa ya bar Mimi, Kawu kayi hakuri da hukuncin da na yankewa rayuwa ta, idan shine ya aiko ka ka koma ka fada masa cewa ni Asma'u d'iyar Sulaimanu mai madara, bazan aure shi ba, idan son gaskiya yake min ya karb'i Mimi 'yar uwata a matsayin matarsa ta sinna domin mu ceto rayuwar ta, daga halaka."
[11/14, 6:35 PM] .: Cikin tashin hankali da damuwa Kawu yake kallon Asma'u, yace." Asma'u kina da hankali kuwa kike fad'ar wannan maganar cewar ke baza ki aure shi ba kin barwa wata."! Gyada kaina nayi  rai na a dagule nace"K'warai kuwa Kawu na rantse bazan aure shi ba, sai da ya hak'ura tunda babu halin ya hada mu mu biyu idan kuma da gaske kaunata yake tsakani da Allah to sai yazo yayi abunda nace." Kawu yace." Baki Isa ba wato Bakin Ku d'aya da Uwar ki ko."? Da sauri! Nace"Ko daya Kawu wannan ra'ayi na ne, kuma don Allah ina Neman alfarmar ka daina zagin Umma haka, kayi hakuri kar kace nayi maka rashin kunya, a matsayin ka na babba bai dace ba da abunda ka keyi ka daina don Allah."

Kawu yayi mamakin abunda yarinyar tace wato suna so suyi musu bakin ciki suga samu suga rashi,babun bad'ulahu kenan abunda bazai yiwu ba wallahi ko gawar Asma'u ce sai an kaita Gidan Amjadu sai dai idan shine yace ya fasa auran.

A fusace !   Yace." Duk wani iya shege da zakuyi ke da uwarki a tafin hannuna kuke, kuma ku rubuta Ku aje, jibi I war haka kin zama matar Amjadu kin zama Mallakin sa, in dai nine wakilin ki." Ya futa a fusace. !!

  Umma naje na rungume da kyau! Ina kuka ina share mata hawaye nace"Umma ki kwantar da hankalin ki duk yanda kike so haka za'ayi ki zab'a min miji Wanda kike so Amjadu na bar wa Mimi ."

   Umma tace." Asma'u kina jin abunda Kawun Ku yake fada ko akan ki kina jin irin cin mutumcin da yake min ko.? Nace" Umma duk naji kiyi hakuri ki kyalesu dama ba yau suka saba miki cin mutum ci. Ni nasan yanda zanyi insha Allahu Mimi bata da miji sai Amjadu ki kwantar da hankalin ki."

Hannun d'iyar tata ta rike tare da fad'in"Ubangiji Allah yayi miki albarka Asma'u Yanda kike min biyyaya Allah ya baki 'yaya masu biyayya kema, yanda kike ceci rai ubangiji Allah yasa Annabi ya cece ki kema." Wasu zafafan hawaye na hau sharewa lokaci guda tausayin kaina ya kama ni,  wani irin hali na shiga a lokacin ta inda naji gwara min mutuwa da rayuwa Allah-Allah nake naga Mimi a gidan Amjadu ko ma samu hankalin mu ya kwanta, Alluma ajirin fi musibati wa aklifni kairan minha itace addu'ar Dana ke ta maimatawa a zuciyata tare da Innalillahi wa inna ilahi raji'un, lokaci guda naji zuciyata tayi sanyi na kalli Umma tare da fadin"Don Allah Umma kar a kara tayar da maganar nan domin I Dan Mimi taji to wani tashin hankalin ne, Umma kija kunnen Ya Aminu a kan hakan." Umma tace"Nima abun ya soma damuna Asma'u Insha Allah zan ja kunnen sa, ke dai Allah yayi miki albarka insha Allahu yanda kika sanya ni farin ciki kema 'yayan ki zasu sanya ki."


     Bacci ne ya soma fizgar sa kad'an-kad'an yaji ringing din wayar sa, cikin kunnen sa, dalili airpic din dake manne a kunnen sa, a hankali ya dauki wayar dake saman k'irjinsa yana dubawa. Mik'ewa yayi da sauri ganin numbar da ta kirashi.

   Ba tare da ya cire airpix din ba ya latsa wayar tare da fadin"Salamu alaikum." Murya Asma'u yaji sama-sama ta amsa da wa'alaikasalm. " gabansa ya fad'i sosai lumshe idonsa yayi hade da cije leb'anshi fargabar abunda zaiji daga bakin ta yake."

   Kai tsaye yaji tace"Barka da yamma." A hankali yace." Barka ya kike Husnah."!!
"Lafiya.'! Tafad'a babu wani sassauci ta cigaba da cewa " Yanzu Kawu Yunusa ya bar gidanmu bayan ya Sanar damu sak'on ka."

"Owk" shine abunda Yace yaja bakinsa yayi shiru yana sauraran ta. Ta cigaba da cewa" Allah ya kadddara ni ba matar ka bace, ina yi maka fatan alkairi idan son da kake min na gaskiya ne, to a madadina da aka zab'a akan Mimi ni na hak'ura ka mai da maganar auranmu kan 'yar Uwata domin ceto rayuwar ta.".

   Wani irin gumi ne yake tsayaya daga jikinsa bakinsa yayi wani irin daci ya soma Jin zazzab'i na shigar shi, jin abunda take cewa, amma da yake NAMIJIN duniya ne, muryarsa a tsaye yace." Meye hujjar ki ta fad'ar haka, shin nine bakya so ko kuma akwai wata manufa taki."? Cike da dakiyar zuciya tace." Eh duk biyun ne bawai bana sonka ba ne, Mimi tafi ni sonka bayan haka kuma kayi mata alk'awarin aure ka yaudare ta da kalaman ka hade da zakin bakin ka, kayi kwance kwance ka lasa mata Zuma a baki daga baya kuma kace ka fasa auran ta, shin baka tunanin halin da zata shifa ko kuma kana so mu rasa ta, son da Mimi take maka zai iya kashe ta."! 

  Wani irin yammm!! Yake ji a jikinsa tsigar jikinsa tana Mik'ewa jin abunda yarinyar take fada, a kausashe yace." Shine Hujjar ki."! ?
"Eh shine Hujja ta." Ta fada babu wasa a cikin maganar ta."

Ajiyar zuciya ya sauke minti uku tsakani yace."Shikkenan tunda haka kika Zab'a mana ni dake muyi rayuwa na karb'i Mimi a matsayin mata kamar yanda kika bukata, Allah ya sa haka shi yafi alkairi.".
Da sauri nace"Ameen auran Mimi alkairi ne a gare ka insha Allahu." Kashe wayarsa yayi ba tare da yace min komai ba.

Lokacin naji damuwar da ke cikin raina ta ragu burina kawai inga Mimi gidan Amjadu mu huta da wannan masifar, duk abunda ya faru tsakanina dashi na Sanar da Umma ita ma taji dadin yanda ya amunce lokaci guda.


Hannusa ya sanya ya dafe kansa dashi lokaci guda kansa ya shiga Sara masa wani irin bakin ciki da damuwa sun taro sun tsaya masa a mak'ogwaro da kyar yake had'iyar yau!! Sosai yake jin bakin ciki da takaicin zafafen maganganun da yarinyar ta watsa masa lallai inda ranka kasha kallo wai shine yau 'ya mace take furta cewa bata son sa baki da baki  yarinyar ma k'arama irin Asma'u.





*14/November/2019*
[11/15, 10:20 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*52*


Yana zaune a gurin hannunsa saman goshin sa granny da Iyami me aikinta suka shigo parlor Iyami ta nufi daining tana gyara gurin, ita kuma Granny ta k'araso kusa dashi da sauri ganin yanda yake cije bakinsa yasa ta dafa kafadar sa, tare da fadin"Kar ka sake ka sanya damuwa cikin zuciyar ka har ta haifar maka da wani ciwon ni dai a ra'ayi na nafi so ka auri 'yar bak'ar yarinyar a cikin su biyun naga kamar tana da kunya da hankali." Ta k'arashe maganar ta a tausashe.

   Da kyar ya iya bude bakinsa yace." Tace bata sona Granny. " Zama tayi kusa dashi cike da mamaki tace" Amma Wannan anyi 'yar banza ta samu namiji me zafi da kwarjini kamar tace bata so, in banda ma Matsalar ka nasan ko mata dozin aka aje maka zaka iya dasu, amma wannan yarinyar ta bani haushi wallahi. "  Kwanciya  ya gyara hade da lumshe idonsa shi kadai yasan abunda yake damun zuciyar sa. Granny kuwa mita take tayi tace"Tun farko sai da nace maka kaje ka nemi auran Hafsatu ka kiji kaga ni ai abunda nake guje maka."

A hankali yace." Granny magana ta wuce a halin yanzu insha Allah jibi za'a d'aura min aure da Ma ko wacece na yadda haka Allah ya shirya min." Tace"Tunda dai kayi niyyar auran mata biyu mai zai hana ka hada da Hafsatu nasan in kayi magana baza su ki ba."

Jajayen idonsa ya bude ya sauke su a kanta, fuskar shi a murtuke yace." Ki k'yaleni da wani zance Inji da guda d'ayan ma ni da ba cikkakiyar Lafiya ba."

Hararasa tayi tace"Au! Ashe munafurci ne yasa kace zaka hada mata biyu hummm! Kai dai ka sani ma  kanka."

Shiru yayi cikin zuciyar sa Yace ." Granny in batayi wasa ba zai sauke fushinsa akan ta yanzu juya mata baya yayi ta gaji da mitar ta tashi daga gurin.
Wayoyinsa duk kashe su Yayi domin baya bukatar damu a halin da yake ciki ji yake zuciyarsa tana iya bugawa ta tarwatse.

Sai daf da magari ba ya tashi daga kwanciyar da Yayi kai tsaye masjid ya nufa yayi sallolinshi tare da addu'ar Neman zabin Allah ya futo daga massalaci Jama'a na ta mik'o masa gaisuwa Amjadu bashi da wulakanci sosai ya tsaya ya gaisa da mutane, cikin ikon Allah yana shiga gidan yaji zuciyar sa tayi masa sanyi, sakamakon karatun alk'uranin dake tashi a parlor Granny ta kamo tashar Saudiya tv Jama'a na ta kewaye dakin Allah *(Ka'aba)* zama yayi kusa da ita da carbi a hannunta sai da ta kammala  tukkuna ta kalleshi cike da kulawa tace." Iyami ta girki dafaduka shinkafa da daddawa nasan kana son shi, tayi amfani da bussasan kifi yayi dad'i sosai. " Murmushi yayi yace."naji dad'i kuwa domin rabo na da cin abunci me nauyi har na manta. Granny ta mike hade da aje carbin NATA a kan kujera tace." Naga alama kazo kaci ka koshi naga alamun yunwa a tare da kai."
Mik'ewa yayi yabi bayan ta, yana 'yar Dariya domin ya kwantar mata da hankali shi kam a irin halin da yake ciki yanzu kome za'a bashi bazai faran ta masa ba Idan ba Asma'u aka bashi ba."

*****
Shirye shiryen aure ya kammala duk wani Abu da ake bukata akwai shi a aje idan da kud'in ka ka wuce Matsalar komai, Tun safe su Kawu Yunusa suka yo gayya 'yaya da jikoki suka zo suka kare mana zagi ni da Umma munji bakin ciki da ciwo Abunda suka zo suka yi mana a unguwa amma daga k'arshe muka hak'ura muka cigaba da sabgar mu. Duk Abunda. Amarya take yi nida aunt Hauwa mun sanya Mimi tayi domin me lallai har gida tazo tayi mata ja da baki, aunt ce ta sanya mata man shamfo a kanta, ta had'a kayan gyaran jiki na sanya Mimi a gaba na dinga mulka mata a jiki ina gogewa yinin ranar abunda muka yini kenan, lokaci guda Mimi tayi Wani uban kyau jikinta sai shek'i yake,murmushi kawai take yi ga lallan ta ya futo radau abunka da farar fata.

Bayan mun idar da sallahr La'asar ne, muka tafi can yakasai gurin dinki kayamu kala uku duk iri daya dinki iri daya komai iri daya muka karbo a dai-dai muka shiga muka dawo gida sai murna nake Mimi ta saki ranta, Muna Isa gida muka tadda Munnu tazo dakinmu muka shige muka cigaba da tsara yadda zamu gudanar da walima domin lokaci yazo a kurace gobe daurin aure jibi kuma walima kuma a ranar za'a kai Mimi.

*****

K'arfe biyar da kwata na ranar alahamis yana zaune a harabar gidan shi jikinsa sanye da kayan motsa jiki Rambo ya shigo cikin gida a mota ya gyara parking ya futo hannunsa rike da ledoji manya manya masu dauke da tambari na sunan company nin sa, karasowa yayi kusa da shi tare da fadin"Sir barka da yamma." Dago kanshi yayi yana kallonsa kana ya amsa, Rambo yace." Komai ya kammala kamar yanda ka Umarta naje har gidansu na kai kayan. " Fuskarsa babu wasa yace." Alhmdullahi ina bunkice da na sanya kayi min." Rbow yace." Mahaifin yarinyar dai kamar yanda aka fad'a talaka ne sosai Dan duk 'yan uwansa sun fi shi rufin asiri yana aikine karkashin company madara ta cowbell bayan rasuwar sa, haka naji daga bakin abokan sana'ar shi ya rasu sanadiyar hatsari a titin sharada mota ta take shi."

A hankali yace." Wane company yake wa aiki a lokacin."? Rambo yace." Cowbell ne Sir. Kuma na samu labarin durkushewar company shekaru biyu da suka wuce."

Gyada kansa yayi shi bai taba jin sunan company madara wani cowbell ba Niko nace dama yaushe zaka ji tunda k'aramin company k'ananun madara yake kawowa irin ta Leda ta yaku bayi irin 'yar Hamsin a shirin da biyar.

Yace." Rambo kasa yara su gyara Wannan gidan nawa na Badawa nasan dai yayi kura sosai a wanke ko ina a tsaftace ka duna kaga inda akwai abunda aje bukata a ciki kayi magana sai a sanya musu, bayan d'aurin aure sai ka kai musu key din gidan."

Rambo yace." Insha Allahu za'ayi yanda kace Yallab'ai yanzu za'a sanya yara su fara aiki." Girgiza kansa yayi hade daga masa hannu Rambo ya nufi mota da sauri, shiko Doh! Na bayan shi a tsaye sai zare ido yake.

Rambo na kokarin futa da mota ne sai ga motar Hibbah tana kokarin shigowa ciki, Amjad na gane ta ya mike da sauri ya shige cikin gidan domin yana gudun tayi masa shirme gaban ya ransa.

Hibbah bata cikin nutsuwar ta tun lokacin da ta samu labarin auran sa take kuka kamar ranta zai futa ta kira wayarsa yafi curin masaki yak'i dauka wani lokacin ma sai taji wayar a kashe, kuka sosai ta sanyawa mahaifin ta, dole ta sanya babu shiri Mai citta ya dinga kiran Amjadu din a waya bai same shi ba, lallaba ta yayi yace." Tayi hakuri insha Allah bata da miji sai Amjad tunda tana sonsa. Gani tayi baza ta iya hak'ura ba ya sanya ta biyo shi har gida.

Yana kokarin shiga bedroom d'insa ta fad'o parlor da gudun tsiya taje ta rungume bayansa tana wani irin kuka me shiga zuciya, tace." My Apple Yanzu aure zaka yi ka barni auran ma ka rasa wadda zaka aura sai Mara tushe da Asali wacce ake zargin shegiya ce." Tana kuka take maganar.

Fuskar shi a daure ya sanya hannunshi ya jawo ta gaban shi ido ya tsira mata tare da fadin"Waye yace miki matar da zan aura Shegiya CE." Hibbah na kuka tace"A gurin jama'ar gari da gidanan redio."
Kara hade fuskar sa yayi yace." Kar in kara jin Kim fad'i haka matar da zan aura tana da asali duk sharrin jama'ar gari ne., cikin kuka Hibbah tace." Nasan duk irin Asalin ta da nasabar ta na fita, ni ya kamata k aura ko don son da nake maka."

Zama yayi da ita cikin kujera  muryar shi a cunkushe yace."Hibbah bana son wata damuwa a halin da nake ciki, ina me tabbatar miki da cewar duk son da kike min tafi ki nima zan aure tane domin sadaukar wa."

Tana kuka tace." Don Allah ka auremu tare, nayi maka alk'awarin zan jiyar dakai dad'i zan kula da kai kamar kwai zan tarairaye ka fiye da tsammani ka, ka taimaka ka aurmu tare."
Kallonta yake da rinannun idanunsa yace."Kije ki tambayi Asma'u idan ta amunce shikkenan ko bayan d'aurin auramu da Mimi ne sai mu shirya aure dake." D'ago kanta tayi dake kafadarsa ta rike hannunsa tana murzawa tare da fadin wacece Asma'u." Idanunsa ya lumshe a hankali yac" Tsohuwar budurwa ta CE." Hibbah taji gabanta ya buga daram!!!! Yana nufin tsohuwar budurwar sa zata  roka ta sanya shi ya aure ta, lallai da sake shi ko wane irin so yake mata haka, ranta nayi mata suya tace." Shin kana nufin kace da ita itace ta sanya ka auri Wannan din."? Daga kansa yayi alamar Eh.
Hibbah ta sunkuyar da kanta tana wani tunani sannan Tace. " zan tambayeta kuma in roketa domin durkusawa wada ba gajiyawa bane indai akan Kane babu abunda bazan yi ba, ka bani numbar ta." Tafad'a tana mik'a masa wayar ta.

Karba yayi ya sanya mata numbar Asma'u. Ta maida wayar cikin jakar ta bayan tayi serving numbar. Fuskarsa ta kurawa ido tana kallon dan k'aramin bakinsa idanunsa a lumshe suke yaji kamar ana kallonshi yana bude idonsa ya sauke kan Hibbah ta kura masa ido kamar tsohuwar mayya, mai da idanunsa yayi ya rufe yana jin takaicin ta, a hankali Hibbah ta matsa jikinsa sosai ta rungume shi hade da hayewa jikinshi ta tallafo kanshi ta Dora a k'irjinsa kamar mai bawa YARO mama haka tayi masa, kawai sai ya tsinci kansa da gogo fuskarsa tsakanin k'irjinta Hibbah ta saki wata zazzafar ajiyar zuciya ta cigaba da sha sumar kansa da take bala'in so, murya a sark'e tace." Inayi maka wani irin so da ban San iya adadin sa, ba, zan iya shiga wani hali mutukar ban same ka ba ka tallafi rayuwa ta. Amjadu da duk irin bakin ciki da damuwar da yake ci baya hanashi fitinar sa Idan ta motsa Yanzu ma mantawa yayi da damuwar sa zuciyarsa ta kwadaitu da son kasancewa da Hibbah ko banza ta iya salo kuma ta iya romcing sosai yake jin dadin ta, d'aukar ta yayi ya shige bedroom d'insa da ita ya jefa ta akan gado, Hibbah ta mike da sauri hade da cire d'ankwalin kanta, kafin ta Ankara runi ya danneta hade da ciccusa hannunsa biyu cikin matsatstsiyar rigar ta, nishi ta saki ta zura hannuta ta baya ta zage zif din rigar da hannunta ta cire masa, jiki na karkawara ya balle briziyar ya cafko manyan breast dinta yana murzawa duk jikinsa ya rikice.
Muna zaune a tsakar gida muna duba kayamu babu laifi gidan ya soma cika da baki, k'awayenmu Wanda suka samu labari sun soma zuwa, Kawai muka ji Sallama gabana ne ya fad'i lokacin da naji muryar me sallamar irin ta Rambo,  gudun abun kunya yasa na mike da sauri hade da zura hijab dina na leka soron aikuwa Rambo ne tsaye gaban shi wasu manya manya ledoji ne guda hudu.

Fuskata na hade sosai nace" Lafiya ko.."? Kamar me jin tsorona yace." Yallab'ai ne ya aiko ni." Ledojin dake gaban shi nake kallo yace." Gashi yace.",A kawo muku kuyi amfani da wannan bayan d'aurin aure zai hada mata lefan ta." Nace"Babu laifi ai kace mungode kaji." Rbow yace." Akwai kayan abunci mota guda yace a kawo." Shiru nayi na minti biyu daga bisani nace" Ka sanya yara su shigo dasu." Da sauri yace." Shikkenan ." futa yayi da sauri ni kuma na fara d'aukar kayan ina shiga dasu gida d'aya bayan d'aya.

Buhunan shin kafa ne da taliya ledojin maggi da jarkokin mai, kai duk wani Abu da za'a bukata gashinan har da nama da kifi ciki wani kwali a sinke Rambo ya bawa wani YARO k'atuwar takarda an nannad'eta da wani Abu me kyalli Muna budewa kudi sabbi dall suka soma zubewa kasa, 'yan dubu dubu tas aunt Hauwa ta lissafa kud'in dubu Dari biyu sai wata k'aramar ta karda ya rubuta da turanci cewar a yi cefane da kud'in. Dukaninnu mamaki muke yi, daga k'arshe ni futa nayi na koma cikin k'awayenmu domin nasan zai yi fiye da abunda yayi a yanzu.

Naje na tadda sun sanya Mimi a gaba kowa na fad'ar albarkacin bakinsa a kanta daya daga cikinsu murna suke ta ya ta in sukaji wa zata aura sosai suke ji a zuciyar su cewar ina ma sune, na lura itama walwalar ta ta karu fiye da ta da hat Yanzu kuma batasan cewar ba dani za a d'aura auran ba, tunda tana gani nima sai shirye-shirye nake yi.

*****
Sosai ya sassaki Hibbah ya jigata ta ya sauke duk wani b'acin ransa a kanta sai da yayi  a wa uku a kanta yana Abu d'aya yau ta tsokoshi sosai baya bukatar romonce  sex kawai yake bukata ya samu, Yanzu ya kara tabbatar da cewar maganin da Granny ta karbo masa mai kyau ne, domin jinsa yake da mugun k'arfi kofa za'a hada masa mata a shirin a gabansa zai iya dasu, Hibbah dai dauriya take domin ta kai geji tayi reliazing har sau biyu gogon yak'i sauka daga kanta sai ta fara k'ananun hawaye na sarewa, da kyar ya samu yayi realizing ya sauka daga kanta hade da  nananade jikinsa da bedshirt din da ya cukurkude ta shige toilet ba tare da ya kalleta ba.
Hibbah ta mike zaune cikin jigata! Da kyar ta ke motsa cinyoyinta da sukayi mata balain tsami da tayi motsi zata ji gabanta yayi wani motsi sai zugi yake mata gaskiya ta sha gurza gurin shi wannan wace irin jaraba ce haka, murmushi ta saki a hankali tace." Idan ma baka aure ni ba inda zaka dinga mu'amula dani kamar matar ka ta aure dai-dai ne."

Jikinsa daure da towel ya futo bai ko kalli inda take zaune ba, dama haka kaidar shi take yana jimawa kafin ya hada ido da mace indai yayi sex da ita. Hibbah ta miki a dadaddafe ta shiga toilet ta gasa kanta ta futo ta tar har ta shirya ya fuce daga dakin cikin sauri ta sanya kayanta ta futa.... Yana tsaye a parlor yana idanunsa kan TV yana kallon labarai na k'arfe shida na yamma Hibbah ta futo hannunta ta sanya ta sakalo wuyansa tare da fadin "Mazaje." Kiss ta manna masa a kumatunsa cike da shauki. Idonsa na tsaye kan TV yana jin abunda take masa, sakin sa tayi ta zauna kan kujera hade da futo da wayar ta tara Neman numbar da ya bata da sunan ta budurwar sa kamar yanda ya fad'a.
Bugu daya tayi aka dauka ..........Hayaniyar da tayi yawa ne yasa na yi saurin futa soro domin naga sabuwar numbar CE, sallama nayi naji shiru INA kokarin kashe wayar naji tayi magana cike da izzah tace." Sunana Hibbatu y kk?."? Cike da mamaki nace"Lafiya Lou kefa."? Ba ta amsa min ba, tace." Amjad ne ya bani numbar ki Yanzu. " naji wata irin fad'uwar gaba jin ta ambaci sunan sa. Nace "Lafiya dai in ce ko."? Kasaitaccan murmushi tayi tace." Alfarma nake nema a gurin ki, kamar yanda shi uban gayyar ya umarce ni." Ajiyar zuciya na sauke nace"Ina jiniki ki fad'i abunda zaki fada min INA da uzuri. A Dan tunzure na k'arashe maganar tawa.

Har yanzu yana tsaye inda yake idonshi tsaye a TV amma hankalinsa yanzu na kan maganar da Hibbah takeyi da Asma'u a waya, yana daga inda yake yana jiyo sautin muryar ta, Asma'u akwai zakin murya Uwa uba kuma sai ka saka kunne sosai sannan zaka ji maganar ta saboda yadda take da saurin baki.

Hibbah tace"Yace in nemi alfarma a gurin ki kamar yanda kika yarje masa zai auri matar da kika zab'a masa nima ki yarje masa ya aure ni, domin duk cikin Ku nafi Ku son shi."

Asma'u taji wata magana kamar ta shashashai sai taga kamar ma da rainin hankali cikin ta, kashe wayar tayi hade da Jan tsaki ta koma cikin gida abunta.

Hibbah tayi sakato da waya a hannunta tana mamaki kiran wayar ta kara yi a karo na biyu har ta katse ba dauka ba, ta kara kira a karo na uku . Da sauri na mike na kara komawa soron a fusace nace"Wai meye hakane malama kin dame ni da kiran waya, mtsssss.! Cike da taikacinta Hibbah tace"Ke ni zaki fad'awa magana kin San ko ni wacece kuwa."?
"Sanin ko ke wacece bai dame ni ba, nasan dai  bazai wuce ire-ire 'yan matan shi bane irin Ku 'yan iska karya." Hibbah ta rike wayar da k'arfi ranta a mugun bace tace."Ni kike cewa 'yar iska." Ko a jikina nace"Yo idan ba 'yar iska bace ke mecece ke. Har da zaki kirani a waya kice na nema miki alfarma gurinsa ya aure ki, ni meye hadina dashi meye damuwa ta dashi, idan auran ki zai yi sai ya nemi amincewa ta tare na ganku ban San sanda kuka had'u ba, saboda haka kar ki kara kira na a waya mtssssss." Kashe wayar nayi ina jin wani mugun takaici lallai ma guy nan  Dan rainin hankali ne, haka kawai na tsinci kaina da mugun jin haushin sa dashi da 'yar iskar budurwar tasa, tsaki kurrum nake Tabkawa.

Hibbah ta kalleshi ranta a mugun b'ace Tace"Kaga abunda ka janyo min ko.? Na lura yarinyar nan bata da kirki wallahi sai na koya mata zama a garin kano har ni zata bude baki ta gayawa magana irin wannan."!! Dariya yake cikin ransa yace." Indai wannan yarinyar ce halinta ya wuce yanda kike tsammani. A zahiri kuwa cewa yayi "Idan kinga abunda kikayi kina iya tafiya." Hibbah ta mike ranta a bace ta dauki Jakarta tana fadin"Wato ka gama more ni kana ji wata yar iska na zagina kaki ka dauki mataki shikkenan. " murmushi yayi yadan Sosa sumar shi, yace." Nima rarrashin ta nake yi kin San itace ruhina bana son abunda zai b'ats mata rai!!.. Hibbah ta fashe da wani irin kuka me cin rai lallai namiji kanin Ajali kamar ba yanzu ya gama sukuwa a kanta ba ya kwashi romonta amma dubi yanda yake gasa mata magana me zafi.! A fusace!! Ta futa daga parlor . Tsaki yaja me k'arfi hade da zama cikin kujera yana fad'in "Sai kace ni ns kirata 'yar iska zata zo ta dame ni da kukan banza." Zama yayi yana shawarwari da zuciyarsa me. Zaiyi ya kuntatawa zuciyar Asma'u kan abunda tayi masa lallai ta dauki bashi domin bazai tab'a yafe mata ba halin da ta sanya zuciyarsa a ciki zai nuna mata shi namijin duniya ne jarumi zai danne sonta cikin zuciyarsa kamar bai tab'a yi ba, sai tagane kuranta zata gane wautar da ta tafka a rayuwar ta.

Bayan Sallah Jama'a aka d'aura auran Asma'u da Mimi a babban masacin juma'a Mai Martaba sarki ne ya karb'i wakilcin Amjadu duk da cewar akwai wakilan sa, d'aurin auran ya samu halatar manya manya mutane sosai abunka da na Jama'a garin labarin d'aurin auran Amjadu ya baza garin kano da ma kewayen ta, 'yan jarida sun samu abinyi,da kyar ya samu ya futo daga cikin jama'a ya shiga mota ba tare da b'ata lokaci ba ya umarci doh, ya wuce dashi gidan granny saboda yasan in gidansa ya wuce wata Matsalar ce Jama'a gami da 'yan jarida baza su kyaleshi ba.







*15/November/2019*
[11/16, 10:02 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*53*


To gidan granny ma cike yake da 'yan uwa da abokanan arzikinta sun zo taya ta farin ciki mutanan Chadi ma suna kan hanyar zuwa, aikuwa suka yi masa caaa! A ka masu tsokanar sa nayi masu fad'a masa magana nayi a fakaice Inna Suwaiba take yar masa da magana yak'i d'iyar ta Hafsa gashinan ya kwasowa kansa kara da kiyashi, wad'anda suka San akwai maganar sune suka fahimci inda ta dosa basu dad'in abunda tace ba ko babu komai ai matar mutum kabarin sa ce, Granny ma bata ji dadin abunda Inna Suwaiba take yi ba, tunda tazo gidan take yar da haibaci sai kace k'aramar yarinya.
Shi dai shigewar sa yayi bedroom din granny don har ga Allah baya cikin nutsuwar sa ballanta ma ya fahimci Abunda Innarshi take nufi

******
Wallahi duk makiyin mu idan ya kallemu sai mun burge shi, munyi kyau ni da Mimi har mun gaji duk inda muka wuce cikin jama'a sai kaji suna fad'in "Wai wacece amaryar ne tsakanin su biyu sai da a nuna Mimi kawai amma lokaci guda baza ka ban bance mu ba, sai hotona muke da  k'awayenmu, ko wacce da k'atuwar wayar ta, nima hannu na rike da wayarshi da ya bawa Mimi mai muguwar camera mai fidda mutum nasa Munnu ta dinga d'aukar mu hoto ni da Mimi, wacce take cikin tsananin farin ciki da annushuwa.
Umma ita da jama'ar ta sai hidima suke yi aunt Hauwa kuwa ai ba'a ganinta, tun da safe da suka gama rigima da Mimi kan wani magani tazo dashi cikin jarka wai lallai Mimi sai ta shanye shi, Mimi taki shine take tayi mata masifa, nice na lallab'ata ina fada mata amfanin maganin a jikinta sannan ta dauka tasha, magani iri-iri aunt Take dirkawa Mimi wai lallai sai tayi ni'ima ni kuwa dariya kawai nake musu mussaman in naga Mimi na kuka tana shan magani. Yanzu ma gidan kawarta ta tafi wai zata karbo wani turare duk dai Mimi ake so tayi amfani dashi kafin a kaita dakin mijinta.

Dakinmu cike da 'yan uwanmu da k'awayenmu sai surutu kake ji ana shewa zan can aure kawai mukeyi ina gefe ina sanja kayana wayar Mimi tayi kara, dama tana kusa dani ina dubawa naga heartbeat nace" Mimi zo ki d'auka. " da sauri tazo ta karb'i wayar daga hannuna, ihu! 'Yan dakin suka sa, suna fadin"Da Alama ango ne ko."? Gyada kaina nayi nace." Shine ya kira yaji lafiyar amaryar shi" suka fashe da dariya hade da tafawa suna Fadin "hohh-hohh Yau Mimi zata ji maza."! Ita dai futa Tayi daga dakin tana murmushi.

Yana kwance kan bed din granny ya cire babbar rigar jikinshi daga shi sai singlet da dogon wandon arniyar shadda da yayi futar d'aurin auren sa, da ita, juyi kawai yake yi zuciyarsa babu dad'i, ji yayi kawai yana sha'awar jin muryar Asma'u yasan hakan ba dai-dai bane, to ya rasa ya zaiyi da zuciyar sa, wacce take nema tafi karfinsa a kan Asma'u, wayar sa ya dauka ya kira numbar Mimi yana fatan Asma'u ta dauka kamar ko da yaushe, sai dai sab'anin haka Muryar Mimi yaji tana yi masa sallama, lumshe idonsa yayi hade da d'an cije lips d'insa na kasa, yace." momyna ya hidima."? Mimi ta damkewar wayar sosai wani irin dad'i na ziyartar zuciyar ta, a hankali tace." Alhamdullahi." "Ok babu wata matsala ko." "Eh babu mungode sosai da Hidima" murmushi yayi kawai yana jin tausayin yarinyar yasan so masifa ne, abunda yake ji a halin yanzu yasan shi take ji a zuciyar ta dole ya girmama mai sonshi yace." Haka nake so, Idan anjima Ku shirya akwai Walima da abokina masu mak'otaka dani suka shirya min,zan aiko a dauke Ku a mota OK." Mimi tace." Insha Allahu.  Kokarin kashe wayar yake tace" ko in bawa Asma'u wayar ne." ? Girgiza kansa yayi kamar tana kallonsa yace." K'yaleta kawai Momyna zamu gaisa idan anjima OK."
Kafin Mimi tace Wani Abu ya kashe wayar yana jin wani mugun daci a bakinsa, ko wane ango yana farin ciki ranar d'aurin auransa mussaman idan ya tuna amaryar sa, amma shi ranar d'aurin sa ta zame masa ranar bakin cikinsa Asma'u ta cuce shi, bai ta tunanin zai fada rudani na so irin wannan ba.dole yayi kokarin sa Mimi cikin zuciyar sa, ko don ya haddasa Asma'u ciwan zuciya kamar yadda take kokarin haddasa masa, wannan itace shawarar da ya yanke.

****
Mimi ta dawo fuskar ta cike da walwala da farin ciki, tace"Asma'u yace." Mu shirya bayan sallah magariba zai turo a dauke mu akwai walima da a bokanshi suka hada masa, da har nace ko in baki wayar Ku gaisa yace A'a in k'yale ki." 'Yan dakin suka kwashe da dariya tare da fad'in"Haka kurrum yana jin zakin muryar ki, zaki had'a shi da masifaffiya mai saurin baki, mai zai fuskanta ya burgini da ya gwale ki." Dariya suka kwashe da ita har Mimi din, wani irin b'acin rai ne ya kamani lokaci guda, ganin yanda suke min dariya sai naga kamar da gayya suke yi min har ita Mimi din, raina ya b'aci mutuka, Mimi tace. A bani wayar yace baya bukata lallai ma guy nan, cikin jin haushin su nace banzaye 'yan iska kawai baku da aiki sai iskanci da dariya Ko wacce ta rasa mashinshini don Allah a daure ayi aure ko kwa rage zumudi da tsiyayar da kuke yi." Ihu!! Suka sanya kamar wasu shashasha, Maryam tace"Dallah malama yi mana shiru ke akwai wacce ta fiki zuba, daga an fara zancan aure zaki hau lumshe ido idonki har ja yake yi "yar iska, hahahahaha " ta k'arashe maganar tana dariya Tare da bawa ta kusa da ita hannu suka tafa tsaki naja me k'arfi nace "Kanku a keji, kun dai ji Abunda Mimi tace ko, gaskiya Ku kintsa sosai bana son shirme a gurin ku zama manyan baby's kar Ku bani kunya shegu." Munnu tace"Dole ne ai nasan gurin zai had'a had'addan Samari gaskiya

Dariya muka kwashe da ita nace"Munnu ta Shamsu kenan" Hararata tayi, ni ko na cigaba da shiryawa ta ina mata dariya, aunt Hauwa ce ta lek'o dakin tare da kiran Mimi hannunta taja suka futa, nace"Mimi yau kin bannu a gurin aunt Hauwa.

****
K'arfe takwas dai-dai gurin Walima ya k'ayatu, nan cikin Estate din aka shirya komai guri Tasha decoration, haske ko ta ina ga wasu shegun kujeru an ajiye guda biyu na ango da amarya ne, su uku ne kacal cikin Estate din, Ma'aruf Mujahid Hafiz sai Amjadu din, dukanin su ma'aikata ne,  Hafiz yana aiki a babban banki najeria, shi kuma Ma'auruf yana aiki a babban Asibiti na nasarawa Mujahid yana aiki a Company d'angote cement shine manager dukaninsu suna da aure da yara biyu Hafiz ne me D'a d'aya tunda shi bai jima da yin auran ba, sai Amjad da yayi aure yanzu, suna zama na fahimtar juna a tsakaninsu, kasamcewar su Ma'aikata yasa basa haduwa sosai sai weak end suke had'uwa su gaisa da junansu sai kuma lokacin azimi suke shan ruwa tare, yau idan an sha ruwa gidan wannan gobe a sha gidan wancan, Amjad sai dai yaje domin shi bashi da matar ma, sunyi ciwon baki har sun gaji, Matar Hafiz me suna Samina ita ce ta dinga nanika masa k'anwar ta yana basarwa da ta lura ba auran zaiyi ba kawai sai ta hak'ura, amma dukaninsu sun yi mamaki da suka ji labarin auran sa katsaham! Shine suka shirya masa walima domin taya murna, amma da ba don haka ba , shi babu wani shiri da yayi domin murnar ranar.

Dukaninsu sun gayyaci abokanan su shiyasa guru ya tsaru domin duk manyan 'yan boko ne samari masu kwalisa gayu kenan, ango kuwa babu wani abokan shi da ya gayyata, to yawanci ma shi bai fiye sakewa da mutane ba, kuma abokan shi da suka shak'u da juna turawa ne, 'yan gari daban-daban shiyasa sam bai da abokai a najeria sai Wanda ba'a rasa ba.

Shigar wani irin yadi suke yi baki Wanda bantab'a ganin irin shi ba, dinki iri daya huluna iri daya takalman su iri daya kai hatta da agogon hannunsu iri daya ne, sunyi kyau sosai da sosai, Amjad ya futo ango dashi sai gaisawa yake da jama'a fuskar shi babu yabo babu fallasa.

****
To muma namu b'angaran haka take mun shirya sosai ko wacce ta k'ure kwalliyar ta, ni da Mimi kayan mu iri d'aya, cikin Wanda ya aiko Rambo dasu ne jiya muka dauki wani masifaffan les  ruwan Zuma, anyi mishi wani irin dinki mai tutoci gaba da baya dinki Riga da siket ne rigar kuma bata da girma babu abunda yafi burge ni da dinki sai yanda aka kaya ta hannun rigar d'aya dogone d'aya kuma gajere gajeran anyi masa wani falmaran a saman sa cif rigar tayi min amma duk da haka saman k'irjina sai da suka futo  k'aida ne dama indai zan sanya Riga pitatd to sai saman nonuwana sun futo har tsagar su, saboda Allah yayi min baiwar su, sai nayi amfani da gyale mai Dan fad'i inda na samu ya rufe min mazaunai na, amma  yana da sharara dole sai an ga komai nawa, hakan ma dai dashi gwara babu, ni kuma bazan yi kwalliya ta in sanya babban mayafi ba.
Mimi kam net ta sanya kamar yanda amare suke yi muka futo waje muna ta d'aukar hoto, wayar na hannuna naga kira, shine na daga kaina ina Neman Mimi tana can suna hoto, a dake na daga wayar nayi sallama.

Zuciyarsa yaji dam!! Jin muryar ta, dake namiji ne sai ya maze cikin wata 'yar iskar murya yace." Mommahh ga motoci nan sun tawo d'aukar Ku, na k'agu naga fuskar ki, wallahi naji k'amshin ki, humm! Ina fatan zan same ki, a yanda nake tsammani, sai kunzo."! Kashe wayar yayi ba tare da ya bari tace komai ba, ya maida ita aljihunsa, ya cigaba da sabgar shi da jama'a.

Saroro nayi da waya a hannuna gwiwa tayi sanyi sai naji duk wani karsashi da kuzari na, yayi kasa, tunanin guy nake, dama can yana son Mimi Ashe yake pretending ko kuma yanzu ya fara sonta, ni dai tunda nake dashi ban tab'a jinshi da irin wannan muryar ba, gashi yana fad'a mata kalamai na so,  zuciyata ta shiga  zullumi da wasi-wasi, gashi tayi min wani nauyi ina jin bakin ciki a cikinta da kyar na dai-dai ta kaina na shiga cikin jama'a muka cigaba da hoto amma lokaci lokaci sai inji fad'uwar gaba idan na tuno guy din.

Motoci uku ya turo masu zafi dama ba mu fi mu bakwai ba, muka shiga sai Jan bolo gurin parking motocin suka k'arasa da mu sannan ko wacce ta futo, haske ko ina da ina kamar rana ga wasu manya manyan motoci a fake a gurin, k'amshin turare kuwa na wannan yana wane wancan,  can hango shi ya tawo abokanshi biyu a bayan shi, gabana ya dinga bugawa tun kafin su k'araso nake kokarin nemo jarumta ta tana guduwa yayi min masifar kyau! Farin mutum cikin bak'aken kaya, sai ya zama kamar wani tauraro cikin abokan nasa abun mamaki tunda ga nesa nake hango wani kwantaccan murmushi k'ayattace a fuskar sa, Suna karasowa gurin ya rike hannun Mimi tuni abokan shi da masu d'aukar hoto suka fara aikin su,  suka fara tafiya mukuma muka rufa musu baya, na lura bani kadai ce na shiga halin d'imuwa ba har da k'awayemu suma duk jikinsu yayi sanyi ganinshi narasa me yasa yake wa mutane kwarjini haka,mussaman mata.
Addu'ar Neman
nake cikin zuciyata, *"Wallahu galibun ala'amri."* wannan addu'ar nake yi cikin zuciyata domin ina ganin zuciyata zata iya tona mun asiri, a gurin, shiyasa na dauki alk'awarin bazan k'ara kallon inda yake ba, suna. Tafiya ana musu vedio da hotona har suka Isa gurin zaman su, muma muka samu guri muka zauna, sannan guri yayi shiru mai gabatar wa ya tashi ya gabatar da malamin da zai fad'a kar kam zaman aure da  abunda auran ya kunsa
Wa'azi yayi kyau kuma ya fad'ar kar sosai bayan ya gama. Masu rabo suka shigo suka fara raba wasu manya-manyan ledoji komai cikin nutsuwa akeyin shi, ko da wasa naki kallon inda suke zaune, hira ma muke yi da Maryam tana k'ara fada min Yanda Mimi tayi dace da miji tana fadin"Dole sai tayi da gaske domin akwai 'yan matan shi da suka d'aura arinyar akanta mussaman Alina." Nace"Dole kuwa Alina kinga ko zuwa bata yi ba." Maryam tace"Yaushe zata zo matar da tunda taji abun take tada Aljanu." Dariya nasa Ina rufe fuskata da hannuna kawai sai naga hasken flash  dago kaina nayi da sauri, naga d'aya daga cikin abokan shi Wanda suka sanya kaya iri daya yana tsaye a kanmu nida Maryam sai daukarmu a hoto yake mussaman ni. Bata fuska nayi ina kallon shi, murmushi ya sakar min, tare da kashe min ido daya. Dauke kaina nayi ina Jan tsaki k'asa-k'asa. Gurin ya bari yana duba wayar shi, hotona yake dubawa

Duk abunda yake faruwa tsakanin Mujahid da Asma'u a kan idonshi, yasan halin Mujahid akwai son matan tsiya gashi dai da auran shi, amma in yaga mata jikinsa har tsuma yake, yaji wani iri a zuciyarsa amma kallon da yaga Asma'u na watsa ma Mujahid din ya ji dad'i a zuciyarsa yace." Mata masu daraja kenan."

Mik'ewa nayi daga gurin ina waige-waige Su Munnu na can baya an had'u da samari ana hira da ciye-ciye ganin na mike yasa Maryam mik'ewa muka fara ratsa jama'a tafiya zamu yi tunda dai an gama ango ya kawo amaryar sa gida domin na tsani kallon da maza suke min. Aikuwa ido yayi caaaaa! A kanmu ni kaina a jikina nasan kallona ake yi, cikin sauri sauri nake tafiya inda sassaan jikina yake motsawa, sai tsaki nake.

Amjadu kuwa tun lokacin da ta mike tsaye ya karewa jikinta kallo kuma yaga yanda shatin jikinta ya futo ta cikin  sharara din mayafin ta,  sai yaji kamar ana soka masa kibiya a kahon zuciyarsa, mussaman. Yanda yaga maza da dama sun raja'a a kanta, gumi ya tsinke masa, lips d'insa ya tura a baki yana ji kamar ya hadiyi  zuciyarsa ya huta da wannan bakin ci, Mimi ya kalla a sace ya ga Sam ita babu wani abun assha da dinkin ya futo mata dashi, ya rasa wace iri ce Asma'u me karuwan jiki, ko wane irin kaya tasa sai sun tona mata asirin jiki. Innalillahi wa'inna'ilah raji'un. " shine abunda yake nanatawa cikin zuciyarsa ko ya samu sassauci.

Ganin duk sun mike ne suna kokarin futa daga gate sai hakan yayi masa dad'i mutuka wayar sa ya dauka yana kiran Rambo yace." Maza'a maida su gida shi da kansa zai kawo Mimi gida aikuwa haka aka yi, muna kokarin shiga mota ne sai ga Muhajid ya k'araso gurin, hade da kure ni da ido yana sakin wani murmushi, yace." Asma'u." Nayi mamakin yanda ya San sunana haka, babu yabo babu fallasa nace." Na'am ya kake."?
Murmushi yayi Wanda na lura hakan  d'abiar shi yace." Lafiya amma ba Lou ba, tunda na ganki na rikice na gigice na dimauce na rasa nutsuwa ta, Asma'u ina kaunar ki fisabillah." Ya k'arashe maganar sa har da kwantar da kansa, Su Munnu kuwa dariya suke masa, yace." Ina da mata da yara biyu ni ma'aikacin lafiya ne, ina aiki a nasarawa hospital ina fata zaki so ni kar kice na miki tsufa." Yanayin barkwancin sa da yanda yake da sakin fuska da wasa da dariya yasa na saki fuskata nace"Ashe dai ka sani ni kam kayi min tsufa bazan auri me mata ba." Marairaice fuska yayi hade da fadin "Don Allah kinji. " sai na tsinci kaina da sakin dariya har fararen hak'ura na suka bayyana Wanda yayi dai-dai da zuwan Amjadu gurin Hannunshi rike da na Mimi,  ina ganinshi na dauke kaina da sauri gaba na lugude, ko kallonmu bai yi ba nida Mujahid ya fara magana dasu Rambo Wanda suke kokarin saka mutane a mota, Ina jin Mujahid nace "Aboki nifa nayi mata a gurin nan gaskiya naji dadin wannan ranar wallahi na tsinci dami a kala."
Babu yabo babu fallasa ya kallemu dani  dashi yayi wani killer smile As'usuel ya sosa kanshi tare da fadin"Kayi dace Aboki amma bakayi gaggawa ba, kuwa." Mujahid yasa dariya tare da fadin" Wane irin gaggawa kuma in tsaya kallon ruwa kwad'o yayi min k'afa."
Kamar babu abunda yaje damunsa ya sanya dariya tare da fad'in"OK ni babu ruwana wallahi kai da Madam."! Mujahid din yace." Shareta ai ba da ita kadai zan zauna ba." Shiru yayi masa ya cigaba da magana da Rambo, ko da wasa ban kalli shi ba sai ma sauri da nayi na bude motar na shiga.

Ina kallonshi ya rungume kafad'un Mimi a jikinshi lokaci-lokaci yana sumbatar goshin ta, hade da yi mata magana k'asa-k'asa, da sauri na kauda kaina dama tsautsayi ne yasa na kalleshi, Yanzu kuwa Allah Allah nake motar ta tashi mubar gurin.






*16/November/2019*
[11/17, 1:56 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*54*


Sai ya tabbatar da motocin su sun tashi sannan yaja hannun Mimi suka bar gurin, cikin sauran abokan sa ya koma masu hoto suka dinga d'aukar shi da Mimi sai sunkuyar da kanta take cike da kunya shi kuwa rumgumeta yake jikinsa fuskar sa a sake, 'yan jaradi ma ba a bar su a baya na sai da suka zo ganin k'waf tare da d'aukar amarya da ango hoto da vedio  walima tayi kyau sosai kuma ta k'ayatu, k'arfe 11:30 gurin yayi sauki jama'a duk sun a watse a gajiye yake sosai amma babu yadda ya iya dole ya maida Mimi gida. Hannunsa rike da nata babu um bare umum suka shiga mota tare Doh! Yazo da sauri, sai ya daga masa hannu alamun a'a baya ya matsa, yana d'aga masa hannu yaja motar suka futa daga Estate din.. Sai da ya hau kan kwalta sannan ya kalleta a fakaice yace." Momy kin gaji wannan idon naki akwai bacci a cikinsa."? Mimi tayi kasa da kanta tana wasa da hannunta tace." Wallahi na gaji sosai hankalina yayi gida." Cike da tsokana yace." Da har ina cewa kinzo kenan baza ki koma gida ba." Kauda kanta tayi cike da kunya, hira sama-sama suke yi da ita kamar wasu surukai  har suka Isa badawa yayi parking a inda ya saba, kallonta yayi da lumsassun idonsa saurin dauke kanta tayi, ya saki murmushi tare da fadin "Kije ki huta kinji ko gobe ina jiran ki, kiyi min tanadi me kyau." Kofar motar ya bude mata hade da sumbatar hannunta guda, Mimi ta futa a hankali tana d'aga masa hannu, motar yaja ya bar gurin, dake da wutar NEPA a unguwar yasa matasa basu watse ba. Mimi ta tsallaka ta shiga lokonsu cikin sauri

Hira muke da su Munnu amma hankalina da tunani na nakan Mimi gamin har k'arfe goma sha biyu saura bata shigo gidan nan ba, Umma ma ta leko dakin kusan sau uku tana tambayar ta shigo, aunt Hauwa ce ta kwantar da hankalin ta, tunda dai tana gurin mijinta,Ni da Munnu hirar muke Mimi ta shigo da sallama, duk muka bita da kallo, 'yar dariya tayi tare da fadin'Meye daga shigowa ta zaku zuba min ido."? Tsaki naja ina d'an hararata nace." Mimi dubi lokaci fa ke ko tsoro bakya ji, bakya ce masa dare yayi." Maryam dake danne-danne a waya tace "Wane irin tsoro tana tare da mijinta." Munnu tace "Nima dai abunda na gani kenan." Tab'e bakina nayi kawai ina kallonta ta tsallako har inda nake zaune k'amshin turaran sa ya buge ni, domin duk jikin Mimi k'amshin masifaffan turaran sa take, d'an rungume ta da yayi, sai naji zuciya babu dad'i wani irin kallo nake mata cike da zargi ina tunanin ko wani Abu ya shiga tsakanin ta dashi, tunda nasan halinsa ba hakuri ne dashi ba, mik'ewa nayi na futa daga dakin domin ji nayi wani irin fleelings na taso min jin k'amshin turaran sa sai na dunga tuno da salon soyayyar shi, Uwar dakin Umma na shifa duk mutane kwance a rumfa na tsallake su, kwanciya nayi kan gadon ta, gefan aunt Hauwa wacce take bacci sosai nasan gajiya ce." Lumshe idona nayi ina addu'ar kar Allah ya dora min tashin sha'awa ta a wannan daran nasan zan shiga mugun hali ga jama'a a gidan.

****
Shima bashi bangaran damuwa da tsanani gajiya su suka dame shi,  don haka yana shiga part dinshi yayi wanka ya futo parlor ya kwanta kan doguwar kujera  lokaci guda bacci ya dauke shi, mai cike da mafarkai bar katai.

****
Washe gari da kuncin zuciya na tashi har 'yan buki suka so su gane ganin naki walwala kamar jiya yasa suka dame ni da tambaya dole na sake na cigaba da wurda da mutane kamar yanda na saba.

K'arfe bakwai dai-dai motoci sun fi ashirin kofar gidanmu da bakin layinmu duk na d'aukar amarya ne da 'yan uwanta kowa sai da ya samu guri wasu ma basuyi niyyar zuwa ba, mussaman makotanmu amma saboda su kashe kwarkwatar idonsu yasa suka dinga futowa daga gidan jansu su da gayyar 'yayansu suna fadin"Hali Yayi yau Dole suje suga gidan *Young millionaire*  Estate din sai da ya kusa cika da mutane sai hauka suke da ihu hade da k'auyanci aikuwa karnuka na rufe a gurinsu suka dinga haushi sosai, saboda ganin sabon Abu.

Kowa fadin albarka cin bakinsa yake game da kyau da tsaruwar gidansa ni da Munnu da ita kanta Mimi gidan ba bakonmu bane, saboda haka bamu damu ba, amma dai naga sauye-sauye a parlor ba kamar zuwana na baya ba.

Mimi kuka take sosai da sosai ta rirrike Aunt Hauwa wacce take kuka a fakaice,ji nayi idanuna na kokarin kawo ruwa da sauri na fuce daga dakin, Umma kuwa dama kin zuwa tayi domin ba k'aramin artabu aka sha da ita da Mimi ba, tana kuka Mimi na kuka aka futo da ita.

Da kyar mutane suka futa daga gidan ko wacce tana jin ina ma itace a cikin gidan Mimi mussaman 'yan matan gurin. Munnu da Mimi kuka suke sosai, naja tsaki tare da fadin"Dallah Munnu ki tashi mu tafi ki rabu da ita." Mimi ta dago kanta tana kallona cikin hawaye take fadin "Haka zaka ce, ko ? Shine kika munafurce ni wato kin San bada ke aka d'aura auranan ba, kukayi min shiru ni yanzu yaya za'ayi na iya rayuwa ba tare dake ba." Kuka take sosai, nace"Haka Allah ya nufa kiyi hakuri mu zamu tafi." Tashi Tayi da gudu taje ta kulle kofar hade da tsayawa jikin kofar tana kuka, ni da Munnu muka bita da kallon mamaki! Nace" zaki bata kwalliyar taki tun kafin angon yazo." Cikin kuka tace"Asma'u baki yi min adalci ba, yanzu ke idan aka ce  ki tafi ki barni a gidan nan sai ki tafi ki barni." Dariya ta bani sosai nace"Mimi mata nawa akai wa aure suka zauna su kadai kema kiyu hakuri dama mace 'yar haka CE." Tace"Ni dai na fada miki babu inda zaku je Wallahi."

Tun muna d'aukar abun da wasa har mu ka dawo rarrashin Mimi amma kememe ta ki bude mana kofa, agogon dake manne a dakin na kalla k'arfe goma da kwata nace" Mimi dubi lokaci don girman Allah ki bude Mana kofa." Ki tayi, Munnu ta kwanta kan gado tare da fadin""Ki k'yaleta dole idan angon yazo komai abunta mu tafi, gwara mu d'ana gadon amarya." Bude bakina nayi zanyi magana naji muryar shi k'asa kasa yana kiran Mimi da "Momyna" yana kokarin bude kofar. Da sauri na janye ta daga jikin kofar na zaunar da ita kan bed din hade da rufe mata jikinta.

Jan kofar yake yana kiran sunanta a hankali na gyara fuskata sosai naje na bude hade da juyawa. Idonshi yayi masa tozali da bayan Asma'u tana tafiya, take yaji yana nema ya fadin saboda abunda ya tsone masa ido, saurin kauda kansa yayi ya shiga dakin sosai hade da rufe kofar, babu yabo babu fallasa ya kalleni tare da fadin"Me ya hana Ku tafiya."? Idona tsaye kanshi yana sanye da jallabiya me ruwan tuka, fuskar shi fayau da ita, nace"Mimi ce ta hana mu tafiya amma tunda kazo zamu tafi yanzu.." Na fada ina kokarin futa, Munnu ta mike ta itama tana YAFE mayafin ta

Da wani mugun gudu Mimi tayo kaina hade da rungume ni muka kusa fad'uwa ni da ita kuka take sosai tana fadin"Wallahi babu inda zaki je."

Cike da mamaki nake kallonta kuka take haik'an sai naji tausayin ta ya kama ni da gaske murya ta ta karye tana rawa nace"Wai meye haka Mimi wannan abunda kike ba dai-dai bane gaskiya ni sake ni don Allah."! Kin sakina tayi ta cukyukuye min mayafi har d'ankwalin kaina na cire wa yalwatacciyar suman kaina ta bayyana, banyi ki tso ba, tunda aka wanke min kai sai na tattarashi guri guda na Daure da k'aton ribbom. Takaicin ta ya kamani, kokarin nake in janyo mayafina in rufe kaina dashi ganin yanda Yayi tsaye a kanmu hade da kura mana ido, kafin in Ankara mayafin ya fad'i kasa saboda yanda take rikeni rai a bace nace ja Tsaki tare da fadin"Ki sake dallah."!!! Ki Tayi har ilahi yau tana kuka.

A hankali ya karasa kusa dasu, ya sanya hannunsa yana kokarin janye Mimi tana kara rungume ni kamar cingum, nima nawa b'angaran kokari nake in kwace kaina mussaman yanda nake jin hucin nuffashin sa kusa dani hade da k'amshin sa, yayi yayi ya janye Mimi taki Munnu dai na tsaye tana kallon ikon Allah.
Da ya kasa janye Mimi sai ya dawo kaina babu kunya ya rike kafad'una wai zai janye ni. Hannunsa na tankwabe da sauri ina watsa masa mugun kallo
Ya kalleni na kalleshi, bai ce uffan ba, ya kara kai hannu a karo na biyu na goce da sauri, gabana na fad'uwa.
Da sauri ya fuzgo ni daga jikin Mimi nayi taga-taga zan fad'i can na tsaya daga k'afafuna ina haki! Mimi ya rungume a jikinsa yana Dan dukan bayan ta alamun rarrashi. Da sauri na tsuguna kasan k'afafun su na dauki dankwalina da mayafina na mike INA d'aura d'ankwalin ina kokarin bude kofa bana kallon gabana sosai gabana yake fad'uwa.
Munnu ta biyo bayana da sauri muka futa.

Mimi kuwa tun lokacin da ya rungume ta ta nemi nutsuwar ta tarasa a hankali ya zaunar da  ita kan bed ya futa daga dakin tare da kulle kofar da key don kar ta futo.
Lokacin har mun futa harabar gidan Tsit!! Sai hasken fitilo ko ina INA, kai tsaye muka fara tafiya a k'afa. Can naji hon din mota Munnu tace."Asma'u tsaya ina jin za'a kaimu gida ne ga motanan za tawo. Bana cikin nutsuwa ta shiyasa banji abunda take cewa ba, sai gani nayi motar taja burki a gabana, da sauri na tsaya, a gurin, ya bude motar tare da fadin "Shigo i n kai Ku gida dare yayi Yanzu." Bani da zab'i dole sai hakan Munnu tayi saurin shiga na shiga na zauna kusa da ita, kamar wani dravar haka muka mai dashi, yaja motar muka futa daga gurin.

Sosai yake gudu a   kwalta Dan har gabana ya soma fad'uwa ganin irin gudun da take, babu Wanda ya yi wata magana a cikunmu, tunda na dago kaina sau daya muka hada idoshi ban kara dago wa ba, har muka Isa gida, yayi parking inda ya saba, bude motar nayi na futo da sauri!
Shi kuma yaja motar da Wani irin gudu yabar gurin kamar walkiya Jikina duk babu k'wari haka muka tsallaka  titi muka nufi gida babu mai magana a cikinmu.

*****
Mimi na zaune a inda ya aje ta har yanzu kuka take yi sosai kamar wacce akai wa wani Abu, itafa sai yanzu ta gane ba da Asma'u a ka d'aura auransu ba, gani take kamar tayi wani laifi tana mamakin abunda ya hana Amjadu auran ta, gashi dai ta San yana sonta.

Haka ya shigo dakin ya same ta, zama yayi gefan ta hade da Jan mayafin ta yana yi mata magana k'asa k'asa Shiru tayi gabanta na fad'uwa yace." Tashi kije ki dauro alwala munyi sallah godiya.." Jikinta babu kuzari ta mik'e ya bita da kallo gwanin tausayi, minti biyar ta futo tana boye fuskarta lokacin yana tsaye kan dadduma hijab ta  ta sanya ta tsaya bayanshi ya tada sallah.

Bayan sun idar yayi addu'a sosai sannan ya mike  a nutse ya zauna gefan bed dinta tare da fad'in "Momyna wai kukan me kike yi ne ko yunwa kike ji."? A hankali tace" Ina kukan rabuwa da 'yar uwanta ne nayi mamaki da baka had'amu ka aura ba kamar yanda ka fada." Murmushi yayi yace." Allah yayi ita din ba matata bace kinsa matar mutum kabarin sa inji malam bahaushe." Shiru ya ratsa dakin, minti biyar yace." Idan kina jin yunwa kiyi magana yanzu in ciyar dake kazar amarci." Mimi taji gabanta ya fad'i jin abunda yace
Ganin tayi shuru yasa ya mike kan bed din yans fadin"Ok ki shirya ki zo ki kwanta nasan dai a koshe kike ko." Mimi dai yayi shiru. Bata ce komai ba.
Shima sai ya share ta ya kwanta sosai yana lumshe idonsa Asma'u ce kawai take masa gizo yayi da yake jin gabansa na kara mik'ewa wata irin shahararriyar sha'awa na yunkuro masa,
Jin yayi shiru kusan minti goma yasa Mimi mik'ewa tana satar kallon inda yake kwance, wardrobe ta nufa ta fara tube kayan ta, wata rigar bacci ta sanya cotton me k'aramin hannu, me hula toilet ta nufa ta wanke bakinta ta futo
Idonsa dake lumshe ya bude yana kallonta sanda take zuwa gurin shi, k'irjinta ya zubawa ido ya gansu wasu cibir dasu 'yan kananu amma a tsaye car dake rigar me kwanciya a jiki CE, dama baya yi mata kallon me nonowa lumshe idonsa yayi yana sak'a abubuwa da yawa a kanta.
A hankali tazo ta zauna kusa dashi, yaji k'amshin jikinta ya buge shi.
Bude lumsassun idonsa yayi ya zubawa bayan ta kallo, Mimi tana kyawun fata sumul-suml da ita gashi sai shek'i takeyi Tasha gyara, hannusa ya sanya ya jawo ta tafad'a jikinshi, us rumgumets tsam!
Sha'awar shi na kara tsananta tunda  suka hada ido da Asma'u yinin yau yake fama da sha'awa gefe guda kuma maganin granny yana aiki sosai a jikinsa.
Kwantar da ita yayi kan bed din ya rufe ta da jikinsa hade da cusa fuskarsa tsakanin wuyanta Mimi ta kwance lokaci guda ta fara mik'a tana sakin nishi, soyayyar shi me wahalar samu yake mata inda ta kasa gane cikin duniya take ko a lahira sosai ta sakar masa jiki yayi mata sintir yana wasa da k'ananun nonowan ta, Wanda yake jin mugun banbanci  a hannusa domin dai duk Neman matansa bai taba cin karo mace me k'ananun nonowa irin na Mimi ba amma dake idonsa ya rufe bai damu ba kokari kawai yake yaga ya shigi Mimi wacce take kuka tana ture shi, shi kuwa sai cije baki yake yana sakin nishi!
*Nan na futo na barsu*





*27/11/2019*
[11/18, 11:33 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



08089965176
07084653262

*WANNAN SUNE NUMBOBIN WAYATA IN KANA BUK'ATAR CIGABA DA KARANTA BOOK DIN NAN SAI KA TUNTUB'I DAYA DAGA CIKIN NUMBABO NA DOMIN IN FADA MAKA YANDA ZAKA BIYA KUDIN KARATU D'ARI UKU NE KACAL*

```Ina maraba da dukanin masoya na masu kaunar rubutuna a duk inda suke```



*55*


Amjadu bai yiwa Mimi da sauki ba, duk da ya fahimci cikkakiyar budurwa ce bai saurara mata ba har sai da ya gamsu sosai sannan ya dawo hayyacin sa, Mimi ta galabaita sosai da sosai kuka kawai take yi bakinta duk ya bushe, cike da rashin kwarin jiki ya mike ya nufi toilet tsaye yayi cikin band'akin yana kallon joystick dinshi inda take mike zindir gashi dai ya gamsu a lokacin amma ji yake idan da kari zai iya k'araea domin bai kai geji ba, cikin dauriya ya hada ruwa yayi wankan tsarki sai Jan tsaki yake yi ko na menene oho masa jikinsa daure da towel me girma ya futo Lokacin Mimi ta mike a daddafe, ganin tana kokarin fad'uwa yasa ya karasa gurin da take da sauri ya kamata tana tafiya kamar 'yar kaciya ya kaita toilet ruwa ya hada mata me zafi a cunkushe yace. " kiyi wanka ki gasa jikin ki." Futowa yayi bai saurari abunda zata ce, jallabiyar sabuwa dal ya cire cikin ledar ta, ya sanya a jikinsa zuciyar nayi masa wani irin zafi ya hau kan dadduma sallah yayi raka'a biyu ta na fila Wanda ta zame masa ka'ida kafin ya kwanta sai yayi, yana zaune kan dadduma yana addu'a ta futo cikin tashi kuzari sai tale cinya ta, zama tayi a hankali gefan gado tana laluben rigar baccin ta, ta sanya ta kwanta hade da lumshe idonta tana jin wani irin mugun zafi cikin gabanta, ga wata irin azabbiyar yunwa tana sasakar cikinta, bacci ya soma fuzgarta kad'an kad'an
Shi kuwa Amjadu zama kawai yayi yana matse jikinsa domin har yanzu bai gama dawowa dai-dai ba, mamaki yake sosai idan yayi Sex da Hibbah tana kaishi geji yana gamsuwa da ita sosai, Abun mamaki Mimi kuwa sai da yayi realizing a kan ta sau biyu amma still joystick dinshi mik'ewa kawai take tana harbar wa, mik'ewa yayi Sam baya ganin gabanshi, ya Isa bed din, Mimi dake kwance kawai taji mutum a kanta, Ihu ta sanya cike da tsoro da fargaba, bai saurari komai ba ya hade bakinsu guri guda Yana kici-kicin cire mata Riga, duk ya futa daga hayyancinsa, k'ananun nonowanta ya kama yana musu wata muguwar murza a hannunshi, Mimi bata jin dadin komai sai zafi da kan nonon ta yake mata domin Sam baya yi mata yanda zata ji dad'i, kuka kawai take tana rokanshi ta kasa daga hannuta guda saboda yanda ya sakar mata nauyin jikinshi Mimi raguwa ce sosai, sai hawaye take zirararwa shi kuwa gogon Ku da takasa cire mata rigar kawai sai ya daga kafarta guda daya dama babu pant ya jire jallabiyar shi, hade da sanya hannunshi ya kashe fitar gefan gado,dakin yayi  duhu dumd'um  ga jeran wandon shi ya cire sosai ya daga k'afafunta sama, ta kurma ihu! Tana du kanshi, a k'irjinsa baya ji ba yaga ni, ya danna joystick dinshi jikinta, wani Marayan kuka ta saki hada da rirrike damtsen sa, shi kam aiki ya fara babu ji babu gani, burin shi kawai yaji ya zubar da jarabar dake  damunshi a mararsa.

Sosai yake sasakar Mimi a karo na biyu yana sakin wani irin nishi da gurnani, Mimi ko tun tana kokarin k'watar kanta ta daina domin jikinta ya mutu tana karb'ar. Gashi gurin Gwarzon maza, kimanin mintuna talatin yayi a kan Mimi a karo na biyu ya samu da kyar ya kawo, kwanciya yayi rigijif a kanta Yana jin wata irin hajijiya akan shi, Mimi kan suma tayi bai sani ba, Mintuna biyar yana cikin  wannan hali sannan ya mike da sassarafa ya shige toilet ko ta kan Mimi bai bi ba, to yanzu ya samu ta jijiyar shi ta rusuna ba kamar d'azu ba, shifa shiyasa Sam bai fiye damuwa da sex ba, saboda yasan yanayin shi, ba ko wacce mace ce zata iya d'aukar shi, ba sai me irin halin shi, idan San samu ne ya samu romantins masu kyau a tsotse shi ya fi masa ya lura Mimi bata da wata jarumta ko kadan, daure da towel ya futo, ganin bata motsa ba, yasa ya Isa bed din, kura mata ido yayi da sauri kuma ya dago kanta yana dubata suma tayi, ya mike da sauri ya Isa toilet ruwa ya dauko me sanya ya fesa mata a fuska Mimi ta saki wata shegiyar ajiyar zuciya ta bude idonta da kyar kallonta yayi yaji ta bashi tausayi sosai rike hannunsa tayi tana magana dakyar sai da ya kasa kunne sannan yaji me take cewa." K'irjina ciwo ka kira min Asma'u kaji ko."? Babu yabo babu fallasa yace." Me zata yi miki."? Shiru tayi tana zurarar da hawaye tausayi ta bashi yace." Zan kira ta a insha Allahu daina kuka kinji ko Momyna.". D'aukar ta yayi ya kaita toilet ya hada ruwa tare da sanya ta ciki yace." Kiyi wanka ki futo muyi bacci zaki daina jin zafi. " futa yayi da sauri domin baya son irin kallon da take masa.

Zama yayi gefan gado wani Abu na tsinkulin shi, Mimi a zuciyar sa, har Mimi ta futo ya mike da sauri ya kamata tare da kwantar da ita bed din. Shima ya kwanta gefan ta, rarrashin ta yake da kalamai masu sanyi, da haka bacci ya dauke ta. Da kyar ya samu bacci shima, bayan yaga ma tunani tunanen shi, Asma'u ta haramta agareshi ta tabbata tunda gashi har ya hada shimfida da Mimi dole ya sanya son ta cikin zuciyarsa

Sai wajan goma na safe suka tashi, Mimi ta tashi da wani irin zazzab'i mai zafin gaske, a daddafe yayi wanka ga wata irin yunwa yana ji, k'ananun kaya ya sanya a jikinshi, hade da feshe jikinsa da turaran shi na fama, zama yayi gefanta hade da rik'o hannunta a tausashe yace." Momyna pls ki daina kuka don Allah kinji ko." A hankali tace." Ka kira min Asma'u. " Jim yayi minti biyu yace." Wai me zata yi miki ne."? Domin baya kaunar ganin Asma'u a gidan shi, saboda halin da yake shiga a kanta, cikin kuka tace." Ina son in ganta ne." Tab'e baki yayi yace. " kiyi shiru OK yanzu  zan sanya doh-doh ys dauko ta shikkenan ko."? Gyada kanta tayi kawai, mik'ewa yayi ya futa daga dakin yana jan tsaki, yunwa kawai yake ji. Futa yayi harabar gidan. Doh-doh Da Rambo na tsaye da sauri suka k'araso gurinsa Umarni ya bawa Doh yaje ya dauko Asma'u, suka tsaya da Rambo suna magana, shima minti biyar ya bar gurin, ya koma cikin gida.
A farlor ya zauna hade da dafe kansa, Rambo ya sanya yaje can sharararn gurin abincin nan na *Mai takobi* ya dauko masa kuku guda d'aya bazai iya jurarar yunwa zai iya biyan shi ko nawa ne, domin ya gaji da yin take away.

*****
Muna zaune a rumfa ni Umma aunt Hauwa ya Aminu Munnu domin itama bata tafi gida ba, karyawa muke yi, ina jinsu suna hira har da Ya Aminu ya sake sai dariya yake yi sosai, ni kuwa ni kadai nasan abunda yake damuna.

Sallama muka ji Ya Aminu ya mike da sauri ya futa minti uku sai gashi ya dawo yana kallona kana ya kalli Umma yace." Yaron Young millionaire ne yazo d'aukar Asma'u wai Mimi tace tazo."
Gabana ya wani irin fad'uwa wani kallo na watsawa Ya Aminu, Umma ta kalleni tare da fadin "Kinji ko sai ki tashi ki shirya watak'ila wani Abu zaki mata."
Haushi da takaici suka kamani nace"Umma kin San Ds yanda muka rabo da ita kuwa jiya."?
Tace"Eh dole ne amma yanzu ai tunda ta kwana zata saba.".
Aunt Hauwa tace"Ga Munnu nan kuje tare da ita, domin ni bazan je ba, kar rashin hankalin yayi yawa.
Gaddama na fara yi Umma ta b'ata fuskarta sosai tace"Yanzu kina son ganin b'acin raina ko."?
Mik'ewa nayi zuciyata babu dad'i na futa daga dakin.

Hijab na zura kan doguwar rigar shaddar dake jikina daga bakin kofa na tsaya tare da fadin"Munnu futo mu tafi. " Umma tace"kije kawai Yanzu aka kirata a waya tazo gida, futa nayi da sauri ba tare da nayi musu sallama ba, Motar na nufa doh ya bude min da sauri na shiga ko kallonshi Banyi ba, yaja motar da sauri muka bar gurin.

Mintuna ashirin ne suka kaimu unguwar ta Jambulo sosai na murtuke fuskata hade da futowa daga motar, Kai tsaye kofar parlor na nufa.
Rambo dake tsaye bakin kofar ya bude min ba tare da nace masa komai ba na shiga.

Yana zaune a farlor da cup din tae a hannunshi yana kurb'a kad'an-kad'an nayi sallama na shiga, kanshi ya d'aga yana kallonta har ta k'araso ciki sosai.

Babu yabo babu fallasa nace." Ina kwana." Shiru yayi yana binta da wani kallo shi ba na tsana ba shi ba na so ba, mugun haushi ya bani ana gaidashi shi kuma yans faman kallon mutane tsaki naja na nufi bedroom din Mimi, wani irin kallo ya bita dashi, wato shi take wa tsaki lallai ne. Cigaba yayi da kurbar tea d'insa hankalinsa kwance.

Halin da naga Mimi a ciki ya d'aga min hankali kuma ta bani tausayi mutuka hawaye na fara yi sosai ta rike hannuna tana kuka take fadin "Asma'u ciwo nake ji a gabana na kasa daga k'afafuna." Cike da takaici nace "Mimi kina nufin kice har ya kwanta dake ko d'aga k'afa babu ki gama warware gajiyar biki."
Rikeni tayi tana yunk'urin tashi zaune tace." Gashi kuwa kingani Asma'u sau hudu yayi min zafi wallahi."! Naji wani irin bakin ciki cikin zuciyata wai wannan guy wane irin Dan iska ne, budurwa ba bazawara ba, kayi sau hudu sai kace wani bunsuru.
Cike da takaici nace"Kinyi ruwan zafi ko."?
Gyada kanta tayi tare da fadin"Sau biyu ma nayi.
Nace"To yanzu kiran me kike min ne."?
"Kawai kizo in ganki." Tafad'a muryar ta na rawa."
Ajiyar zuciya na sauke nace." Tom gani shikkenan ko." Rike ni tayi ni kuma ina tunanin
taimakon Da zan yi mata

Shigowa dakin yayi cikin tafiyar shi ta jarumai ya k'araso kusa damu hannunshi rike da cup din tea dinshi, ya kalleni fuskarsa dauke da murmushi yace." Ina ganin ki had'a mata ruwan zafi ta gasa jikinta sosai tun jiya take kiran ki sunan ki, duk ts hanani sakewa da ita, a matsayin ki na makusanciyar ta, ki tamaka min ki gasa mata jikinta ba sai na dauko dector ba, idan kuma da matsala ta fada miki sai a dauko dector ya duba ta OK."

Ji nayi ina nema in kifa daga zaune zantukan shi suka dinga yi min yawo aka wai in hadawa Mimi ruwan zafi jiya tana kiran sunana me yake nufi guy nan ne." Tambayar kaina nake yi babu me bani amsa.
Zama tayi kusa da k'afafunta tare da janye bargon dake rufe a jikinta, da sauri na mike na bar gurin jin zuciyata tana wani irin bugawa toilet Din na nufa bana kallon gabana.

Tsayuwa nayi cikin toilet din narasa me ma zanyi shikkenan ta tabbata Mimi matar Amjadu tunda gashi har ya kwanta da ita ya raya sunna shikkenan ita dashi sun haramta da junnan su, wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubowa daga idonna jingina nayi jiginayi jikin garo ina wani irin kuka me Sosa zuciya lokacin ji naka yi gwara in mutu in huta da wannan bakin cikin.
Motsin bude kofar toilet din naji firgit na dawo hayyacina ina goge fuskata ya shigo toilet din, sauri nayi na juya baya na soma had'a ruwan zafi da na sanyi jikina sai b'ari yake.

Bayanta ya k'ura ido da lumsassan idanun sa, kamar na mashaya sarai ya fahimci kuka take yi tunda ya gan hawayen a fuskar ta tana gogewa, murmushi yayi yana shafa siririn sajan shi, a hankali ya k'arasa har inda take, saura kad'an jikinsu ya had'u, gyaran murya yayi tare da fadin "Jimana."!  Tun sanda ya iso kusa dani nake addu'ar Neman tsari dama nasan Neman fitina ne ya sanya aka dauko ni a daga gidanmu, fuskata a mugun hade da juyo k'irjina da nasa suka sad'u hakanan fuska ta da tashi ta had'u  dogon hancin shi na tab'a goshina,
Zame wa nake kokarin yi ya babbake gurin, fuskar shi na kalla da tawa fuskar wacce take a mutukar daure!! Wannan d'an iskan murmushin nasa ya saki tare da tsare ni da fitinanun idanuwan sa, da babu d'igon kunya ko kad'an a cikinsu yace." Kukan me kike yi uhumm."? Wani irin masiffafan fleengs naji yana taso min a lokacin sai na fara addu ar neman tsari daga sharrin shi, cike da jarumta kamar ko da yaushe nace." Ina kuka ne kawai saboda rashin imanin da ka gwada akan Mimi Wallahi baka da Imani."!!
'Yar dariya yayi as'usuel ya shafa sumar shi hade da sajan shi, yace." Wane irin rashin Imani humm? Ko ke na samu haka zanwa tunda hakkina ne kuma sadaki na ne, mallakina ne, yanzu ma na kiraki ne kawai ki gasa min amarya ta, zuwa dare idan ta warware in lallab'ata in kwashi gara yanda ya kamata." Cike da iskanci yayi maganar.

Wani irin haushin sa da takaicin sa nake ji a lokacin sai na rasa me zance masa, kawai na buge k'irjinsa da mugun k'arfi na futa daga tsaka insa tare da fad'in"Dan iska kawai."
Mamakin ta yake yi wai d'an iska take kiran shi a kan hakkin shi, ya gano kishi tsagwaron sa a idanunta dama so yake ya tunzurata, babu wata damuwa a tare da shi yace." Ni kam babu mahalukin mutumin da zai kirani da wannan Kalmar a kan HAKKINA, kawai Dan nayi marking love da Matata sai a ce min d'an iska, kin ci albarka cin My Wife Mimi na da sai kin gane kuran ki."
Yana gama maganar shi ya futa daga toilet din ba tare da ya saurari abunda zata ce ba.

Zamewa nayi na zauna dab'as! Kan tayal din dake kasan toilet din na hada kaina da gwiwa ta wani irin kuka ya kufce min Wanda nayi ta kokarin danne shi, kuka nake sosai da sosai ina addu'ar Neman samun sauki daga Allah, wani irin sabon sonshi da kaunar shi naji yana taso min a zuciyata take jikina ya kama rawa duk narasa me zanyi inji dad'i a rayuwa ta.
Motsin bude  kofar naji na mike zumbur domin na dauka shine ya dawo sai naga Mimi ta shigo tana bin bango, da sauri naje na kama ta, ita kuma ta dinga bin fuskata da kallo bakinta a bushe tace"Habibty kukan kike yi ko." Babu karya domin ga hawaye ne nan tana gani a kwarmin idona nace" Mimi kukan tausayin ki kawai kawai nake yi." Murmushi kawai tayi min tana fyada kanta, ruwan ha hada mata cike wani baho na zuba detol kad'an a hankali na zaunar da ita ciki. Kara ta k'walla ra tana rike hannuna nace" Mimi ki zauna ki Dade a ciki ZAKIJI dad'i jikin ki." Gyda min kai tayi tana rintse idonta, futa nayi daga toilet din na barta.

Babu kowa a dakin, na hau cire bedshirt din shina duk ga d'igon jini nan, gashi duk ya cukurkude raina babu dad'i ko na kwabo na cire shi hade da aje shi gefa guda, wani na ciro kai kyau na shimfid'a kan bed din, na Ciro mata kaya masu kyau na aje gefan gado, zama nayi ina jiran futowar ta,

Minti ashirin tayi ta futo yanzu tafiyar ta ta sauya  ba kamar d'azu ba, na kalleta naga duk ta rame lokaci guda.
Zama tayi kusa dani tana fadin,"Kinga yanzu naji dad'i wallahi."
Nace "Dole haka zaki dinga yi in anjima da yamma ma ki kara shiga ruwan zafin."
Tace"To."
Shiru mukayi tana kokarin sanya kayan ta, ina taya ta. Nace"Kin San me."? Girgiza min kai tayi. Nace"Duk sanda ya kara zuwa yace zai yi sex dake Wallahi kar ki yadda har sai kin warke in ba haka ba tafiya ma zata gagare ki, domin na lura ba imani ne dashi ba."
Karaf!! A kunansa lokacin za yake shigowa dakin yaji Hud'ubar da Asma'u take wa Mimi.






*18/11/2019*
[11/19, 10:01 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*56*



Cike da mamaki yake  kallon Asma'u wacce tayi tsili-tsili da ita tasan tabbas yaji maganar da take fadawa Mimi ga yanayin kallon da yake mata.
K'araso wa yayi dakin sosai hannun shi rike da wata Leda har ya zauna gefan Mimi idanunsa na kàn Asma'u yana tuhumar ta da idonsa, sunkuyar da kaina nayi kamar wacce tayi wa sarki k'arya.

Gyada kansa yayi hade da rungumo k'afafun Mimi yana kallona yace." Manene hujjar ki, na bata wannan gurguwar shawarar.?
Kunya ta hanani in d'ago kaina na kalleshi.
Dariya naji yanayi kasa kasa yace." Saboda mugunta kike zugata ta bujere min a shimfid'a kina mata bakin ciki tafi ki ta ko wane fanni, ga lada ga dad'i zata kwanta a kirjin mijinta shi kike wa bakin ciki ai na gane yanzu."
Kaina na dago in kallonsa yanda ya wani matse Mimi a jikinsa yayi mugun bani haushi a zuciya ta nace "Wannan guy wai wane irin tantiri ne?
Ba tare da nace komai ba na mike tsaye hade da gyara hijab dina INA kallon Mimi dake lumshe ido a ka fad'ar sa, nace" Ni Zan tafi idan kin dauki shawara ta kan ki kika yiwa Allah ya bamu alkairi."
Kofa na nufa da sauri.!

Mimi ta yunk'ura da sauri ta mike ta biyo bayana cikin dingisa k'afafu shima bayan ta ya biyo lokacin har na Isa parlor Tarar gabana tayi hade da marairaice fuska tace "Don girman Allah kar ki tafi yanzu ki bari sai gobe."
Kallon baki da hankali nayi mata wai in Bari sai gobe lallai Mimi, ni idan nabar gidanan nayi rantsuwar babu Wanda zai sanya ni na kara dawowa cikin shi, kokarin bude kofa nake in futa yazo ya bake kofar Yana min wani kallo  kasa-kasa yace." Malama Madam tace ki bari sai anjima kya tafi kin ji, yanzu ki shiga kicin kiyi mana girki ni da ita."
Hararsa nayi a lokacin sai ya bani dariya saboda nasan duk abunda yake yi domin ya bani haushi pretending yake ina kallon wani Abu boyayye a k'wayar idonsa.
Nace"Wallahi da Kai da Mimi babu Wanda zan yiwa girki Kaji na fada maka ma."
Babu yabo babu fallasa yace." Wato kinanan da Wannan gantsarar taki ko? Na hanani sanya Wannan bakin hijab din kinki ji ke gaki da baki kamar shuni."!!

Naji haushin ba'ar da yayi min sosai na kalleshi fuskata a daure nace",Bani hanya na wuce." Ki yayi ya tsira min ido, Mimi ta k'araso gurin jikinta a sanyaye tace."My heart ka k'yaleta ta tafi tunda baza ta zauna ba."
Kallonta yayi yace." Ok tunda kince a k'yaleta ta tafi kar ki k'ara kiramin sunan ta, idan anjima, dama don kin damu a dauko ta ne."
Hannunsa ta rike tana murmushi,
Matsawa yayi daga jikin kofar na bude na futa ko kallonsu ban yi ba.
Harabar gidan na tsaya INA waige-waige karaf ! Muka hada ido da Mujahid ya futo daga part din shi, jikinshi sanye da kayan kwallo shi da wani boy da bool a hannunsa suna bugawa a filin gurin.
Saurin dauke kaina nayi na fara tafiya
Da sauri Mujahid ya mik'ewa yaron shi, boll din ya Isa gurin ta fuskar sa dauke da kayattacan murmushi.

"Asma'u" sanyayyar murya shi naji yana ambatar sunana, tsayuwa nayi hade da sakin fuskata nace"Na'am kana lafiya."? Ya saki murmushi tare da fad'in"Lafiya Lou nake sai dai tunanin ki ya hanani Sakat! Jiya da kyar nayi bacci wallahi." Dariya na danyi nace"Ka fiye ban dariya har da rantsuwar ka."
"Am serious wallahi babu karya a magana ta jiya da kyar nayi bacci Allah ya Dora min so da kaunar ki kamar raina."  Shiru nayi ina kallonshi fuskata a sake, yace." Kin lek'a amare har zaki tafi." Nace" Wallahi kuwa." Agogon hannunsa ya kalla tare da fadin"Gaskiya ana rana bari in futo da mota in kai har gida."
Nace"Aikuwa da ka kyauta." Juya wa yayi da sauri ya nufi part dinshi, kallo na bishi dashi ina murmushi guy yana da kyau da sanyin hali ga nutsuwa.
Mintuna uku naga motar shi na futowa daga nashi gurin, saurin dauke kaina nayi ganin shine yake driving din.
Kusa dani ya tsaya yana yi min Hon!
Banza nayi dashi ina kallon part din Mujahid aikuwa sai gashi ya futo cikin motar shi, ya k'araso gurimu tare da futowa.
Fuskar sa a sake ya mik'awa Amjadu Hannu tare da fad'in "Ango! Ango."!! Dariya suka yi a tare Amjadu ya Sosa kanshi As'usuel yace." Wato dama wayo kuka yi min Ashe haka ake Jin dad'i shine kuka b'oye min."
Mujahid ya bashi hannu suka tafa, tare suna kyalkyala dariyar shakiyan ci, Mujahid yace."Baka da wasa fa wato har an wuce gurin kenan. "
Amjadu yace." Tuntuni Alhaji yanzo sai jiran sakamako."
Dariya suka kece da ita a karo na uku suna tafawa.

Ji nayi tsayuwar gurin ta ishe ni, domin gani nake yi duk abunda yake yi kamar da hujja yake yi,  motar Mujahid na fufa jikina duk babu k'wari ,wai ni guy nan yakewa wannan tozarci, wallahi babu abunda zai kara kawo ni gidansa
Bude motar nayi na shiga na zauna abuna.
Amjadu yana kallonta a take ya gimtse fuskar sa daga dariyar da yake yi, kafin ya Ankara Mujahid ya saki hannunsa tare da fadin"Bari i n kai  wife  dina gida insha Allah."
Fuska ya had'e sosai yana kallon bayan Mujahid da yayi gaba, har ya bude motar sa ya shiga idonsa na kansa yana mamaki yaushe suka shaku shi da Asme yasan halin yarinyar da girman kan tsiya.
Duk yanayin da ya shiga ina kallon shi, tunda motar Mujahid tana gefan tashi, naji dadin ganin yanda ya shiga halin damuwa
Kawai sai na shiga dariya babu gaira babu dalili, shima Muhajid din dariya yake yana kallona cike da so ya kunna motar shi muka wuce motar Amjad din da sauri.

Gumi ne yake tsiyaya a jikinshi wato wulakanci. Da yarinyar nan zata yi mishi kenan, da kanshi ya futo domin ya kaita gida, Dalili ya aiki su Rambo shine zatayi masa wannan cin mutumcin ya lura fa Mujahid da gaske yake ganin yanda yake zak'ewa akan yarinyar bude motar yayi a fusace! Ya nufi part dinshi yana wani taka k'asa da k'arfi sai huci yake yana jin wani irin kishin ta a zuciyar sa.

*****
Hira sosai muke da Mujahid sai yanzu na kare mishi kallo kyakyawa ne sosai yana da d'an kiba amma ba sosai ba fari ne amma ba kai Amjadu ba, fuskar sa kullum a sake, take naji ya kwanta min domin duk cikin samari na babu Wanda na tab'a sakarwa fuska kamar shi, a yanda yake fada min shi da gaske yake aurena zai yi kuma, baya so aja wani dogon lokaci, to nima gaskiya ya kwanta min a rai naji zuciya ta ya kwanta min shiyasa na bashi numbar wayata da zamu rabu, tare da yi min alk'awarin zai kirani da daddare mu sha shira nace masa ina sauraren sa.

Ko da na koma gida a lokacin aunt Hauwa ta tafi gidan sai Umma kadai tana gyare-gyaren abunda ba'a rasa ba, tana kallona cike da mamaki take fadin ",Har kin dawo kenan."? Nace" Eh Umma zaman me zanyi"
"Lafiya dai ko."? Umma ta fada tana kokarin futa daga dakin, ta San dai ta tsuniyar gizo bata wuce ta koki.
Shiru nayi mata domin ina jin nauyin fada mata dalilin kiran Mimi di.

*****
Rayuwa kenan yau kwanan Mimi biyar a dakin mijinta, inda Umma kullum ya zauna zancan Mimi take yi, duk da cewar kullum sai sunyi waya da ita, wani lokacin ta bani wayar mu gaisa ta k'araci korafin ta ta gama , sai dai in ce mata kawai tayi hakuri zan zo. Wani lokacin kuma idan ta kira wayar kin karba nake yi ko in tashi in bar gurin.

Ya Aminu da Babban su Munnu sune suke mana cukucukun makaranta nan FCE Babban su Munnu yake sha'awar muyi mu samu  ko Diploma ne  tsakanin Munnu da Ya Aminu soyayya tayi k'arfi domin Babansu ya kori Shamsu tunda yayi da shi ya turo manya a yi magana shikkenan ya gudu daga ranar be kara zuwa ba.

Gaskiya naji dadin koma wa makarantar da zamu yi ina mutukar  son in ga nayi karatu me zurfi a rayuwata.
Ni da Munnu sai shirye-shirye muke yi wacce tayi tayi dani muje gidan Mimi naki zuwa, ita kuma tace baza taje ita kadai ba.

********

Rayuwa suke da Mimi babu yabo babu fallasa Shine me Dan shige mata jiki ita kuwa kullum kamar suruka take a gurin shi, idan yana guri ta dinga b'oye-boye kenan shi dai sai dai yayi dariya kawai yana mamakin me zata b'oye masa Wanda be gani ba.
Tun ranar da ya kwanta da ita kwamciyar aure bai kara takar ta ba, sai dai duk daran duniya yana ragewa kansa zafi da ita, amma bai kara gangancin yin sex da ita saboda baiji da dad'i ba a farko.

Misalin k'arfe goma sha biyu da rabi na ranar Asabar Wanda yayi dai-dai da satin Mimi biyu gidan Amjadu, tana zaune a parlor ita kadai lokacin ya futa zuwa company sa kuma dai shirye-shiryen tafiya Chana yake yi shiyasa kwana biyu baya zama sosai.
Kallo take yi ita daya kamar tsuntsuwa, sai ta soma jin takun takalmi za'a shigo parlor da sauri ta kallo kofar shigowa, suka Had'a Ido da Alina ta shigo cikin wasu 'yan iskan kaya fuskar ta tasha make up sai taunar cingum take, hannunta rike key din motar ta tana kar kad'a shi, tazo ta tsaya kan Mimi tana girgiza jikinta, cikin shigar raini.
Mimi tace" Alina babu sallama kika fado min gida."
Wata irin mahaukaciyar dariya Alina ta kwashe da ita tare da fadin"Su Mimi masu gida!!!! Hahahahaha.'' Mimi ta bita da kallo cike da mamaki.
Wani irin tauna tayi wa cingum din bakinta tayi kwai dashi ta kalli Mimi a d'age tace."Ina sugar Boy yake yi."?
Alina ce kawai take kiran shi da wannan sunan."
Mimi tasha kunu tare da fadin "Ban sani ba ni Zak........ Kafin ta karasa Maganar tata Alina ta wanke ta da mari tare da fadin" Kinyi ganganci Wallahi!! Kinyi gangamcin shiga gona ta, shigiya 'yar mutsiya ta, kar ki ce bam san abunda yake faruwa tun daga farkon auran Ku har karshen sa, duk nasan komai, Wallahi i n da nasan haka zakuyi min da ban gayyace Ku brhday na ba, Maciya amana kawai."

Mimi ta mike tsaye da sauri tare da buge hannun Alina dake kokarin kai mata wani sabon marin, tace"Ba Isa kizo har cikin gidana kiyi min iskanci ba, wallahi yanzu zan sanya ayi miki fata-fata a gidan nan."!! Dariya Alina ta kwashe dashi ta daki! Kirjin Mimi tana watsa mata kallon raini tace"Nasan fa komai banza kawai kema da kike rawar Kai kin aure Sugar Boy a banza domin bake ya ke so. Ba ya fi son wancan mutsiya ciyar yarinyar mummuna Asma'u, to Wallahi duk sai nayi maganin maciya amana kawai."
Mimi ta fusata ta d'aga hannunta zata kai mata duka Alina ta goce da sauri ta sanya gwiwar hannunta cike da mugunta ta mangare Mimi ta fad'i kan kujera, takalman ta masu tsini ta cire ta fara dukan Mimi dasu abun.  Mamaki, Mimi ta fara kokarin k'watar kanta tana kare fuskar ta, inda Alina ta sanya tsinin takalmin ta ta buga mata a goshi da mugun k'arfi sai jini ya soma zuba, da sauri ta futa daga parlor.Mimi ihu kawai take hade da dafa goshin ta dake zubar da jini duk ya b'ata mata fuska.

Alina kuwa a fusace ta figi motar ta ta fuce daga gidan.
Da kyar ta dauki wayar ya ta fara Neman numbar sa, kira kusan biyar bai dauka ba, gashi dai tana ringing aje wayar tayi tana kuka ta nufi firji k'ankara ta dauko ta Dora a goshinta inda yake zubar da jini gurin har ya kumbura yayi tsini

Alina kuwa tana tafiya cikin motar ta tana tunanin sharrin da zata kulawa Mimi gurin Amjadu. Wayar ta dauka ta fara kiran shi, sai da tayi ringing sau uku ba 'a dauka ba. Ana hudu ne ya d'auka,
Murya sa s tsaye yayi sallama domin ya gane numbar Alina ce.
Wani irin mahaukacin kuka ta fashe dashi, tana fadin "Na shiga uku na lalace!! Hubby naje gidanka sun taru sunyi min duka."
Kasa gane inda maganar ta ta dosa yayi yace." Ke wai meye ne, ina da uziri yanzu."
Alina tana gursken kuka tace." Asma'u da matarka Mimi ne sukayi min dukan mutuwa Yanzu na ina kan hanyar zuwa hospital."
Cike da mamaki yace." Me kika yi musu? Kuma me ya kaiki gidana." Cikin kuka kamar gaske tace"Kasan munyi skull tare dasu sai ince maka gurin zaman mu d'aya dasu, dake ban samu damar zuwa bukin ba, sun gayyace ni, shine naje nayi musu Allah ya sanya alkairi Asma'u tazo gidan ,shine suka taru suka dinga dukana."

Kashe wayar yayi saboda tsabar takaici, Alina ta fashe da dariya tana draving tace"Shegu 'yan iska ai tunda bani na aure shi ba, sai na hada muku sharri a gurin sa, wayar sa ta kara kira yana kallon kiran yak'i dauka.
Tunani yake wato bayan futowar shi daga gida Asma'u taje gidan shi, yasan duk abunda Alina ta fad'a Asma'u zata aikata sun mayar masa da gida sansanin yak'i baya ganin laifin kowa sai na Mimi gani yake Asma'u ce take murza akalar ta, sai abunda tace da ita sannan take yi,
Wayarsa ya dauka ranshi a b'ace! Sai yaga kiran Mimi kusan sau shida, lallai zancan kenan, bugu daya wayar tayi Mimi ta d'auka tana shashshekar kuka.
Wata irin tsawa ya buga mata tare Da fadin"Babu babban mai laifi sai ke Momy menene zaku Tara mata a gidana kuna fadace-fadace sai kace wasu yara, na lura sai abunda Asma'u tace kiyi kike yi ko."!!
Mimi ta tsananta kukan ta tana so ta fahimtar dashi amma Sam yak'i sauraranta masifa yake mata.
Daga k'arshe yace." Kafin in dawo ki sallami Asma'u domin baza ta zo gidana tana tada min da fitina ba."
Kashe wayar yayi bai bari tace Komai ba.

Mimi rasa abunda yake mata dad'i tayi goshinta ya suntume yayi tsini ga zugi yana yi mata, ta lailaiya shi, duk da haka babu sauki, kwamciya tayi kar kujera tana kuka tare da tunanin maganganun Amjadu da inda suka dosa, wanene Ya sako Asma'u cikin case din gidan sa, da zai kama fad'ar bakaken maganganu Sam ya maki tsayawa ya saurari maganar ta.

Wayar ta ta d'auka ta nemo numbar Asma'u lokacin ina kwance kam katifa sai juyi naje yi yanzu har na saba da kwanciya ni kadai a daki, k'atuwar waya tace a hannuna wacce Mujahid ya kawo min ita shekaran jiya, yanzu ka chat muke dashi sai dariya nake ni daya.guy ya iya zuba kalaman soyayya ina so ayi ta nuna min so, ina tsaka da bashi amsa kiran Mimi ya shigo cikin wayata
Da sauri na daga wayar murya ta a sake nace"Mimi yane."? Kuka ta fashe dashi! Nayi saurin mik'ewa zaune tare da fadin "Menene."? Tace." Asma'u Alina yazo har gida tayi cin mutumcin har da su duka da mari baki ga yanda ta fasa min goshi ba." Kai tsaye nace"Zata ai kata abunda yafi haka, tunda naji labarin cewar haukane kawai bata yi ba, da ta samu labarin d'aurin Ku.
Yanzu ke wane mataki kika dauka."?
Cikin kuka Mimi tace"Asma'u kin San dai halin Alina da sharri da kitifi shi kan shi Amjadu ta hada ni dashi, baki ga yanda ya bugu min waya ba yana cimin mutumci har dake a ciki."

Shiru nayi ina mamakin maganar ta yo ni me ya kawo ni cikin sabgar su, idan ba Neman fitina ba, meye alakata dasu ina gefe guda.
Nace "Mimi kar ki kara Bari wata 'yar iska tazo har cikin gidan ki ta doke ki kuma duk sabda Alina ta kara zuwa gidan ki kira ni a waya, Wallahi sai taci kutumar ubanta."
Mimi tace"Shikkenan ni kaina nayi kokarin k'watar kaina ta samu rinjaye a kaina. " tsaki naja cike Da takaicin ta da jin haushin ta nace"Banza kema babu abunda zaki iya sai aukin kuka idan zaki d'age ki kwatarwa kanki 'yanci ki zage ki kwata."
Ina gama magana ta kashe wayar cike da jin haushin Mimi domin duk shashancin ta ne, mace tazo Har cikin gidan ka ta doke ka, lallai Alina tayi kaurin suna.

Ko da ya dawo gidan ma fad'a sosai ya dinga sirfawa Mimi har ta dinga mamakin dama haka yake da fad'a kuka take tana bashi hakuri, bedroom d'insa ya shige cike da b'acin rai.!
Wanka yayi ya futo daure da towel me girma zama yayi gefen bed ya dauki lopto dinshi yana dubawa.
Mimi tayi sallama simi-simi ta shigo dakin. Ba tare da ya d'ago kansa ba ya amsa mata sallamar, hankalinsa nakan loptop dinshi.
Zama tayi kusa dashi jikinta a sanyaye!
Da gefan ido ya kalleta yaga goshinta s kumbure d'ago kansa yayi yana kara kallon gurin, shi Sam bai lura da gurin ba
A ya mutse yace." Kin ce Alina karya take muku ga shaida nanan a goshin ki alamun kun daki juna da ita."
Shiru Mimi tayi saboda ita yanzu bata son a kara maganar.
Tsaki yaja abunsa ya cigaba da duba loptp dinda
Mintin goma sha biyar ya aje ta gefan bed din, ya kamo Mimi tare da rungume ta a jikinsa.
Goshin ta ya kama ya sanya karfinsa sosai ya hau mulmulawa, kuka take sosai, sai da ya tabbatar gurin ya koma sannan ya sake ta, tare da fadin"Idan har kin San Asma'u zata dinga zuwa gidana tana hada min husuma da tashin hankali tom kice mata inji ni bama Neman ta tayi zaman ta inda take, ina laifin Alina don tazo taya ki murna. Kawai sai Ku hauta da duka sai kace marasa hankali, nasan sharrin duk ba na kowa bane sai na Asma'u."

Cikin dauriya Mimi tace"Wai Alina ce tace maka har da Asma'u? To wallahi karya take tsabar sharrinta ne, tun ranar da Asma'u tazo gidanan bata kara zuwa ba." Yace." Dole ki kare ta dama saboda kar ta tsigale ki, ni dai na fada miki ki kiyaye." Cikin kwantar da Kai tace shikkenan Insha Allah haka baza ta kara faruwa ba."
Kwanciya yayi kan bed din yana lumshe idonsa, ita kuma ta tashi jiki babu k'wari ta nufi toilet wanka tayi ta futo  salau-salau ta bude wardrobe kayan baccin ta ta dauko ta sanya Riga da wando ne amma irin masu santsin nan, a hankali ta nufo bed din, ta kwanta gefan sa.
Gogan Ku kuwa k'amshin turaran ta ya dame shi, abunka da mayen turare nan take ya jawo ta a zafafe ya hau ya mutsa ta, yanzu Mimi ta saba da jarabar shi, haka ta hak'ura yana ta murza mata nonowa yana wasa da joystick dinshi a gurin. Mimi Sam bata iya komai ba, ta dinga kauda kanta kenan wai ita kunya shi kuma ya dinga buga mata tsaki da harara ya na nuna mata inda zata tab'a masa, idan taki sao ya dau hannunta ya d'ora a gurin.da kyar take kamawa take masa wasa, inda yake sakin wani irin nishi na dad'i
Haka suke rayuwar sai tayi wuta sannan zai yi sex da ita amma yana samu ya kawo sai daya yake rabuwa da ita.

*******

Tsaf ya futo cikin shiri yana sanye da wasu suit blue and white wanda suka yi masa kyau sosai komai na jikin shi kalar blue da white ne, sai kamshi yake Mimi na binsa a baya idanunta duk sun kode da kuka, wai tafiya chana zai yi dagan ya wuce Ingila kuma yak'i Sanar mata da ranar da zai dawo, shine ta damu.

Hannunta ya rike sosai yace." Momy kiyi hakuri kinji ko, ki kwantar da hankalin ki, granny zata zo ta taya ki zama har in dawo babu matsala cikin tafiya dama nasa ba lokaci zuwa lokaci." Mimi ta fashe da kuka hade da rungume shi, da kyar ya cire ta daga jikinsa ya futa daga parlor cikin sauri bodyguard d'insa suka rufa masa baya.

Zubewa tayi tsakiyar parlor tana wani irin kuka ta ina zata fara rayuwa a cikin gidanan ita d'aya ko sati biyu bata cika ba an tafi wata uwa duniya an bar ta, kuka take sosai.

Mimi tafi a wa gudu a gurin tana kuka daga bisani ta mike jikinta babu k'wari ta shiga bedroom dinta wayar ta ta dauka ta kira Asma'u.

Ina d'aukar wayar naji ta fashe da kuka, tsaki naja da k'arfi nace"Wallahi Mimi Matsalar ki ta fara isata da me zanji ne? Da karatun ko da Matsalar ki, kullum sai ki kira ni kina min kuka, ke baza ki iya gyara Matsalar ki da mijin ki ba."?
Da shashsheka tace"Asma'u yayi tafiya ya barni kuma yak'i fada min yaushe zai dawo." Tsaki naja a karo na biyu nace"To sai me."?  Kiyi zaman ki mana." Tace"Yace ma kakar shi zata zo ts taya ni za ma." Nace"To kin huta ai amma don Allah ki daina Wannan kukan da kike yi bashi da amfani."
Mimi tace"Habibty Wallahi kwana biyu bana jin dadin jikina kullum bana iya cin abunci ga jiri da tashin zuciya ina ji." Nace" kinji asibiti ko kin San dai kina da maleria." Tace." Banje wallahi, amma don Allah gobe kizo muje ki rakani." Nace" Allah ya kaimu, yanzu kakar tashi tazo ko kuwa."?
"Tana kan hanya." Nace "Shikkenan Allah ya sawake don Allah ki kwantar da hankalin ki." To tace mun na kashe wayar.
Munnu ta kalle ni tare da fadin "Bata da Lafiya ne." Nace"Wai zazzab'i take ji da jiri. "
Munnu tasa dariya tare da fadin"Shikkenan Mimi ta hau network sai fatan sauka Lafiya. "
Take naji wani muguwar fad'uwar gaba, na kalli Munnu cikin mamaki nace"Ciki."? Munnu na dariya tace"Eh mana wallahi ko kaffara bazan yi ba Mimi ciki gare ta, kinsan ranar d'aurin auran ta tayi wank ma tsarki kin manta har su  Maryam suka dinga tsokanar ta, tana shiga zatayi gamo aikuwa gashinan. "
Rasa miyau nayi a bakina ya bushe Kama's gashi babu wani tes ko na kwabo jikina yayi sanyi sosai Wahidun k'ahar Allah mai barwa da hanawa..........






*19/11/2019*
[11/20, 10:07 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*57*


Munnu ce kawai take surutun ta i ta kad'ai ni kam ina can duniyar tunani lamarin ubangiji wai Mimi har tayi ciki zata haihu, Allah babu yanda baya tsara almarin shi. Yanzu Sai dai kawai mu taya ta addu'ar sauka Lafiya, yau sama-sama nake a makarantar, domin na kasa sakewa da abun ya fado min zan ji fad'uwar gaba, ya zama Dole na cire son shi a cikin zuciya tunda yanzu nasan yayi min nisa na har a bada.

******
Ina koma wa gida Umma take min zancan Miki ta kirata a waya wai bata da lafiya bayan haka kuma Mijinta yayi tafiya tace kije ki taya zama."

A tausashe nace"Umma nima munyi waya da ita d'azu ta fad'a min, amma ni dai bata ce min naje in taya ta zama ba, tace kakarshi zata zo ta taya ta zama. Amma dai munyi maganar zan rakata hospital taga dactor. "

Umma tace"To tunda kakar shi zata zo sai kiyi zaman ki, ai na dauka ita kadai zata zauna a gidan."
Girgiza kaina nayi. Mik'ewa nayi na shiga kicin domin wata irin yunwa nake ji.

Washe gari da wuri na shirya Dan ma Allah yasa bamu da lecture a ranan da ko sai dai Mimi ta hak'ura Umma nayi wa sallama na tafi tana fadin 'ki gaishe min ita da jiki. Umma ba yarinya bace ta fahimci Mimi ta samu ciki. Sosai take murna da farin ciki.

A dai-dai ta sahu na samu har gidan Mimi na biya shi kudinsa sannan na tsallaka Titi na Isa jikin gate din inda nake hango masu gadi a zaune, fuskata ba b'oyayya bace a gurin su, nan d'aya daga ciki ya tawo da sauri ya bude min na shiga ciki ba tare da na kalle shi ba na wuce part din Mimi cikin nutsuwa.

Suna zaune ita da granny a parlor suna hira nayi sallama na shiga, Mimi ta amsa tare,da mik'ewa da sauri ta tare ni, kallon fuskar ta nayi sosai naga ta rame amma tayi haske sosai.

Zama nayi kan kujera ina gaida Granny ta amsa fuskarta a sake, take fadin"ai gwara kuje likita ya dubata tun d'azu take amai gashi bata ci komai ba Mimi na kalla dake ya mutse fuska nace"Ina gani ba sai munje asibiti ko in kira Mujahid ya duba ki, ko ya kika gani."

Shuru tayi daga bisani tace"Bari in yi masa waya jiya na fad'a masa zamu je asibiti dake yace." Babu matsala amma yanzu nasan babu abunda zai ce tunda yasan Mujahid din. " Shiru nayi ina kallonta na dauki wayarta tana kiran sa, ina ji sai da tayi ringing sai biyu ana ukun ya d'aga muryar da da alamun bacci da gajiya naji yana fad'in"My wife kin tashi Lafiya ."? Mimi tace." Lafiya Lou Alhmdullahi nayi ta kiran wayar ka, tun d'azu baka dauka ba."
A hankali yace." Bacci nake Momy nayi aiki na gaji."
Mimi tace." Dama Asma'u ce tace ko Dector Mujahid za muyi wa magana tunda likita ne ba sai munje asibiti ba."

Tunda Mimi ta fara magana naji kamar in tashi in fuzge wayar daga hannunta in kwad'a mata mari, Mimi wata irin sukuwa ce da bata da wayo.

Nashi b'angaran kuwa Mik'ewa yayi zumbur ya wani hade fuskar sa tam! Yace." Bani Asma'u muyi magana da ita."

Wayar ta mik'o mun da sauri na bi hannunta da kallo, Idanun kakar shi ya sanya na karb'i wayar raina a b'ace.!

A hasale yace." Ke kar ki kuskura ki gayyato min wani gardi cikin gidana, wai da sunan yazo duba wife dina, saboda rashin hankali irin naki. Wallahi sai na b'ata miki rai, mutukar kika shigo min da saurayin ki gida, ki kaita Asibiti a duba ta ko nawa ne a kashe amma ban yarda da wannan iskan cin ba."!!

Shuru nayi INA saura shi yanda yake wani magana a zafafe nace k'ila da yana kusa duka na zai yi.

"Kinji ko baki ji ba."! Yafad'a cikin tsawa! Raina ya b'aci sosai amma ganin granny dake zaune idanunta a kaina yasa nace " Naji." Tsaki yaja ya kashe wayar sa.

Mimi ta karb'i wayar jikinta a salube domin da ita da granny din duk sunji irin tsawar da yake buga min.

Granny tace"Rabu dashi don Allah kinji Ina ce shi Mujahid din abokinsa ne kuma makocin sa, ne don zai taimaki iyalinsa sai ya hana kan wane dalili."?

Tace 'kira shi a wayar yazo ya duba ta Allah yasa bai futa aiki ba." Nace"A'a tunda yace kar ayi to a barshi granny kibar maganar Mimi ta tashi kawai muje a sibiti kamar yanda ya fad'a."

K'wafa tayi tace"Sai kuje Allah ya tsare nasan dai ta tsuniyar gizo bata wuce koki Allah ya raba Lafiya sai kun dawo."
Ta fadi maganar tana gyara zaman ta cikin kujera.

Abun mamaki muna futa sai ga motar Mujahid ya futo, tsaf cikin shirin futa aiki.
Da sauri ya tsayar da motar kusa damu, fuskarsa a sake ya leko da kansa yana yi min wani irin kallo na so yace." Me yasa baki fada min zaki zo ba."?

Murmushi nayi kurrum, dauke kansa yayi ya kalli Mimi tare da fad'in"Madam yane da'alama babu Lafiya domin ga alamu nan na gani."

Nace"Aikuwa asibiti zamu je." Murmushi yayi yace." Shine baki Sanar da ni, ba, Ku shigo muje." Nace"A'a kaje kurrum." Fuskarsa ya b'ata yana kallona yace." Bana son gaddama Asma'u don Allah Ku shigo mu tafi."

Mimi da tsayuwa gurin ta gagare ta saboda jiri ta bude motar da sauri ta shiga, kallon ta. Nayi ina girgiza kaina, saboda kar ya fuskanci wani Abu yasa na bude motar na shiga na zauna kusa da ita yaja motar muka tafi

Rambo da doh da suke tsaye suna kallon duk abunda yake faruwa suka koma gurin zaman su, dama sun taso ne saboda su cika umarnin ogan su.

Rambo ya dauki wayarsa ya fara Neman numbar ogan shi. Bugu guda ya dauka, inda yake akwai hayaniyar mutane yasa yace da Rambo ya kashe wayar zai kira shi anjima Rambo ya kashe wayar kamar yanda ya fad'a, doh yace." Tunda ka kira zaka yi masa bayani ya kawo uziri shikkenan nasan ko kayi masa baya ni daga baya zai gamsu, Rambo yace." Ni tsoron fad'an mutumin nake ji, akwai abunda na fuskanta game dashi da yarinyar nan." Doh yace." Nima haka Asma'u  yana masifar sonta, Allah bai kaddara matar shi bace." Rambo da doh-doh suka dinga gulmar ogan nasu.

Asibitin nasarawa  muka nufa, ba tare da b'ata lokoci ba, Mujahid ya sanya nurse ta dauki fitsarin Mimi a wata 'yar kwalba domin auna shi, muna zaune a ofis din sa, Sam yak'i duba marasa Lafiya wai lallai sai ya sallame mu, Kusan mintuna talatin sai gata ta shigo fuskarta a sake tace." Dr sakamako ya nuna positive tana dauke da ciki na sati biyu." Dr Mujahid ya saki murmushi yace." Alhmdullahi dama abunda nake tsammani kenan. "
Nurse ta futa tana 'yar dariya, ni da Mimi kuwa kallon juna muke yi, nace "Mimi Allah ya sauke ki lafiya."
Gani nayi idonta yayi rau-rau za ta fara kuka, saurin dauke kaina nayi daga kanta.

Mujahid kuwa dariya yake mata yana tsokanar ta, wai ko ta soma tunanin ranar haihuwa ne, ita dai bata ce komai ba.
Wayarsa ya dauka yana fadin"Ni zan fara yiwa mutumina albishir sai ya fara kiran wayar Amjadu, gabana ne ya fad'i nasan wata masifar ce,tunda mutumin nan yace babu ruwan sa, dani kar in kara shiga harkar shi,  ya nuna baya so Dr ya duba mishi mata. Shuru dai nayi kawai INA l sauraron abunda zai biyo baya.

Mujahid da dariyar sa suka gaisa dashi, naji yana tambayar sa gida da sauran mak'otan sa, yace kowa Lafiya Lou sannan yace." Dama na kira ne ka bani gurin albishir. " yana dariya ya fad'i. Maganar. Sam bai kawo komai cikin ransa ba, kuma bai taba tsammanin za su bujurewa umarnin sa ba yace." Kome kake so zan baka."
Yace." Madam na dauke da ciki insha Allah ka kusa zama dady yanzu na sanya aka duba ta." Wani irin nauyi yaji a kansa, lokacin da Mujahid yake wannan maganar, Mimi na dauke da cikinsa, har yaushe daran yayi balle gari ya waye, dududu sau nawa ya kwanta da ita har ta dauki cikinsa. ? Shuru yayi Mujahid yace." Kayi shiru ko baka murna ne."

Da sauri yace." Wane ni, kawai ina mamakin hukuncin Allah ne, nagode K'warai Aboki bani Madam din." Mujahid yace." Babu godiya a tsakaninmu domun mun zama daya dakai ina fatan alkarmu dakai ta dore har  a bada."

Mimi ya mik'awa wayar yana fadin "Ga mijin ki za kuyi magana dashi Mimi ta karb'i wayar jikinta a mace tunda akace tana da ciki tayi lak'was.
Muryarsa sama-sama naji yana fadin"Ya jikin naki."?
"Bakinta na rawa tace" Da sauk'i. "
"OK Allah ya sawake ki kula da kanki." Abunda yace kenan ya kashe wayar sa. Mimi ta mik'awa Dr wayar jikinta duk babu k'wari na dauka ma zai yi mata masifa sai naga a kasin haka, ni kaina banji dadin yanda ya ki nuna kulawar shi kan Mimi ba, ko wane namiji akai mishi albishir da matar shi na da ciki yana sakewa yayi ta murna, amma shi magana a cunkushe, Itama na lura bata ji dadin abunda yayi ba.

Dr Mujahid shine ya mai damu gida yana bayan ya hadawa Mimi magunguna dole yace ta zauna ta samu Hutu cikin ya danyi k'wari sannan.

Granny na zaune ita kadai  a parlor tana kallo muna shigowa tace "Naji dadin dawowar Ku da ina zaune ni kadai kamar wata mayya, Dariya nayi na zauna kusa da ita cikin gajiya  tace." Ina fatan dai komai lafiya nasan dai ciki ne da ita."

'Yar Dariya nayi nace"Eh ciki gareta Dr ya bata magungunan Karin jini kuma ta kula sosai da jikinta."

Wani irin farin ciki naga granny tana yi sai washe baki take yi tana fadin"Allah na gode maka 'yar nan ubangji Allah ya sauke ki lafiya naji dadin wannan al'amari dole zama ya kama ni a gidan."

Tausayi tsohuwar ta bani ganin yanda take murna da farin ciki. Na kalli Mimi wacce take ta b'oye k'walla ko ta mecece oho mata.

Bayan sallah azhar nayi musu sallama babu yanda basu yi dani ba kan in zauna in ci abunci naki zama.
Ko da na koma gida Umma har ta sauke nata,zama nayi rumfar ta ina ci muna hira nan nake fada mata Mimi ciki gareta, itama murna take sosai har da 'yar kwallar ta.
Ni dai mamaki nake ko kwallar me suke yi oho.

**********

Kullum Mimi sai ta kirani a waya tana min magiya kan naje gidan ta wai na taya ta zama kafin ya dawo wataran sai na zage ta sannan muke dai-dai tawa da ita. Wataran ma kin d'aukar wayar nake yi.

*******

Yau watan Amjadu Uku a chana Wanda yayi dai-dai da watanin auran su da Mimi komai yayi masa yanda yake so, don haka sai ya fara shirye-shiryen dawowa gida.

Lokacin kuma Mimi tana fama da Matsalar ciwon ciki matsananci Dr Mujahid shine tsaye a kanta scanning anyi mata sau biyar kullum Abu guda yake nunawa Cikin Mimi na zaune a bayan mahaifa Mujahid ya tsorata mutuka duk scanning din da zai sanya ayi mata zai nuna masa  twins amma ko gurin wanne kwanciyar daban, daya cikin mahaifa daya a waje Innalillahi wa'innailahi raji'un.

Duk wannan fad'in tashin da muke yi Sam bai sani ba domin Mujahid yace kar Wanda ya fada masa, Ni kad'ai ya fadawa abunda yake faruwa nima tare da gargadin kar in fadawa kowa saboda kwanciyar hankalin su duk da haka granny tayi mugun tada hankalin ta, saboda ta Dora wa cikin Mimi son duniya.

Tuni na tare a gidan Mimi kusan wata guda kenan muke cikin wannan tashin hankali Mimi ta fige tayi wata shegiyar rama sai uban haske gashi bata cin abunci sai nayi da gaske sannan take ciki ko kuma taga raina ya b'aci kullum da daddare ta dinga murkususu kenan Cikin ta, kuka nake yi sosai ina mata addu'a.

Ganin halin da take ciki yana kara yin gaba, ya sanya Dr tununin Sanar wa da Amjadu dole kome yake yi ya aje ya dawo gida domin duba halin da gidan yake ciki, Duk da cewa kullum yana kiran waya safe da dare amma kira da ban zuwa daban, Dr yana ganin dole ayi mata aiki shine za'a samu maslaha. To ko da ya kira Amjadu din a waya ya fad'a masa abunda yake faruwa bai wani nuna damuwar sa ba yace." Insha Allah yana kan hanya.

Zaman mu guri guda da Mujahid ya sanya wata matsananciyar soyayya ta shiga tsakanin mu, gani nake yanzu nake soyayya Mujahid ya cika mutum mai kyawun hali da tausayi tabbas duk macan da ta aure shi tayi dace da miji na saki jikina sosai dashi, domin shine yake kaini makaranta cikin motar shi kullum, siyayya kuwa babu irin wacce baya min, har yaron shi sai da ya kawo min ya yini a gurini
Grnay tayi ta tsokanar sa, sai dai yayi dariya kawai.

Ina dawo wa daga makaranta granny take fada min yau Mai gidan zai dawo domin yayi waya bayan futa ta yace." Yana jirgi, shikkenan na nemi nutsuwata na rasa domin Sam bana kaunar abunda zai sake hada ni dashi, tunanin hada kaya na nafara yi domun ina gudun cin mutumcin da zai yi min a gidan shi....







*20/11/2019*
[11/21, 10:38 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*58*




Mimi na sanya tayi wanka ta gyara jikinta tsaf! Nima  nayi wanka ban yi wata kwalliya ba, na sanya atamfar mu ta anko Candy mu, ina kokarin zama kusa da ita tace." Asma'u ya kamata a shirya masa abunci ko."? Kallonta nayi na minti biyu kana nace"Kina da tabbacin zai ci abincin idan ka shirya masa nifa bana son wulakanci domin yanzu ma na had'a kayana tsaf! Zan tafi inda nafi wayo."
Marairaice fuska tayi tace"Don Allah kar ki tafi yau kinji ki bari na warware tukkuna." Tsaki naja tare da fad'in "Kinsan inuwarmu bata had'uwa guri guda dashi, bana son abun bata rai." Tace" Ki rabu dashi don Allah duk abunda zai miki."
Shiru nayi kawai, Granny ta futo daga d'akinta da carbi a hannunta ta idar da sallahr la'asar, ta kalli Mimi sai ta saki dariya tana zama kan kujera tace." Wato da kika ji Mijin ki na kan hanya kinyi wanka tsaf har da kwalliyar fuska." Dariya nayi kadan nace"Dole tayi kar taje ki kwace mata gakinan kin rambad'a kwalli har da sabuwar atamfa." Granny tace"Sai kiyi kuma komai abunki bazan baki kwallina ba."
Dariya nayi nace"Ni ba kwalli nake so ba ki bani lallai me ja irin na k'afafunki."
Kallon k'afar tata tayi tace." Yana gidana nima Iyami ce ta kawo min daga garinsu, duk sanda zata zo gidanan zan ce ta Zo miki dashi."
Nace"Yawwa granny ko yanzu ma a kira ta a waya ai tana da waya ko?"?
Granny tace"Tana da waya to wai ke meye kika damu da kunshi sai kace wata me miji, ki bari mu masu miji muyi."
Dariya ta bani sosai nake yi nace"Ni ko nake da miji a hannu kin San shi don kullum yana zuwa gaishe k.............Kafin in karasa ya shigo parlor tuni k'amshin turaran sa, ya mamaye parlor. Yana sanya da Riga shart fara tas tana da gaje ran hannu, wando jikinsa jins ne blue  ya sanya fencing cap (hana sallah) idanunsa sake da bakin glass wuyan shi wata siririyar sark'e ce silver sai shek'i take, hakama a gogon hannun Shi, shi kanshi blet din da yayi amfani dashi abun kallo ne kafin kazo kan takalmin k'afar shi, booth mai igiyoyi blue colour in da kasan bature haka ya koma.
Duk zancan da Asma'u suke da granny a kunne shi.
Fuskarsa murtuk! Ya tsaya bakin kofa, yana karb'ar wayoyin shi daga hannun Rambo

Granny ta washe baki tana fad'in"Oyoyo angon karni ya dawo sannu da zuwa angon Aishatu sannu da zuwa."! Mik'ewa tayi karasa bakin kofar sai washe baki take, fuskarsa ya saki kad'an ganin kakar tashi ya rungomta jikinsa hade da sumbatar goshin ta yana fadin"Granny na same Ku lafiya."? A sake tace." Lafiya ba lafiya gaskiya amma shige ka huta tukkuna."
Hannunta ya rik'o suka k'araso parlor, ina kallon Mimi ta yunk'ura ta mike tsaye ta nufi inda suke, sakin Granny yayi ya kamo ta ya rungume ta hadda lumshe ido! Kauda kaina nayi da sauri ina da na sanin zama na a gurin.
Fuskar ta ya d'ago da hannunshi yace." Momyna haka kika koma."!? Mimi ta fara k'walla, saurin rungume ta yayi yana Dan dukan bayan ta kad'an cikin sigar rarrashi yace." Sorry baby na ya taso ki a gaba kiyi hakuri insa Allahu zaki warware."
Kungunta ya riko har suka k'araso tsakiyar parlor.
Ya kalleni a d'age. Nima na kalle shi babu yabo babu fallasa.
Wuce wa yake kokarin yi, granny tace "Zaka wuce baku gaisa da Asma'u ba, yarinya hazika kuma jajurtacciya ta tsaya kan matarka sosai, gaskiya samun me zumuncin ta sai an tona."

Babu yabo babu fallasa tace." Granny na ganta ai ni da ita waye zai fara gaida wani ko banza na girme ta nesa ba kusa ba, bayan haka kuma a gidana take dole ta girmama ni."
Tsaki granny Taja tana fadin"kai dad'i na da kai kenan,son girma kowa ai da irin tashi fahimtar ko kaga ka wuce bata gaishe ka ba."

Fuskata na saki don kar in kunya ta granny nace"Sannu da zuwa ka dawo Lafiya. "? A fakaice ya kalle ta, yayi saurin dauke kansa, jin muryar ta ya tayar masa da abubuwa da dama, yana tafiya yace." Lafiya k'alau na dawo."
Bedroom d'insa ya shige da Mimi rungume a jikin sa.
Wanka ya shiga ya futo Mimi na kwance kan bed ya kalleta cike da tausayi ya dawo da matsananciyar sha'awa babu hali domin akwai rashin imani ya kusanci Mimi duba da halin da take ciki.
Sabbin kaya ya sanya ya shirya tsaf dashi kana ya zauna kusa da ita.
Mik'ewa tayi zaune cikin kasala, shi kuma ya tsira mata idonsa.
A hankali yace." Momy kin rame sosai laulayi ya sanya ki a gaba ko." ? Mimi tace." In laulayi ne kadai da sauk'i kullum da daddare fa bana iya bacci ciwon ciki, Dr Mujahid ne a tsaye a kaina sai Asma'u, domun ta dalilinsa take zaune a gidanan tunda shi ya tursasa ta, yana da kirki wallahi, kusan kullum sai ya shigo ya duba ni."

Fuskarsa ya kirne! Kamar bai tab'a Dariya ba yace." Kina so kice min kun karya mun doka ke da Asma'u, bana nan kuna shigo mun da k'ato cikin gida. "!?
Mimi ta tsorata ganin yanda yake zare mata idonsa.
Tsawa ya buga mata tare da fadin" Kinyi shuru ki bani amsa ta."
Gyada kanta tayi tace." Tun ranar ya ganmu zamu hospital shine ya dauke mu a mota can asibitin su ya akaimu shine ya sanya akai min duk wasu gwaje-gwaje."

Mik'ewa yayi tsaye da sauri ya nuna ta da hannu Cikin daga murya yace." Da kika kirani a waya me na fada miki."?
Mimi tayi shiru gabanta sai fad'uwa yake yi.
Ni da granny duk muna jiyo hayaniyar shi, yace." Ko ba cewa nayi dake kar Ki sake ki bi ra'ayin wancan yarinyar ba, wato ni ban Isa dake ba kenan , in banda lalacewa da kudina da komai Ku shigo mun da wani banza cikin gidana bayan bananan, me hakan  yake nufi."!!? Mimi har ta fara kuka tana bashi hakuri
Cikin banbami masifa ya cigaba da cewa" Nace dake akwai kudi a dakina ku yi amfani da ko nawa ne, shine zaku zumar mun da mutumci, ni d'an maula ne."!? Ya fada da wata irin tsawa.!

Mamaki ya kamani jin wata irin magana tana futowa daga bakinsa, dama alkairi yana koma wa sharri ? Me ya kawo maula cikin taimako na tabbata Mujahid bada wata NIYYA ya taimake Mimi ba sai dai hakkin makota ka.

Shashshekar kukan Mimi muka ji nida granny sai hakuri take bashi shi kuma yana kara fusata sai hayaniya yake mata cike da rashin tausayi.

Cike da b'acin rai granny ta mike tana fadin"Wannan rashin hakuri dame yayi kama? Daga zuwan ka, ka fara fad'a ki tausayi babu, wato kai duk irin abun da akai maka na taimako baka gani."

Dakin ta bude ta shiga tana cigaba da fad'an ta.
Mimi tace"Don Allah kayi hakuri wallahi ba laifi na bane."
Da sauri yace." Dama nasan ba laifin ki bane nasan me zuga ki, duk abunda kike yi tunda da kunne na naji."

Granny tace"Kai ko daga dawo wa zaka soma tashin hankali ka duba halin da take ci ki mana, kila da bama gidan dukan ta zaka yi ko."? Ranshi a bace Yace. " granny a gaban ki ake shigo min da namiji gida bananan,duk da cewa makoci na ne, amma shigowar shi cikin gidana bashi da wani amfani mutukar bani na kawo shi ba, kuma nasan dalilin da yake kawo shi gidana,kune kuke ganin taimako ne yake kawo shi ni za'a rainawa hankali."!
Ya k'arashe maganar sa cikin hayaniya.
Duk ina jinsa, a zuciya ta nace"Ikon Allah daga taimako ya koma tashin hankali, mik'ewa nayi da sauri na nufi bedroom din Mimi domin in fara had'a kayana zama bai ganni ba.

Granny rarrashin Mimi take sosai ganin yanda take wani irin haki! Ya tsorata sosai, ta zauna kusa da ita  tana fadin "Kiyi hakuri ki daina kuka shi namiji ba'ayi masa haka, kinga yanzu kin nuna masa langon ki." Ita dai Mimi hawaye kawai take sharewa tana mamakin jarabar mijin nata .

Shi kam Amjad tuni ya bar dakin. Ko da ya futo yaso ya samu Asma'u a zaune ya wanke ta tas sai yaga bata gurin, k'wafa yayi a fili yace."Zamu hadu dake kema."
Parlor ya zauna hade da Dora kafa daya kan daya ya k'urawa TV ido sai faman huci yake.

Futowa nayi daga bedroom din bayan na gama hada kayana,kawai na ganshi zaune da har zan koma ciki kawai na dake sosai Nazo na gifta shi zan nufi kicin, k'afar shi ya sanya ya tad'o tata cike da mugunta

Taga-taga nayi zan fad'i da sauri na rike hannun kujera, sai ya sanya hannunsa guda da k'arfi ya buge min hannuna na fad'a jikinsa kaina ya daki k'irjinsa.

Kafin inyi wani yunkuri ya ture ni daga jikinsa hade da Jan tsaki, yana min wani irin kallo.
Kamar zan fashe da kuka na mike tsaye hade da d'aukar dankwalina da ya cire na d'aura.
Murya na rawa nace"Allah ya Isa wallahi."
Zuba min ido yayi yana kallona.
K'irjina nayi saurin kalla ganin shi yake kallo, saman breast dina duk sun futo dama kaida ne hakan.
Tsaki naja nace"Iskanci a cikin gidan aure Allah ya raba mu da irin auran wannan mazan." Kicin din na wuce da sauri ina hard'ewa nasan kallona yake yi.
Dauke kansa yayi bayan shigowar ta har yanzu ya rasa wane irin hukunci zai yi ma yarinyar .

Tsayuwa nayi tsakiyar kicin din ina tunanin abunda ya kawo ni, minti biyu na tuna Mimi nake so inyi wa miyar ogon da hanta, kullum nake mata taci da bread ko gurasa domin su kadai take iya ci,sai wainar fulawa, gurara sa, Mujahid ne yake jigilar kawo mata, in bashi ba, Umma ta aiko mata.

Cikin sauri na fara had'a abun bukata, Allah-Allah nake in gama in bar gidan.
Ina tsaka da Yanka hanta ya fad'o kicin din.
Saboda tsoro saura kadan in yanke hannuna. Jarumta na aro na daure fuska ta tamau.!

Cikin yanayin tafiyar shi ya k'araso inda nake tsaye. Ya kalleni shekeke tare da fad'in "Mara kunya Nazo ki maimata min zagin da kika yi min."
Cike da mamaki nake kallon shi, zallahr fitina na hango a kwayar idon shi, shiru nayi masa na cigaba da abunda nake yi.
Fuzgo ni yayi da sauri bisa tsautsayi knife din hannuna ta yanke ni, a Dan ya tsaya. Da sauri na aje ta ina yarfar da hannun Cikin azabar zafi, sai cije bakina nake.
Gurin yarfar da hannun nawa duk na bata mishi kayan jikinsa.
Ko a jikinsa, zare min ido yayi yace." Wane d'an iskan ne, yace ki shigo min da saurayin ki gidana."
K'walla ce take kokarin zubo min, ga zafin da nake ciki ga jarabar sa.

Shiru nayi ina kallonsa, yace." Zaki daina kallona ko sai na tsone miki ido! Nace"Wane shegen ne yasa ki shigo min da wancan banzan gida, ko an fada miki kowa ma irin ki ne."!

Murya ta na rawa nace"Kullum baka da zance sai gida-gida dai gida-gida wai meye a cikin gidan ne? Da har kake ihu! Ina ce duk gida sunan shi gida mutukar za'a shiga a kwanta a cikinsa, sannan za'ayi kashi da futsari a cikinsa, ko da ko gidan bunu ne Wanda aka yi da karare sunan shi, gida kuma bashi da maraba da Wannan da kake magana a  kan sa."!

Mari! Ya kai mata a fusace! Yace." Ni kike kokarin fad'awa magana Cikin gidana, na fad'a gidana idan kinyi zuciya kar ki kara zuwa balantana kiyi min shirme dama rashin zuciya ne, tuntuni na fad'a miki bana son ganin k'afar ki a gidana ko. Ba haka ba."!? Ya fada cikin sigar rashin mutumci.

Cikin mugun takaicin sa nace"Tabbas gida gidan ka ne, kuma dole inzo gidan nan,tunda 'yar uwata na cikin sa, da bata cikin gidan kai kanka kasan babu abunda zai had'a ni da kai."
Tsaki yaja ya nuna ni da Dan ya tsaya "Wallahi wannan ne na farko da k'arshe a gurin ki ko da wasa kar ki kara shigo min da wani banza cikin gidana."
Cikin sigar kuntatawa nace"Mutum da kake magana akan shi ni yafi min daraja a kan ka, so ina mutukar jin ciwo idan ka zage shi."
A kufule yace." Owk don Allah kiyi gangancin sake shigo min dashi gida, Wallahi ke dashi sai na daure Ku! Duk iskancin da zakiyi kije kiyi shi a waje ya fi miki sauk'i ba sai kin kawo min gardi gida ba."!! Wani irin kallo nayi masa sai naga duk ya wani burkuce sai hura hanci yake!
Nasan na kular dashi
Nace"Allah sarki My Jahid hummm yanda ka dauke shi shi ba haka yake ba, a tunani na kai zaka yi shaidar shi, tunda ka rigani sanin sa, wallahi tunda nake dashi ko gyalena bai tab'a rikewa ba, balle har ta ja shi ga tab'a jikina."!
A hasale! Yace." Me kike nufi."?
Shiru nayi mishi ina kokarin barin gurin.
Jawo ni yayi da sauri ya matse jikin bango, muka fara kallon juna ni dashi. Murya ta na rawa nace"Kasan da wannan abun da kake aikata wa haramun ne ko? Idan da Kayi min iskanci son ranka yanzu ka tab'a ni ka tab'a haram! Kana auran 'yar uwata."
Sam! Baya cikin hayyacin sa, idonsa na can wuyan ta idan yake bin lafiyayyar fatar wuyan ta da gashi ya kwanta a gurin, lumshe idon sa yayi ya bude su a gurin, jiki na kyarma ya cusa fuskar shi tsakin gurin yana sakin wata shegiyar ajiyar zuciya, k'ugunta ya rungume da hannu d'aya Jikinshi na wani irin kyarma, sosai yake murza gemun shi a wuyan ta had'e da kuncin ta.
Wani irin masifaffan yanayi na shiga mai wahalar fassarawa gabobina suka yi wani irin laushi! Yayin da na fara Jin k'asa  na ya fara tsiko.
Kamar yanda ya saba min duk lokacin da ya kusance ni, lumshe idona nayi, kokarin tuno addu'ar Neman tsari nake na kasa, gashi duk ya bi ya matse ni jikin bango tare da sake min k'arfin shi, zubewa nayi a gurin ina nishi!
Ya bini hade da Dora hab'arshi kafad'a ta, idanunsa sunyi wani irin ja, duk sun kankance fuskar shi, yake gogo mun a gefan fuska ta, tsigar jikina na mik'ewa, a hankali naji muryar shi na fad'i"Kin cuci ni.!!! Cikin zafin nama na mike ya maida ni da sauri, a hard'e yace." Babu inda zaki je sai kin  bani sweet lips dinki na tsotsa, shine hukuncin ki."!!!!! Kallon Mara hankali nayi masa, da kyar! Nace"Kaji tsoron Allah a duk inda kake." Hannunsa ya Dora kan lips dina yana d'an girgiza kai yace." Ke tsoron sa kike ji? Me zai sanya ki saka wad'annan kayan a gidana."? Yafad'a yana kallon jikina, da k'irjina da suka futo Samar Riga.
Fuskar sa ya Dora a gurin yana murzawa.!
Wata shegiyar a jiyar zuciya na saki, tare da fashewa da kuka, nace" Ka Ubangji kayi min maganin ka" : Cikin wata irin shashsheka yace." Nima Allah yayi min maganin ki."!
Kauda kaina nake yi yana kara kusanto da fuskar sa, bakina. Bana son in bude bakin inyi magana hakan zai bashi damar yin abunda yayi niyya shiyasa na ki budewa, cikin shakakkiyar murya yace." Harshen ki kawai zan tsotsa in k'yale ki, ni shi kadai nake muradi." A zuciya ta nace ban tab'a ganin tantari irin guy nan ba
Hawaye ne ya cigaba da zubowa a idona hakuri nake bashi da ido ko da wasa naki bude bakina kar ya samu dama. "
Miskilin murmushi yayi yace." OK tunda kin ki bude min sweet month din bari in tsotsi  sweets nipple din ki, da alama shi kike so in tab'a miki." Hannunsa ya sanya yana kokarin bank'are min k'irji.ihu! Na kurma!

Granny da Mimi suka nufo kicin din da sauri. Surutun granny yaji tun kafin su k'araso kicin din ya sa ya mike da sauri! Kofar da zata sada ka da store ya bude da sauri ya mai da kofar ya rufe.
Mik'ewa nayi da sauri sai haki nake yi. Rigata na gyara da sauri! Na dauki wuk'ar da ta fad'i kasa. Suka shigo kicin din.
Granny tace"Menene kike yin ihu!? Ina kuka nace"Granny yanke wa nayi."
Mimi ta k'araso gurin tana duba hannuna kuka ta sanya tace"Muje ki zauna na fasa cin miyar."

Nace"Mimi me zaki ci ki bari in k'arasa miki domin yau Zan tafi." Granny tace" A'a kije ki huta kinji yau dai daya."
Rike hannuna tayi muka futa daga kicin din gabana na fad'uwa.
Yana dai na jin motsin su ya futo yana Jan tsaki. Parlor ya shiga lokacin duk suna dakin Mimi. Kai tsaye dakin shi ya nufa, dole ya sake yin wanka, domin jikinsa duk ya b'aci ga wata irin kullewa da mararsa take masa, ba bu tantama dole ya nemi me biya masa buk'ata.

Kuka Mimi take min kar in tafi ita a ganin ta nice garkuwar ta a gidan nace"Mimi ciwo da lafiya duk na Allah ne ki kwantar da hankalin ki insha Allahu zaki samu lafiya."
Granny ta sanya bakin ta tace"Kiyi hakuri ki zauna mata tunda tana son zaman ki kuma tana walwala zaki samu lada gurin Allah, kinji ko, ubangiji Allah yayi miki albarka.'

Karamcin matar ya sanya na hak'ura amma ni kaina nasan zama a gidan hadari ne ina ganin mutumin nan zai iya fad'o min tsakar dare. Dole in dawo kwana da granny.

Sai daf da sallahr magrib ya futo daga dakin shi, lokacin muna zaune a parlor muna kallo ko ince suna kallo  domin ni Sam bana Cikin hankalina.

Yana sanye da jallabiya ash coulor hannunshi rike da carbi me maddanai, yayi shirin zuwa masjid, Granny ta kalle shi tare da fadin"Au! Kana cikin gidan Ashe."? Babu walwala yace." Eh zan je massalaci."kallonsa nayi cike da wani irin tsanar sa, kullum yana nunawa duniya shi na Allah ne amma bayan fage yana aikata sab'o Allah ya shirye shi idan me shiryuwa ne.
Futa yayi ba tare da ya kalle mu ba, granny tace." Yau me zamu ci ne me mana girki ta yanke a hannu."
Mimi tace"Rambo yayi mana take away kawai.
"Ke kika San wani take away ni kam ban San shi ba, gashi me gidan ki ya dawo bai ci abunci ba kuma naga baki damu ba, ya kamata ki shiga kicin din in zaki iya kiyi masa girki ko."
Mimi tace"Granny baki San halinsa ba, wallahi zai iya cewa baya ci." Shiru tayi minti biyu tace"Nasan halinsa farin sani, amma bari inyi sallah ni da kaina zan shiga kicin din."

Kafin Isha'i granny ta kammala girki tsaf inda ta shirya jalop din macaroni da  dankalin turawa hade da kayan Lambu da bushashen kifi
Kamshi ne kawai yake tashi.
Mik'ewa nayi ina taya shirya daining din tsaf ya shigo hankalinsa a kanmu ganin granny a tsaye a gurin ya k'araso da sauri yana fatan ita CE tayi abunci
Matsawa nayi daga gurin da sauri, ni yanzu tsoro yake bani.
Mimi ce ta hada masa abunci ta zauna kusa dashi
Yana ci suna hira sama-sama, ni da granny muna parlor a zaune. Mujahid yayi sallama ya shigo kamar yanda ya saba, babu iso babu komai yana ganin duk an zama d'aya.





*21/11/2019*
[11/22, 9:48 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*


*59*



Da murna granny ta tare shi tana fad'in"D'an halak yanzu nake zancan ka, a zuciya ta Ashe kana tafe."
Mujahid ya k'araso tsakiyar parlor fuskar sa a sake yake fadin" Ina shigo wa naga alamun mutumin ya dawo shiyasa ko gida ban shiga ba na shigo." Granny tace" Aikuwa ka kyauta. "
Daining din ya nufa yana fadin"Kai baka ce mun kana kan hanya ba, muje dauka ka."
Amjadu fuskarsa ya ya mutse Sam! Yak'i sakar wa Mujahid din yace." Akan me zan kashe maka aiki."
Jahid ya sanya dariya yana kallon Mimi yace." Kai kake ganin haka amma kafi k'arfin komai a gurina."
Shuru yayi masa ya cigaba da cin abuncin sa.
Mimi tayi saurin mik'ewa domin kar ya fuskanci komai tace"Dr zauna ina hada maka abunci."
Zama yayi kamar yanda ta umarce shi.
Yace." Madam lallai yau lafiya ta samu, har da shiga kicin."?
Mimi na hada masa abunci tace"Aikin granny ne."
Girgiza kansa yayi yana fadin " lallai yau zanci abunci me gamsarwa domin girki tsaffi daban yake da 'yara."
Granny ta sa Dariya domin duk tana jin hirar su tana parlor a zaune.
Ni kuwa tun shigowar sa na mike da sauri na bar gurin,
Saboda tun kafin ya zauna naga kallon wulakancin da Amjad din yake masa
Simi-simi ta Mimi ta hada masa abincin ta bar gurin.
Domin itama ta lura da kallon rainin da Amjad din yake masa Sam bata so ayi abun kunya.
Mujahid bude ciki yayi yaci abunci sosai suna hira sama-sama, Wanda shi Jahid din ne yafi magana Amjad sai ya ga dama yake amsa masa.

Tsaf suka kammala ko wanne ya goge bakin shi da tissue, Mujahid ya kalle shi, cikin nutsuwa yace." K'warai naji dadin dawowar ka wallahi."
Gyara fuskarsa yayi yace." Alhamdullahi, nima naji dadin dawowa Cikin nagode K'warai da kulawa Allah ya kara zumunci."
Jahid yace." Kar ka damu Aboki duk yiwa kai ne, nima ban sani ba ko akwai ranar da zaka yi min nan gaba."
Murmushi Amjad yayi halin Jahid yana burge shi guy akwai saukin kai Sam! Bai dauki duniya komai ba.

Mujahid yace." Cikin madam wata uku ne, amma hakikanin gaskiya tana cikin hadari tare da yaron dake cikin ta, domin NASA anyi mata scanning kuma Abu guda yake nuna min.
Twins ne daya cikin mahaifa daya bayan mahaifa, to amma kasan ba yadda Allah baya tsara al'amarin shi."" Wani irin shocking jikinsa yayi lokacin da yaji abunda Jahid yake cewa, da sauri yace"Please ka fada min in fahimta Dr akwai k'wayaye na cikin Mimi sai me kuma kace."?
Ganin Amjad din ya gigice lokaci guda yasa Jahid din yace." Tabbas hakane amma gurin kwanciyar kowa daban. Ma'ana kowa na da mahaifar shi, kuma d'aya yana zaune a wajen da ba'a so."
Wata irin zufa ce ta ke to masa.
Take ya ci wata irin fad'uwar gaba ta rikito masa.
Baki na rawa yace." Jahid meye abun yi yanzu, Ina son baby's dina duka."
Cikin damuwa Jahid din yace." Ka kwantar da hankalin ka, insha Allahu komai zai zo da sauki, aiki kawai za'a yi mata mugani tunda cikin bai yi k'wari ba, sai a cire shi akwai a huta."

Jim! Yayi yana tunani yace." Dr babu yadda za'ayi dole sai abunda ka fada."
Jahid yace." K'warai kuwa shi ne zamu samu Madam insha Allah Amma tabbas idan cikin jikinta ya kai wata biyar tabbas tana cikin hadari ita da baby."

Kamar zai yi kuka yace." OK amma babu abunda zai samu d'ayan ko." ? Murmushi Jahid yayi yace." Babu insha Allah mu fatan nasara muke yi."

Amjad duk ya rud'e  Allah da ya hallice shi yana da mutukar son yara mussaman Twins shiyasa yanzu duk ya damu, wani irin tausayin Mimi da kaunar ta suka dura a zuciyarsa. Ya manta ma da haushin Mujahid din da yake ji.

Nan suka zauna suna tattauna maganar, cike da tausayi da al'ajabi.

A nutse na futo ina Jan jakar kayana.
Duk suka bini da kallo har shi uban gayyar.

Granny tace"ke 'yar nan ina ce ba mun kashe magana ba, ya kuma na ganki da jakar kaya a hannu."

Tsayuwa nayi bakin kofa babu yabo babu fallasa nace"Granny kiyi hakuri Don Allah, Umma babu lafiya zanje in kama mata aiki. Dama saboda mijinta baya gari ya sanya na zo, to tunda ya dawo zan tafi."

Mimi ta k'araso gurina da sauri ta rike jakar kayan, tana fadin "Me ye haka Habbity."?

Tab'e bakina nayi nace" Abunda kika gani sakar min don Allah in tafi gida haka."
Rau-rau idonta yayi tace." Please Asma'u wallahi in ina ganin ki cikin gidanan nafi walwala ina jin dad'i don Allah kar ki tafi."

Mujahid ne ya k'araso kusa damu ya Dan bata fuskar sa tare da kallona cikin tuhuma yace." Ya muka yi dake."?

Marairaice fuska ta nayi cikin sigir shagwaba da han hankali nace."My Jahid please Umma bata ji dad'i ba, zazzab'in nan da ake fama dashi, Yanzu ina shiga daki Ya Aminu ya kira ni a waya Dole ce ta sanya ni tafiya please. "

Jakar kayana ya rike yana kallonta kurr! Nasan sigar da nayi magana dashi ne yaja hankalinsa.
Murmushi nayi masa nace"Kayi hakuri kullum ai muna tare a waya ko."?
Daga kansa yayi kamar wani yaro Karami.

Amjadu yana zaune a daining duk yana ganin abunda yake faruwa haushi duk ya k'umshi ganin yanda Mimi take rarrashin Asma'u tana bata hakuri amma tayi buris da ita.

Da kuzari a jikinsa ya mike gami da Isa inda suke tsaye, Mimi yazo ya kama ya rungume yana rarrashin, shifa yanzu duk wani Abu da zai b'ata mata rai bai so, sosai yake  rarrashin ta.

Tace"Hobby kace da ita kar ta tafi."
Kallona yayi da Jan ido ko bata fada masa ba yasan abunda zai sanya ta bar gidan
Yace."wai ke dole sai da ita zaki iya rayuwa ne? Uhumm! Kinyi aure kina da 'yan kin fita daraja ta ko wane fanni kike zubar da hawaye ki a banza ki daina wannan kuka kina ganin lafiya bata is he ki ba."

Jahid ne yayi masa wani irin kallo yace." Kalaman ka sunyi tsauri malam, itama Asma'u ta kusa shiga wannan sahu."!! Yanda Jahid ya fad'i maganar ne ya tabbatar masa da cewar ransa ya b'aci
Dariya yayi kad'an Dan ya kara tun zura musu zuciya yace." Ai ba karya bane sai ka bari idan ta hau wannan matakin kayi magana."
Ni kam nan tsaya jin karshen maganar sa ba na futa da sauri domin idan na tsaya zuciya ta tana iya mutuwa saboda yadda nake jin bakin cikin bak'aken maganganun da yake tafka min

Bayan ta Mujahid ya bi da sauri ba tare da yayi musu sallama ba, wani irin tsaki Amjadu din yaja ya ja hannun Mimi dake kokarin mayar da hawayen ta suka koma parlor
Granny tace." Ai yarinyar ma tayi kokari wallahi kam bana ganin laifin ta, ka shigo gida kamar wani mala'ika sai muzurai kake dole taji zaman gidan ya gundure ta."
Ba tan ka mata ba ya ja hannun Mimi suka shige dakin shi shi da ita zuciyoyonsu duk babu dad'i
Shi kanshi bai so tafiyar yarinyar ba a wannan lokacin Zata d'ebewa Mimi kewa sosai.

Mujahid ne ya kaini har gida muka yi sallama dashi cikin so da kauna alk'awari yayi min zai zo a sati nan, sai sa motar shi ta bar gurin na ja jakar kayana na wuce gida

Umma na zaune a tsakar gida tana d'aurin kayan miya duk da dare ne amma yara sai shigowa siyan kalanzur suke yi, nayi sallama na gidan.

Cike da mamaki take kallona tace"Kece da daddaran nan." ? Zama nayi kusa da ita INA fadin"Wallahi kuwa Umma ya dawo me gidan dama nagani da zama ." tace"Dama ba kyaso a tursasaki."
'Yar dariya nayi tace"Ya jikin Mimi INA fata da sauki kuma tana cin abunci."

Jim! Nayi ina tunanin maganar Da Jahid yayi min a mota game da Mimi ni tsoron fadawa Umma nake yi saboda nasan halinta Yanzu zata tada hankalin ta.

Kallona tayi tace" Kinyi shuru."?

"Umma jikinta da sauki Alhamdulilahi amma Jahid yace." Dole ayi mata aiki fa."!
Cikin fad'uwar gaba Umma ta aje farar ledar dake hannunta, tana kallona .
Nace"Wallahi haka yace domin hakan shine mafuta.
Take naga hawaye yana kokarin zubawa a idonta, muryar ta na rawa tace"Banji dadin wannan labarin ba Asma'u, nifa idan naji ance za'a yiwa mace me ciki aiki sai naga kamar mutuwa zata yi
Nace"Umma ki daina wannan tunanin insha Allahu Mimi zata sauka Lafiya ."
Shiru tay min tana goge hawaye. A fakaice.
Zuciya ta naji ta karya nima na meke da sauri jin hawaye yana kokarin zubo min mutukar nayi kuka a gaban Umma to itama kukan zata yi.
Dakinmu na shiga na tube kayan jikina yunwa nake ji sosai domin ban samu damar cin abunci da granny ta girka ba saboda fargaba.
Da d'aurin k'irji na futo nace"Umma Allah yasa da akwai ruwan zaki a Fula's Wanka zanyi." Ba tare da ta kalle ni ba tace"Da akwai cikin babban Fula's din nan."
Kicin na nufa da sauri na hada ruwan zafi a bokiti dauka nayi na shiga band'aki.

*******

Tsanin azabar da Mimi ta sha a wannan daran ya d'agawa Amjadu hankali domin kuwa a zaune suka kwana Mimi rungume a jikinsa, kamar ranta zai futa rik'on shi kawai take ya YAFE mata. Saboda tausayin ta bai San sanda ya fara zurarar da hawaye ba, rungume ta yayi tsam!! A jikinsa yana tofa mata addu'oi. Sai daf da asubahi bacci ya dauke ta, shi kuwa dungurgur ya kwana a zaune yana kallonta sai da yaji kiran sallahr sannan ya mike toilet ya shiga yayi Wanka ya futo tsaf shirin massalaci yayi yazo ya tsaya kanta, bacci yaga tanayi sosai, cike da tausayi yake kallon fuskarta inda idonuwan ta suka  zurma cuki
[11/22, 8:02 AM] BintuUmarAbbale: Ko da ya dawo daga massalaci Mimi bata tashi ba,  bai tashe taba sai ya zauna kusa da ita hade da rik'o hannunta ya rike tam! Ya k'urawa fuskar ta ido, Cikin zuciyar sa ya jinjinawa mata da irin wahalar da suke sha yayi d'aukar ciki da haihuwa.
Ya minti talatin a zaune a gurun yana sakawa da kwancewa, kana ya mike ya dauko wayar sa yana kunnawa sakkoni suka dinga shigo wa Sam bai bi takan su ba, numbar Mujahid ya kira. Mujahid yace." Gashinan zuwa gidan.
Kashe wayar sa yayi ya futo parlor lokacin granny ta futo tana kicin tana hada musu kalaci zama yayi a cikin kujera cike da damuwa.

Jahid yana shigowa ya ganshi a hargitse zama yayi kusa dashi ya bashi hannu suka gaisa, yace."yana ga duk ka wani furgice ne."?
Ajiyar zuciya Amjad ya sauke yace." Jahid yanzu haka Momy take shan wahala jiya kwanan zaune muka yi na tausaya mata wallahi."

Jahid yace." Dole kam abun tausayi CE, dama abunda ya kama ta ayi mata kenan." Ajiyar zuciya ya sauke a karo na biyu yace." Da har na fara tunanin futa da ita waje a duba ta."
Murmushi Jahid yayi yace." Kar ka damu Aboki duk abunda kake tsammanin za'ayi mata  k'asar waje insha Allahu zamu yi mata zan tsaya tsayin daka kan almarin ta kasan sai asibitin mu muna da likitoci k'wararru so kar ka damu."

Gyada kansa yayi yace." Yaushe za'ayi aikin." ? Jahid yace." Insha Allah ranar Monday za'ayi." Saura kwana uku kenan."? Jahid yace." Eh saura kwana uku. " OK Allah ya kaimu nagode K'warai. "

Nan granny ta futo daga kicin ta same su, suka gaisa da Mujahid cikin barkwanci sannan ya bar gidan
Amjad din ta kalla a nutse tace" Aishatu ta tashi ne."? Girgiza kansa yayi kamar wani maraya.
Granny tace"Sai hakuri ka kwantar da hankalin ka naga kamar ka tada hankalin ka, insha Allah komai me wuce wa ne." Shiru yayi mata kawai. Ita kuma ta wuce daining domin shirya kayan breakfast.

*******

A gajiye na dawo daga makaranta na zube rumfar Umma cikin gajiya da ishirwa nace"Wallahi Umma da nasan zan sha wahala haka da ban dauki azimin nan ba, kinga yau juma'a anyi rana mutuka ."
Tace"Hakane ai zaki samu lada sosai. " lumshe idona nayi kawai ishirwa Duk ta dame ni, so nake a idar da sallahr la'asar nayi wanka ko zanji dadin jikina.

*********

Tunda motar shi ta shiga prison din, masu gadi da ma'aikatan gurin suke murna da zuwansa dama duk karshen wata yake ziyartar su, irin wannan ranar ta juma'a bayan sakkowa daga sallahr juma'a.

Daurarru dake kulle suna hangoshi ta tagogin dakunan su. Murna da farin ciki ya ishe su. Bayan motar shi wasu manya manyan motoci ne na company *Dangote* suka dinga shigowa cikin prison din, dukaninsu suna dauke da kayayyakin abunci na'ui ka daban-daban.
Ba tare da b'ata lokaci ba, 'yan jarida dake gefe guda suka mike domin fara'a aikunsu, dama duk wannan ranar sukan kasance a gurin da suka San yana zuwa kai ziyara, matasa majiya k'arfi ne suka fara sauke kaya suna ajewa inda aka tana da
Yana cikin mota Duk yana kallon abunda yake faruwa da irin hayaniyar da ake a gurin. Sai da suka gama kwashe kayan tsaf, sannan ya futo daga motar Aikuwa  'yan jarida suka yi caaaa! A kansa basu nemi suyi magana dashi ba, amma sun baibaye shi suna d'aukar hotonsa hade da vidio duk wani motsi NASA sai sun dauka duk inda ya sanya kafa sai sun bishi.
Ofis din shugaban gurin ya nufa.
Suka bishi a baya sai da suka ga ya shiga ofis din sannan suka dakata, Rambo da doh-doh suka tsaye bakin kofar suna zare ido.

Hamshakin mutum ne zaune kan kujerar sa sai juyi yake, kana kallonsa zaka San bashi da imani fuskarsa a murtuke take leb'anshi baki kirin kana gani kasan yana shan taba da abunda ba'a rasa ba, yana da manya manyan idanu,hanci sa yana da fad'i amma ba sosai ba, sannan yana da kiba dai-dai misali. Duk wani Abu da yake faruwa ya na gani ta CCTV Duk ta hasko masa komai da zuwan Amjadu gurin da yanda mutane suke ihu da yanda 'yan jarida suke turereniya akan sa, duk ya ga komai.
Wani irin b'acin rai da kyashi duk suka dame shi, mugun haushin yaron yake ji saboda ya zame su kadangaran bakin tulu.
Abun mamaki suna hada ido da Amjadu din yaji gabansa ya fad'i, Yaron yana da kwarjini da haiba, take ya gyara zama yana masa barka da zuwa
Kafin ya zauna hannu ya fara mik'a masa suka gaisa a muntunce.

Sannan Amjadu yace." Fatan duk na same Ku lafiya."?
Alhaji Gali yace." Lafiya lou Alhmdullahi Ashe ka dawo gari. "
Babu walwala a fuskarsa yace." K'warai kuwa jiya na dawo insha Allah."
Kamar gaske Alhaji Gali yace." Ka cika Dan halak me son talakawa abunda gomnati ya dace tayi bata yi kai gashi kayi mungode K'warai ubangiji Allah ya kara k'arfin a arziki. "
Amjadu ya bashi hannu suka gaisa, yace." Naga muna daf da shiga wata me albarka ga kayan abunci nan insha Allah daf da sallah zan turo musu kayan sawa." Alhaji Godiya yake kamar gaske.
Amjadu ya Mike hade da yi masa sallama ya futa.

Yana futa Aljani  Gali ya dauki wayarsa ya fara kiran me girma governor, sai da ya kira sau kusan uku sannan aka dauka, da sauri Alhaji Gali yace." Allah ya tai make ka?" Governor ya gyara zama kan kujrrarsa Cikin ginshera yace." Tare da kai mutumin." Gali yace." Yaron nan fa ya dawo wane shiri zamu yi a kanshi."?
Governor yace." Na sani ai duk wani Abu da ya faru a gidan yarin gashi a gabana ina gani, akwai shirin da muke masa ni da su Alhaji Hashimu insha Allahu sai mun rusa shi.
Alhaji Gali yace." Yana da kyau hakan , gaya nan ya kawo uban kayan abunci ." dariya governor yayi yace."ka d'ibi iya yanda kake so ka bawa Wanda kake so sauran a zubah a store na gidan, kar ka sake ka sakar mu, ka cuzguna musu abunci sau d'aya nake so a dunga basu haka ruwa ma sau d'aya zasu sha a rana."
Alhaji Gali ya saki dariya tare da fadin"Yallab'ai ai ba sai ka fad'a ba, haka ce zata kasance insha Allah. "
Dariya suka kyalkyale da ita sannan suka kashe wayoyin su, dukanin su suna cike da farin ciki da annushuwa.

Amjadu kuwa bayan futar sa daga gidan prison din kai tsaye gidan marayu suka nufa. Nan ma duk wani Abu da ya sauke gudin prison din  haka ya sauke musu, marayu da marasa galihu ranar murna da dad'i duk ya ishe su, sosai kuma yayi Rabon kudi, musaman mata masu raino rainon yara k'anano sosai suka samu kud'in a gurun shi.

Sai daf da magariba ya koma gida. Granny da Mimi na zaune a parlor duk suna kallon abunda ya faru a TV.
Granny ta hau share hawaye tana tuno iyayen sa , addu'a take masa Allah ya kare shi daga sharrin magauta tabbas idan ya zama shugaba a garin kano za'a huta dashi.
Amma Sam bata yi masa sha'awar mulki.

*********

K'arfe bakwai ta ranar lititin dai-dai tayi mana a babban  hospital din Nasarawa dake jahar kano.
Ranar ina da makaranta amma haka Na kashe ta saboda nasan ko naje babu abunda zan iya yi tun jiya nake Cikin halin damuwa INA wa Mimi addu'a Allah yasa ayi lafiya,
Umma kuwa kwanan zaune tayi da carbi a hannu, a subar fari aunt hauwa ta iso gida saboda haka gari na waye wa muka nufi asibiti kowanne bakin shi da  dauke da addu'a.

Muna zaune suka shigo a sibitin Amjadu da granny sai Mimi dake rungume a jikinsa, ta kara yin haske sosai. Tana ganin Umma ta rugu da gudu ta rungume ta hade da fashewa da kuka, Umma ta fara rarrashin ta tana fadin"Mimi kina dauke da da lalura kina gudu, ki daina kuka kinji ko." Cikin kuka Mimi tace"Umma ki YAFE min ko da Zan mutu."
Naji gabana ya fad'i jin abunda tace
Kallonta nayi nace"Don Allah ki daina mana wannan maganar Mimi."
Shiru tayi min ta k'araso gurin aunt Hauwa dake share hawaye rungume ta tayi tana kuka, aunt rarrashin ta take da kalamai masu sanyi.

Hada ido muka yi dashi yana yana tsaye jikin kofa Yana  kallonmu jikin sa sanye da shadda fara tas! K'afafun shi sanye da takalman me gidan ya tsaya baki , yayi kyau sosai da sosai,
Idan ba idona ne yayi kin gizo ba sai naga ya fad'a idanunsa sun zurma ciki, a hankali ya k'araso kusa da Umma hade da Dan risanawa yana gaishe ta.
Granny ma k'araso wa tayi tana tsokan Mimi alhalin itama Cikin zuciyar ta daurewa kawai take, tun kafin Suzo take share hawaye: Cikin k'arfin hali aunt Hauwa take rarrashin Mimi hade da karfafa mata gwiwa, shi kam Amjadu suna gama gaisawa da Umma bar gurin.
Motar sa ya nufa, ya zauna bayan ya kunna karatun alk'urani, me girma yana saurara

Muna zaune aka zo a tafi da Mimi.
Duk muka bita da addu'ar samun nasara.

K'arfe Biyu da kwata Dr ya futo ya same mu inda muke zaune.
Umma ya kalle ta da ta zuba masa ido,Sam ta manta da wata surukutaka dake tsakanin su, tsugunawa yayi suka gaisa a mutum CE.
Tace"Ina fatan anyi Lafiya Dr."?
Cikin kwantar da hankali yace." Alhmdullahi anyi nasara insha Allahu an samu damar Ciro k'wayar hallitar da izinin ubangiji d'ayan zai cigaba da rayuwa cikin hukuncin Allah kuma zata haife shi lafiya."
Ajiyar zuciya Umma ta sauke tana tayi ma Dr godiya duk ta rasa yanda zata yi
Sauri kawai nake na idar da sallah ta tun a sujjadar k'arshe nake godewa Allah.
Granny da aunt Hauwa baki har kunne sai addu'a suke masa.
Ciki ya koma ya futo da wani Abu cikin kwali. Kai tsaye hanyar futa ya nufa.
Motar Amjad ya nufa domin yasan yana nan.

Yana ganin zuwan Jahid din gurin shi ya futo daga motar yana bin hannunshi da kallo cikin fad'uwar gaba.

Bakinsa na rawa yace." Meye wannan."?
Jahid yace." Alhmdullahi wannan hallitar ce da aka ciro dole zaka gani sannan ka binne domin ubangji ya soma fidda masa hallita ."
Zuciyarsa babu dad'i yace." Jahid Dole sai na gani hummm? Kawai a binne ubangji Allah ya bani wani."
Cikin sanyin murya ya fad'i maganar.
Ajiye kwalin Jahid yayi  ya dafa ka fad'ar Amjad d'in yana fad'in"Colm down Aboki na, ba dole sai ka gani ba, hakkin kane Dole a nuna maka, amma insha Allah ni anan zan sanya a binne shi, ka kwantar da hankalin ka."
A tausashe ya k'arasa maganar.

Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace." Ya jikin Momyna. " ? Dr jahid yace." Alhmdullahi jikinta da sauki hakama babynta insha Allahu zata samu kulawa ka kwantar fa hankalin ka."

Hamdala yayi a fili yana godewa Allah yace." Muje in ganta OK." Ganin yanda ya daga hankalin sa yasa Jahid din kasa yi masa musu, domin babu halin yace. Masa ba'a futo da ita ba tukkuna, dole ya jagoran CE shi har dakin da Mimi take kwance.







*22/11/2019*
[11/23, 10:28 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*

*60*


Lokacin da zasu shiga dakin da Mimi take ji nayi kamar in biso domin na k'agara na ganta, Ashe bani kad'ai ba har su Umma, nauyi ya hanata magana granny tace"Muma zamu iya shiga gurin ta ne."? Mujahid yace." A'a granny Ku bari a futo da ita shima Dan dai mijinta ne, kuma in na hanashi zai iya shak'eni ga yadda yake muzurai."!
Dariya  suka yi ni kam yak'e kurrum nake yi nasan da babu shi tsaf! Mujahid zai shiga dani gurin Mimi.

Kusan Mintuna ashir yayi a ciki sannan ya futo domin shi Mujahid din tunda ya raka shi ya futo ya koma bakin aiki. Kallonsa muka yi dukaninmu,
Tsayuwar sa ya gyara kusa da kakarshi ya futo da wani farin hankici daga aljihun sa, yana goge fuskar sa.
Granny tace"Ya jikin nata ta farko amma."?
Girgiza kansa yayi kamar ba yaso yace." Bata farko ba amma dai Jahid yace." Zuwa magariba zata farko insha Allah."
Hamdala tayi tana kallon mu cike da farin ciki tace"Kunji abunda Mujahid yace ko. ? Muna sauraren ikon Allah."

Umma tace"Shine abun dubawa kuma shine abun godiya." Shiru ne ya ratsa gurin na minti biyu kana yace." Zan wuce ina sa meeting da ma'aikatana bayan sallahr isha'i." Umma tace"Ubangji Allah yayi maja jagora mun gode kwarai."

Da "Ameen yake amsawa ya futa daga reception din cikin tafiyar shi ta zaratan maza. Yanzu ya samu kwamciyar hankali kuma jakinsa na bashi cewar akwai nasara kan aikin da a kaiwa Mimi fatan shi ta farfado lafiya domin yanzu a zuciyarsa yaji yana yi mata wani sahihin so na gaskiya ga wani mugun tausayin ta da yake ji mussaman idan ya tuno rayuwar ta, ubanta ya gudu ta taso bata San mahaifiyar ta ba, shiyasa kullum yake jinjinawa Ummansu Asma'u uwace ita me baiwa D'a mama a yanda ya fuskanta yanda ta rike Mimi tamkar ita ta haifeta tana kula da ita sosai kular da bata yiwa 'yar cikin ta Asma'u.

Aikuwa kamar yanda Dr ya fada bayan sallahr magariba Mimi ta farko kuma sa sunana a bakin ta, take Jahidi ya zo ya kira ni.
Ina shiga dakin muka hada ido da ita. Idanunta duk sun kode sunyi ja sosai.
Kallona take yi har na karasa kusa da ita gefan bed din na zauna hade da kamo hannunta na rike tamau.
Nace"Mimi ya jikin naki."?
A hankali tace"Da sauki Habibty kice wa Jahid ya bani ruwa nasha yak'i ya bani. "
Mujahid na kalla cikin tuhuma yace." Ba yanzu za'a bata ruwa ba."

Hannuna ta rike lebanta duk ya bushe, Mimi tayi mutukar bani tausayi. Nan na zauna ina rarrashin ta, su Umma suka shigo dakin. Tunda ta ganta hankalin ta ya kwanta.
Granny kuwa fad'i take"Sannu kinji ko kishiya ta ko wace haihuwa da irin ta sai dai fatan Allah yasa Ku gama lafiya."

Dr Jahid futa yayi daga dakin ya barmu da Mimi. Hannuna na nata bacci ya kara dauke ta.
Kin tashi nayi daga gurin bare in cire hannuna daga nata har wajan k'arfe goma na dare, Amjadu ya shigo lokacin granny har ta soma gyangyadi.

Sallamar sa naji dakin gabana ya fad'i , ciki-ciki na amsa masa, domin Lokacin Umma na toilet aunt Hauwa kuma ta tafi, muryar baban su Munnu na ji sun shigo tare.

Amsawa nayi da sauri na juya INA masa barka da zuwa.
Kan Mimi ya tsaya cike da tausayi da al'ajabi yake fadin"Ashe Abunda ya faru dake kenan Mimi."
Umma dake futowa daga band'aki tace"Sannu da Zuwa."
Baban su Munnu ya juya suna gaisawa da Umma.
Nan yake jajan ta mata abunda ya faru yana kara addu'a ga Mimi tare da fadin"Sam shi bashi da labarin abunda yake faruwa in banda shi Amjad din ya fada masa a waya.

Umma tace"Alkairi shi ake fada bata tashin hankali ba, duk da dai nasan hakkin Ku ne a fada muku munyi laifi."

Baban su Munnu yace." Ya wuce yanzu babu Lokacin yin k'orafi ta lafiyar ta Muke ubamgji Allah ya bata lafiya ."

Duk wannan abun da ake gogon yana tsaye kusa da kan Mimi ya rutsawa fuskar ta kallo kamar wani maye gani a zaune bayan haka kuma ko kunyar su Umma baya ji.

Sallama Baban su Munnu yayi mana ya kama hanya ya futa Amjad din ya bishi a baya  Umma kuwa zama tayi kan wata kujera tana fadin"Ni na manta shaf ban sanya kin kira Munnu a waya kin fada mata halin da ake ciki ba, in yaso ita sai ta fadawa Baban nasu."
Nace"Wallahi nima na manta shafa."!

Granny ce ta bude ido da sauri tana kallanmu ni da Umma tace"Kaddai bacci nayi a gurin nan."? Umma tayi murmushi tare da fadin"Bacci kika yi amma bai yi tsayi ba." Mayafin ta ta gyara tana fadin"Haba shiyasa kamar a mafar ki naji muryar k'ato ya shigo ko."
Nida Umma ka kalli juna wanene k'ato kuma."? Kafin muga tunani mu ya shigo dakin hannunsa rike da wasu manya manyan ledoji.

Kusa da Umma ya aje ledojin cikin nutsuwa yace." Umma zamu tafi gida. Ga abun bukata nan insha Allahu babu matsala."

Umma tace"Godiya muke Ubangiji Allah yayi albarka a rayuwa. "
Granny mik'ewa tayi tana wa Umma sallama, shikam tuni ya futa ko kallon inda nake zaune bai yi ba, Kai sai ince tun d'azu da safe da muka hada ido dashi ban kara ganin ya kalleni ba ko da wasa
Shige da fucen sa kawai yake.
Naji dadin Wannan sauyin da aka samu ta b'angaran shi.
Ya daina samun ido zan sake sosai dama idanunsa mugun dafi ne a tattare dani.

****

Alhmdullahi Mimi kullum samun sauki take yi yau kwannmu goma a sibiti kuma Alhmdullahi jikinta yayi sauki sosai tunda tana cin abunci Mara nauyi kuma tana zuwa ko INA, kwakwaran motsine dai Dr ya hanata

Amjadu kuwa kullum sai yazo shi da granny tare da kayan ciye-ciye hummm mu dake muke jinya maimakon muyi rama muka yi kiba ta sati biyu sosai na ware ganin baya shiga harkata ko yazo gaisuwace take hadani dashi, to shima tunda yaga jikin Mimi yayi sauki baya wani dadewa yake tafiya sabgoginsa, Kullum ina cikin Ac fatata tayi luwai gashi kullum muna tare da Mujahid muna shan soyayarmu ko Amjadu yazo ya tadda mu baya nuna damuwar komai karkari su gaisa ya wuce ciki.ko a fuska baya nuna Alamun wani Abu wai don ya fanni tare da jahid ni ni kaina yanzu tunani sauayrwa shi nace tafarar daya duk wannan rawar kan da yake akaina ya daina yi, ta lafiyar matar shi yake.
To nima hakan yayi mun dad'i yanzu zuciyata ta Riga ta tsayar min da Mujahid a matsayin miji maganar mu har gaban su Kawu Yunusa domun da suka zo duba Mimi sun gaisa da Mujahid din a matsayin sa na me Neman aure na.

*****

Kwanan Mimi goma sha takwas ta warware sosai ni kuma dama tuni na koma gida saboda makaranta, take Mujahid ya sanya ranar sallamar Mimi tare da tsauraran matakai babu yawan motsa jiki da cin abun mai nauyi babu kar zurga zurga tayi yawa, shima Amjad din banda tsawwala gurin yin sex wannan sune sharadan da Dr ya shimfid'a wa Mimi.

Granny itace ta dauki nauyi komai na gidan tunda anyi anyi dani kan na dawo gidan da zama har Mimi ta haihu naki ya Umma ma babu yanda bata yi dani ba, Amjad da kanshi ya turo Jahid gurina wai ya rarrashe ni naje na kula da Mimi fafar naki nace nima makaranta, lokacin mujahid har fushi yayi dani ya daina kirana a waya, kwana uku, nima shareshi nayi na cigaba da sabgata, da yaga Uwar bari ne yazo har inda nake ni kuma a lokacin na butsare masa sai ya dinga bani hakuri muka cigaba da sosyayar mu Cikin aminci da yardar juna.

****
Tun da watan azimi ya kama yake zurga-zurga har sai da ya tabbatar komai ya kammala ta fannin company shi sosai ake aiki tare da fidda kaya samfura iri-iri abun sai son barka sosai jama'a suke tsallakowa daga garuruwa suna zuwa d'aukar kaya.

Yaduka na mussaman ya sanya company ya shirya masa mai manyan zane ko wane kusan bandur dubu aka futa dashi gidanan yari(prison)  bayan nan ya sanya aka futa da bandura na tampopi aka dinga shiga kauyi ka ana rabo, hatta da takalma sai da aka futa dasu aka rabawa mabukata.
Farkon wata kenan tsakiyar wata ma haka ne ya kasance, karshen wata ma haka.
Addu'a da fatan alkairi babu irin Wanda bai sha ba abakun mutanan gari

Yau saura kwana bakwai sallah.
Muna ta shirye-shiryen sallah. Lokacin Cikin Mimi ya futo sosai tunda yana matakin watanni shida tayi kiba sosai sa sosai kuma ta kwantar da hankalin ta.

TV muke kallo inda muke kallon tafsiri daga bakin Marigayi shak Isa Waziri Allah ya jikansa.

Kawai. Umma ta kunna redio murya wani shararan Dan jarida muka ji yana fadin"Salamu alaikum jama'ar jahar kano, labari da dumi-dumin sa, an yaka dai ta tashi yanzu-yanzu muka samu labari daga majiya me k'arfi shararar mutumin nan Wanda yayi suna a jahar kano, wato *Young millionaire Amjadu Abul Abbas mai nasara* wato  mamallakin wannan shararan company me kawo muku nauin kayan sawa kama daga atamfoffi yadiga lesuka mayafai dogwayen riguna bulawus kayan yara hijab da sauran su, wannan company mun samu labari yanzu yanzu daga bakunan wadanda suke sari a cikinsa, cewa company ya hada baki da yahudawa nasara masu yak'i addinin musulunci masu adawa da fad'ar Annabi Allah wato Annabi Muhhamadu Slw a takaice dai an samu jikin takalman da company ya ke kerawa kasan takalmi an rubuta sunan Allah da manzon sa wato Allahu Muhammad, Jama'ar gari me zaku ce da wannan shirkar da wannan yaro da kuka amunce masa ya aikata.""

"Innalillahi wa'ina ilahi raji'un shine abunda Umma take fad'a, take ta fashe da kuka tana gyda kanta take fad'in" Wannan zan sharri ne tswagaran sa na tabbatar yaron nan bazai aikata wannan danyan aikin ba."

Nima jikina wani irin shocking yake jin abunda Dan jaridar yaje fad'a, Cikin zuciya ta nace"Anya kuwa guy nan zai aikata Wannan Abu, duk da dai nasan Duk ak'idun shi na nasara ne kuma Duk yawanci abokan shi turawa ne, wata zuciyar tace min tabbas zasu iya rinyarsa dama ba wani tsoron Allah yake ba, tunda yana aikata zina." Kuka Umma take yi sosai da sosai Ya Aminu ya shigo gidan hannunshi rike da Leda me zane-zane da Lemo da a yaba a ciki.
Ganin Umma na kuka ya tabbatar labari ya same su
Umma tace"Kaji sharrin da jama'ar gari sukaiwa wannan yaron mijin Mimi ko."?
Ya Aminu ya zauna tare da sauke ajiyar zuciya yace." Duk naji Umma gashi can ko ina ana surutu zancan ya cika gari.
Matasa sun fara gazgatawa domin wani Dan kasuwa ya futo da takalma na company an duba an ga gaskiya al'amarin.
Umma tace." Karya ne sharri ne aka shirya masa ni na tabbatar.
Ya Aminu yace." Umma sai ta iya kasamcewar gaskiya ne Wallahi mutane da basa tsoron Allah, ni dama wannan uban kud'in sa suna tsorata ni, akan ya samu duniya babu abunda ba zai yi ba."
Nace"Wallahi Ya Aminu nima na gasgata saboda d'abi'un sa duk na turawa ne.
Gaskiya gomnati ta shiga maganar kuma kamata yayi a dauki mataki akan sa, domin Allah da manzon sa ba abun wasa bane."

Ya Aminu ya bude baki zai yi magana kawai mukaji ihu!!! Da hanayi ana gudu radadada!!! Da gudu nayi waje ya Aminu ya biyo ni a baya.
Gungun matasa majiya k'arfi ne suke tada k'ura ko wanne hannunsa rike da makami wasu jarkar fetur da kalamzir da tayoyi suna fadin "Billahillazi sai mun k'one company mu zai yaudara! Sai mun konashi mu kashe shi!! Mu kashe banza."!!!!!!!!!
D'uuuuuu suke wucewa sunfi su Dari ga magariba ta gabato ana shirye-shiryen shan ruwa
Umma ta tsorata mutuka fad'i take" Asma'u maza buga wa Mimi waya ta tawo gida innalillahi wa'ina ilahi raji'un. " Jikina na kyarma! Na koma cikin gida zuciya sai harbawa take yi mutukar wad'annan matasan sukayi arangama dashi to babu shakka sai sunga bayan sa, hannuna na rawa nake Neman numbar Mimi, kiran duniya taki shiga. K'afafuna na rawa na futo in na fadawa Umma halin da ake ciki.

Hannunshi rike da jarida yake zagaye parlor bashi, Rambo da doh Mimi da granny duk suna tsaye suna tararrabi da al'ajabin wannan Abu.wayoyinsa kuwa tuntuni ya sanya rambo ya kashe su, saboda a halin da yake ciki magana ma bazai iya yi ba. Shin wai me ya tsarewa mutane ne a duniya.?

Granny kuka take yi tana fadin"Wannan kaddara da masifa Allah ka ije mana ita, Ubangji kaga zuciyoyin mu bamu aiktaba Allah ka tona asirin masu San su ga bayanmu.

Granny ya rungume a jikinsa yana d'an dukan bayanta da hannunshi ya ma kasa cewa komai, idanunsa sunyi wani irin jajazur! Tsabar tashin hankalin da yake ciki.

Tv suka k'urawa ido inda suke ganin jama'ar gari kofar company sa sune turareniya da rigima da masu gadi kan lallai sai sun shifa ciki wasun su kuwa tuni sun soma k'ona tayoyi suna watsa fetur da kalanzir jikin company, ihu!  Da hayaniya ya cika gurin, 'yan jarida sai dauka suke yi. Tuni wani tsagera daga cikinsu ya k'yatta ashana ya yi wani tsalle hade da jefa ashanar sama, kafin k'iftawa da bisimillah wuta ta kama fa!fa!fa! Jikin gatangun company har ta soma haurawa ciki, hucin wuta yasa jama'a darewa kowa na gudu domin ceton ransa, ciki kuwa har da masu gadi.

Tuni matasan suka samu damar shiga ciki kasancewar gurin ya hargitse kowa na ceton ransa.
Take 'yan jarida suka rufa musu baya domin dauko rahoto.
Lungu da sak'u ko ina sai da suka bi suka watsa fetur ko zafin wuta basa ji, da gudu ma'aikatan suka dinga futowa suna kama Katanga suna haurawa domin ceton rayukansu, ganin yanda wuta take ci ne ba!ba!ba! Yasa 'yan jaridar dasu matasan suka dinga gudu suna kama Katanga suna dura kasa, duk da haka wasu sun jikkata kuma sun k'one cikinsu sudai kawai burin su ya cika ganin sun rusa company.

******

*"Hahahahahaha"* wata mahaukaciyar dariya na juyo a ofis din me girma governor, da sauri na lek'a ta k'afar mukuli, na gansu sun fi su goma zaune Cikin kujeru tsakiyar su kwalebe ne da cup reras kan wani makeken teble. Mai citta ya dauki abunda yake cikin cup din gaban sa ya kurba tare da ajewa fuskarsa cike da annuri da farin ciki, naji yana fadin"Shegen kaya! Wa yaga masa barno gabas take! Ai sai ya daina motsi a duniyar nan sannan zamu saurara masa."!! Dariya suka shek'e da ita "Hahhahahahahaha."!!!!

*****
Har aka sha ruwa yana tsaye a tsakiyar parlor babu yanda granny bata yi dashi ba kan yazo ya karya yak'i kamar ma kurma ya zama Wanda baya ji ba ya gani, kawai ya zubawa guri guda ido .Su Kansu Rambo da doh-doh sun tausayawa masa.
Mimi na kuka tazo ta rungume shi tana rarrashin sa, da sauri ya juyo jin tsinin cikin ta yana zungirin shi a bayan sa.
Tsungunawa yayi ya kasa kunnesa cikin NATA yana lumshe ido.
Kamar wani zautacce ya d'aga rigar ta yana shafa cikin nata, a hankali yace." My boy ina cikin damuwa!!!! Innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!!! Kalmar da ya kamata ya fad'eta tun farko fara abun bai fada ba sai yanzu Allah ya bashi iko.

Mimi kuka granny kuka an rasa me rarrashin wani a cikin su.

Wata irin hayagaga! Da hayaniya! Suka ji ta cika gidan.
Zumbur! Ya mike yana niyyar futa
Rambo da doh-doh suka dakatar dashi da sauri suka futa.
Gungun! Jama'ar gari suka hango suna kokawa da masu gadi dole sai sun shigo Estate din......... Rambo ya koma ciki da sauri yana fadin "Sir babu lafiy!... Kafin ya rufe bakin sa saga Mujahid da Khalid sun shigo da sauri. Mujahid yace." Meye abun yi ne? Idan fa suka shugo gurin nan zasu yi barna domin dukanin su 'yan daba ne da 'yan Sara suka."!!! Amjad yace." Ni suke nema baku ba,  zan futa su kashe ni kan abunda ban aikata ba."
Da sauri yayi nufin futa. Mimi tq buga wani irin ihu!!! Da gudu tayo kansa tana fad'in"Kar ka futa su kashe ka."!!!!!!!!! Hannunta ta mik'a tana son rik'o shi santsin tayal ya kayar sa ita ta fad'i a kan cikin ta hade da sakin wata razananniyar k'ara!
Hankalin su duk ya koma kanta suna salati,
Hakan ya bashi damar fucewa da sauri! Ba tare da ya juyu yaga me yake faruwa ba.





*23/11/2019*
[11/24, 12:07 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*61*

Wani irin nishi! Mimi take yi idanunta na lumshewa yayin da bakin ta yake motsawa tana so tayi magana amma babu hali hannunta biyu tasa ta damk'e cikinta dashi da kyar ta fad'i"Innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!!! Sharaf! Ta zube a jikin granny.
Rungume ta tayi ta fashe da kuka hade da d'ago kanta tana Neman Amjad, wayam babu Shi a gurin, da sauri ta kalli Mujahid murya a sark'e tace" Ya futa shima zasu kashe shi."!
Dukaninsu hankalin su ya dawo jikin su, take suka fara rige-rigen futa, suna salati.
Granny kuwa rungume Mimi tayi tana kuka duk basirar ta ta toshe a lokacin.

Yana futa ya hangosu sun samu nasarar shigowa, ciki dake akwai tazara mai mugun tsayi kafin su gurin shi, sai suka yanko da gudu suna ihu!
K'ik'am ya tsaya had'e da hard'e hannunsa a kirjin sa yana jiran k'arasowar su.
Mujahid Khalid da Su Rambo sun tsorata mutuka suka fara Jan rigar shi.
Fuzgewa yayi a zuciya! Yace. " Ku jira Ku ga abunda zai faru, wallahi duk Wanda yazo gurin nan to sai dai Uwarshi ta haifi wani."
Ja da baya suka yi cike da tsoro! Fito yayi sai ga DOG dinshi ya shek'o a guje! Yana wani irin haushi!!! Magana yayi masa da ido. Aikuwa sai ya buga wani uban tsalle ya tunkari su yana wani danbanzan zufa ya cafki k'afar daya daga cikinsu sai da ya huda ta tukkuna ya sake shi. Kafin kace kwabo ya fad'i a gurin yana nishi ga jini ya fara zuba.
Wani tsagera ne ya kawo sharb'eb'iyar wuk'ar zai  dab'a masa, da sauri yayi sufa ya datsa masa hak'oran sa a fuskar sa, dai-dai hancin sa, ya yago Innalillahi sai ga rabin hancin sa da naman  kumatun sa a bakin DOG din. Kwanciya yayi a gurin yana ihu! Shi kuwa Amjad nad'e hannun Riga yayi ya tunkare su, yana wani zare idonsa!
Tsoro ne ya shige su dukanin su ganin yanda dog din yake barna har ya jikkata mutum biyar gasu nan a kwance a gurun.
Take suka fara guduwa domin ceton ransu.
Amjad ya buga musu wata irin tsawa! Tare da fad'in"Ku tsaya mana ku kashe ni kamar yanda kuke bukata."!!! Ko juyo wa basu yi ba, gudu kawai suke su Isa bakin gate.
Daga murya yayi sosai Wanda sai da gurin ya amsa yana magana da masu gadi cewar maza su rufe gate din nan, kar su bar kowa ya futa."
Aikuwa suka mike da kuzari suka ja gate din da k'arfi suka datse
A nutse yake tafiya hannunshi goye a bayan shi, fuskar sa a murtuke ya k'araso gurin su: One by one yake kallonsu tsawon  five minutes, murmushi yayi mai ciwo yayi gyaran murya gami da gyad'a kansa har sau biyu murya sama! Yace." Kun shigo da shirin aika ni barzahu ko."? Shiru su kayi suna muzurai! Gefe guda kuma ga *Tegar* na wani irin haushi!!!!! Shiru suka yi........ Ya cigaba da cewa"Zaku kashe ni kan abunda kuke zargina dashi, Wanda ni nasan ban aikata ba hakane ko ba haka bane."?
Sunkuyar da Kansu suka yi cikin mutuwar jiki. Girgiza kansa yayi cikin takaici da tsabar bakin ciki yace." Gani ga ban Ku Ku kashe ni, ni Ku kashe banza kamar yanda kuke fad'a. "! Tsit! Suka yi.
Yace." Duk Ku aje makaman hannun Ku."
Aikuwa suka aje da sauri!
Yace." Kuna so Ku kashe ni Wanda baku San in kuka aikata haka ba, to babu shakka hukuma zata dauki mataki akan Ku, tunda ba ita ta sanya Ku ba,hakane ko ba haka ba."
Duk suka ce "Hakane."! Yace." Duk abunda kuke zargina dashi ban aikata ba, sharri ne kawai, akai mun. "
Shiru suka yi ya cigaba da cewa"Kuma Ku zuba ido zaku ga irin hukunci da za'a dauka a kaina, tunda dai kun k'one company na kunji dad'i shikkenan, amma babu shakka sai na binciko Wanda aka had'a baki dasu aka kullamin wannan k'azafin." Duk sai suka ji jikin su ya mutu, take suka zube suna bashi hakuri.

Murmushi yayi yace." Ba wai na fad'a muku Wannan maganar ba ne domin Ku yarda da ita, A'a duk wani hukunci da zaku yanke kaina Ku yanke Ku kashe ni ku kashe banza."!
Ya fada da wani murmushi a fuskar sa, na tsantsar takaici.

Hakuri kawai suke bashi cikinsu kuwa har da masu kuka saboda tausayin sa. Yace." Mutukar nakama mutanan da aka hada baki dasu cikin ma'aikatana tom ni da kaina zan hukunata su da kaina in yaso nima a kashe ni saboda kishin Allah da manzon sa." Ya nagama maganar shi ya juya bayan ya bada umarnin a bude musu k'ofa su futa.
*Tega* ya bishi a baya Yana shinshina m asa jiki: Wani irin salati Granny take yi,lokaci kank'ani jikinta ya kama rawa ganin wani irin jini yana malalowa k'asa daga jikin Mimi.
Kuka ta fashe dashi tana salati ta janye Mimi daga jikinta
Ta mike Da sauri ta nufi kofar futa.
Karo suka buga dashi ya shigo.
Hannunsa ta rike takasa cewa dashi komai sai dai nuna masa gurin da Mimi take kwance take.
Da sauri ya kalli gurin, jini duk ya kwaranya kan tayal din gurin. Wani irin ihu! Ya kurma! Ya saki granny da gudu ya k'arasa gurin Mimi ya dauke ta kamar zautacce yake kiran sunan ta"Momy na."!!!!!!! Ina Mimi bata San wace duniyar take ciki ba, da gudu ya futa daga Palo, mota ya nufa da gudu su Rambo dake tsaye suka bishi, Mujahid ya bude motar da sauri ya shiga mazaunin dravar, jiki na rawa Rambo ya bude masa mota ya shiga rungume da Mimi a jikinsa jini duk ya b'ata shi har ila yau bai daina zuba ba.!!

Da gudu Jahid ya figi motar masu gadi suka bude gate din tun kafin motar ta karaso. Wani irin gudu Jahid yake yi kamar zasu tashi sama, Allah yasa titi akwai saukin motoci kasancewar kowa na gida an sha ruwa an gaji wasu kuma na massalaci suna sallahr tarawi.

Rungume da Mimi yake yana tofa mata duk addu'ar da tazo bakin sa, wasu zafaffan hawaye ne su ka fara zuba a kuncin sa Amjad jarumi ne da kafin kaga kukan sa a duniya sai ka manta ko da iyayansa suka mutu bai yi wani kuka ba, yanzu tsananin tausayin Mimi da irin azabar da take sha akan soyayyar sa yasa shi zubar da hawaye masu zafi, matseta yayi sosai a jikinsa yana tuno maganar ta ta d'azu lokacin da zai futa *"Kar ka futa su kashe ka."!!!!* Innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!!! Abunda ya fada a fili kenan hawaye na zubo mishi wato shi irin tashi kaddarar kenan.

Tun kafin su karasa hospital din Jahid ya kira waya cewar su futo da gado ga emergency nan, aikuwa suna shiga ciki da sauri wasu mata ma'aikata suka turo gado na d'aukar marasa lafiya, ya bude motar da sauri ya zagayo ya budewa Amjad din dake ruk'unk'ume da Mimi dake cikin halin rai da rayuwa.
Futowa yayi ko kallonsu bai yi balle ya saurari abunda suke CE masa, Mimi na rungume a jikinsa ya wuce su. Dr Jahid ya bishi a baya, suna nurses din suka rufa musu baya da sauri.

Likitoci kusan biyar kan Mimi ciki kuwa har da Jahid din sun dukufa domin ceto rayuwar ta.

Yana zaune a reception ya hade fuskarsa da tafukan hannayen sa, kwata-kwata baya so ya bude idonsa ganin irin kallon da jama'ar gurin suke masa, wato yanzu ya zama abun kallo kenan? Tsoron sa d'aya kada Allah ya kawo 'yan jarida gurin, yasan sai sun fed'e biri har hutsiyar ta.
Aikuwa Ko minti talatin bai yi da zama a gurin ba suka shiga su uku. Daya daga gidan redio daya daga gidan television daya kuma daga gidan jaridar Gaskiya dokin k'arfe
Kewaye shi sukayi suna gyara kayan aikin su, ya d'ago kanshi Yana kallon su da idanunsa wanda sukayi wani irin ja!! Babu fargaba a tare dasu tunda a kan aikin su suke .
Daya daga Cikin su yace." Ranka ya dad'e me zaka ce game da zargin da mutane suke maka."? Shiru yayi musu yana binsu da kallo
D'ayan yace." Kuma muna son karin baya ni daga bakin ka, shin zargin da ake maka cewar ka had'a baki da yahudawa domin Ku tuzarta Allah da manzon shin hakane."?
Amjadu yaji wani k'aton bakin ciki ya tokare masa a mak'ogwaro shiru yayi bai ce musu komai ba, kallonsu kawai yake kamar zautacce.! D'ayan da bai yi magana ba shine yace." Ranka ya dade jama'ar gari sun ci alwashin sai sun kashe ka kan abunda ka aikata sai sun k'one gidan ka sai sun k'one company ka, sai sun kona ka, yanzu dai sun samu nasarar k'one company ka kurmus! Ta inda babu wani Abu da zaka Mora a cikinsa, abun mamaki da daure kai kuma sunyi zanga-zanga sun je har inda kake sun kasa aikata Abunda suka yi niyya, gashi kuma yanzu mungan ka a hospital cikin halin damuwa da d'imuwa ran ka ya Dade muna bukatar garin haske a gurin ka.

A jiyar zuciya ya sauke ya mike tsaye da sauri! Suka fara kara masa lasifikar su a bakin sa,
Sunkuyar da kansa yayi kasa hade da soka hannunwan shi duk biyun cikin aljihun wandon dake jikinshi yace." Alhmdullahi Allah ne abun godiya a halin yanzu." Shiru ya rasa gurin, ga 'yan kallo duk sun nutsu
Ya cigaba da cewa"Ban yi niyyar magana daku ba amma dole tasa zan fad'i Abu guda akan wannan k'azafi da akai min, cewar  ni *Amjadu Abul Abbas* zan tsaurara bunkice akan mutanan da suka shirya min wannan sharrin, mutukar na kama su, babu shakka dani dasu za muyi kare buri jini dasu, domin sai dai a dauki gawarsu ko a dauki tawa, ni *Amjadu* bana had'a Allah da ma'aiki da kowa, Wallahi wallahi sai dai idan na kashe su hukuma ta kashe ni, duk Wanda zai yi wasa da Allah da manzo to tabbata barin sa a ban duniya shirka CE,idan ban kashe su ba, I promise Sai na raunatasu! Sai na jikkatasu! Sai na sassab'a musu kamannii!!!!!, wannan shine magana ta."!!!
Ya fada yayin da yake wata irin zabura!!!!
Dan jarida d'aya yace." Ranka ya Dade shin baka jin ciwo da bakin ciki akan b'arnar da akai maka, gashi duka duka company ka ko shekara guda bai yi ba shin yake jin zuciyar ka a wannan lokacin."?

Girgiza kansa yayi ba tare da wata damuwa ba yace." Company na da suka k'ona bai min ciwo ba, da sun barshi ma ni da kaina zan zazzaga masa fetur in kona shi, saboda bashi da amfani a gurina, company da ya tara miyagu marasa tsoran Allah a ciki barinsa babban hadari ne, naji dad'i mutuka da suka kona shi. " ya k'arasa maganar sa yana futo da hankici daga aljihunsa ya goge fuskarsa.

Daya Dan jarida ne yace." Ranka ya Dade sai tambaya ta k'arshe kayi hakuri muna son muji me ya kawo ka asibiti gashi dai a zahiri jikinka babu ko kwarzane babu jini balle ace ko daga gurij mutanan da suka kai maka har....... Kafin ya karasa maganar shi ya katse shi ta hanyar fadin"My wife dina tana ciki cikin halin rai da rayuwa duk ta dalilin wannan ibtila'in babu abunda zan ce sai dai Allah Ubangji ya saka mata ga dukkanin mutanan da suka shirya faruwan hakan.""""""Yana gama maganar shi ya maida hannun sa fuskar sa ya rufe ruf! Yana kukan zuciya
Duk wani mai imani da tausayi a lokacin zai tausaya masa mata masu rauni tuni sun soma zubar da hawaye, jiki a sanyaye 'yan jaridar suka masa sallama suka futa.

Dukanin abunda yake faruwa bamu da labari mun dai ji labarin yanda mutanan gari suka k'one company ya Aminu ya kawo mana video mun gani a wayar abokinsa garba har yanzu Umma kuka take yi tana tunanin wane irin hali Mimi take ciki dashi kanshi Amjadu din, domin da har ta dauki mayafi zata futa Ya Aminu ya hanata da sauri yaje ya kulle kofar waje da kwado domin rigima muke da ita wai sai ta futa taje gurin su Mimi.

*****
Yana zaune a gurin shi kadai sai gilmawar nurses da d'aid'aikun marasa lafiya da suke shigowa asibitin.
A gogon hannunsa ya kalla K'arfe goma shaura, cikin tararrabi da tsinkewar zuciya ya mik'e tsaye yana kallon room din da aka shiga da Mimi ciki.
Kai tsaye ya durfafi d'akin baya ko kallon gabansa.
Karo suka buga da Jahid ya futo daga dakin hannunsa sanye sa safa, duk ta b'aci da jini.!! Wani kallo yayi masa yana bin hannunsa da kallo cikin fad'uwar gaba.!
Jahid ya gyara yanayin fuskar sa, cikin rashin kuzari yace.''tana bukatar jini cikin gaggawa."!! Amjad kokari yake ya bangaje Jahid ya shiga dakin.
Jahid ya tare hanya cikin sigar rarrashi yace." Colm down Aboki tsaya ka saurare ni tukkuna." Cikin  damuwa da fargaba yace." Muje ka sanya mata nawa jinin kar Ku kashe min matana."!!! Muryar shi na kyarma ya k'arashe maganar tasa."

Jahid ya rike hannunsa ba tare da ya damu da jini da. Yake hannun nasa ba ya damk'e sosai yace." A halin yanzu bani da masoyi sama da ita bani da kowa sai ita da abunda yake Cikin ta sai granny su kadai suka rage min a duniya my friend bana so in rasa Momyna."!!!!! Tsabar tausayi ta hana Jahid cewa komai ya ja hannunsa suka shiga wani d'aki.

A gigice Ya Aminu ya shigo gidan Hannunsa rike da wayar Garba abokisa.
Kamar dai d'azu da ya shigo mana da ita, duk ya rasa inda zai tsoma ransa, ya mik'o min wayar bakinsa na kyarma yakasa cewa komai
Hannu na rawa na fara dubawa
Farko abunda na gani ya sani kurma wani ihu na jefar da wayar hanna hannu na d'ora aka ina fad'in "Innalila wa'ina ilahi raji'un, shikkenan sun kashe mana Mimi mu."!!!!!!
Umma ta dauki wayar da sauri tana dubawa, Mimi ce rungume a hannun Amjadu lokacin da suka shiga asibitin nasarawa abunka da mutumin da yayi suna a duniya aka samu wasu suka dauke su vedio a wayoyin su, a lokacin suka fara turawa Media hade da sharhi cewa jama'ar gari sun shiga har gidan *Young millionaire* sun Sassari matar shi mai dauke da ciki Dan wata shida gashinan tana halin rai da rayuwa.!
Abunda ya k'ara tayar mana da hankali shine yanda mu ga jikin Mimi dashi kansa Amjadu din duk ya b'aci da jini duk da cewar dare ne amma akwai hasken fitulu a ko ina na asibitin.
Umma ta mik'e tsaye cikin tawakkali ta kalli Ya Aminu da yayi tsaye a gurin duk ya rasa me zai yi tace" Muje mu gani Aminu Mimi tata kaddarar kenan, bawa baya wucewa kaddarar sa, muje idan ta mutu ne sai mu karbo gawar ta."

Hawaye Ya Aminu ya share ya futa daga gidan da sauri domin samo abun hawa.
Ni da Umma muka futa daga gidan kamar wasu zautattu! Shi kanshi hijab din dana sa a baibai na sanya shi, hawaye ne kawai yake zura ra a idona shikkenan Mimi sai ta Allah a yanda na ganta ina gani kamar kafin mu Isa a sibitin za'ace ta mutu.





*24/11/2019*
[11/25, 8:46 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*


*62*

Lokacin da muka Isa asibitin goma da rabi ta wuce, Dan dai ma daran azimi ne akwai jama'a a bakin asibitin suna siye da siyarwa, har ciki mai a dai-dai ta sahun ya shiga damu, Ya Aminu ya biyashi kud'in sa, ni kam tuni na Dade da futowa daga a dai-dai sahun sai kyarma jikina yake yi.

Ko da muka shiga ciki babu mutane sosai wasu kujera muka samu muka zauna. Ya Aminu ya nufi wani d'aki da sauri.
Waya ta dake hannuna na kunna na fara Neman numbar Jahid, sai da na kira sau biyar a kashe, cikin mutuwar jiki na aje wayar a cinya ta, Ya Aminu ya futo daga dakin da ya shiga ya nufo mu, fuskar sa babu walwala
Gaban Umma ya tsaya yace. "Yanzu wata nurse take min bayani cewar Mimi tana ciki har yanzu ba'a futo da ita ba, kuma abun mamaki na dauka zamu samu mijin nata anan gurin bab........ Kafin Ya Aminu ya rufe bakin sa, Jahid da Amjadu sun futo daga wani d'aki. Da sauri Jahid ya k'araso gurin mu. Shi kam Amjad yana tsaye a gurin da yake.
Jahid ya kalli Umma tare da fadin" Ashe har kun samu labari."
Umma tace"Ba dole ba wannan tashin hankali dai Allah ya sawwake, mana shi, yanzu ya jikin Mimi yake. "!!?
Jahid yace." Jikinta Alhmdullahi Umma ku kwantar da hankalin Ku, jini ake bukata sosai za'a kara mata saboda ta zubar da jini sakomakon fad'uwar da tayi."

Mik'ewa nayi zumbur nace"Muje ka sa mata nawa jinin kaji Don Allah ka cece rayuwar ta." Murya ta na rawa na k'arashe maganar.

Jahid yace." Dole haka za'ayi muje a dauka a auna mu gani, idan yayi dai-dai sai a d'aura mata yanzu ma an d'ibi na Amjadu ne."

Kallon shi nayi dake tsaye kamar wani maraya sai ya bani tausayi mutuka wata zuciyar tace ba abun tausayi bane mutumin nan.

Wani daki muka shiga da Jahid ya dauki jinina ya duba yayi dai-dai Dana Mimi take ya umarce ni na kwanta kan wani gado  domin ya dauki jinin.

Amjad kuwa jingina yayi jikin bango hade da lumshe idonsa Sam ya kasa zuwa ma ya gaishe da Umma saboda halin masifar da yake ciki.....Muryar Granny yaji ta shigo gurin cikin kuka take fadin"Sai da tace kar ka futa kar ka futa ka futa gashi da ka futa ka dawo sumul k'alau! Da kai ita kuma saboda tsananin son da take maka,  ta fadi kan cikin ta."!
Komai a kunne magangan da granny take yi domin dakin da nake ciki a bude yake, Jahid na kalla Ina daga kwance nace "Nasan kasan dukanin abunda ya faru don Allah ka fad'a min komai."?

Ba tare da tunanin komai ba Jahid yace." Wallahi Asma'u tsautsayi ne ya afka kan Mimi lokacin da abun ya afku, tana hana Amjad din futa saboda jama'ar garin da suka kawo masa hari har gida, garin kokarin rik'o rigar sa, kawai santsi ya kwashe ta ta fad'i kan cikin ta to shine fa take ta zubda jini, amma insha Allahu zata dawo normal.
Murya ta a cunkushe nace"Kana nufin ya sane ya futa bayan tace masa kar ya futa yanzu me futar tashi ta jawo mana, ai dai gashinan da kunnen ka kaji Abunda kakar shi take fad'a ko." ? Jahid ya sauke ajiyar zuciya tare da fadin "Tsautsayi fa baya wuce ranar sa, don Allah mu bar maganar bana so Ku Dora alhakin abun kan shi." Shiru nayi ganin ranshi ya b'aci Jahid yana da saukin kai da dad'in mu'amula amma baya son musu da taurin kai shiyasa nayi shiru kawai amma cikin zuciya ta nayi alk'awari sai na fad'awa guy nan magana a kan Mimi komai daran dad'ewa kawai don yaga tana da hakuri sai ya dunga gara ta kamar gare-gare kullum cikin damuwar sa, da bata mata rai.

Jini Leda biyu a kauda a jikina nan Jahid din yace min na kwanta kan gadon na huta mintuna talatin, INA kallon shi ya futa daga d'akin. Granny ce ta fad'o  dakin tana kuka tana  k'ara tisa maganar da abunda ya faru. Fad'i take "wannan yarinya Ubangiji Allah ya tashi kafad'unta amma babu shakka tana shan wahalar rayuwa. " Shiru nayi mata kawai ina bin ta da kallo.
Amjadu masjid ya nufa domin yin sallah istigufari kawai yake a fili da Cikin zuciyarsa. Ta shi nayi jikina babu kuzari na futo daga dakin, har yanzu su Umma na zaune cikin sauraron hukuncin Ubangiji, kusan awa guda da shigar Jahid dakin da Mimi take ya futo, kallon mu yayi ya kalli a gogon hannunsa sha biyu na dare saura minti ashirin, futa yayi ya nufi gurin Amjad dake cikin mota
Amjad yace." Ta farko ko."? Daga kai Jahid yayi a hankali yace "Alhmdullahi ta farko kuma munyi nasarar tsayar da jinin insha Allahu an sanya mata, shi gobe dole za'ayi scanning din cikin domin ganin wane hali yake ciki.
Sunkuyar da kansa yayi cikin tawakalli yace." Allah ya kaimu lafiya Jahid ina cikin halin damuwa ina bukatar rarrashin." Kafadunsa ya dafa yana rarrashin sa da kalamai masu sanyi.
Amjadu Rambo ya sanya ya je can *Mai takobi* ya  karb'o nau'i kan abunci da abun sha, duk ya sanya ya shiga dasu gurin mu, tsabar damuwa da fargaba bata bari munci komai ba, ko da asubah ruwa kawai muka sha fafur abunci yak'i samun shiga a gurin mu, Ya Aminu dama ya tafi gida ni da Umma ne kawai sai granny

Ko da muka yi sallahr asubah bamu koma ba, muna zaune daki daya muna jiran hukuncin ubangji, granny na zaune kan dadduma da carbi a hannu Umma na kwance gefan ta. Itama dai carbin ne a hannunta tana ja, cikin damuwa, ni kam ai fad'ar halin damuwar da nake ciki sai a hankali, a Dan baccin da ya kwashe ni ne nayi mafarkin gani ga Mimi a tsaye a wani gurin tana sanye da wasu fararan kaya duk jikinta fuskar ta dauke da wani irin annuri ta kara haske mutuka, hannu nake mik'a mata tana mik'o min NATA hannun tana min murmushi, so nake in kamo hannunta na kasa gani dai a kusa da ita amma na kasa kamo hannunta, gani nayi ta juya da sauri ba tare da tace min komai ba ta fara d'ago min hannunta kafin in Ankara na nema ta na rasa. Ni da kaina na fassarawa kaina wannan mafarkin tabbas Mimi zata yi nisa da rayuwar mu Mimi zata yi nisa damu. Shine fa tunda na tashi na kasa sukuni ina kwance kan wani k'aramin gado nayi lamo wasu irin hawaye masu zafi suna zubo min.

*****

K'arfe bakwai dai-dai Jahid ya shigo a sibitin cikin mota ya tadda Amjad yana bacci a zaune ya bashi tausayi mutuka ya kalli su Rambo dake tsaye jikin motar yace."Kar Wanda ya tashe shi Ku k'yale shi ya samu bacci shima Hutu ne. A gurin shi."
Gyada kai suka yi alamun sun amsa.

Kai tsaye dakin da Mimi take ya nufa, lokacin mu bamu futo ba, shiyasa bamu ga zuwan shi ba, abun mamaki yana shiga dakin yaga  nurses tsaye a kanta d'aya na goge mata baki daya na kokarin gyara gadon, yaji dadin yanda ya same ta, gaisawa yayi dasu, suka futa da sauri, shi kuma ya kalli Mimi fuskarsa a sake yace." Madam ya jikin ki."? A hankali tace"Da sauki." Yace." Me  kike ji yana miki ciwo a jikin ki."
Cikin ta ta nuna da hannunta." Yace." Kiyi hakuri zaji sauki insha Allahu." Mimi ta gyda kanta, gurin yayi shiru na minti biyu dago kanta tayi, cikin sanyin murya tace"Sun kashe shi ko."!!!? Jahid ya girgiza kansa alamar a'a saboda ya San ko wa take nufi.... Bude baki tayi zata yi magana yace." Ko in kira miki shi ne."? Gyada kanta tayi, ya mike da sauri ya futa, lokacin mun futo, muna zaune a wasu kujeru, granny ce ta tare shi tare da fadin"Kai Mujahid ka futo zigwi-zigwi ko kallon mu naka yi ba kun barmu cikin alhini da tashin hankali ko."
Jahid shiru yayi mata kawai ya futa.

Mik'ewa tayi tana gyara d'aurin zanin ta tace"Ku tashi mu shiga ciki muna da kafafunmu sai anyi mana iso Ku muje muga halin da take ciki baiwar Allah."
Aikuwa bayan ta muka bi, ni da Umma. Mimi na zaune kan bed kanta a kasa hawaye na zurarowa a kuncin ta kuka take sosai, muka shiga, da sauri naje na rungume ta, tare da fashewa da kuka INA fadin "Mimi ALLAH ya saka miki dukanin Wanda ya cuce ki." Rungume ni tayi tana kuka sosai.
Umma da granny suka k'araso gurin suna rarrashin mu, mussaman ita Mimi din. Zama nayi kusa da ita hannuna cikin NATA, Yanzu zuciya ta tayi sanyi sosai na yarda mafarki karya ne tun daga Mimi zaune a gaba muna magana da ita..... Dakin suka shigo hade da sallama. Tunda nayi masa kallo guda na dauke kaina ina mamakin yanda hallintun sa suka jurkita mutum Dan gaye Dan kwalisa mai kudi mai kyau mai jiji da kansa amma lokaci guda kamanin sa duk sun sauya ya fyade lokaci guda, fuskarsa Tayi fururu, shi kanshi takalimin dake k'afafun shi na wanka ne, kayan jikinsa ne kawai masu kyau.
Kai tsaye gurin Mimi ya nufa ya zauna kusa da ita inda bayana da nashi ya kusa haduwa sai nayi saurin mik'ewa daga gurin, na koma kusa da Umma na tsaya, shi da Mimi kallon juna suke yi sun kasa magana shine ma yayi k'arfin halin fadin "Momy ya jikin ki hope yanzu ba kyajin ko wane irin ciwo ko."? Gyada kanta tayi har yanzu hawaye bai daina zuba mata ba.
Sosai yake rarrashin ta da kalamai masu dad'i ko kunyar Umma baya ji har sai da yaga ta saki tana dariya sannan ya daina shima ya saki jikinsa sosai ana hira dashi sama-sama shi da Umma granny na sanya musu baki.
Kimanin Rabin a wa yayi ya mike tare da fadin zai je gida yayi wanka zai dawo bayan sallahr azahar. Sallama yayi wa su Umma ni bishi da wani mugun kallo na tsana da kyama ji nake bani da babban makiyi a duniya karma shi saboda guy a fiye son kanshi a duniya.

*****
Takardar scanning ta futa Dr Jahid ya shiga damuwa sosai da yaga abunda yake faruwa wato baby girl dake cikin Mimi ta juya ma'ana kwanciyar ta ta sauya daga inda ake bukata tana zaune daram! Cikin Mimi gashi cibiyar ta ta nade mata wuyan ta, amma tana rayuwa a haka Cikin hukuncin Allah, lafiyarta lau, cikin ya nuna wata shida da kwana takwas wato ya shiga wata na bakwai duk wasu hallitu ubangiji ya gama abun shi, wahudun kahar  Dole ya kwantar da Mimi a asibiti domin kula da cikin ta da ranar haihuwa, domin kar hankalin su ya tashi ya sanya yak'i fada musu abunda yake faruwa ganin yanda duk suka saki jikinsu har shi Amjad din da ya dakatar da komai na rayuwar sa, yanzu ta lafiyar matar sa yake.

Ko da ya fada musu maganar bata gado basu kawo komai ba, har shi Amjad din ya yarda saboda Jahid din yace masa yana so Mimi ta samu cikkakiyar kulawa har ta haihu, shiyasa ya yarda da hakan.

Kwananmu bakwai a sibitin  Mimi ta warware sosai babu inda bata zuwa, domiin Jahid cewa yayi muna futowa da ita tana zurga zurga saboda shi yana gani kafin lokacin haihuwar tata kwanciyar baby ya dawo dai-dai kamar yanda ake so.
Ganin ta warware sosai ya sanya na tafi gida saboda makaranta Mimi bata so tafiya ta ba amma da na rarrashe ta na kawo mata misalai sai ta hak'ura.

Umma da Granny ne suke jiyyar ta sai Ummansu Munnu dake zuwa kullum tana kawo musu abunci bayan an sha ruwa, duk da cewa Amjadu yana iya bakin kokari su akan su, komai sai ya sanya an kawo musu na ci da bukatar rayuwa.

Ni ma ina zuwa amma ba kullum ba, watarana idan muka taso daga makaranta ni da Munnu sai mu wuce aikuwa Mimi tayi ta murna, ranar yini muke ni da Munnu muna sanya ta motsa jikin ta, kamar yanda Jahid ya fada.

Yau sati na guda da barin asibiti Wanda yayi dai-dai da satin Mimi biyu a asibitin kuma yau sallahr saura kwana bakwai sati daya kenan. Ranar juma'a ne na tashi da wani irin mutuwar jiki. Naji bana son zuwa skull din, cikin sauri na shirya jikina na bar gidan, kai tsaye asibitin nasarawa na nufa, duk sunyi mamakin ganina lokacin makaranta nace musu yau baza ni ba, muna tsaka da hira Mimi ta mike ta shiga toilet din dake cikin dakin. Minti biyu naji ta kwalamin kira, da sauri na bude band'akin na shiga ina fadin"Menen..... Kafin in karasa naga jini jazur nabin kasan gurin gata a tsugune ta rike kan famfo na toliet din tana cije bakinta cikin azaba ta rike Cikin nata tana ynukurin tashi tsaye amma ta kasa
[11/25, 7:38 AM] BintuUmarAbbale: Hannun ta na rike ina kokarin mikar da ita tsaye abun ya gagara, babban abunda ya bani tsoro da ita shine yanda naga jini na zuba da sauri na fita na kira Umma ta shigo taga halin da ake ciki, itama hankalin ta ya tashi tace"Maza ki karawo Jahid din zubar jini na da matsala  futa nayi da sauri kafafuna na rawa, Granny tana tambaya ta menene? Ko juyowa banyi ba, Ina kokarin shiga ofis din ne shi kuma yana kokarin futowa muka buga karo dashi, dauke kaina nayi daga kanshi ina kokarin shigewa, tunda ya ganta a d'amauce ya tabbatar akwai matsala da sauri ya fada dakin da Mimi take, dama zuwan shi kenan asibiti ya tsaya ofis din Jahid domin su gaisa, yana shiga yaga granny tsaye kofar toilet tana fadin"Kama ta Ku futo a hankali, kai amma dai jinin yayi yawa likita yazo ya duba ta." Granny yake kokarin bugewa yana kutsa kai ban dakin inda Umma take kokarin mikar da Mimi ta kasa ko da d'aga k'afarta guda d'aya, da sauri ya mik'awa granny wayoyin shi ya tartare hannun rigar shi, ba tare da damuwar komai ba ya d'auki Mimi hankalin sa duk a tashe ya futo da ita jikinsa duk jini hakanan itama doguwar rigar dake jikinta sharkaf take da jini. Hannunta ta mik'a ta kamo wuyansa tana lumshe ido dishi-dishi take gani. Ya kwantar da ita da sauri ya futa daga dakin, Jahid da Asma'u ya ci karo dasu, sai yayi saurin koma wa dakin, shi kuwa Jahid ganin jikin Amjad din da jini ya tabbatar masa da akwai matsala, aikuwa suna shiga dakin suka tadda Mimi tana wani irin buge-buge kan bed din tana wani cije bakin ta ga idanunta sunyi sama sun k'afe fari tas!! Da su. Innalillahi wa'ina ilahi raji'un " Shine Abunda Jahid ya fad'a ya futa daga dakin da saurin tsiya, mu kuwa rifuwa mukayi kanta Umma addu'a kawai take tofa mata, ni kam baki na ya kulle a lokacin kallon ta nake kurrum tana buge-buge na rasa wane taimako zanyi mata, a takaice ma da naji ina Neman fad'uwa sai na zube a gurin ina fad'in "Innalillahi wa'ina ilahi raji'un." Amjad hannunta yake kokarin rikewa abun ya faskara domin yau duk k'arfin sa Mimi yafi shi, kokarin fadowa take daga bed din yayi saurin tare ta ta fad'i jikin shi, har ila yau ba daina cije-cije da take ba.

Likitoci kusan biyar ne suka rufu a kan Mimi domin ceto rayuwar ta suma sun tsorata da al'amarin kuma yayi musu bazata lallai ubangji Shahidi ne kuma shine yasan gaibu kana taka Allah na tashi, duk iya bunkicen su a kan Mimi bai nuna musu wata alamar na cewa zata yi jijjiga ba, amma dake Allah Allah ne ya saukar da hukuncin sa kan baiwar shi, a war su biyu a kanta suna kokarin shawo kan Matsalar da tsayar da jinin da yake zuba Abu ya fassakara, Wanda a wannan lokacin Mimi ta amsa kiran Ubangji dukanin su sun tsorata mutuka duk da suke likitoci suna ganin irin wannan tashin hankali amma al'amarin Mimi ya girgiza su, Dr Faruk ya lura cikin na na motsi take suka shirya   yi mata CS domin a Ciro abunda yake Cikin tunda da ran shi.
Jahid daure wa yake akeyin aikin dashi, zuciyar sa nacan tunanin ya za'ayi ya Sanar da Amjadu wannan mummunan labarin. Cikin hukuncin Allah suka samu nasarar ciro baby girl 'yar wattani bakwai ba sati d'aya, yarinyar 'yar mitsitsya da ita, tana cikin koshin lafiya take suka sanya ta Cikin kwalabar su, da aka tana da domin irin su, suka kimtsa gawar Mimi , cike da alhini da tausayi suka futo
Da Amjad suka yi karo tsaye a kofar dakin dasu ke, Jahid yaji gaban shi na fad'uwa, hannunsa yaja suka shiga ofis din sa.
Amajad yace." Jikina na bani bazan ji alkairi ba daga gare ka, kawai ka fad'a min menene? Domin fuskar ka ta nuna alamun damuwa." Babu wani kwane-kwane da b'oye-b'oye domin dole ya Sanar dashi hakkin shi, yace." Allah yayi wa Mimi rasuw..... Kafin ya karasa ya d'aga masa hannu da saurin! Yace." Kar ka k'arasa min naji."!!!!!!! Jahid ya mike daga inda yake ya zauna kusa dashi da kalamai masu taushi yace." Ubangji shine ya hallice ta a sanda yaso babu tsammani kuma a karb'i abunsa a sanda yaso kar ka manta dani da kai duk zamu je inda Mimi taje komai daran dad'ewa mutuwa riga CE, aya ce ga dukanin wani musulmi Mimi tayi sha hada ta mutu ta farkin haihuwa addu'a zaka yi mata."!!
Hannun Jahid ya rike tamau! Leb'anshi na rawa haka zalika jikin shi na wani irin tsuma yace." Innalillahi wa'ina ilahi raji'un. "!!!!!!!!! Jahid ya dinga dukan kafad'un shi alamun rarrashin yana tausar zuciyarsa da kalamai masu sanyi, d'ago idonsa yayi Wanda suka zama kamar Jan gauta bakin shi na rawa yace." Muje a shirya min gawar Momyna  ayi mata suttura."!!
Jahid ya mike tare da shi suka futa kai tsaye dakin dasu ke aje gawarwaki suka nufa, tuni an daure Mimi guri guda tana kwance sambal kan wani siririn gado an lullub'e ta da wani farin zani, fuskar ta ya bude, yaga tayi kyau sai murmushi take kamar yayi mata magana ta amsa, zubewa yayi jikin gado yana sakin wani irin kuka. Tare da fad'in"Momyna Allah ya jikan ki, halin ki nagari ya biki, Momyna na hafe miki insha Allahu kece Uwar gida na a aljannar Fiddausi."!

Jahid na tsaye yana kallon shi cike da tausayi da alhini, mik'ewa yayi hade da sanya tafukan hannayen shi ya shafe fuskar shi, ya kalli Jahid din a dake yace." Muje." Jahid ya bishi a baya suka futa.
Ko da ya shigo dakin da muke bai yadda ya had'a ido da kowa ba yace." Zamu je gida yanzu Jahid ya bamu sallama."
Granny da Umma ba yara bane balle maganar sa ta shige su Granny tace"Kai k'ato bana son kumbiya-kumbiya kawai ka fad'a ma kome yi mu 'yan Adam ne zamu dauki kaddara rufewar bata da amfani, shin ya jikin Aishatu ne."? Yana kokarin futa yace." Allah ya amshi ta." Wani irin ihu! Na kurma had'e da bin bayan sa a guje, ina kokarin taddashi tafiyar mu ba d'aya bace ina kuka nake fad'in"Karya kake mugu azzalimi sai dai idan Kaine ka kashe mana ita, idan hakan ta kasance sai na dauki fansa."!!!!!!! Ko juyowa bai ba, ya shiga wani daki, kokarin binsa nake wasu nurses suka rirrike ni suna bani hakuri, wani k'arfi ne ya zo min a lokacin na fuzge daga jikin su sai kace wata mai iskokai na afka dakin a guje! Abunda na gani ya sani jin wani irin jiri tuni na fad'i a gurin ina kallonsu dishi-dishi inda suke kokarin Dora mimi kan wani gado Duk an dad'adaure mata k'afafunta da hannaye ta babu Wanda yabi ta kaina harshi kanshi Jahid din suka tura Mimi dake kwance kan Wani k'arfe suka futa.
Silalewa nayi na fad'i a gurin ba tare dana San a wace duniyar nake ciki ba.
Tuni Umma da Granny sun futa sun tsaitsaya aka futo da gawar Mimi tare da sanya ta a motar asibiti Umma sai share hawaye take yi, suka shiga, dravar yaja motar, lokacin kowa ya manta dani sai Jahid din da ya dawo ta kaina shine duk yayi min taimakon su na likitoci na dawo hayyacina kuka sosai nake yi had'e da dukan shi kamar mahaukaci nake cewa an hada baki dashi an kashe min Mimi, ganin kamar bata cikin hankalin ta ya sanya yayi mata allura take bacci me nauyi yayi gaba da ni.

Wasu nurses ya sanya suka shigar masa da ita mota, ya bar asibitin cikin halin damuwa da tashin hankali, Kamar gawa a ka shiga dani cikin gidan Amjadu inda ya cika da Jama'a maza da mata lokacin tuni an shirya gawar Mimi an futo da ita, saboda haka Jahid kawai ya tsaya nan aka sallace shi da ita, shine a gefe Amjad din a gafe suka dauki makarar dukanin su zuciyoyin su babu dad'i amma dai komai ubangji ya saukar kan bawan shi ne dai-dai.





*25/11/2019*
[11/26, 9:20 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*63*


Mutuwar Mimi ta girgiza zuk'atan Al'umma bamu kad'ai ba hatta da masu gadin gidan sai da suka ji a mutuwar a jikin su, Jama'a kuwa daga ko ina b'arkowa suke yi ta'aziyya wasu kuma gulma ce take kawo su, domin 'yan jarida sun ruga sun gama wa tsawa duniya cewa mutuwar mayar Young millionaire tana da nasaba ne da harin da jama'ar gari suka kai masa, wa 'yanda basu San yayi aure ba suka dinga mamaki shine suke zuwa zaman makoki, mai girma governor Sarkin kano duk dasu akai sadakar uku, su mai citta ma duk dasu babu tsoron Allah ko na kwabo a tare dasu, a fili sun nunawa Amjadu kara a zuciyarsu kuwa murna suke yi sosai, shi kuwa governor abun ne ya soma bashi tsoro ganin yanda yazo zaman sa na k'arshe jama'ar gari na raka shi da dutsina suna fadin "Ba mayi."!!! Kuma tunda ga mutuwar Mimi jama'a suka fara gane cewa harda sa hannun governor akan sharrin da akai wa Amjdin, ranar a tsorace ya bar kofar gidan Amjad ganin yanda matasa suke jifansa kamar ba governor ba, sai da jami'an tsaro suka fara sakin harbi sannan kowa yq shifa taitayin sa, Umma kuwa jin irin zantukan da jama'ar gari suke yi kan mutuwar Mimi yasa tace" Suyi hakuri kar su bata wa Mimi gawa kawai Allah ya amshi abunsa lokacin da yaso.

*****
Yau kwanan Mimi bakwai a karkashin k'asa, na fige na tsigale sai Umma tayi da gaske nake cin abinci kullum ina zaune zukud'inm! Ko kuma in tafi dakin ta in kwanta kam bed dinta hade da rungume wani k'aramin hoton mu, dake cikin frem a kan drowr gefan gado ta aje shi, kuka nake yi sosai, Umma granny dashi kanshi Uban gayya naga duk sun saki jikinsu har hira suke yi suci abunci hankali kwance kuma suyi dariya, ni kadai ce nake cikin halin damuwa da bakin cikin rashin Mimi, tsakanina dashi kallone domun tunda Mimi ta mutum magana ta fatar baki bata hada mu dashi yau kwanakinmu bakwai kenan a cikin gidan shi, ya sake sosai yayi wanka ya shirya harda fesa turare sai abun yayi ta bani mamaki ina zargin sa, dama ya fi son Mimi ta mutu ya cigaba da tsula tsiyarsa take wata irin tsanar sa ta cika min zuciya ta.

Jahid kullum yana kirana a waya sai dai Sam bana sakewa dashi domin gani nake yi kamar bakin su da daya da Amjad din, matar shi Hafsa me kirki da ita duk a gama zaman makokin INA lura da ita da yanda take satar kallona a fakaice.

Babu kuzari a jikina na futo daga dakin Mimi hannuna rike da k'aramin hoton mu, kusa da Umma na zaune a hankali nace"Umma zaman me muke yi a gidan nan? Wallahi nagaji gani nake kamar Mimi zata dawo gwara mu tafi." Umma tace"Eh dama yau kam zamu tafi tunda an share makoki, muna jira maigidan ya futo ne zamu je duba baby insha Allah daga asibitin sai mu wuce gida." Granny tace"Habadai Ku kuwa ai sai kace Wanda ake kora kwabari kuyi sati biyu mana in baza Ku bari ayi ar'bain ba, har yanzu fa ana zuwa gaisuwa." Umma tace"Tafiyar tamu ta dole CE Hajiya ni kaina a takure nake a gidanan wallahi, kiyi hakuri duk Wanda zai mun gaisuwa ya same ni a gida." Granny tace"To Allah dai ya gafartawa wannan yarinya.
Tsaf ya futo Cikin dogayen kaya,na lura tunda akayi mutuwar nan bai sanya k'ananun kaya ba, k'amshin sa ne ya cika parlor ya tsaya bakin kofar shi yana gyara links dinshi, saurin kauda kaina nayi daga kanshi ina jan tsaki kasa-kasa wallahi wani mugun haushin sa nake ji. Umma tace"Ka futo kenan."? A hankali yace." Eh Umma Ku tashi muje yanzu, amma naji kuna wata magana ko." ? Umma tace"Eh kam yau zamu tafi gida." Yace." Umma kuyi hakuri ayi sadakar ar'abain mana." Umma tace"Bazai yiwu ba, INA da uziri Asma'u kuma makaranta zamana a gidanan bashi zai dawo da Mimi ba." Yace." Hakane Umma shikkenan Allah yasa ka da alkairi. " mik'e wa Nayi  da sauri na bar gurin, hijab dina na dauko dama tunda nazo kayan Mimi nake amfani dasu, Umma ko granny ce ta dauko mata wasu sabbin atampopi super take sanya wa yanzu daya daga cikinsu a jikin ta, Granny ta mike tana fadin "Baza Ku barni a baya ba, muje inga 'yar yarinya cikin kwalba."

Aikuwa ko da sukaje Asibitin fafur likitoci suka hana su shiga ganin baby Aisha yarinyar da Ubanta yayi mata huduba da sunan mahaifiyar ta, shi kam ai dactors din sun San shi farin sani dolen su suke kyaleshi ya shiga yaga babynshi kullum baya iya bacci sai yaje ya ganta haka kazalika kullum kara kaunar yarinyar yake Cikin zuciyar sa, yarinyar kamar su daya da uwarta sai dai ta kwaso hasken fatar shi, fara ce sosai, Amjad kam yafi Mimi haske nesa ba kusa ba, Alhmdullahi tana samun kulawa sosai daga gurin dactors  ta fara k'wari da girma jikinta ya fara murjewa tana rayuwa cikin kwalba cikin hukunci ubangji.
Babu yanda muka iya haka muka hakura amma naji babu dad'i a zuciya ta domin naso inga baby nan wallahi ga yanda naji ubanta na fadin kamar si daya da Mimi, Jahid nayi ta kira a waya yak'i dauka saboda yasan zancan dokar asibitin CE, yana ganin kan Asma'u ba zai sanya ya karya ba.
Amjad har gida ya kaimu Cikin motarsa, zuciya babu dad'i na futo daga motar ba tare da na jira su Umma da aunt Hauwa ba, barin su nayi tare dashi suna sallama, Ya Aminu ne kawai a gidan dama yasan da dawowar mu tunda aunt Hauwa tayi masa waya tsaf muka tadda gidan, rumfa na zube kan leda na fara kuka.
Suka shigo suka same ni a haka aunt tace"Wannan wane irin shirme ne." ? Cikin kuka nace"Aunt don baki San yanda nake ji bane a zuciya wallahi Ashe duk gujewa mutuwa da muke yi akan Mimi tana jika aunt Mimi tasha wahala a rayuwar ta wallahi" aunt tace"Sai hakuri dukanin mai rai mamaci ne addu'a kawai zamu yi mata."
Ya Aminu ya shigo dakin yana fadin"Wannan kukan da kike yi kina kara mata azaba ne idan ta fado miki a rai kiyi mata addu'a. " shiru kawai nayi musu.

Ko da na koma makaranta ba wani sake ba, kullum muna tare da Munnu muna zancan Mimi da halayen ta na hakuri da ban dariyar ta da saurin kukan ta wani lokacin idan na tuno hae sai na share hawaye sai kawai inyi mata addu'a samun rahamar Allah.

Kullum kuwa sai na damu Umma da zancan babyn Mimi nace ta nemi alfarma gurin Amjad ta dauko ta ta raine ta kamar yanda ta raini Mimi, Umma tace wannan kuma nice zanyi hidima tunda nice mamanta a yanzu, nan na dauki a niyar fad'awa Mujahid kudirina kan Baby Aisha, yarinyar da ta zama cikkakiyar mutum domin yanzu tayi k'wari sosai ta cika wataninta na haihuwa, Jahid yace." Zai fad'awa mahaifin ta ko zai amunce, dama ya karb'i babyn sa, yau kwana uku kenan, jin abunda Jahid din yace sai ya d'aga min hankali Ashe har sun bashi baby babu labari mu gamu a zaune kullum muna kwadayin ganinta, to yanzu da ya karb'a wa ya kaiwa? Ni kadai nake tambayar kaina, ina dawowa daga makaranta na fad'awa Umma halin da ake ciki, tace "Aikuwa bai kyauta mana ba, muma ai muna da hakki a kanta, gashi kwana biyu  ya daina kiran Aminu a waya balle kusan halin da ake ciki." Nace"Umma to yanzu wa zai kaiwa babyn ma." Umma tace "Kakarshi mana." Shiru na minti biyu nace "Umma kakarshi bata da k'wari don Allah ki amunce a dauko ta." Umma tace"Ai dama bani naki amincewa mutukar zai bamu muna so hakkin sa ne." Nace "Nayiwa Jahid magana zai nemi alfarma a gurin shi." """"

Rayuwa kenan duniya babu tabbas yau kwanan Mimi Hamsin da bakwai a karkashin kasa komai yayi farko yana da k'arshe Amjad ya sake ya barwa Allah komai ya tabbatar dukanin Abunda ya same shi daga Allah ne.
A halin yanzu ya maida hankalin sa ne gurin k'ara bunk'asa harkokinsa na waje, a cewar sa mu'amula da turawa yanzu ya fara saboda wasun su sun fi muslumin mu amana da tausayi, tunda gashi da Dan uwanshi musulmi aka hada baki dashi gurin cutar shi da izgilanci ga Allah ga manzon sa, yana nan ya sanya matakan tsaro ko ta ina yayi lamfu bunkice yake sosai aka mutanan da suka kulla masa sharri, maganar company kuma tunda sun rusa shi babu wasu kudinsa da zai futo dasu ya saka tada wani, suje kawai Wanda bai ji bari ba zai ji hoho.. Loptop ce a kan cinyar shi yana duba sakkonin da Anthony ya turo mishi tsawon lokuta dama wasu ya bashi amsa wasu bai bashi ba, ya bari ne in yaje can sai suyi maganar. Granny CE ta futo daga dakin ta ta zauna kusa dashi.. Hankalinsa na kan Loptop din bai dago ba yace." Ina Sweetheart yau banji motsin ta ba." Granny tace"Tana gurun Iyami tun safe da tayi mata wanka take bacci." Dariya yayi yace." Wannan Aishar ai rigamammiya ce tafi uwarta fitina." Granny tace"Mai suna Aisha kuka ne da ita ai." Yace." Granny ina tunanin cikin satin nan Zan tafi Chana kuma zan kai wata uku a can insha Allah, amma ina tunanin tafiya in barku fa."

Granny tace"Allah ya taimaka ni kam babu wata chana da zan biki to kaji."!! Dariya yayi yace." Shikkenan zamu je da sweetheart d'ina OK." Hararshi tayi tace"Kaje ka bawa wa ita wannan garin ai ku da ku ga zaku iya zuwa." Murmushi yayi kawai ya cigaba da duba lptop d'insa.
A hankali tace"Ni ko nace dama akwai wata magana da na yanke a kanka." Gyada kansa yayi tare da fadin"Ina sauraren ki." Tace"Mai zai hana ka nemi auran Hafsatu. Da zan ce ko yarinyar nan Asma'u to amma naga wannan yaron Dan albarka Mujahid yana nemanta ana barin halas Dan kunya ko ba haka ba ne."? Bata fuska yayi had'e da ya mutse ta yace."granny ki k'yaleni in huta tukkuna ni kam yanzu babu maganar aure a gurina sai an kwana biyu sannan. " Tace"Aikuwa dole kayi aure domin shine cikar mutum ka kai munzali kace baza kayi aure ba, baka Isa ba."
'Yar dariya yayi yace." Granny nayi aure har na samu riba mutuwa ta rabani da mata ta, ki k'yale ni na huta tukkuna zanyi amma ba yanzu ba." Tace." Ni kam bazan ta kallon ka a haka ba dole ni nayi maka aure. " dariya yake yana mamakin rigimar ta, yace." Ok kiyi min aure sai in barki da matar wallahi inyi tafiya ta tunda bani na saki ba." Granny ta hau zuba masa masifa, dafe kansa yayi yace." Ina aiki kin hani oh my god."!!! Iyami ce ta shigo da Baby Aisha a goye a bayanta tana motsi, alamun ta tashi. Granny tace" Ta tashi ne."? Iyami tace"Gashinan fa da alama Dadynta take so." Rufe loptp din yayi yana kokarin karb'a baby daga hannun granny sai murmushi yake, yarinya tayi mulmul da ita tayi wata irin kib'a hasken fatarta ya kara futowa Iyami ta iya raino gaskiya sai wani kamshi take yi, tana cikin kayansu na jira jira abun gwanin sha'awa, leb'anshi ya manna a kumcinta yana sakin ajiyar zuciya yace." Momyna 'yar rigima  hummmm! Yau ba kuka kenan. "? Kamar yana da magana da babban mutum haka yake yin magana da baby Aisha.

Granny tace"Aiki ya same ka kana magana kamar kana magana da babban mutum." Dariya yayi hade da kamo bakin baby yana Dan tsotsa yarinyar ta fara mamular leb'an shi da sauri.
'Yar dariya yayi ya cire bakinsa ya kalli Iyami dake zaune kusa da granny yace." Allah Iyami zanci tarar ki sweet heart dina yunwa take ji ga alamu nan na gani." Iyami tace"Afuwa Uban gida dama yanzu nake so in dama mata madarar ta, kaga ai bacci take kuma sweeh Hart din naka ci ne da ita Wallahi ." Dariya ya kyalkyale dashi jin yanda Iyami take fadi wai sweeh hart. Yace." Ungo ta ki bata bana so tayi kuka yanzu dai kin San halinta." Iyami ta karb'e ta da sauri ta futa...... Wayar shi tayi k'ara yana dubawa yaga Jahid ne, murmushi yayi hade da daga wayar sallama yayi Jahid yace." Kana gida ne." ?
"Eh ina Gida yanzu amma k'arfe biyar dai-dai zanje government house." Jahid yace." OK ganinan zuwa nima ina Gida kasan yau Sunday  muna Hutu. " Amjad yace." OK sai ka shigo din." Kashe wayar yayi ya cigaba da abunda yake yi.

Minti goma tsakani sai ga Jahid ya shigo parlor yana zama yace." Ina baby Aysha take." Amjad ya rufe loptop tare da fad'in"Tana gurin me raino yanzu kuwa ta dauke ta suka bar gurinan granny ma yanzu ta tashi." Jahid yayi Dariya tare da fadin "Babu wasa cikin al'amarin muna so ka bamu baby Aysha fa."" ! Amjad yace." Ai gatanan ga kanan Aboki baby Aysha taku ce kai da Madam." Jahid yace." Thank you my friend, wallahi Asma'u ce tun jiya ta dame ni lallai a basu ita shine nace zanyi maka magana nasan dai baza ka hana ba." Tunda ya ambaci sunan Asma'u ranshi ya b'aci don har sai da fuskarsa ta nuna ya kalli Jahid din babu alamun wasa a tare dashi yace." Babu wannan maganar my friend babu Wanda zan iya bawa sweet heart gaskiyar magana." Jahid yace." Kuma yanzu kace ka bani ita."
"Yes Ni nace na baka ita saboda nasan muna tare da Kai har abada, naji ka sanyo min zancan wata Asma'u ne, am sorry my  friend Asma'u bata da haleyan K'warai Wanda zata iya tarbiyan tar da d'an wani. Bana jin Zan iya bari baby Aysha ta yini a gidansu ma balle har ta kaita ga kwana gudun ta d'auko d'abiun yarinyar." Jahid ya sha kunnu mutuka yace." Kayi dai-dai Asma'u kake ciwa fuska a gabana ko."? Dariya Amjadu ya sanya tare da fad'in"Sorry halin ta ne fa, amma da baka yimin wannan maganar ba ni babu ruwana." Jahid ya bude hannunsa dake kan kafad'un sa yace." Wato kana nufin matar da zan aura bata da tarbiya ko me."? Hannu Amjad ya d'aga cikin sigar bada hakuri fuskarsa da murmushi yace."  Ban fad'i haka ba my friend.........................






*26/11/2019*
[11/26, 9:01 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*64*


Sosai Jahid yaji babu dad'i saboda yana k'aunar Asma'u tsakani da Allah kuma sam baya kaunar yaji wani ya fad'i mummunar magana a kanta, kokarin mik'ewa yake Amjad din ya mai dashi ya zaunar, gyara fuskar shi yayi babu alamun wasa yace." Karfa kayi magana ta wata fahimta ta daban, ba wai na fad'i wannan maganar bane domin ranka ya b'aci ko kuma kaji wani fargaba a game da k'udirin ka kan yarinyar kace zaka janye auran ta. No kawai na fad'i iya abun da nasa ni a kanta, kuma kasan ko wane mutum Tara yake bai cika goma ba, amma hak'ika ka cancanci yabo da godiya a gare ni abokina babu abunda zaka nema a gurina na kasa yi maka shi, misali kace min in baka Baby Aysha zaka had'a ta da Salim ka rike min, wallahi  babu abunda zai hanani in baka saboda nasan Maman Salim macace da take da nutsuwa gami  da tarbiyya sai ince maka ma kusan halayen su d'aya da Mimi Allah ya jikanta, amma maganar In bawa Asma'u baby ka aje ta gefe guda a halin yanzu babu ita." Jahid ya Dan ji sanyi a ransa, amma duk da haka bai hak'ura ba saboda kwata kwata baya son b'acin ran Asma'u yace." Yanzu idan Allah ya kaddara auramu da Asma'u zaka bamu ita ko ? Tunda kana ganinta a kusa dakai sai kayi mata tarbiyar da kake so." Amjad yayi Dari hade da Sosa kansa yace." Mai zai hana kuwa zan baku wannan nasan muna kusa kuma kai ma zaka samin ido sosai." Jahid yaja tsaki tare da mik'ewa tsaye yace." Baza ka fasa ba kenan ? Ni kaga tafiya ta." Amjad ya mike tsaye shima yana dariya ya rufa masa baya. To kafin suyi sallama ma sai da suka d'an jima a tsaye sannan suka rabu, dama kuma tun Asali cikin makotan sa, sunfi shiri da Mujahid din saboda saukin kansa.

****
K'arfe  takwas dai-dai Mujahid ya kirani a waya cewar gashinan a waje yana jirana, a shirye nake saboda nasan da zuwan sa, cikin motarsa na same shi,  Duk sanda zai zo gurina da sabbin kaya a zuciya nace Jahid ba dai gayu ba, budewa nayi na zauna sosai ya sakar min murmushi tare da fad'in "Yau kin futo da Wuri."
'Yar dariya nayi nace"A shirye nake dama ya maganar mu da kai." Fad'uwar gaba yaji amma dake namiji ne sai ya dake yace." Kya bari mu gaisa ko."?

Rife fuska ta nayi da tafin hannuna ina dariya, shima dariyar yake yace." Ke kinfi baby Aysha rigima ma." Bude idona nayi har yanzu da murmushi a fuskata nace"Wallahi na damu na ga babyn ne." Yace." Kina da gaskiya amma kin san me."? Girgiza kaina nayi, yace." Babanta ya hana wallahi yace ki Bari tukkuna muyi aure zai bamu ita." Raina a bace nake kallon Jahid din nace"Ban gane ya hana ba."? A hankali yace."Shima baya so tayi nisa dashi a yanda na fahimta yana kallonta baby ne yaji sanyi a ransa duk lokacin da ya tuna matarsa.
Nace." Jahid abun da bangane ba shine, shi kad'ai ne yake da hakki da yarinyar? Mu da muke a matsayin iyayen ta bamu da amfani kenan Jahid gani ba ci ba, dama baby 'yar shi waye yace ba tashi ba."! A zafafe na k'arashe maganar.
Jahid ya gyad'a kansa ya San zai fuskanci haka daga gurin ta, yace." Matsala ta dake saurin d'aukar zafi kiyi wa magana ta kyakyawar fahimta mana." Cikin takaici da jin haushin sa nace"Na lura kamar bakin Ku d'aya Jahid baka San yanda nake ji ba Wallahi tallahi tunda naji kuna fadin baby suna kama da Mimi naji ina mugun kaunar ta." Cikin rawar murya ta karasa maganar, cike da tausayin ta yace." Kiyi hakuri dai yanzu dai kar kiyi min kuka Jahid UA fad'a cikin rarrashi. Nace"Wallahi na saki jiki zangan ka da tare da ita." Cikin shagwaba take maganar,Jahid yaji kamar zai suma a gurin hannunsa na rawa yace." Bari kiga hotonta hankalin ki ya kwanta, nima dai kin kusa bani nawa babyn ko."?

Murmushi kawai nayi masa ina Allah-Allah ya mik'o min wayar in gani.. Da sauri na karb'a ina dubawa sosai baby Aysha take kama da Mimi sai da tafi ta haske kamar yanda naji suna fad'a ta murmure sosai da gani ma hoton tana jikin babanta aka dauka don ga jikin shi nan ya futo da hannunshi guda da ya rike ta, Dole in gane saboda manya manyan azurfan dake bisa yatsun sa.
Wayar na rungume a k'irjina ina sakin ajiyar zuciya nace"Jahid baby Aysha na kama da Mimi wallahi ka bani wayar nan yau ta kwana a hannuna in kwana ina kallonta kaji. " dariya yayi yace." Kece kin ki ki bude whatsp da sai na turo miki hoton." Da sauri na mik'a mishi wayar nace "Bari in dauko wayar tawa ka tura min wsp din don Baby Aysha amma da na daina yi." Dariya yake min har na futa daga motar. A tsakaice dai sai da Jahid ya bude min wsp dina da na rufe tun bayan rasuwar Mimi ya tura min dukanin. Hotonan baby Aysha, yace" kullum zai dinga d'aukar ta sabbin pictures Yana turo min sosai naji dadin haka na saki jikina sosai muka yi shirarmu nan yace insha Allahu a karshen wata yake so ya turo magabatan sa gurin Kawu Yunusa nace"Allah yasa nan mukayi sallama dashi ya tafi.

Ko da Umma taga hoton baby Aysha tayi ta mamaki sosai sai taji sha'awar ganin yarinyar a zahiri tace." To tunda ya hamu ita ni zanje da kaina in duba ta ai hakan ba laifi bane." Umma da kin kyaleshi dai komai abunda baby Dole ta nemi dangin uwarta wallahi." Umma tace"Ai baza'ayi haka ba, domin bamu San munufar sa tayin haka ba, to koma dai menene abar shi da d'iyar shi yayi yanda yake so da ita." Shiru nayi ina raya wani Abu a raina

Abunci naci nayi wa Umma sallama, kai tsaye dakinmu na nufa, na tube kayan jikina wata duguwar Riga na sanya a jikina mai uban kyau da tsada duk cikin kayan Mimi suke, hula na sanya a kaina na kwanta kan katifa, hade da rufe k'afafuna hotan baby na tsurawa ido ina murmushi nima wallahi na damu inga yarinyar a zuciya ta.

Wsp na shiga na d'ora pic dinta kan df na, wsp din dake amfani a waya ta mai Gb ne ya nuna min Amjad na online wata zuciyar tace kiyi masa magana kawai tunda gashi a onile da sauri na shiga gurin shi naga ya sauka akai. Yanzu Df shi na kamo da sauri ina dubawa, pic dinshi ne da baby Aysha ya d'aga ta sama yana dariya hat tada dimple dinshi sai da ya futo saboda dariya itama babyn dariya take naji sun bani sha'awa, zuciya ta tace min "Shi yana Cikin jin dad'i har da dariya gashi ga 'yar shi hummm! Ai in da mutumci Amjad bamu cancanci haka daga gurin shi ba,   message  na tura masa kamar haka

_" Duk d'an halak baya bance alkairi kuma tilas! Ace da mijin iya baba, duk talaucin mu, baby na tabbata sai ta neme mu, domin mune dai dangin uwarta."_

Tura masa nayi na  kashe data ta, tsawon mintuna ashirin, na k'ara bud'e datar, ina dubawa naga har ya gani, sai naji wata fad'uwar gaba, messenges na cigaba da dubawa ina sauraron amsar sa, shiru kusan minti talatin kuma duk dubawar da zanyi sai inga yana online, bakin ciki da takaici suka ishe ni, abunda na tsana a rayuwa ta shariya guy nan yaga sakona zai wulakanta ni, lallai ya sanja sabbin halaye, ji nayi wasu zafafan hawaye na nema su kufce min. Kira ne ya shigo wayar tawa ina dubawa naga shine.....







*26/11/2019*
[11/27, 4:45 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*

*65*

Cikin fad'uwar gaba na mik'e zaune sosai ina k'ara duba wayar tabbas shine ya kira ni. Cikin zuciyata nace to me zai ce min lallai ma, kin d'agawa nayi har ra katse wani kiran ya k'ara shigowa ina kallon wayar nan ma ta katse band'aga ba, sai da ya kira sau uku nak'i dagawa sannan ya hak'ura, kwanciya nayi ina sak'e-sak'e a zuciya ta, data ta kara kunnawa aikuwa sak'on shi na farko hannuna na rawa na shiga ina dubawa. Ga Abunda yace.

_"Maganar ki gaskiya ne 'yan mata, Sweetheart bata da wani dangi sai ku domin kune iyayen ta, Abunda na kasa fahimta a maganar da kika ce duk D'an halal ba ya mance alkairi, shin wane alkairi kuka yi min da har na manta? Bayan nan kuma ina so in k'ara jaddada miki cewar Aysha d'iya tace domin nine k'ashin bayan Samar da ita, dukanin Ku baku da iko akanta, ni nake da iko akan kaya ta, so bana son damuwa don Allah daga yau sai yau karki kara yi min magana makamamciyar wannan, ina fatan kin fahimta? Kin turo min Jahid kan bukatar ki, to baki isa ba indai nine uban Aysha bazan tab'a Bari ki raine ta ba ballanta ki koya mata munanan d'abi'un ki, tabbas yanzu na tabbatar da cewa a baya nayi wauta da nake kokarin rabuwa da mace tagari a kanki , na tabbata Mimi alkairi ce a rayuwa ta, kuma duk macan da zan aura sai dai tabi bayanta wallahi,a halin da ake ciki yanzu soyayyar ta ta cika min zuciyata duk da bata Raye, ta inda nake yi wa mata kallon maza ciki kuwa har dake, saboda haka ki kiyaye fad'a min magana ko wace iri ce,ni Amjadu AbulAbbas ma nasara na shafe ki a babin rayuwa ta."_

~AMJD ABUL ABBAS~

Wani irin gumi ne yake tsiyaya a jikina take wasu zafaffan hawaye suka kece min, Dana San wad'annan mugayen maganganun guy nan zai fad'a mun da ban mishi magana ba, hannuna na karkarwa nake bashi amsa..... Da sauri na tura masa, na kashe data hade da jefar da wayar kan Katifa na rungume filo ina tik'ar kuka harda sharb'e majina,wato ni guy nan yake nunawa iyaka ta kan abunda Mimi ta tafi ta bari gashi Ubangji ya zuba min kauna da son baby Aysha a cikin raina, nafi awa guda ina kuka k'asa kasa don kar Umma taji fa kyar na rarrashi kaina tare da alk'awarin cewar bazan kara shiga harkar shi ba har a bada..Data na k'ara kunnuwa ina tunanin zanga sak'on shi domin nasan na fad'a masa bak'aken maganganu Wanda suka fi nashi abun mamaki, ko da na duba sai naga yayi bloking d'ina, sak'on Dana tura masa Yanan yanda yake,  ajiye wayar nayi ina da na sanin bud'e whatsp din inda nasan wannan bakin cikin zan riske, da kyar bacci ya dauke ni mai cike da mafarkin baby Aysha da Mahaifiyar ta.

Ko dana tashi da safe sukuku na tashi jikina duk babu kuzari har Umma ta fahimci wan Abu amma bata ce min komai ba, saboda tana tunanin a jizanci ne irin na d'an Adam, sallama nayi mata na tafi makaranta. To ko A skull din ma kasa b'oyewa Munnu nayi sai da na fad'a mata komai kuma na nuna mata text din da ya turo min, Munnu ta dinga mamaki tsabar haushi da takaici yasa ta dinga zaginsa hotonan baby take dubawa sosai tana fad'in"Wallahi karya yake in Ku ya rabaku da ita mu bai isaba sai munje mu daukota Wallahi munganta ai wannan rashin imani ne ace kamar jinin Mimi sai dai mu ganta a hoto gaskiya bai isa ba."!! Yanda Munnu take masifa sai ya bani dariya nace"Munnu ni da zaki bi ta tawa da mun hak'ura wallahi duk son ki da baby baki kaini ba, amma na hak'ura na bar masa kayan sa kamar yanda ya fad'a d'in, nasan duk daran dadewa baby zata neme mu." Munnu tace"Ai sai munje har gidan mun ganta wallahi hakkin mu, dole zan hurawa Babanmu waya muje tare." Shuru nayi mata ita kuma ta hau tura hoton baby a wayar ta.

******
Amjadu kuwa ranar da yaje amsa kiran da me girma governor yayi masa basu kwashe da dad'i ba, domin wasu zantukan banza yake masa wai yaga jama'ar gari suna zargin sa kan harda sa hannunsa kan afkuwar abunda ya faru, ya kama rantse-rantse yana fad'in kwata-kwata bai San zancan ba, don haka yayi hakuri kar ya kulle CE shi kuma a matsayin sa na shugaba insha Allah zai sanya a tsaurara bunkice domin gano wadanda suka aikata haka." Kallon shashasha Amjad din yake masa domin ya ma kasa cewa dashi komai kawai ya mike zai bar gurin, governor yadawo dashi, cikin sigar rarrashi yace." Sai magana ta biyu cewar nayi maka alk'awari insha Allah wannan kujerar tawa Kaine zaka maye gurbin ta, tunda na lura jama'ar gari na sonka zamu had'a baki dakai muyi murdiya ga Wanda yaji zab'e zaka tsaya takara a jam'iyya ta, sai milki ya dawo hannuna." Amjad yaji kamar ta kwakwkwad'a masa Mari lallai shaye-shayen da yake yi ya soma tab'a masa kwakwalwa da har yake tunanin dashi zaiyi wannan aiki.
Kallon banza Amjad yayi masa yace." Idan ina sha'awar mulki kai! Baka isa ka sanya ni nayi ba, lokacin da zaka ji ni a duk jam'iyyar da nake so zakayi mamaki so wannan Ba damuwar ka bace tawa ce, maganar zaka tsaurara binkice kan mutanan da suka shirya wannan sharri gami da yin izgili ga Allah da manzon sa, wannan bai dame ni ba, saboda ni nasan ko su waye kar ka bawa kanka wahala kuma zan dauki mataki a Kansu."!! Tebur din gaban shi ya buga da k'arfi! Ya mike tsaye hade da fad'in"Na barka lafiya." Futa yayi cikin yanayin tafiyar shi, ta gwarazan maza.
Governor ya bishi da kallon mamaki! Wato duk inda yake tsammanin yaron ya wuce nan, lallai su Alhaji Hashimu mai citta sun shirya masa sakiyar da babu ruwa ya tabbata da babu wannan maganar a kasa, zai iya Jan ra'ayin yaron ya karb'i takarar governor kano a jam'iyyar su, domin ya tabbatar Da babu abunda zai hanashi ya lashe zab'e saboda kaunar da jama'ar gari suke masa, shi kuma tanan sai yayi amfani da damar shi, shiru yayi yana tunanin mutukar ya sauka daga kan mulki kashin sa ya bushe zai tabbata bashi da tsunsu bashi da tarko.

****
Tsaf ya fito cikin shiri, granny da Iyami na zaune a parlor suna hira, ya k'araso tsakiyar parlorn hannu ya mik'a ya dauki baby dake jikin granny a kwance sai wuntsin-wuntsil take, sama ya d'aga ta kamar yanda ya saba yi mata yana kyalkyala dariya itama na b'angale baki, yafi minti goma yana wasa da yarinyar sannan ya zauna da ita a jikinsa yana fad'in"Baby zanyi missing dinki fa....Granny don Allah Ku shirya mu tafi tare kinji. " cikin shagwaba yayi maganar, granny tace"Kasan Allah babu inda zamu bika kai dai kaje kurrum Allah ya bada sa'a idan ka dawo ma ina so muje muga 'yan uwa Chadi. " yace." Sai dai idan kin yarda mu tafi tare bayan nagama Abunda ya kaini sai mu wuce Chadi din ko ya kika ce." Girgiza Kai tayi tana fad'in"Oh-oh!! Kaje dai ka dawo idan kuma kak'i kaini ai da k'afafuna sai in tafi ka dawo ka tadda bama nan." Yace." Ki Bari zamu je granny nasan halin don girman Allah kar ki d'aukar min Baby kuje wani guri." Tsakaninsa da Allah yake maganar. Granny tace"Ikon Allah!! Yanzu ni kakewa gargad'i kan 'yar ka K'ato! Lallai baka da ta ido!! Dariya yayi ya mike yana fad'in"Granny soyayyar sweetheart dina ta cika min zuciya ta shiyasa idona yake rufewa. " romot din dake kusa da ita ta dauka ta jefe shi dashi, tace"Marakunya kawai, ni kam bana maka fatan samun matsala da duk matar da zaka aura nasan kam Aysha zaka iya sakin ta." Babu wasa a fuskar shi yace." Granny duk wacce zata zauna min da sweet heart lafiya ina maraba da ita, zaman lafiyar mu da ita ta so baby Aysha." Granny da Iyami suka girgiza kai cikin mamaki

Iyami ya mik'awa baby din ya  kalli agogon dake daure a hannunsa, Cikin nutsuwa yace." Ni zan tafi sai munyi waya ko
"? Granny tace" Allah ya kiyaye hanya muna maka fatan alkairi,Iyami ma fatan alkairi take masa ya fuce daga parlor da sauri,baby ta bishi da kallo tana d'aga hannunwan ta, yarinyar sun saba sosai da baban ta.
Yana futa su Rambo suka rufa masa baya, kai tsaye airport suka kaishi sai da suka ga tashin jirgin su sannan suka bar gurin. Hade da yi masa fatan dawo wa lafiya.

****
Gurin Jahid naji cewar yayi tafiya sai ban nuna komai ba, ko da wasa ban fada masa abunda ya faru tsakanina dashi ba, haka muke tafiya dashi cike da kauna da kulawa kullum kuwa idan ya shiga gaida granny sai ya dauko min picture din baby ya turo min, mu yini muna kallonta ni da Umma.
Allah mai iko tsakanin Ya Aminu da Munnu soyayya ce mai k'arfi ta kullu shiyasa ma Munnu ta rage zuwa gidanmu a cewar ta wai kunyar Umma take ji,magar auran su ta kankama inda Baban su Munnu da Kawu Yunusa suka tsaida magana insha Allah wata uku za'a d'aura auransu tunda Ya Aminu ya yarda ta cigaba da makaranta a gidan shi, Kawu Yunusa da kansa yazo gidanmu ya karewa Umma zagi har dani sai da ya had'a ya dinga zaginmu da cin mutumci iri-iri wai tunda na ki auran Amjadu to in fito da miji a hada da Aminu ya fuskanci wannan yaron da yake Neman aurena Mujahid yaudara ta zaiyi tunda gashinan kullum sai yace zai turo magabatan sa a tsaida magana sai yak'i saboda haka inyi maza in futo da miji ko kuma Wallahi ya d'aura min aure da Musa tunda dama tuntuni shine ya fara cewa yana sona." Ranar kuka ns yini ina yi ina samun chaji a waya ta ns kira Jahid din tare da fashe masa da kuka duk na kwashe Abunda yake faruwa na fada masa. Shima babu shiri ya je ya Sanar da mahaifin sa halin da ake ciki. Take Alhaji Auwalu yace." Zai tura akai kud'in aure da sadaki. To ko da Jahid ya samu mahaifiyar sa da maganar tsalle tayi ta dire tace wallahi Sam! Bata yadda yaje ya auro 'yar talakawa ba, domin baza ta tab'a had'a jinita da talakawa masu dattin hula ba, tsaf! Ta sanya akaje akayi mata bunkican su waye su Asma'u kai har gidan su sai Da tasa aka binkito mata. Aikuwa ita da Aminiyar ta suka shirya cikin shiga ta alfarma suka tafi gidan, Baban abunda ya tayar mata da hankali yanda taga wani k'aramin gida kamar akurki wai nan gidan Mujahid dinta zaije ya nemi aure salon ya zubar mata da mutumci da kima a fusace! Suka shiga gidan Momy Mujahid din ns karkada key dinta motar ta cikin izgili
Ina sunkuye bakin rijiya ina dauraye hijabai na, Umma kuma na cikin rumfa tana d'aurin sukari hira baby Aysha muke yi da ita kawai naji wani mugun kamshi ya bak'unci hancina sawun tafiya naji na kalli kofar shigowa da sauri, wasu hamshakan mata ne suka shigo cikin ya tsine fuska sukayi sallama, na d'ago Cikin nutsuwa nake amsa musu, Hajiya Fatima ta kalleni ya a mutse tace"Da'alama kece "Asma'u ko."? Babu walwala a tare dani nace" Nice." Kallon banza tayi min ta wani ya mutse fuskar ta had'e da tofar da miyau! "She is ugly girl!!." Ta fad'a tana kallon Momyn Jahid dake bin tsakar Gidanmu da kallo kamar Wanda take Neman wani Abu.... Wani irin tsinkewar zuciya naji lokacin da tafad'i min wannan Kalmar kallo nake binsu dashi cikin mamaki!! Momy Jahid ta kalleni a wulakance tace"Ke! Ina uwarki kwad'ayyaya gurun ta nazo ni." Umms ta futo tana fad'in "Asma'u ke da waye ne."? Cikin takaici da jin haushi nace "Umma wad'annan sakarkarun matan ne suka shigo mana gida babu sallama ko wacce tana fama ra karnin bleecing sune har suke kiran wani da mummuna."! Momy Jahid ta kawo min wani bahagon mari tare da fadin" Ke don ubanki kin San kuwa ni wacece a gari nan. "? Kaucewa nayi da sauri ina fadin " Sanin ko ke wacece bai dame ni ba nasan dai ke macace mara tarbiyya mace mai izgil...... Kafin in karasa Umma ta gwab'e min bakina tare da fad'in"Asma'u baki da hankali ko."? Nace. " Umma kin..... Tsawa tw buga min tare da fadin",wallahi in bakiyi shiru ba ranki zai b'aci a gurina."!!Momy Mujahid tace "Ki k'yaleta ta zageni da kyau! Nagode Allah da ya nuna min halin ki tun kafin Dana ya aure ki dama jama'ar gari na fadin haka a kanki,to bari kuji gargadi na daku da babban murya tun wuri Ku janye jikin Ku domin har indai nice mahaifiyar Mujahid wallahi bazai aure ki ba bazan hada jini da talakawa fakirai irin Ku ba, mutsiyata kawai."

Mamaki ne ya lullub'e ni jin Ashe da da mahaifiyar Jahid nake magana naji tsoro da kunya sosai amma lokaci guda naji wata irin muguwar tsanar matar domin a rayuwata na tsani masu kudi marasa kaunar talaka ya rab'e su. Cikin daki na shige cike da takaici a fili nace "Wallahi kinci darajar Mujahid ne kawai." Ashe taji duk da k'asa kasa nayi maganar aikuwa naji tana fad'in"Da kin sani kin dake ni kamar yanda kikayi NIYYA marakunyar yarinya kawai. " Umma kuwa hakuri kawai take basu Hajiya Fatima ta daka mata wata irin tsawa "Dallah rufe mana baki."? Umma ta rike hab'a cike da mamaki! Hajiya Fatima ta cigaba Da cewa" DUk laifin naki ne ai hausawa suka ce ido na mudu ba yasan k'ima, in banda abunki ina mu INA Ku kwadayi ne ya rud'e ku kuma kinyi a banza domin dai d'anmu bazai auri yarinyar Ku ba." Umma taji zafin maganar da Hajiya Fatima ta fad'a to dake kowa na da nashi hankalin, sai ta share kawai tace "Shi aure nufi ne daga Allah idan Mujahid shine mijin Asma'u babu mahalukin da ya isa ya hana, idan kuma bashi bane Allah ne masa ni don haka Ku kwantar da hankalin Ku."

Momy Jahid ta Ciro d'aurarrun kudi cikin jakar ta dauri uku ta watsa ma Umma a jiki cikin izgili tace"Ki tofar da bakin miyau na bakin ki domun kinyi sab'o Wallahi Mujahid bazai auri yarki ba mutukar ina Raye. "!!! A fusace taja hannun Hjy Fatima suka futa daga gidan.
Umma ta shigo inda nake tana fad'in" Ikon Allah Ashe haka wasu masu kud'in suke? Ashe mahaifiyar Mujahid bata da kirki shikam yaron kirki dashi lallai albasa bata tayi halin ruwa ba." Nace Umma ki k'yaleta badai Jahid ne bata so na aura tom ni. Kuma sai na aure shi sai inga ya zata yi."!

Umma tac"A'a ni bana yi miki sha'awar auran shi tunda uwarsa bata so ko anyi anyi auran ma to ba dad'i zakiji ba, kowa ya shaida cewar matar shi mutuniyar kirki ce kingani ke babu Matsalar kishiya tunda ta amunce ko ka bata amunce mijinta ya aure ki ba tom Allah da manzon sa, sun hallasta amma gaskiya matar nan ta bani tsoro." Nace"Umma ki kwantar da hankalin ki, kamar yanda kika fad'a cewa aure nufi ne na ubangiji to ni ina nan kan bakana Wallahi babu gudu babu ja da baya sai dai in Jahid din ne yace ya janye maganar aure na tom sai in hak'ura. " Umma tace "To Allah ya zab'a abunda yafi alkairi dai." Amin nace zuciyata duk babu dad'i.

Kuka sosai Momyn tasa take da kyar ya shawo kanta tayi shiru yace." Ki fada min ko menene Mommy" Tace"Wai ni yau ka kajawo wa zagi a gurin wadanda basu isa ba, Mujahid yau matar da kake Neman auranta ta zage ni ta kirani  karuwa wai mai bleecing sai ta kara fashewa da kuka sosai har da dafe kanta." Jahid ya sunkuyar da kansa cike da mamaki  anya kuwa Asma'u zata iya zagin Momyn sa kamar yanda ta fad'a to wai ma shin a ina suka had'u da juna ne.?






*27/11/2019*
[11/28, 7:55 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*66*

Mujahid ya cigaba da rarrashin Momyn sa har sai da tayi shiru tukkuna ya kalleta a nutsu yace."Momy wai ina kika ga Asma'u da har tayi miki rashin kunya nifa abun nan ya bani mamaki."! Cikin fusata Momy tace"Naga kamar kana shakka ne Jahid har kana titsiyeni ka tambaye ni, to gidansu nasa aka kaini domin in gargade ta ta fita harkar ka domin naga mayu ne kana zaune da matar ka ta kirki ka je ka kwasowa kanka kaska shine fa ta yi mana wankin babban bargo nida Hajiya Fatima." Mujahid yayi kasa da dansa cikin mamaki jin wai momy gidansu Asma'u taje to in hakane Ashe itace ta jawowa kanta raina yasan halin Momyn sa da zubda girma mybe taje tayi wulakancin da ta saba ne. Tace "Saboda haka in dai nice mahaifiyar ka ban yarda k auri yarinyar ba, shida shiru yayi mata har sanda ta kare fad'an ta yayi mata sallama ya tafi gida. To ko da yaje gida ma matarshi kasa gane kansa tayi dama 'yan kwanakin nan haka yake mata duk ya sauya kwayenta nace mata dama idan namiji zai kara aure canza hali yake, ita dai tunda ta hada masa abunci sai ta shige d'akinta domin ta lura kamar zamanta a kusa dashu baya so. Jahid kuwa ba wani ci abunci da yawa ba, ta kwanta duguwar kujera yana tunanin ala'amri lokacin yi wayar su nayi ya kirata. Lokacin ina zaune ina yin game a wayata naga kiransa dama na tsammaci haka, Muka gaisa kamar yanda muka saba kana ya d'ora da maganar shi kamar haka" Asma'u wai da gaske Momyna tazo gidanmu."? Nace"Babu wai Mujahid Momynka tazo gidanmu. " shiru yayi na minti biyu yace."Ki fada mun gaskiyar Abunda ya faru." Nace"Jahid Momyn ka tazo tayi mana cin mutumci sosai takai har sai da na mayar mata da martani a rashin sani sai daga baya da ta fad'i cewar itace Momynka sannan naji kunya don Allah kayi hakuri nasan duk zata fada maka abunda ya faru tsakaminmu amma ni abunda nayi mata a rashin sanine." Jahid yaji ya kara kaunar Asma'u yana ganin ba zai iya janye kudirinsa akanta ba zai lallaba Momysa ta hak'ura ta barshi ya aure ta A halin yanzu ita kurrum yake gani yaji sanyi Asma'u tw zame masa wani b'angare na jikinshi, take ya manta da b'acin ran Momyna suka cigaba da hira shi da Asma'u Cikin shaukin so Sam! Ya manta ma cewar a cikin gidan shi yake kuma a patlor Maman Salim zata iya jinshi, Aikuwa tana daki tana tik'ar kukan takaici a zuciyarta tana ji ta tsani Asma'u tunda ta shiga tsakanin ta da mijinta da suka Gina rayuwar su cikin aminci da yardar juna.

****
Mujahid ya nunawa Momynsa kamar ya janye maganar auran sa da Asma'u a b'oye kuwa sun hada baki da mahaifin sa, har anje gidan su Asma'u ankai kud'in aure da sadaki lokaci kurrum ake jira kuma kullum suna tare domin shakuwar su ta yanzu tafi ta da waya kullum babu dare babu rana haka suke yi.

****
Watan Amjadu Biyu a chana komai ya kammala nan ya wuce Ingila domin can ma akwai bukatar yaje din domin duba company shi da ganin irin cigaban da aka samu. A shkekarar kullum suna tare da granny a waya maganar guda ce Babu Aysha tayi kaza kaza wani lokacin sai dai granny ta kashe wayar ta kyaleshi ko kuma ta kara wayar bakin baby Aysha tayi ta gwalantu shi kuma yana kyalkyala dariya sai Granny ts karb'i wayar sannan zai ce da ita wai tana fad'a masa ne tayi missing d'insa sosai. Granny tsabar haushi sai ta kashe wayar tana fadin'Kai da ita kuka San wannan."

****
Muna a dai-dai sahu nida Munnu tace"Ke Wallahi yau sai munje gidan Young millionaire mun dauko baby Aysha ta kwana biyu a hannun mu tunda kince ai mahaifin nata bayanan ko."?Nace " Bayan nan yayi tafiya lallai Munnu ke 'yar rigima ce ni kam babu ruwana Wallahi. " Munnu tace"Ki sa wasa ki gani, mai a dai-dai muje Jambulo." Aikuwa Mai a dai-dai ta ya Karya kwana , nace "Munnu sai dai in ki shiga ke ni kam bazan shiga ba." Tace"Wallahi sai mun shiga tare "Dariya NASA Nace " Zakiyi kaffara kuwa. Muna isa Munnu ta biyashi kudinsa muka tsaya bakin gate din, take masu gadi suka bude mu din ba bakin bane a gidan, Jan hannuna take wai dole sai na shiga ganin kar abun ya zama da zargi yasa na bi bayanta gabana na fad'uwa ni yanzu Sam bana kaunar abunda zai hada ni da guy nan tunda yace s k'yale masa 'yar sa to sai a k'yaleta domin a zauna lafiya.

Granny da Iyami na zaune a parlor suna kallon shirin dadin kowa tashar Arewa24 muka yi sallama. Granny ta amsa tana fad'in "Lale maraba da manya baki lallai yau Baby Aysha na da baki domin dai nasan domin ita kuka zo gidanan." Murmushi nayi na zauna Cikin kujera a nutse muka gaisa sosai tace"Shikkenan saboda babu Aisha sai Ku yanke zumunci damu har Umman taku ma ai wallahi bata kyauta ba." Hakuri na dinga bata INA fad'in"Bana samun lokacin zuwa ne saboda makaranta. Granny tace" Yau watan baby Hudu a duniya ace kuna a matsayin iyayenta babu Wanda yazo duba ta ai gaskiya naji haushin wannan Abu." Mu dai hakuri muke bata, sannan muka gaisa da Iyami dake kallon tana dariyar durmarmu d Granny  tace"Iyami Kawu musu abunci." Duk da ina jin yunwa sai da nace "Granny a koshe muke Wallahi." Hararata tayi tace"Wato kinanan da halin ki na cutar kai ko? Dubi bakin Ku a bushe kice min a koshe kuke ai nasan daga makaranta kuka dawo." Shiru nayi kawai domin nasan dukanin abunda zan fada Granny ba yarda zata yi ba. Munnu tace"Ina baby Aysha ne? Domin munzo aba mu aronta." Granny tace"Yanzu kuwa tayi bacci wallahi ai kun fi k'arfin abaku Aron ta idan ma kyauta kuka je a baku za'a baku ita kyauta." Munnu tace"Granny da gaske nake wallahi zamuje da ita ta kwana biyu sai mu dawo da ita." Granny tace "Nima ai da gaske nake." Iyami ce ta shigo da k'aton tire cike da nau'ikan abunci da abunsha ta aje kan dogun tebur din da yake gabanmu. Granny tace "Iyami maza hada kayan baby Iyayenta zasu je da ita su ta kwana biyu." Iyami tace"To Hajiya amma fa zamu sha kewa da yawa." Granny tace"Zamu huta da rigima dai kinga zamuyi bacci harda munshari musamman ke." Dariya muka yi harda Iyami ta nufi wani daki da sauri tana fad'in "Baby Aysha rigima kenan. Sosai muka saki jiki muka ci muka koshi mana hira da granny Cikin barkwanci ni kam Allah-Allah nake a fito da baby Aysha na ganta. Aikuwa sai ga Iyami ta fito da ita a kafadar ta daya hannun NATA kuma k'aramin akwatu ne. Ni da Munnu rige-rige karb'ar ta mukayi Allah ya  bani sa'a ina karb'ar ta na manna mata kiss a kumatu ina dariya ganin yanda take motsa bakinta tana tsotsar hannunta, da alama yunwa take ji. Granny tace" oh! Oh oh!! Wai meye amfanin abunda kuke yi ne, kuyi ta tsotsar kumatun yarinya shima haka wancan sakaran yake yi, mata har bakinta tsotsa yake." Ni da Munnu muka dariya nace"Ni kam sumbatar kumatun ta kawai nayi granny gaskiya Iyami ta iya raino naji dadin ganin baby Aysha haa duna granny kamar ba bakwai ni ba."

Tana dariya tace"Yanzu zata nuna muka halin nata na k'uya Iyami kadai ta sani saboda ita take bata abunci ni kaina wani lokacin sai taga dama take yarda dani." Aikuwa sai ta fara tab'e baki tana so tasa kuka, rungume ta nayi ina rarrashin ta, granny kuwa sai dariya take mana, Iyami ta shigo da fidar ta da sauri ta sanya mata a baki ta kama tana tsotsa sosai, Dan kanta ta cire bakinta sannan ta fara daga hannu wai zataje gurin Iyami aikuwa Munnu tace"Baki isa ba kuwa kin bar hannunta da sauri ta karb'a ta a hannuna ta dauki towel dinta ta goya ta a bayan ta, mik'ewa nayi da sauri Iyami ta mik'o min duk abunda zamu bukata nata, nace "Granny zamu tafi gida." Tace"To Ku gaida min Ummanku da kyau kuce ta kyauta." Nace insha Allah kuwa. "Har waje Iyami ta rako mu tana d'agawa baby hannu ita kuwa sai dariya take bangala  mata tana daga  bayan Munnu."  Ganin rana ta kwalle nace dama zanga su Rambo da sun kaimu gida. Wata zuciyar tace min lallai Asma'u kina da samun shiga. Ni kaina dariya nayiwa kaina. A dai-dai sahu muka shiga nace"Munnu muje gida yau Umma taga baby inyaso sai ki tafi da ita ko."? Munnu tace "Shikkenan muje.""' Wasa nake ma baby daga bayan Munnu ita kuma sai bangale min baki take, nace"Laa Munnu kinga har ta soma hakori wallahi. " Munnu tace"Da gaske ne." Nace sakkota ki gani.' Aikuwa ta fara kokarin saukota tana dubawa, Kuka ta fara yi da alama tafi son goyon nace"Munnu mai da ita bayan baki ji yanda nake jin zafin Ku kanta Cikin raina ba." Kokarin mai da ita take, naji kira ya shigo waya ta, hankalina na can gurin rarrashinta ban duba waye me kiran ba na d'aga wayar hade da sallama.
Kukan Sweet heart dinshi ne yayi masa sallama, ranshi ya kara b'aci a fusace! Yace." Wai ke wace irin mayya ce ne? Meye alak'ar ki da baby da zakiji har gida ki dauke ta, OK naji kamar alamu kuna cikin abun hawa ne ana min gwajab-gwajab da yarinya tana kuka na rashin sabo. Maza ki mai da ita inda kika daukota tun wuri."! Hannuna ne yake rawa bakina na motsi na rasa abunda zan ce masa, Munnu dake kusa dani duk taji abunda yake cewa, hannu ta mik'a min wai in bata wayar , domin in fidda kaina a gurin shi nayi saurin bata wayar ta karb'a a nutse tace"Yallab'ai barka da rana." Jin muryar da bata Asma'u ba ya amsa da " Barka dai wacece ke."? Munnu ta tsorata jin muryar sa a kausashe!! Tace." Munnubiya ce, dama umm! Dama.... Babanmu ne yace muzo humm nazo in d'aukar masa baby Aysha yana so ya ganta.......... Sam bai gane Abunda take nufi domin shi har ga Allah ya mance da Kawun Mimi wato babban su Munnu, yace." Ke! Bana son shashanci dallah!Ku mai da min da yarinya wato wayar ta baki domin Ku shirya  karya ni sa'anku ne."!? Cikin tsawa ya fad'i maganar! Nan Munnu ta kara daburcewa tace"Da gaske ne kayi hakuri Wallahi an turo ni daga gidan profesor Muktar Gyaranya ne ni 'yar shi CE" sai da ta fadin sunan Profesor Muktar sannan ya tuna da Mutumin , kashe wayar yayi ba tare da yace komai ba .Munnu ta kalleni tana dafe k'irji tace"Bala'i wannan guy anyi masifafe irin sune suke rigima da matayen su akan 'yaya gaskiya yana do son "yaya tab!!!!!!!

Girgiza kaina nayi ina tunanin abunda zanyi na huce takaicin abunda guy nan yake min aka 'yar Mimi wai ni yake kira da mayya lallai duniya. Ji nayi wasu hawaye na kokarin zubo min. Cikin zuciya ta nace zaka cigaba da kirana da wannan sunan indai akan baby ne. Nafi maye ma maita!
Umma taji dadin ganin baby sosai ta karbe ta ta rungume ta sosai a jikinta tana kallon Munnu tace"Ki bar min ita ta kwana a gurina gobe sai ki zo ki dauke ta ki kaita can gidan NAKU." Munnu tace"To Shikkenan, haka tayi mana sallama cike da jin kunyar Umma.

****
Amjad Kuwa bayan futar Su Asma'u ne ya kira wayar granny domin ya ji gwalatun babyn shi dama baya minti ashirin bai kira waya ba,  kawai granny tace masa wai su Asma'u sun zu sun tafi da ita, a lokacin ji yayi kamar ya bar Abunda yake yi ya dira najeria ya  yaga yarinyar saboda rashin zuciyarta har granny ma sai da ta fuskanci b'acin ransa dama ta saba indai akan baby ne rufe ido yake yayi kamar bai San mutum ba shiyasa Iyami take takatsatsan dashi, kashe wayarta tayi ta k'yale shi shine fa ya kira Asma'u a waya ya sauke mata rashin mutumci, ya Riga ya saba da baby kullum kafin yayi bacci sai sunyi hira Sam bai ji dadin wannan Abu ba, Dan dai kawai yana ganin mutumcin Mutumin ne.

****
Kwata kwata na mance da rashin mutumcin da guy yayi min, hidimar baby kawai nake yi yini Abu daya. Don har gidan aunt  Hauwa mukaje da ita wai lallai sai na bar mata ita naje bazan iya ba. Ko sallama banyi mata ba na futo daga gidan.

Misalin goma na dare na gama lallab'ata tayi bacci na bude data muna hira da Mujahid, kira ya shigo wayata, ina dubawa naga numbar k'asar waje ne sai nayi mamakin waye zai kirani da wannan numbar ne. Cikin sanyin murya nayi sallama, nashi b'angaran yaji wani irin fad'uwar gaba jin muryar ta da alamun bacci ta kashe masa jiki,  gyaran murya yayi yana kokarin dai-dai ta nutsuwar shi, yace." Ki duba na miki magana ta whstsap ki bani amsa yanzu."! D'iff! Ya kashe wayar mik'ewa zaune nayi da sauri ina kara duba numbar, tabbas shine domin numbar irin ta d'azu ce da ya kira lokacin muna a dai-dai sahu. Messages na fara dubawa Aikuwa na ga nashi can k'asa, ni ban ma San sanda ya shigo ba, girgiza kaina nayi kawai na bude ina dubawa.

_Ki turo min numbar wannan k'awar taki ina so muyi hira da Sweetheart_

Abunda ya rubuta kenan. Na karanta ya Kai sau goma da gayya na kashe data ta ganin yana online nasan ni yake jira. Cikin rashin sa'a kuma Jahid ya kirani a waya ganin na rufe data yace." Ko bace zakiyi ne naga kin rufe data gashi ni kuma ban gaji Da jin muryar ki ba." Nace"Nima haka my Jahid muyi hira mai dad'i aikuwa muka dinga hiraramu ta soyayya

Amjad nashi b'angaran yana sauraron yaga ta turo masa da numbar Munnu kawai sai yaga ta rufe data kuma gashi ta ga sakon bashi,ranshi a b'ace " ya fara kiran wayar ta a karo na biyu . wayar taki tafiya sai ace masa busy ya kira ya kai sau goma busy jifar da wayar yayi kan bed din da yake kwance yana Jan wani mutsiyacin tsaki tare da mamaki dawa take yin waya tsawon wannan lokacin..........................





*28/11/2019*
[11/29, 9:22 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO*

*MALLAKAR_ BINTA UMAR*

*LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI*



*67*




Mun fi rabin awa muna hira da Jahid a waya sannan yayi min sallama tare da fad'in"My Wife insha Allah, kiyi bacci mai dad'i kuma kiyi mafarkin kina gidana da yardar Allah." Cike da kulawa nace"Insha Allah Jahid zan kwana mana addu'a ni da kai." Sosai yaji dadin kalamai na cike da farin ciki ya kashe wayar......Mik'ewa nayi nima na futa domin wani irin futsari ne ya kulle min Mara, tsakar gidan shuru Umma ta juma da yin bacci, ina dawo wa na tadda baby ta farka tana cilla k'afafu daukar ta nayi da sauri don kar tayi min kuka, ruwa na fara bata sha ina kokarin bata madarar ta naga ta zura k'aramin ya tsanta a baki tana tsotsa bacci ya dauke ta, ajiyar zuciya na sauke na gyara mata kwanciya na kwanta kusa da ita, bacci ya soma fizgata naji  shigowar kira waya ta na manta ban kashe ba, idona a lumshe na dauki wayar ina dubawa tsaki naja kamar in kashe wayar sai kuma wata zuciyar tace dauki kiji me zai miki." "Hello." Abunda na fada kenan kamar me ciwon baki,,  sama-sama naji shi yana fadin"Ke ni kika rainawa hankali na miki magana kin share ni, kuma na kira wayar ki kina waya Lokaci mai tsayi! Nace "Ki turo min numbar Munnubiya ko." Kamar wani Ubana haka yake min magana da masifa! Cikin sigar kuntatawa nace"Ni fa duk ka dame da wani surutun ka, bani da numbar Munnu ko ina da ita ma bazan bayar ba, ba dai a kan 'yar kake min wannan hayaniyar ba Tom sha kurumin ka baby Aysha na gurina yanzu ma ta farka daga bacci na bata ruwa tasha, ka cigaba da kirana mayya a kanta wallahi dad'i nake ji, maganar da wa nake waya bai dame ka ba, mutum na son yayi bacci an dame shi."!! Kashe wayar nayi gaba ki d'ayan ta, wani irin sanyi naji cikin zuciyata na mayar masa da Martani Nasan yau da kyar in zai iya bacci.

Aikuwa sakato yayi da waya a hannu yana kallon abun kamar almara baby Aysha na hannun Asma'u wato duk kauce kaucen sa yarinyar nan sai da taje ta dauko mata sweetheart, yasan halin Asma'u farin sani bata munafurci yasan da gaske take, shifa yanzu babu wacce yake jin haushi sai granny domin yana ganin itace ta bada fuskar a dauko masa 'yar sa, da kyar bacci ya dauke shi yana tunanin maganganun da Asma'u ta dankara masa. Abunda yafi tsaya masa a ransa shine tunanin da wa take waya, yasan dai idan da 'yar uwarta mace take waya baza su kai kusan a wa guda ba, wata zuciyar tace masa ko Mujahid ne? Take ya yardar wa zuciyar sa shi din ne....... Cike da tunani. Ta da mafarkin sweetheart d'insa yayi bacci. Ko da safe ma da ya tashi babu kuzari a jikinsa har abokansa suka gane, nan yace musu baya jin dad'i ne kawai, yini yayi a kwance yana kewar gwalantun baby kuma yayi alk'awarin bazai k'ara kiranta a waya ba balle ta kara fada masa magana shifa Yanzu neman hanyar da zai yi nesa da ita yake saboda alak'arsu da Mujahid.

Da safe da kyar baby Aysha ta yarda da Umma lokacin da zan tafi skull ma sai Goya ta Umma tayi ta shige da ita daki don kar taga futata ko gilmawa ta ta gani zata fara zillo idan kuwa ban dauketa ba sai ta sanya kuka.

Koda muka had'u da Munnu a skull cewa tayi wai kunyar Umma take ji baza ta iya zuwa ta dauki baby ba, sai nace ta bari zan kawo ta insha Allahu. Bayan sallahr la'asar na fito tsaf dani baby na bayan Umma a goye ta sauko ta, ina kokarin sab'ata a kafad'a Umma tace"Ki Goya ta akwai sanyi- sanyi hadarin nan ya zama sanyi, towel din na karba na Goya ta sosai na saki hijab kana nayi wa Umma sallama, gidan su Munnu na nufa kai tsaye.

*****
Ummansu Munnu tayi farin ciki sosai ta karb'i baby ta goya ta tam a bayan ta har sai da tayi bacci ta tashi sannan ta sakko da ita, tace " Ya kamata a gwada bata abunci fa." Dariya nayi nace"Ta isa cin abunci yanzu."? Tace"Bari ki gani." Wake ta Mirza ta sanya mata a baki Aikuwa baby ta lamushe ni da Munnu muka dinga dariya, Ummansu Munnu tace"Yaran yanzu da wayon su ake haifar su, gashi dai daga laluba mata wake ta lamushe, haka Ummansu Munnu tayi mata kusan sau biyar sannan ta k'yaleta ta bata ruwa, kuma Allah ya taimaka bata yi kuka ba, sai bayan magariba Babansu Munnu ya dawo gida, ya dauki baby Aysha yayi mata addu'a hade da sanya mata albarka yayi mata addu'a sosai da sosai kana ya sanya k'aramin yaron shi yaje kanti yayi mata siyayya sosai kalolin biscuits iri-iri Ummansu Munnu tayi ta dariya tana fad'in "Irin wannan siyayar akai wa kishiyata alhalin gani a zaune ba'a min ba, dadin abun dai cin abunci ma ni na koya mata." Baban su Munnu yace." Da kin sani Baki koya mata ba ai." Mudai dariya kurrum muke musu, hira muke da Munnu sosai wacce ta dauke min hankalina sai da Ummansu Munnu ta leko dakin tana fad'in "Asma'u ko anan zaki kwana ne ga hadari nan yana had'owa." Agogo na kallah da sauri naga tara shaura da sauri na mike INA fad'in "A'a wallahi Yanzu zan tafi." Baby na dauke wacce ta Dade da yin bacci na Goya ta da sauri na zura hijab na fito wani bakin hadari na gani a gabas Nace"Munnu Allah ya kiyaye ni da dukan ruwa." Tace "ameen dai amma ni shawara ta ki bari sai gobe kawai kya tafi." Ko kallonta banyi ba nayi hanyar futa ina sallama da Ummansu dake Uwar daki.
Ina futowa titi aka fara wata irin iska mai k'arfi abubuwan hawa sai gudu suke akan titi duk yawanci motocin gida ne da kyar na samu a d'an sahu Wanda ya rage mutum d'aya a ciki na shiga aikuwa kamar almara ruwa ya kece kamar da bakin kwarya,ni da nake gefe ruwa ya fara duka na, kafin kice me na jike jagab, ta karewa nayi ina tsoran kar ruwa ya taba baby sai ta fara motsi tana k'ananun kuka, gaba na ya fad'i jijjigata nake yi INA so tayi shiru yarinya kamar wacce ake zugawa  ga feshin ruwa sai dukan fuskata yake, kamar zanyi kuka nace "Don Allah kayi sauri babyna na Kuka."! Mai dai-dai ta yace." Hajiya ai ina ganin parking ma zanyi saboda ban San iya inda ruwan zai tsaya ba, domin karfinsa yayi yawa sai ya tsagaita sai mu tafi." Kafin ince komai ya tsayar da 'Dan sahunsa, nace"Na shiga uku ni Asma'u nayi da na sani tawowa da na hak'ura na zauna na kwana gidansu Munnu zai fi min, tausayin baby nake ji jin yadda take sakin ajiyar zuciya tana baya sai kyarmar sanyi jikinta yake yi, ni da ita duk mun jike matan dake a dai dai ta na kalla naga sai hirarasu suke yi babu abunda ya dame su, su kadai ne single babu wacce take da yaro Karami balle tayi fargaba. Sai da aka dauki 30minutes ana ruwa mai k'arfi sannan ya tsagaita sai wata irin iskar sanyi ta soma kadawa, a lokacin naji Baby ya fara atishawa sakkota nayi ina duba jikinta, naga jagab duk da dabarun da nayi mata sai da ta Nike hatta da gashin kanta, kuka take so tayi ta kasa sai sakin atishawa take, hawaye na fara sharewa kana na rungume ta tsam! A jikina Ina fadin"Duk nice na jawo miki babyna."!

Jagab! Muka shiga gida muna d'igar ruwa Umma na gani cikin ruwa ta dinga min fada "Shin baza ki bari gobe idan Allah ya kaimu kya dawo ba, ko kuwa gidan su Munnu din bak'on ki ne.? Ko tausayin k'aramar yarinya bakya ji sai kinje kin kwaso mata mura da da tari ko." Fada sosai Umma take min, ni kam hankalina na gurin baby wacce take ta motsi majina har ta fara zurara a hancin ta, kayan jikinta na cire mata da sauri na sanya mata Pampers na sanya mata kayan sanyi masu kauri kudindine ta nayi. Umma tace"Bani itanan mu gani." Mik'a mata ita nayi, ina tsaye da jikakkun kaya ban damu da In cire su ba, duk da nima hakan take kamar baby kwata kwata bana son dukan ruwan sama Shikkenan zazzab'i da mura zai kama ni. Robb Umma ta dinga Mirza mata k'irjinta da bayan kunnen ta, da tafin kafarta sannan ta Goya ta.
Futa nayi jikina duk babu kwari, har yanzu da ragowar ruwa kadan kadan yake sauka d'akinta na shiga na kwabe kayan jikina pant fa breziyya ta duk sun jiki jagab suma sai da na sanya sabbi, sannan na dawo rumfar Umma na shafa Robb din duk jikina, can k"uryan dakin ta na shige na k'udindina jikina ina jin shigar zazzab'i. Sama sama naji muryar Umma tana fadin "Yarinyar nan zazzab'i ya kamata ga k'irjinta yana harbawa duk da cewa dare bai yi ba sosai ki kira Mujahid a waya yazo ya kawo mata magani duk ke kika jawo mata." Futowa nayi jikina lullub'e da zanin gadon Umma saboda sanyi da nake ji nace"Umma har dani za'a kawo wa magani domin nima zazzab'i har ya rufe ni wallahi." Umma tace." Ai kema kin San kanki ganganci ne kawai." Handbag dina dake yashe a gefe INA dauka ina kokarin fito da wayar naji duk abunda ke ciki ya jike har wayar, na dauko ina gogewa abunka da babban Abu ina kunnawa ta kama, numbar Mujahid na fara kira... Ya dauka a nutse muka gaisa na fada masa halin da ake ciki. Take yace gashinan zuwa. Kashe wayar nayi na mike har zan shiga daki na dawo ina lekan fuskar baby dake bacci a bayan Umma kanta na taba da hannuna naji zafi rad'au! Gefan Umma na zauna zuciyata duk babu dad'i Jahid kawai nake jira ya zo. Cikin daran Mujahid ya kawo mana magunguna ya fada min yanda zan bata, Cikin ikon Allah da na bata maganin zazzab'in  tsakanin 15mintus zuwa 20minuts zazzab'in ya sauka sai dai majinar da take zuba har yanzu. Maganin na kwanta baby kam a gurin Umma ta kwana domin tunda na sha maganin bacci me nauyi ya dauke ni, Ko da safe wayar Jahid ce ta tashe ni, yana tambayar jikin Baby dalili shima Amjad tun asubah ya kira shi a waya shi ya dauka ma ko har ya samu labarin abunda ya faru yake fad'a masa a jikin da sauki Amjadu ya shiga mamaki sosai ya kira wayar Jahid din ne a matsayin sa na mskusanci ga Asma'u ya sanya ta ta maida baby gida kafin ya dawo domin shi yayi alk'awarin bazai kara kirararn ta a waya ba kawai yaji yana masa wata magana. Bai nuna bai sani ba sai yayi shiru kawai yana sauraron  Jahid, shi kuma ya cigaba da cewa "Hakane da ma idan ruwan sama  ya daki k'ananun yara zasuyi ta fuskantar wannan matsala kafin jikinsu yayi k'wari gobe insha Allahu nake so na auna ta sosai saboda ina gudun nimonia ganin yanda take Jan numfashi da kyar."!

Take ya fahimci inda maganar take wato ruwan sama ne ya doki sweet heart dinsh, babu walwala a tare dashi yace." Jahid idan na fahimci maganar ka kana so kace min ruwan sama ya tab'a lafiyar baby Aysha hakane ko.'? Jahid yace." Eh mana ai na dauka ka sani kaima maganar zakai min." A kaurare yace." Inso in ce dakai ka sanya Asma'u ta mai damin yarinya gida sai naji wannan mummun labarin daga bakinka Asma'u taje ta dauko min yarinya ba tare da yadda ta ba shine dalilin kiran da nayi maka, gaskiyar magana Mujahid Dan dai Kaine ina ganin girman ka a idona amma da sai na dauki mataki kan Asma'u tunda abunda ta shirya min kenan kan wane dalili zata futa da k'aramar yarinya ruwa ya dake ta, kaga irin sakacin da nake fada maka ko, ita bata rike kanta ba taya ya zata iya rike wani."!! Ya k'arashe maganar tasa a zafafe! Jahid yace." Gaskiya bata kyauta ba gani bata gayamin haka ba, amma kayi hakuri don Allah komai ka gani tsautsayi ne amma tabbas bata kyauta ba. " Cike da takaici yace." Yau kwana biyu rabona da in ji sweetheart nayi kewayar jiya babu yanda banyi da yarinyar nan ba ta bani ita muyi hira ta kashe min waya, ni da yarinya ta." Jahid yayi murmushi tare da fadin"Sai kace Wanda zakayi hira da babban mutum ka kwantar da hankalin ka zaka dawo ka yadda sweetheart dinka cikin koshin lafiya." Ajiyar zuciya ya sauke yace." Insha Allah karshen watanan zan dawo zan je Umara insha Allah." Jahid yace." Alhmdullahi kayi mana addu'ar zaman lafiya ni da Asma'u da samun zuria mai kyau kasan karshen wayan aka sanya lokacin d'aurin auranmu." Amjad yaji wani irin fad'uwar gaba ta rikito masa zan can yazo masa a baza ta! Yace." Jahid yaushe aka sanya rana babu labari."! Jahid yac."Wallahi my friend abun yazo a bazata kuma a kurararn lokaci Dan har yanzu hankalina ba a kwance yake ba dalili Momyna bata kaunar auramu da Asma'u, shine nake cikin wani hali shaf na manta ban fada maka ba." Cikin dakiya da kokarin danne damuwa yace." Na tayaka murna Aboki amma INA baka sha'wara cewa ka bi umarnin iyaye domun Neman albarkar su, ina ganin tunda Momy tace bata so kayi hakuri mana ka bari."! Jahid yace." Wallahi nayi kokarin hakan na kasa INA yiwa Asma'u wani irin so Wanda nakasa gane irin shi ka tayani da addu'ar Neman zabin Allah." Girgiza kansa yayi yana jin wani daci Cikin zuciyar sa yace." Insha Allah zan sanya ka a addu'a. " Jahud yace." Nagode my Aboki. " Amjad yayi murmushi tare da fadin. " ka kula min da baby please kuma ka sanya ta ta Mai da ta gurin granny yau INA son muyi hira da ita please. " Jahid dariya kawai yake masa sukayi Sallama. "

***

Babu laifi Zazzab'i ya sauka daga kaina sai baby ce take fama sosai Jahid da yazo kafin ya tafi gurin aiki ya fada min duk yanda sukayi da Amjad din na dinga mamakin rashin kawaici irin nashi nace"Insha Allah Jahid ko baka fada bs yau din nan zan mai da masa yarinyar gida nagaji da wannan gorin wallahi,." Jahid yace." Baki fahimce shi bane shima yana da tasa manufar shiyasa ." nace "Jahid Dan dai abokin ka ne kake kareshi dariya yayi min tare da fad'in"Ya jikin baby dim nace DW sauki kam hancin ta ya daina yoyo sai dai zazzab'i"Yace shima zai sauka Insha Allah." Godiya nayi masa shi kuma ya tafi tare da jaddada min in mai da baby gida nace insha Allahu." Ko da na fadawa Umma abunda mahaifin. Baby yace a kanta sai tace aikuwa baza a maida ita gida tana cikin wannan yanayin ba, Sam baza a fita da ita ko ina ba kasamcewar akwai sanyi a gari har yanzu kuma da akwai sauran hadari, shuru kawai nayi ina jiran Abunda zai biyo baya.

****
Duk abunda yake yi k'arfin hali yake tunda yaji labarin d'aurin auran Jahid da Asma'u ya nemi nutsuwar sa ya rasa hak'ika al'amarin yazo masa a bazata! Kullum ta Allah kokarin sa ya yakice yarinyar daga rayuwar sa, abun ya fassakara duk abunda yake mata yana sane yake mata domin ya kuntata matane suyi fad'an da zai ji tafi ta a ranshi gaba daya amma dake yarinyar taurin rai ne da ita taki yadda suyi fada da ita sha fa yanzu gani yake babu yadda za'ayi ya auri Mimi daga baya kuma ya aure Asma'u a da dai yayi niyyar ya hadasu ya aura dalilin son da yakewa Asma'u, sai bayan ya auri Mimi ne ta koya masa sonta kyawawan haleyen ta suna burge shi, a wannan zamanin dai samun mace kamar Mimi sai an tona... Yini yayi yana tunanin Abu d'aya. K'arfe goma na dare dai-dai ya jira granny dake shirin kwanciya, ta dauka suka gaisa Yace. " Granny bani baby Aysha ko tayi bacci ki tashe ta kinji."" Cike da mamaki tace." Wai kai baka da lokacin kiran waya ne sai dare."? Yace." Time din nake da sukuni ki bani sweetheart please."Ya wani marairaice murya. Tsaki yaja tace." Wace baby kuma wacce take gidan kakaninta." Tashi yayi da sauri yace." Me kika CE Granny. "!? Cewa nayi baby na gidan kakanin ta, yo ko tans gurina kana tunanin zan tashe ta daga bacci saboda shirmen ka." Kashe wayar sa yayi ba tare da ya tsaya ya gama sauraron Abunda granny take fada ba.
Wayar Asma'u yake kira, busy yau ma tana waya da wani, zuciyar sa kamar tayi bundiga ya jefar da wayar kan bed d'in ya  dafe kanshi da duk hannunwan shi biyu.




*29/11/2019*

*BABBAN YARO*

*MALLAKAR_BINTA UMAR*

*68*

Yafi Rabin a wa a Zaune a gurin sannan ya mike Cikin mutuwar jiki ya shiga toilet alwala ya dauro ya fito yana hada hanya, dadduma ya shimfid'a ya fara sallahr nafila cike da Neman zabin Allah domin shu kanshi al'amarin sa tsoro yake bashi. Komai ya da gule masa lokaci guda, bayan yayi idar ya jima yana rokon Allah ya kawo masa dauki a rayuwar sa, yaji wani sanyi cikin zuciyar sa, kwanciya yayi kan daddumar bacci ya dauke shi mai nauyin gaske.
Ni kam bayan mun gama waya da Jahid tunani na fad'a mai tsayi zahiri dai gashi mahaifiyar shi ta nuna bata kaunata karara ko yanzu sai da ya kara fad'a min irin artabun da suke bugawa da ita kan Dole ya janye maganar saboda ta samu labarin kai kud'in da akayi a family lokacin da taje gidan buki suka dinga yi mata Allah ya sanya alkairi, sai abun yayi ta bata mamaki sai daga baya ta fahimta, shine tasa akai kiran sa, ta kare masa tanadi har tana ikirarin zata tsine masa in har bai janye maganar ba, duk yanda naso na fahimtar dashi ya kasa fahimta na lura Jahid idonshi ya rufe a kaina baya tsoron Abunda zai je ya dawo,  dole in Sanar da Umma halin da ake ciki, yanzu jikina ya fara sanyi da al'amarin hak'ika ina son Jahid tsakani da Allah kuma bazan so ya fad'a cikin halaka ba, tunani na gwara ya hak'ura kawai domin ya samu albarka iyaye da wannan tunane-tunanen nayi bacci kwata-kwata na manta da Wani Amjad da damuwar shi. Da safe duk na warware wa Umma abunda yake faruwa tace"Asma'u dama ni tuntuni sai DW nace ki hak'ura da yaron nan tunda uwarsa bata so kika k'i, kuma kin san halin Kawun Ku ba kirki ne dashi Yanzu in wata magana ta sake faruwa zasu har gida su ci mun mutunci ne ki jawo tashin hankali ya kare a kaina da ban ji ba ban gani ba." Shiru nayi wasu zafafan hawaye na zubo min duk ja rasa wane tunani ma zanyi.. Karar waya ta naji a dakinmu da sauri naje na dauko ina duba baby dake bacci cikin kwanciyar hankali, INA   dubawa naga jahid din ne ya kira sallama nayi ya amsa murya babu dad'i ya Dora da fadin"Asma'u duk abunda kike ki aje don Allah ki mai da wa da mutumin nan yarinyar shi, wallahi yai shi ya tashe ni daga bacci dama ga shi da kyar na samu ya dauke ina fama da damuwa."
Nima cikin damuwa nace"Jahid ka kwantar da hankalin ka dama yau nayi niyyar mai da ita saboda Umma tace  a k'yaleta ne yasa saboda sanyi jiya amma insha Allahu yau zan mai da ita Nima na huta da jaraba." Kashe wayar nayi a fusace! Ban saurari maganar shi ba. Hakan ce ta kasance bayan sallahr la'asar Munnu tazo gidanmu nan muka tafi domin mai Da baby kamar yanda nayiwa Jahid din alk'awari munnu tq kalleni cikin damuwa tace"Asma'u fyskar ki ta nuna alamun damuwa tabbas da Abunda yake damun ki."! Girgiza kaina nayi nace"Tabbas Munnu abokin kuka shi ake gayawa mutuwa nan na kwashe duk abunda yake faruwa na fada mata har irin rashin kunyar da nayi Monye Jahid din sai da na fad'a mata. Munnu ta dinga mamaki daga bisani tace"Wallahi wasu masu kud'in haka d'abi'ar su take Sam basa son talaka kiri-kiri ta zo har gida ta ci muku mutumci saboda zubar da girma yanzu kuma idan mukayi aura kuka Tara zuria tace me? Da aure da mutuwa duk na Allah ne mutane ne basa ganewa wallahi." Nace"Ke wace shawara kike gani." Tace"Kawai ki cigaba da nan zabin Allah idan da Rabin auran Ku za'ayi dashi amma ko da wasa kar ki nuna masa kin karaya domun kinga shima yana daurewa gashi saboda ke ya bujerewa mahaifiyar sa." Da wannan zancan muka isa. Babu walwala a tare damu muka shiga, Iyami da Granny na zaune a parlor kamar ko da yaushe ta amsa mana sallama a sake Iyami kuwada saurin ta ta k'araso gurin mu tana fadin "Oyoyo baby kokarin daukar ta take yi nayi saurin kwantota ta dauke ta tana cilla ta sama, yarinyar ta gane ta sai ta fara yi mata dariya. Zama mukayi a nutse muka gaisa da granny dake tambayar mu Umma nace" Tanan k'alau tace ma a gaishe ki da kyau kafin tazo." Granny tace"Ina amsawa nima...Iyami kawo musu abunci." Tafad'a tana kallon Iyami dake wasa da baby  Granny ta karb'i baby ta nufi kicin, cikin zuciya ta nace yau kam baza muci abincin gidannan ba wallahi Mik'ewa nayi Munnu ta mike granny ta bimu da kallo tana fad'in"Za'a kawo muku abunci kun mik'e." Nace"A koshe muke Wallahi." Cikin nazari tace" kamar akwai abunda yake samun Ku kun shigo babu walwala kinji sakewa Lamar yanda kuka saba, yake kawai nayi nace"granny kenan babu komai wallahi mu dai mun tafi sai mun sake zagayo wa." Hanyar futa muka nufa Abun kamaer almara babyta fashe da kuka tana d'ago hannun ta! Granny tace"To maza Ku dawo Ku tafi da ita gashinan tana kukan rabuwa da Ku
" gaba nayi cikin zuciyata nace yarinyar nan ko kukan me zata yi bai same ni ba wallah" Munnu CE  ta koma da baya ni kuwa tuni na fuce da sauri, ina jiyo kukan ta har waje, ko da Munnu taje kin yarda tayi da ita sai kuka take yi Granny tace"Asma'u take nema ba ke ba. iyami ta kwalawa kira tana fadin "Bazan iya da wannan rigimar ba zo ki dauke ta yarinya k'arama da gane mutane." Iyami ta shigo da sauri ta dauke ta tana rarrashin ta, Munnu tace "Asma'u baby ta gane ki sosai wallahi har nayi sha" awar Dadyn ta ya Baki tunda kuna kusa in Allah yayi nufin auran ki da Mujahid." Murmushin takaici nayi nace"Munnu kenan, nasan ko mutuwa zanyi bazai bani ba, kar ki so kiji yanda nake jin zafi a zuciyata jin kukan da take yi." Munnu tace"Allah ya kyauta masa amma gaskiya na lura guy nan ya sanja hali da ba haka yake ba." "Hummm! Munnu kenan dole yayi abunda yake so tunda gonar sa a ka shiga kuma yana ganin ya wuce komai na rayuwa shiyasa." Munnu tace"Wallahi maganar ki gaskiya ce Allah ya kyauta." Nace "Ni Abunda yake damuna Abu daya ne aurana da Jahid wallahi yanzu abun tsoro yake bani ina jin tsoron abunda zanje in Tarar."! Insha Allahu alkairi zaki yadda ke dai ki cigaba da yin addu'a.'a" nace "Nagode Munnu." Da Wannan hirarar muka isa gida.

*******
Amjad zaune a harami ya d'aga hannunwan sa sama sai kwararo addu'a yake, yana zubar da hawaye ni kaina ya mugun bani tausayi, ya kai Rabin awa cikin wannan halin kana ya shafa addu'ar ya mike a nutse ya dauki daddumar sa da glass d'insa dake aje a gefe ya nufi mazaunin sa, ko da ya isa ba zauna ba toilet ya nufa cikin kuzari yati wanka ya fito fes dashi kasamcewar ana zafi bai shafa mai ba, sai ya shafe jikinsa da turare ya sanya wasu ubansu parkinsan ash coulor hade da wata hula mai kamar net fara tasa da ita, takalmi mai gidan yatsa yayi amfani dashi ya d'aura tsaddan a gogon shi, kana ya manna farin tabarau din shi a fuskarshi,  sai ya kara wani uban kyau, kasancewar ya Tara kasumba bai yi aski ba, sai abin ya bada sha'awa Amjadu ya saje da larabawan saudia domun duk kwakwar mutum bazai tab'a cewa ba balarabe bane ga yanayin fatarsa lufluf domin har tafi ta wani balaraben goge wa fuskarsa babu walwala a dauki wayoyin shi hade da wata k'aramar haka irin ta matafiya, kulle dakin yayi da key ya sauka k'asa. Amjad ya nufin koma wa gida Cikin iyalinsa bayan yaje dakin Allah yayi addu'a ga iyayen sa dashi kansa da sauran alumar musulmi.
Yana jirgi ya kira su Rambo ya Sanar musu gashinan kan hanya take suka wuce airport domin tarar sa, Granny ya kira a waya ya fada mata, tace"Amma kayi mana bazata! Mai kake so a girka ma." ? Murmushi yayi yace." Granny kuyi min Dambu da zogale." Dariya tasa tana fadin "Kasamu k'ato Allah ya kawo ka Lafiya." Kashe wayar tayi tana kiran Iyami. Tace" maza a shirya dambu mai kyau ga k'ato nan kam hanya." Iyami tace"Wallahi baby ce take kuka har yanzu taki hak'ura kawai tana wasa sai ta fashe da kuka." Dariya granny tasa tace"Tana tuno uwarta ne, jeki dauko min ita kije kiyi aikin ki." Da sauri Iyami ta dauko baby dake kuka har da majina. Granny ta mik'a hannu tana son ta karbe ta ta make kafad'a wai baza ta zo ba, dariya tayi tana fadin"Kaga ja'ira dole kuwa komai kukan ki kiyi shiru Ubanki na kan hanya. Tace iyami aje ta kije kiyi aikin ki." Iyami ta ajeta a kasan gurin ta nufi kicin da sauri. Lokacin baby ta tsandare da kuka, babu shiri granny ta dauke ta ta Goya Tana zagaye parlor da ita, Tunda ya doso kofar parlor yake jin kukan sweetheart dinshi yaji ranshi ya sosu da sauri ya shiga ciki hade da sallama k'asa_kasa granny ta amsa tana masa barka da zuwa, mamaki yake yi ganin baby a bayan granny a goye amma taba kuka, wayoyinsa ya zube kan teble din gaban shi ya fara kokarin daukar babyn da Granny take kokarin kwance ta, yace." Wai mai akayi mata ne take kuka tun kafin na shigo nake jiyo ihun ta." Granny tace"Sheganta ka ce kawai wallahi tun da taje gurun uwarta tayi kwana biyu Shikkenan ta dawo mana da rigima Don da kyar ma ta yarda da iyami, nu kuwa sai nayi da gaske nake daukar ta." Ya gane inda maganar Granny ta dosa, zama yayi cikin kujera yana goge mata fuska da hakincin sa, yace"Granny nifa bana ganin laifin kowa sai naki ke da kika dauke ta kika basu." Cike da jin haushi yayi maganar. Granny tace"To ka dawo ko zaka fara iyayin naka to me kake nufi iyayenta sunzo su dauke ta sai in hanasu ni kam ban iya wannan k'ek'e da k'ek'en ba irin naka." Baice komai ba ya sanye leb'anshi na k'asa bakin ta, kamar yanda yake mata tana jin jira, aikuwa ta kama tsotsa yarinyar bata manta ba. Kallon ta yake yana jin wani irin tausayin ta cikin zuciyarsa duk sanda zai kalleta sai ya tuna masa da Wife dinshi Mimi ko da yaje Saudia duk Rabin addu'ar shi tata ce. Baby Aysha ta fara lumshe ido kalaman bacco still leb'anshi take tsotsa kad'an kad'an har bacci ya rinjayeta ta saki. Ajiyar zuciya ya sauke ya rungume ta tsam a jikinsa tare da fad'in"Iyami ta gyara mata gurin kwanciya tayi bacci."! Granny ta bude baki zata kwalawa Iyami kira kamar yanda ta saba. Da sauri ya d'aga mata hannu yana yamutse fuska da ido ya nuna mata baby wai kar ta tashe ta. Tsaki granny yaja ta mike daga gurin. Da kanta taje ta gyara mata gurin kwanciya ta dawo zata karb'i ta kamar kurma haka ya zama Mik'ewa yayi ba tare da ya bata babyn ba ya nufi bedroom d'insa da Yarinyar granny tayi sakaro da baki, tana fad'in"On ni naga iyayi da feleke a ka dawo din zaka fara nuna mana iyakarmu ni da Iyami komai mukayi bamu iya ba hummm! Allah ya sawak'e maka."  Ni da Munnu ne zaune a Uwar dakin aunty Hauwa ta sanya muku tsuguna cikin wani dogon bokitin na k'arfe inda ta sanya wata k'aramar tukunyar k'asa da garwashin wuta had'e da wani mugun turare da wasu saiwowi masu wani irin kamshi, kullemu tayi a dakin har da Dan mukkuli, tsaki babu irin wannan banyi ba, a ganina ni budurwa CE ba bazawara ba, mai zasa aunty Hauwa ta dinga azabtar damu da turaran matsi kawai garin Neman gira a rasa ido, tunda akace saura kwana goma sha hudu d'aurin auranmu aunty hauwa ta sanya mu a gaba, domin har munnu ma da take surukar ta tace ita bata dauke ta a matsayin suruka ba, k'anwar tace duk abunda zata min zata yi mata, kuma bayan haka Si Dan uwanta take gyarawa Munnu tun tana jin kunya ta daina ji domin yau kwananmu uku a gidan aunt Hauwa tana yi mana izaya iri-iri, magani kullum ta dama da nono mai Dan iskan bauri da wani irin k'amshi kai hawa ka taje sai mun shanye tasa, wallahi ina daga tsigar jikina na Mik'ewa saboda yanayin dandanon sa a bakina babu dad'i bauri yaji zak'i d'aci duka, ranar dai da taba ni zubarwa nayi Munnu kuwa saboda kunya sai ta shanye tasa ta aje kofin ni kuwa kullum rigima muke da ita kan hakan. Yanzu ma Mik'ewa nayi da sauri jin wani Abu na zuba daga k'asa na, zani na nasaki na mai da pant dina. Munnu tace"Ya kika tashi ne." Cikin b'acin rai nace"Munnu ke in zaki zauna zauna ki cigaba da azabtar da kanki kina budurwa ace wani Dole sai kin matse mtssss to wace irin katsewa kuma ake buk'ata. " munnu tace "Don Allah ki koma ki zauna Wallahi tunda kikaga ta dage akanmu hakan yana da amfani." Tsaki naja nace"Sai kiyi ke ni dai na gaji." Kofa na nufa ina bugawa hade da kiran sunan aunt hauwa nace"kizo ki bude min zan shiga band'aki. " bude min tayi taba fadin kiyi sauri ki fito kar maganin ya sane so nske ya bi jikin Ku sosai." Hararata nayi ganin ta juya baya zumb'ura baki nayi na shiga band'akin ta dake parlor. Ina tsungawa naga ni bu mai yauki na dilala daga gabana, dama tun da aunt ta sanyamu a gaba nake jin  wani azabbaban feelings na taso min. Ruwan zafi cikin wata butar.k'arfe na dauka na daureye gurin sosai sannan na fito raina duk babu dad'i





*30/11/2019*

*BABAN YARO*

*MALLAKAR BINTA UMAR

*69*

Shirye-shirye ta kowa wane fanni ya kammala Ya Aminu ya had'a lefe na gani na fad'a sosai Umma da aunt hauwa sukayi kokari a kansa, yanzu nawa lefan ake jira sai a fara Rabin goro kullum muna tare da Jahid a waya muna shirya tsarin buki da yanda zai kasance.

  Momyn Mujahid ce take kai kawo a parlor ta takasa tsaye ta kasa zaune wato Mujahid ya yaudare ta ya rufe ta sun hada baki da ubanshi ya bujerawa bukatar ta, lallai ne ka haifi da a cikin ka ya wulakanta ka lallai zata nuna masa iyakarsa, yanzu ta sakko daga sama dalili shi mijin NATA ya kira ta tazo taga kayan lefa kuma saboda sun raina mata hankali wai itace zata nemi masu kaiwa don haka baram!_baram suka rabu da mijin nata ta sauko a fusace jiran zuwan Jahid din take domin tayi masa magana ta k'arshe kan auran.

  Tunda ya shigo yaga tana kai kawo hankalinsa ya tashi yasan dole duk abunda yake b'oye wa ta sani, ko k'araso wa bata bari yayi ba ta karasa gurinsa a zafafe ta zabga masa mari Tana huci! Kamar zakanya tace"Ni zaka yaudara Jahid wato kun hada haki da ubanka kun rufe ni saboda baka dauke ni a bakin komai ba ko? Jahid yayi shiru hade da yin kasa da kansa. Ta cigaba da cewa "Wallahi in har nice na haifeka baza ka auri yarinyar da ta zageni ba, idan kuma kayi ganganinci auranta to babu shakka a ranar zaka sake ta ko kuma in d'aga maka nono don tsine maka zanyi wallahi tallahi kaji domin bazan yi kaffara ba."!!! Ta k'arashe maganar tata a zafafe! Ya wani irin huci!
   Jahid ya shiga cikin wani irin mugun yanayi a lokacin gumi ya dinga tsiyayar a jikinsa duk yanda yaso ya fahimtar da mahaifiyar sa al'amarin ta kasa fahimta. Wasu mazan sukan fuskanci matsala daga gurin matayen su a sanda zasu kara aure, shi daga gurin mahaifiyar shi ya fuskanci matsala. Mik'ewa yayi baya ko kallon gabansa, ya fita daga parlor. Wani irin kallo ta bishi dashi ta ta tabka wani irin tsaki, ta zauna kan kujera tana fadin" da in hada jini da talaka gwara duk abunda zai faru ya faru.

   Jahid kuwa kai tsaye b'angaran Amjad ya nufa a lokacin hankalin sa a tashe! Granny na ganinsa cikin wannan halin ta tabbatar babu lafiya, zama yayi kan kujera hade da dafe kansa, granny Tace "Tabbas komai yayi tsanani maganin sa Allah, Mujahudu akwai damuwa a tattare da kai. Ya d'ago kansa yana kallonta, kawai sai taga hawaye a fuskar sa yana zubah, cikin mamaki tace" kafadamun damuwar ka Insha Allah zan taya ka da addu'a. " Cikin karkarwar jiki ya warware mata dukanin abunda yake faruwa. Granny ta jima tana mamakin al'amarin daga bisani tace"Tabbas Hajiya Sa'a ta tabka babban kuskure, waye ya fada mata ana jayayya da al'amarin aure duk yanda bakason hada zuri'a da mutum idan Allah ya kaddara faruwan haka babu makawa sai ya faru idan tana tsananta kamar Yanzu Allah sai ya dauke ta ayi babu ita, tashi muje gurin ta." Jahid ya mike da sauri ita kuma dauki hijab dinta ta zura, suna fita motar Amjad na shigowa gidan, yana kwance a bayan mota ya hango Jahid din da granny sun nufi motar sa, duk da cewa Jahud ya fahimce shine bai tsaya ba, da gudu ya fafari motar sumar bar gidan.. Shi kuma Amjad sai dinga tunanin ko wanine babu lafiya cikin iyalin Jahid din, ya dauki granny domin taje ta dubasu. Sam bai kawo komai cikin ranshi ba, ya shiga gida yanayin tozali da sweetheart dinshi ya manta da koma.

   "Sosai granny take fahimtar da Momy amma ta gagara ganewa da k'arshe ma so tayi tai mata rashin kunya inda take fadin" Kinga Hajiya d'anki ko nawa da zaki dame ni lallai sai na yarda, shin kin Sam irin rashin mutumcin da yarinyar tayi min kuwa, tsinanniyar yarinya mummuna 'yar gidan malam shehu irin wannan har ta kalle mu ni da aminyata tace muna warin dauka da bleecing a i wallahi Jahid ya sake ya auri yarinyar nan sai na tsinke masa."

    Granny tace"Ki daiyi hakuri Asma'u yarinyar arziki ce Wallahi akasi aka samu kuma hada zuria dasu akwai albarka Hajiya baki San ko akwai rabo tsakininsu ba, sai ki mutu saboda wannan abunda kikayi ubangji baya so." Jin abunda granny tace ne yasa Many zuburowa! Tace"kaji ni da tsohuwar najadu tsohuwar kawai! To wallahi sai dai idan kece zaki mutu,au!! Fatan mutuwa kike mun, aikin banza to wallahi ba yanzu zan mutu ba." Jahid ya Dora hannunsa aka cikin tsantsar tashin hankali da nadamar dauko granny inda yasan wannan cin mutumcin za'ayi mata da bai dauko ta ba, ya zama dole duk son da yake wa Asma'u ya hak'ura da ita, domin yana hango mugun rikici a gaba idan ya aure ta Hausawa suka ce idan so cuta ne hakuri magani ne, nan ya mike ya futa daga parlor a karo na biyu, granny ta mike cike da taikacin da b'acin rai tace"Duk yanda naso nussashe dake kin kasa ganewa har kina Neman kiyiwa danki baki, ni zagin da kikayi min bai dame ni ba, tunda kin kwatanta hali irin na Asma'u da kike cewa bata da tarbiyya Shikkenan na barki lafiya." Momy yaja tsaki da k'arfi tana fadin "Allah ya rakataki gona, nace Umma ta gaida Ayshaaaaas."! Granny ko juyowa batayi ba cike da takaici da damuwa ta samu Mujahid tsaye a gurin yana kiranta, mota ya bude mata ta shiga da sauri suka bar gidan. A hanyarsu ne granny take rarrashin sa da kalamai masu sanyi kana tace " Tunda mahaifiyar ka ta nuna bata so tom shawarar da zan baka ka hak'ura ka kwantar da hankalin guri guda rashin Asma'u ba zai hanaka rayuwa ba insha Allah zaka cigaba da rayuwa Cikin amincin Allah da yardar sa, idan Aure kake so ka sake samun mace wacce zucuyarka ta kwanta maka sai is aura mutukar ta amunce din, wannan shine shawara kayi wa uwarka biyayya." Amjad yace." Granny ban taba nadama akan al'amarin auran nan ba sai yau, da Momy ta ci miki mutumci kawai domin kina so ki fahimtar da ita, insha Allahu na hak'ura da Asmau amma INA Neman wata alfarma  agurun ki." Tace" kafad'a komeye insha Allah mutukar INA da iko dashi zanyi maka." Yace." Inaso al'amarin auran nan ya koma kan Amjad ba tare da sani ba inaso ne ranar d'aurin aure yaji bazata !."

   Granny tace'' hak'ika ka cika Aboki na gari Mujahid kuma idan kayi haka babu shakka ka kyauta min, domin ni kaina ina tunanin matar da zai je ya auro wacce zata kula da baby Aysha tsakani da Allah,Dole sai ita Asma'u da take a matsayin Uwa a gare ta, mungode mutuka da alkairi ka." Jahud yace." Granny Amjad yafi k'arfin komai a gurina wallahi." Tace"Yanzu abun damuwar shine ita Asma'u kana ganin ba'a shiga hakkinta ba."? Murmushi yayi yace." Nasan inda zanyi da ita itama baza tasan abunda yake faruwa ba har a d'aura aure zanje cigaba da zuwa gurun ta babu abunda zan FASA, gefe guda kuma zan je na nemi Kawun ta mu kashe magana." Granny tace"Kayi nufin alkairi Allah yayi maka jagora Kai kuma ubangiji Allah ya sanja maka mafi alkairi. " murmushi yayi ya cigaba da driving har ya sauke ta gida ya wuce ofis din mahaifinsa domin ya Sanar dashi abunda ya yanke,  to shima bai Wani jayyaya ba tunda dai Shi Jahid din yace ya hak'ura to shi meye bashi sai fatan alkairi yayi yace inda Allah zamu cigaba da shirye-shiryen d'aurin aure kamar yanda muka tsara, Cike da kwaran gwiwa Jahid ya nufi gurin Kawu Yunusa, duk abunda yaje faruwa ya Sanar dashi a bazata Kawu yaji al'amarin dad'i kamar ya kashe shi sai ya dinga shiwa Jahid albarka kamar me."take ya shaidawa 'yan uwansa suka soma shiri amma ya gargadesu da cewar bayaso maganar ta futa har Asma'u taji. Suka ja bakinsu suka yi shiru.

    Duk wasu shirye-shiryen Jahid ya kammala su dai-dai da kayan da zasu sanya ranar d'aurin aure suna hannunsa hakanan kayan lefe na kece raini da ya yahadawa Asmay an kai kwanaki uku da suka wuce, shi ta b'angaran sa komai ya dai-dai ta. A zahiri ya nunawa Momy nsa ya janye maganar shiyasa ta saki ranta, kuma Mijin ta bai kara tayar mata da maganar ba sai ta yadda da maganar.

   Saura kwanaki uku d'aurin aure aunt hauwa ta bude mans wuta kullum cikin durkar magani kullum INA kwana da ciwon ciki da wata muguwar Sha'awa Mara fasali sai in sanja pant sau uku a rana, maganar gyaran jiki ba'a cewa komai aunt Hauwa na da abokai iri-iri wata kawarta ce ta tsaya a kanmu ni da Munnu ta hado mana kayan gyara jiki kullum sai munyi dake aunt Hauwa ta iya hadawa sosai take samu a daki muna murje jikinmu bayan mun kama wani irin turare ne mai k'amshin tsiya shima zata sanya mun mulke sako da loko na jikinsu dashi sai munyi a wa daya tukkuna zamu wanke jikinmu tuni wani sihirtaccan kamshi ya kama fatar jikin mu, duk inda muka zauna sai kamshi ni kaina bala'in son k'amshin jikina, kullum muna tare da Jahid a waya, duk wasu k'awayenmu na nesa da na kusa mun gayyace d'aurin auramu, Alina sai wani shishshige min take Sam ban Wani saki jiki da ita ba duk sabgar buki da ita akeyi taki yin zuciya.

*Ranar d'aurin aure*

Amjad Jahid Khalid Ma'aruf suka futo cikin shiga iri daya shadda CE fara tas dinki babbar Riga da 'yar ciki fad'ar tsadar shaddar bata lokaci ne, takalman su iri daya hulunsu irin daya agogonsu iri daya komai iri daya sukayi amfani dashi kamar yanda suka yi ranar d'aurin auran Amjad da Mimi mota suka shiga guda  Khalid ne take draving har suka isa gurin d'aurin auran dake cike makil da jama'a take wani maroki ya saki wata shegiyar gangarsa ya fara wasa Amjad da fadin"Ango Na Asma'u sarauniyar mata gwarozo a cikin maza! Sai Amjadu! Hak'ika Wannan yarinya tayi dace da miji na nunawa sa'a fari mai farar aniya yaro mai halin manya gugan k'arfe sha kwarafniya gaba salamin baya salamun.!!!!!!!!! Jama'ar dake gurin suka dinga mamaki yaya ga ango kuma maroka na wasa abokin ango wai meye yake faruwa ne."! Shi kuwa Amjad Sam! Bai Kawo komai cikin ransa ba, kawai dai yafi tunanin ko don yanayin sunansu daya sa Jahid din yasa marok'an suka kasa ganewa wanene angon a cikinsu.

  Kawu Yunusa sai kaiwa yake yana kawo wa ya sha babbar rigar shi, kana ganinsa kasan yana Cikin farin ciki, Liman yayi addu'a kamar yanda addini ya tanada Alhaji Isa mahifin Jahid ya mik'a sadaki Asma'u dubu Dari cif kana Liman ya fatiha tare da shafawa duk Wanda ke kusa da Liman a lokacin ya shaida Amjad da Asma'u Aka d'aura aure ba da Mujahid ba kamar yanda suka gani a rubuce a invitation, tofa wani maroki sake kusa da Liman ya kururuce! Fad'i yake." Allah ya tabbatar da Alkairi yau an d'aura Auran Amjad da Asma'u kan sadaki dubu Dari cif ladan ba ajalan ba, tabbas wani kaya sai amale muna rik'on Allah ya sanya alkairi badi iwar haka mu dawo suna." Take guri ya rikice jama'a da dama da su kasan Amjadu din suka rufu a kansa suna yi masa Allah ya sanya alkairi duk ya rikice a lokacin domin al'amarin ya gigita shi kuma yazo masa bazata! Wato abunda Jahid zai masa kenan, yawan jama'ar dake kansa yasa ya nemi su Mujahid din ya rasa, haka dai ya dinga gaisawa da jama'a babu yabo babu fallasa a tare dashi, shi tunani. Yake meye munufar Jahid din akan haka. Kafin kace kwabo 'yan jarida sun rufu a kanshi kowa naso yaji ta bakinsa da kyar ta sub'uce dafa hannunsu ba tare da tace musu komai ba...............

   Kawai Yunsu da saurn yayyan babanmu suka shigo gidanmu lokacin INA gidan aunt Hauwa mai kunshi nayi mana Dana tunda na tashi nake jin fad'uwar gaba, Kuma ina kallon wani irin kallo da aunt Hauwa take min sai ta gyad'a kanta, Mamakin ko kallon me take min oho, ita aunt hauwa tasan da faruwar abun domin Ya Aminu ya sani shima Kawu Yunusa ne ya fada masa yace masa kuma yayi shiru da bakinsa shine shi kuma ya Sanar da aunt Hauwa din, to dukaninsu sunyi murna da farin ciki sun San Baby Aysha baza tayi maraicin uwa ba. UMMA ta shimfid'a musu ta barma suka zazzauna bayan gaishe-gaishe Kawu Yace." Ga sadakin 'yar kinan Asma'u an d'aura aure." Umma tace"Alhamdullahi Allah ne abun godiya ina yi mata fatan alkairi da samun zaman Lafiya gidan minjinta." Kawu Yunusa yw zakud'a  tare da bata fuska yace." Ba da Wanda kike tunani aka d'aura mata aure ba, yarinyar mu Mun d'aura mata aure ne da yaro Dan kirki Wato Amjadu bisa fa yardar shi wancan yaron wato Mujahid mun b'oye muku faruwar al'amarin ne saboda kar Ku kawo mana nakasu a kai saboda haka shi Mujahid din yaga cancantar ya barwa Amjad din Asma'u saboda wasu dalili NASA,saura Wannan karon ma ki zugata ra bujirewa Umarnin mu."!! Yana gama maganar sa ya Mike yana wani baza babbar Riga, take sauran ma suka mike suka futa daga gidan. Suka bar Umma da kudi a hannu tana mamakin Wannan al'amari.







*31/11/2019*


*BABBAN YARO*

*MALLAKAR BINTA UMAR

*70*

Wannan al'amari ya d'agawa Umma hankali sosai ta inda ta fara tunani. Artabun da zata sha da Asma'u saboda tasan halin taurin kanta da kafiyar ta, Amma itama taji dadin wannan Abu ko babu komai baby Aysha ta samu uwa baza tayi maraici ba. Tanan zaune har jama'a suka fara cika gidan sai ta saki fuskarta ta dinga karb'ar baki. Har lokacin da 'yan d'aurin aure suka shigo Aminu ya shigo gidan da gayyar abokan shi sai fama vedio da hutana suke yi. Dole Umma ts fito aka yi hoton da ita saboda tarihi.Aminu sai washe Baki yake yana gaisawa da jama'a, can ya kalli Umma tare da fad'in"Ina Asma'u ne? Umma tace"Tana gidan auntku ita da kawayen ta." Ya Aminu yace." Ya kamata tazo muyi hoton tarihi."Umma tace"Kai ta hoto kake Aminu shin wai kasan abunda ke faruwa ma kuwa. "? Aminu yace." Na San komai Umma Asma'u dai ta auri Amjad hakuri ne ya kamace ta domin anyi mata laifi dole a rarrashe ta."Umma tace"Ina gudun abunda zai je ya dawo n........ Kafin ta rufe bakinta suka shigo gidan, hankali jama'a yayi caaaa! Kan Asma'u kowa na fadin albarka cin bakinsa akan ta, murmushi kwai tayi hade da rufe fuska su Maryam suka rufa mata baya, Munnu kuwa dama tun ana gobe d'aurin aure ta koma gida. Maryam ce tace"Wallahi kinyi kyawun da baki tab'a yin irinsa  ba  a duniya Asma'u wai dama haka kike da kyau!.
Hafsa da bata San abunda yake faruwa ba, tunda tun ana saura kwana biyu tazo gudansu Asma'u suka had'u da sauran kwayen su irinsu Alina ake gudanar da shagalin buki tare tace"Wallahi nima haka nifa k'amshin da take yi ne nake bala'in so gaskiya dole idan na tashi aure aunty Hauwa tayi min irin wannan gyaran domin in burge autan maza." Shewa! Suka sa, Alina ta tab'e baki tare da fadin"Yo ke dama Hafsi wannan jikin naki ai dole sai da mugayen turarrika masu karfin gaske. " b'ata fuska tayi tace"Alina bana son iskanci aikin banza kawai." Cikin danne damuwar da nake ciki gami da fuduwar
Gaban dake damuna tunda na tashi nace" Alina ki saurara don Allah bana son tashin hankali a bukina." Dariya suka kwashe da ita..... Waya ta dake hannun Hafsa na karba INA dubawa naga 5miscall daga Jahid, kiram shi mayi, aikuwa tana daf da tsinkewa ya dauka muka gaisa a nutse yace." Ganinan zanzo daukar ki zamuyi hotuna da abokaina." Yana gama maganar shi ya kashe wayar .... Tsoro ne ya shiga zuciya ta nace"Allah yasa kar Jahid ya taba ni tunda yanzu yaga an d'aura aurenmu. Sama-sama muke hira dasu Alina Umma ta leko dakin tana fad'in"Asma'u kizo ki daukar muku abunci mana." Maryam ce ta mike da sauri tana fadin"Gaba Umma mu meye aikin mu, amarya guda dama yanzu nake cewa bari in zo in daukar mana towon d'aurin aure. " Umma tace"Nima abunda na gani kenan. Dukanin Ku babu bare a gidan nan duk yan gida ne." Marya ta bi bayan Umma tana fadin Wallahi kuwa.'' Ina kallonsu sun rufu kam abunci suna ci suna shewa cikin farin ciki, sai suka bani sha'awa sosai ko wace mace tana farin ciki da ranar auranta ni kuma na tsinci kaina da bakin ciki komeye dalili oho. Wayar Jahid CE ta katse min tunanin da nake yi yace." Ki fito ina jiran ki amaryar mu." Sam ban fahimci me maganar shi take nufi ba, na miike Alina tace"Ko inzo in raka kine."?
Gyad'a kaina nayi kawai na barsu a dakin. Dakin Umma na shiga tana cikin Uwar daki ita da jama'a. Tana ganina tsabar abunda take  yi jiki a sanyaye ta k'araso inda nake tsaye, Umma duk a tsorace take tana gudun kar Asma'u ta tsinkata cikin jama'a. A hankali nace"Jahid ne ya kirani a waya yanzu wai inje zamuyi hoto da abokansa." Jim! Umma tayi na minti biyu tace"Anya Asma'u akwai dacewar hakan kwa
"? Sunkuyar da kaina nayi tace" Kije tom ban san manufarsa ba amma ki cire wannan yalolon mayafin na jikin ki tunda kinga irin yadin dake jikin ki kamar Net gashi kinyi dinki matsatsatse kamar jaraba idan da hali ma kin sauya kaya kawai.  In babu hali to ki sa mayafi babba tunda kinga gurin da zakuje ba shi kadai bane." Nace"Insha Allah Umma." Wata shegiyar liffaya na zare cikin ledar ta fara kal mai golden d'in stones a jikinta tana da manyan zanen fulawa Umma da kanta ta nad'a min a jikina na rike k'aramar pose dina mahadin takamin dake k'afafuna, na futa daga gidan a nutse. Shi kadai na gani jingine a jikin motar sa, yana sakar min murmushin sa nima na mayar masa bude min motar yayi na shiga na zauna shima ya zauna mazaunin sa ya kunna motar muka bar gurin. Kallona yayi da Murmushi a fuskarsa yace." Amaryamu kinyi kyau mutuka Wallahi." Nace"My Jahid kenan Ina maka fatan alkairi a rayuwar ka." Gyada kansa yayi yana jin wani Abu cikin zuciyarsa yace." Alkairi Allah ya dauwama a duk inda kike Asma'u. " Ameeen ameen mijina " abunda nace kenan cikin jin kunyar sa.
Shi kam Jahid draving yake yana addu'a cikin zuciyarsa kan bala'in son da yake wa Asma'u wacce a yanzu ta zama mallakin wani
Ganin mun dauki hanyar Jambulo yasa nace"Jahid ina zaka kaini ne."?yace." Gidana mana kin San abokai da 'yan uwa sun had'a min walima k'arfe shida na yamma shine na dauko ki ki shirya a gabana idan anjima zan sanya a dauko kawayen ki." Cikin takaicin sa nace"Jahid wannan bayi bane fisabillilahi a ina zan zauna har a wa hudu yanzu." Ya bata fuska tare da  fadin''ki zauna gurin granny mana wani abun ne."! Nace"Jahid kasan bama shiri sosai da mai gidan me zai sanya in zauna masa a gida. " yace." Baya gari Amjad ki kwantar da hankalin ki
" shiru nayi masa ganin ransa kamar ya soma b'aci a zamana dashi na fuskanci baya son ja'inja."
Ko da muka shiga cikin gidan babu kowa a gurin sai masu gadi da karnuka da suke kwance sai dai na lura da karuwar motoci a gurin, kai tsaye  part din Amjadu muka nufa har shi Jahid din. Cikin rashin sanin komai na shiga ciki. Amjad Granny Iyami Baba Rakiya da wasu mata uku suna zaune a parlor suna hira. Sai a lokacin kunya ta kamani nayi kamar in koma da baya. Baby dake jikin iyami ta tsandare da ihu!! Wanda ya sanya shi bude limsassun idonsa ya mike da sauri hankalin sa na kan babyn dake zillo dole sai ta sakko tazo gurina. Granny tace da Iyami ta sake ta, aikuwa Iyami na sakin ta ta rarrafo dasauri ta kamani ta mike tsaye da sauri na dauke ta hade da rungume ta tsam a jikina, baby Aysha ta dinga kyalkyala dariya tana kallon Jahud dake tsaye kusa dani yana kallon abun mamaki.
Kallo guda yayi musu ya koma ya kwanta kan doguwar kujera da  yake kwance lumshe idonsa yayi yana haskon fuskar Asma'u a ganin da yayi mata yanzu, tunani yake yi shi dai iya sanin sa sao dare ake kawo amarya tom ita me ya kawo ta gidan shi da rana tsaka. Jahid ya karasa cikin parlor sosai suna gaisawa da granny cikin mutumci yace." Granny ga alk'awarin mu nan na kawo miki har gida kin gane dai manufata duk Wani Abu da zai biyo baya mai sauki ne." Granny tace"Ka cika d'an halak kuwa ubangji Allah yayi maka albarka ya raba da sharrin duniya." Yace." Ameeen ya rabbi Bari in shiga gida akwai abokanan mu dake jirana, Asma'u zata zauna nan zuwa anjima. " gyada kai kurrum granny tayi domin ita San ya fad'i hakane kawai amma aikin gama ya riga ya gama. Duk abunda yake faruwa a gurin yana jinsu, yayi bakam! Hancin sa ne yake shak'o masa daddad'an kamshi Wanda ya gaura ye parlor gaba daya wato k'amshin Asma'u kenan. Jahid yazo ya wuce ni ba tare da yace min komai bsla ya futa, kallo na bishi dashi cike da mamaki! Lokaci guda fad'uwar gabana ya tsananta jiki babu k'wari na k'araso gurin su, granny ta mike Da sauri hade da rike  hannuna muka nufi wani bedroom
Kallo ya bisu dashi har sai ds suka shige, sannan ya mike zaune hade da dafe kansa yana tunanin irin zaman da zasuyi da Asma'u a cikin gidansa. Gefan gado ta zanar dani ta zauna muna fuskantar juna da ita, a nutsu tace"Aminci Allah ya tabbata agare ki yarinyar kirki." Hannunta ns rike sosai Nace "Tare dake granny, jikina na bani akwai wani Abu ni kam na kasa fahimtar inda maganar Ku ta dosa ke da Jahid." Granny ts girgiza kanta take naga k'walla ns zubo mata. Tafin hannuna na sanya na goge mata INA kallonta cikin mamaki nace"Granny don girman Allahu ki Sanar dani meke faruwa."? Kai tsaye tace",Sanar dake abunda yake faruwa ya zama dole domin an shiga Hakkin ki, mun so kanmu da yawa, to amma ni ina ganin gata akai miki Wanda ko bayan babu raina zaki gode min da wannan alkairin da nayi miki, ina so kiyiwa magana ta kyakyawan fahimta." Nace"Insha Allahu." Granny ta gyara zaman ta sosai ta kwashe dukaninin abunda yake faruwa tsakanin Jahid da mahaifiyar sa da yanda Granny taje har gida domin ta nusasshe da ita ta ci mata mutumci da yanda suka yanke hukunci ita da Jahid din kan auran ta ya koma kan Amjadu domin ta kula da baby Aysha........... Tun kafin granny ta karasa maganar ta hawaye suka wanke fuskata ina mamakin wannan yankan kaunar da suka yi min yanzu Abunda Jahid zai min Kenan? Yaudara kiri-kiri Innalillahi, Jahid ya munafurce ni, yayi min abunda ban taba tsammani ba, ni tunda Amjadu ya auri Mimi a rayuwata ban tab'a kawowaa zai zama mijina bs shine babu Neman shawara babu komai suka yanke min Wannan hukunci kamar wata 'yar tsana. Idan Momyna ta hana shi auranena CE masa akayi Neman kai nake yi da kaina kawai zai sanya a d'aura min aure da Amjadu Wanda a halin yanzu muke buga tsaka dashi saboda rashin jituwa ta yaya zaman aure dashi zai yiwu..... Hawaye kawai nake zubarwa ina kallon granny nama kasa cewa komai. Take itama naga ta fara share hawaye tace"Hak'ika ba'a kyauta Miki ba Asma'u amma kiyi hak'ura Insha Allah zakiyi alfahiri da Wannan auren." Ina Kuka Nace " Granny Yanzu meye ma'anar kawo ni gidanan bayan an  San Abunda akayi min. Cikin sigar rarrashin granny tace" Dole s kawo ki gidan auran ki ko ba yanzu ba, kwai da mun yanke wannan sha'awar ne da Yayarki Hauwa dashi kanshi Mujahid din domin yin hakan shine zai kawo kwanciyar hankali da zaman lafiya ba tare da jama'a sun fahimci abunda yake faruwa ba, kinga wani zai iya fada miki haka cikin gidan Ku babu shakka
Zaki shiga fargaba da tashin hankali a lokacin Wanda hakan zai jawo hankalin mahaifiyar ki ya tashi har jama'a su fuskan ci akwai matsala saboda haka da yardar Allah kin shigo gidan auran ki zaki zauna a karkashin mijin ki kamar yanda ko wace mace take yin biyyayar aure." Kuka na fashe dashi sosai nace"Granny idan akai min haka ba'akyauta min ba, shikensn sai kace wata 'yar tsana ni akwai abunda zanyi a gidanmu yanzu
" granny tayi murmushi Wanda iya kadai ce tasan ma'anar sa tace." Duk abunda zakiyi a gidanku ba kamar nan gidan ba, domin nan shine gidan ki halak malak sai kin fi sakewa kiyi yanda kike so saboda haka ki kwantar da hankali ki insha Allahu kome kike manta a can nasan zasu kawo miki shi har gidan ki." Kwata-kwata bana son yin jayyaya da tsohuwar yasa nayi mata shiru kawai ita kuma ta mike da sauri tana fadin "Bari inzo yanzu." Tana futa na kwanta ka bed din hade da fashewa da Kuka mai tsananin gaske, Wannan wace irin kaddara ce ni Asma'u. " Baby Aysha dake wasa can karshen gado ta rarrafo ta yaye jikina tana kallon yanda hawaye suke tsere a kumatuna. Cike da tausayi ns rungume yarinyar a jikina Mimi ns tuno lokacin naji kamar in bita in huta da wannan rud'un na duniya. Kuka sosai nake yi mai futar da sauti.!Cikin wannan hali suka shigo suka same ta. Amjad daga bakin kofa ya tsaya ya soka hannunwan sa cikin aljuhu fuskarsa babu walwala ko ta kwabo kallon su kawai yake yi yayin da yake jin kukan ta yana masa wani irin zafi a zuciya. Mamaki yake sosai ko kukan me take yi idan hakane shima sai ya Dora hannu aka yayi ta kuka ko ya samu sassauci Cikin zuciyarsa tunda dai bata fishi jin ciwon abunda ya faru ba, don dai Jahid ya wuce komsiba gurin shi shiyasa kawai yayi masa shiru domin har yanzu shi da si magana ta fatar baki bata had'asu ba sai dai ido kawai. Granny ta karasa gadon ta dauke Baby daga jikinta tana kokarin mikar da ita zaune, tace"Kiyi hakuri Asma'u ki tashi zaune ga Mijin ki ya shigo ina so in hada Ku guri guda in muku fad'a kukan bashi da amfani kuma INA me tabbatar miki da cewar kukan nan da kike yi zai zama alkairi a rayuwar ki." Jin Granny tace ga mijinta ya shigo ya sanya fad'uwar gabanta ya tsananta tana tsoron ta kalleshi wai a matsayin miji domin ta lura da kallon banzan da yayi mata tun farkon shigowar ta gidan.... Shi kam Amjadu a zabbaban kamshi turaran Asma'u da ya d'umame dakin shine ya same shi yana nema ya sanya shi cikin wani yanayi.....






*2/12/2019*

No comments