Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

Cheaters Club 12

 _*CHEATERS CLUB...*_ 

 _(Babban goro sai Magogin Æ™arfe...)_ 




#ROMANCE

#FICTION

#ADULTHOOD

#SEXADDICTS

#WOMENPOWER


BY

 _SURAYYAHMS_

 _08060712446_

Hp palace


⏯️1️⃣2️⃣



Daga cikin private room na HIV counselling unit Wani irin kuka mai karfi fadila takeyi tamkar zata cire ranta doctocin biyu duka sun taru akanta suna rirriketa jikinta yay wani irin zafi sai jujjuya kanta gefe takeyi cikin rikicewar tunani tabi ta runtse idanunta gam gam dasuke fidda dumbin ruwan hawaye masu zafi tay tsamm da jiki jin Wai yau itace take dauke da cutar kanjamau? hakan datake nanatawa aranta yasata saki wani irin kakkarfan numfashi mai tattrre da firgici tabita dora hannu akai idonta a rufe cikin rudani tanamai cewa wayyo Allah na nashiga uku wayyo Kun cuceni kun cuceni Allah ya isa wayyo Allah na shiga uku.


Bakaramin tausayi tabawa likitocin ba ganin irin firgicewa da rudewar datayi tanata kuka.


Doctor sai Cewa yake malama Fadila kidena cewa kin shiga uku pls kiyi Addua ki furta innalillahi wa inna ilaihi rajiun kidena cewa kin shiga uku babu kyau.


Bama jinshi take ba tana cikin yanayin firgici daya gama nakasata aranta tana jin ina ma ace mata mummuman mafarki takeyi ba agaske ba.


Izuwa yanzu takai k'ololuwa wjn tashin hankali da firgici, bacin kakkarwa bbu abinda jikinta keyi. Da kyar suka lallameta tay dan shiru, snn dayan docton tahau mata bayanin yadda za'a mata wasu kwaje kwajen co-infections kamar su tuberculosis da wasu kananan infections kmr su oral cancers snn a soma dorata akan maganin HIV na ARV

(Anti retro-viral Drugs). 


Bisaga kwajin da aka mata Viral load dinta ya nuna cewa Da alama cutar ya dan jima ajikinta kimanin tsakanin wata 8 ko shekara daya ganewa ne kawai ba ayi da wuri ba. 


A kasa kan bare floor Fadila ta zauna dabas kamar wacce ta samu tabin kwakwalwa sai hawaye dake sauko mata yuuu sam yaki daukewa, har iyanzu jin kanta take kamar a mafarki tana ta Allah Allah ta bude idanunta ace mata kawai mafarki take amma ina da alama qaddara ya riga ya riga fata.


Sunci kusan mintina sha biyar ahaka suna famar tausasar zuciyarta tare da bata karfin gwiwar amsar rayuwarta ahaka kafin nan da kyar fadila ta iya miƙewa tsaye, tace musu ta gode snn ta kama hanya ta fice a office din tanatafiya ahankli sosai kmr wacce ruwa ya kwasota tana share hawayenta da hannunta dan yadda kasan mutuwa aka mata haka yanayinta ya dawo.


Ita kanta Batasan yadda akayi ta isa bakin motar ta ba tsabar batacikin hayyacinta kafafuwanta taji suna rawa dakansu ta dafe jikin motar ta tsaya gabobin jikinta a mugun ragwabe, saida tay tsayuwar mintina biyu masu kyau tana sauke ajiyan zuciya kafin nan ta bude motar ahankli hannunta na rawa ta shiga ta zauna aciki cikin yanayin jimami.


Rife motar tay kriff snn ta kunna Ac takai shi can koluluwar karshe sanyi ya shiga busota duk dama batajin wani sassauci ajikinta, Kuka mai karfine ya sake kufce mata ta haÉ—a kanta kirif da steering motar tanayin kuka a zafafe jin kamar jijijiyoyin zuciyarta zasu tsinke a lkci guda.


Tsananin Duhun Baqin ciki tare da radadin ciwon da zucyarta yake mata yasaka ta rasa waye ma zata fara dorawa lefin wannn abun??? Shin Meenal talba ce ,ko ko mahaifiyarta ko ita kanta datayi wa meenal din makahuwar biyayya akan saÉ“on Allah daya jawo mata wann  musibar da bazai taÉ“a rabuwa da rayuwarta ba.


This enuf, is a lifelong mental trauma..Hiv fa, Hiv?hiv of all sicknesses, shin Dukkan wayann tantiran karuwan da sauran mutane da sukeyin karuwanci da son ransu basu kamu da cutar kanjamau ba sai ita da ake tursasata takeyin shi na dole kuma ma bakoyaushe ba? Cewa take ita Metayi wa Allah ..Da karfi taja wani kakkarfan numfashi hummmmm tanajin tsananin zafi na tsaga mata zuciyarta sosai.


Wann wata iriyar musiba ce take bbiyar rayuwrsu, shin mutuwar da mahaifinta yay a yayinda yake aikata zina da matar makwbcinsu bai isheta abun kunya a fuskar duniya ba sai kuma ace gata da cutar kanjamau?...ta kara fashewa da kukan sosai tana cewa na shiga uku...na lalace wayyo Allahna pls How is dis fair to me...? Ita Dama can ba wani ilimin Addinin tay ba iyakacinta na sallahne dan ko datazo birni hajy nadia bata kula ta sakata a wani islamiya ba ilimi kawai aka bata na iya handling business sabida ta rika bautawa yarta meenal har iyakar karshen rayuwarta,.


Fadila sam bata gama sanin waye Allah ba bare ta gane babin karban qaddara mai kyau ko mara kyau bare har kuma taayi imani dashi,wanda hakan yasata ta fara tunanin hala Allah baiyima rayuwarta hukunci bisa adalci bane ayau da ya jarrabeta da wann cutar.


she was soo angry and furious da qaddarar da Allah ya dora mata tanajin kamar ta kashe kanta ta rabu da duniyan nan me gabaki daya..


Kukan fitan rai take tana ganin lallai Ubangijinta baya sonta,iyayenta da meenal kuma sun tsaneta gaba daya sun zalunce rayuwarta da suka sakata ta kamu da wann kazantacen cutar mai cike da kalubale na tsangwama da zubewar mutunci aciki.


Tasan inba dan son kudi irinna mahaifyrta ba da bazama ta san meenal ba bare hartakai wann matsayin datake ciki ayanzu.


Wani zuciyace ta debeta ta fixge motar a 360 tabar harabar asibitin aguje tahau kan titi tana tukin tanata kuka at same time kwakwalta na buga mata lissafin inda zata soma juye fushin dake kwarara asaman zucyarta..


Direct hanyar talba grop of companies ta nufa zuciyarta na tafasa dan harga Allah bata san mema zataje ta gayawa meenal din ba amma aynxu tafijin tsanarta fiye da komi arayuwarta.


Ta shararo tafiya kenan  tana daf ta iso motarta ya fara alarming yanamai nuna mata cewa man ta ya kusa ya dauke, a dan dole yasata tay slow down ta lallaba motar ahankli har takai wani gidan mai da baifi minti 10 ba ne nisan su da kamfanin Amina talba ba.


Ahankli ta share hawayenta tana jan tsaki ranta yay baqi matuka da tsayuwar datayi dan Allah Allah take taganta agaban meenal talba ayanxu.


bude motar tayi ta sauko jikinta na rawa rawa ganin akwai layi dolene sai taja jira wayanda suke shan man agabanta.


Rufe motar tay ta dauki wayarta ta koma can gefe inda babu mutane kwata kwata, nan ta soma kirar layin mahaifiryata danma kartaje tay wani abunda zatayi dan danasanin da zaizo ya shafa harda tsakaninsu na har abada.


Hannunta na rawa ta rike wayar har saida ya soma ringing snn ta dora akan kunnenta tana daurawa kuwa batama san sanda aka dauki kirar ba sautin gundumammen muryan mahaifyarta tana mai kwararo mata ashariya daga can ne ya fargan da ita.


Bakinta na rawa tace salam Alaikum umma


Bata amsa ba tace "Shegiya Marar kunyar yarinya yar kutumar uba tsinanniya wanda bata gaji qashin arziki ba saina tsiya,..


wani irin runtse ido fadila tay jin zuciyarta na tafarfasa a kunnenta ta kuma jin,.."Dan durun uwarki gidan wani dan iskan kikaje da har kika saka hajiya nadiya ta dagamin hankli tana kirana tana cimin mutunci akan yarta hajya amina tace mata kin gudu kinbarmata aiki kwana biyu basu ganki a offis ba?nan ma bata barta ta amsa ba cikin azalzalan masifa tace...Wato fadila kin gwammaci kibi kafarki dan iskan ubanki kije dakin saurayi kuta iskancinku akan daki zauna kiyi aiki ki samo halak dinki ko? Wato cin gindi yafi miki aikin da zai ciyar dani da shegun yan uwanki da ubanki ya mutu ya barni dasu ko?kedai fadila bakida imani zuciyarki abakance take kamar na fir'auna.

shashasha kawai haihuwar asara yar iska,

..tou wallh baki isa ki tozartani kamar yadda ubanki ya tozarni ba...

"karyanki matsiyaciya,

Dama shiri nake zanzo har legas din naci kutumar ubanki keda matsiyacin saurayin naki shegiya kawai lalatacciya. Yanxun Uban me kika kira zaki gayamin marar kunya???.


Azuciye cikin rikicewa fadila tace Amma umma wann fa ba adalci bane ko amsa sallamata bakiyi zaki soma duramin irin wnn ashariya ni menayi? ni menayi? Bata san sanda kuka mai cin rai ya kufce mata ba.


Cikin bushe ido da fushi Umma lauratu Tace "An dura miki ashariya, nace kinci kutumar ubanki in kin isa ki tuntsireni da mari daga can insan kin botsare.


Fadila taja numfashi mai zafi kamar ranta zai fice ajikinta muryanta na rawa cikin hatsalallen kuka mai tattare da gajiya da fushi tace


Umma Koma me zan gaya maki ayanzu bazai yi tasiri a zuciyarki ba sabida tunda can ma kudi yafi miki ni, kin sayar dani wa mutanen da basu san darajar dan adam ba,snn kin goya musu baya suna yanke dukkan wata kazamar hukunci akan rayuwata.


Umma anan na kiraki sau bila adadin inamai gaya maki cewa suna sakani karuwanci amma kikace min gadon ubana ne in banyi ba a ina zaki same abincin da zaki bawa yan uwana..ko sau daya baki taba damuwa da illar abunda kike sakani ba..


Muryanta harna shasshakewa cikin kuka tace Toh gashi, ga..sh shi...tafashe da kuka sosai daya saka kirjin umma laure ya buga da karfi.


A tsawace cikin fargaba umma laure tace toh Gashi me?ke Da Allah jahila ki fadi karyan dake tafe dake kawai ai bazai wuce kicemin kinyi cikin shege ba Mtchewwww taja wani mahaukacin tsaki daya saka fadilan kara ragwabewa cikin kuka.


Da kyar ta tattaro kanta cikin dagon murya tace tou ba cikin shege bane umma asibiti naje ba gidan saurayi ba, yanzu haka likita yace cutar  kanjamau ne ajikina.


Wani rambatsau Umma laure taji saukar maganan da wani irin sauri tace cutar kanjamau ajikinki fadila?


Fadila na kuka ta gyada kai.. jin umma laure tay wani irim shiru bayan wasu dakikai batace mata uffan ba.


Sai can cikin sauke nannauyar ajiyar zuciya snn tace "toh  ai wann qaddararki ce tunda ba wani dan uban ya saka maki ba..kece kika jajibo makanki. Ynxu da kike gayamin ni wata uwar zan miki? Kai innalillahi wa inna ilaihi rajiun amma fadila kin cuceni

Yanxu hajya taji wann maganar zata kuma amincewa kimata aiki ne? A  ina kenan zamunq samun rufin asiri


Baki bude cikin daukewar kukan da yy cak a karsashe Fadila tace umma ashe bama tani kikeba tunanin kudi da wayanda suka jefani acikin halin dana nake ciki kikeyi???


Umma zatayi magana cikin tsareta tace

...umma mena taɓa maki a rayuwa da kika hade kai dasu kuka lalata min rayuwata..


Acikin sauri Tace daka min fadila kirufe min shaddar bakinki awajen. Ni ban lalata miki rayuwarki ba, harka ce ta ceto ranmu daga mutuwa, kuma kece babba yau inbaki fita duniya kin nemo kin bamu ba uban waye zai na bamu na sakawa abaki?ubanki bai barmu  da gadon komi ba sai tsangwama da kyamata daga mutanen gari, Indan na ubankin zanbi aida yanzu haka dukkan mu gawawaki ne. Qaddararki ce ta zo miki ahaka, ni ban lalata maki rayuwarki ba.


Runtse idon fadila tay tanajin kamar zata yanke jiki ta fadi kasa tsabar jiri

Da rikicewar tunani.


A tunaninta kowacce uwa dolene zata girgiza intaji yarta acikin wann hali amma da alama nata uwar kam bata da daukeshi awani abu ba tukuna.


Maganganun halisan ne suka kuma dawowa mata, ahankli tana bude lumsashun idonta tace

Naji qaddarata ce kaka umma,amma ki sani bazan kara yin aiki a karkashin wayann mutanen ba inke baki damu da rayuwata ba ni bazan zauna in mutu ahaka ba kuma Allah saiya sakamin akan dukkan wanda suke da hannu akaina.



shewar umma laure ne ya katseta tana cewa lallai yaro yarone, yo ke fadila har wani rayuwa kike dashi na azo agani?

Dik inda zaki je a duniya tijarar da ubanki yay ma kadai ya isheki wallh.


Fadila tace Abunda baba ya aikata daban rayuwata daban ai Allah ma bazai kama ni da lefinsa ba.


Umma ta kuma yin dariya tace "gaskiyane Allah bazai kamaki da lefinsa ba shine zaije ya amsa laifukansa dakansa. Amma ki sani ZINA fa bashi ce. Duk sanda kayi sai anyi akan naka.. A irin halin mahaifinkun nan ai ku kadai bazaku iya biya masa bashinsa ba har jikokun sa sai sun biya wallhi. Ko ce miki akayi shidin ma bai rabawa ya'yan mutane cutar kanjamau dinbane? 


Gaban fadila yay mummunan faduwa


umma laura tana dariya tace Heeheha ohh lallai, aini gata na miki fadila da bana zama in bude miki cikakken tarihin mahaifinki sabida tsabar kazantar dake cikinsa halama da ana gaya miki da tuni kin hadiye ranki kin mutu. Ke bari kiji ma, dalilin daya saka kika girma kikaga bana kwana dashi daki daya kenan tsawon lkcin nan,tun danayi cikinki ya gujeni yaje yana kwana da karuwai abayan gari, wallh bai dawo kauyen nan ba saida kudinshi ya kare ya dawo aikin gona ko wata daya baiyi ba wata yarinya yar shekara sha uku taje aika ajeji ya danneta yay mata fyade a gonar shinkafarsa,mai gari ya saka aka kamashi aka daure shi tun ina da cikinki harna haifeki ba afito dashi ba, to ajikin yar yarinyar nan aka san da cewa ubanki yana dauke da cutar kanjamau iyayen yarinya suka bar garin nan suna masu baqin ciki tare da tsine ma zuriarsa tun bai haifeku ba. 


Har yau maganan daa uban yarinyar ya fada mini ya tsayamin araina fadila." Cike da kunci da baqinciki da ubanki ya qumsa masa ya dubeni da cikinki Yace min In sha Allahu duk wani abunda zan haifa sai Allah ya jarrabe abun da irin Jarabtar da ubanki ya dorawa yar yarsa. Kuma har sukabar garin nan basu yafe masa ba.


Tun alkcin nima na raba hanyana dashi amma kinga da me gari ya rasu ya samu ya fito daga gidan yari wallh bashine ya hanasa cigaba da yaÉ—a cutar nan wa matan da basusan yana dashi ba. Yanzu haka rabi daga cikin kannenki suna dauke dashi sabida uwayensu dayayi ciki dasu awaje basu san yana dauke da cutar ba. 


Danko na yi shelarsa agari ba jina akeyi ba ana zaton zafin kishine yasaka nake cewa mijina yana da kanjamau sabida duk matar da suke biye masa suyi iskancin tare yana basu kudi sosai.  Yo ke waye da zaki tuhume wasu akan dan kin kamu da cutar da ubanki ya riga ya rabawa mata sunfi akirga anan kauyen?


Ni aganina wanm lamarin qaddarare ne saiya sameki, ke kadaice yata a duniya dan haka ki nitsu kije kibawa su hajya hakuri kicigaba da zuwa wajen aikinki bama sai sun ji cewa kina dauke da cutar ba bare su koreki inyaso idan kikaga dama saiki dauki fansarki akan wanda suka saka maki ciwon in kuma kin hakura shikenan ohon miki dai.


Nide damuwata shine ki samu ki basu hakuri kina turo mana kudi dan kinsan dake kawai muka dogara anan kauyen babu mai tausayin mu bare hulda damu, ki aje maganan kanjamau agefe kawai kiyi abunda zai ficceki.


Cikin rasa na cewa Fadila 

Ta katse wayar ahankli batare da tacewa umma laure komi ba. Tafi minti goma a tsaye awajen batare da ta yi motsi ba tanajin kamar da ma a halicce ta tazo duniyan nan ba. cire sim dinta tay ta rike a hannunta snn ta jefar da wayar tata a wani rami hawaye masu sanyi suka sauko daga cikin idanunta.


Sosai hanklinta ya tashi da wann labarin dataji na mahaifinta sai kuma taji zafin datakeji aranta ya soma raguwa ta dawo tanamai tunanin yarinyar da ubanta yay mata fyade ya saka mata cutar kanjamau tun tana karama shin ko ya rayuwanta dana iyayenta zai kasance oho.


Jikinta a mugun sanyaye tazo ta samu har layi yazo kanta ta biya aka saka mata mai snn ta kamo hanyar izuwa talba grp of companies.


Wann karon ahankli take tafiya sakamakon dumbin lissafin datake ayyanawa acikin zuciyarta da kwakwarlta.


Shin itama ta karaya da samun rayuwa mai kyau tabi salon umma laurene data zauna acikin inuwar baqinciki da wahala a dalilin munanan qadaddarar mahaifinsu koko tabi shawarar halisa data ce mata koda ka tsince kanka a cikin mutanen da Allah yayosu da mummunn qaddara,  tabbas tanada ikon jajircewa dan ganin ya sauyawa kansa rayuwa daga mai muni zuwa mai tsafta sai yaga mummunan qaddarar tasa tayi masa sauki...


Ayanzu haka ita neman rayuwa mai sauki takeyi makanta saidai batajin tana da karfin gwiwar fuskartan irin wancan rayuwar duba da halisa ta taɓa cemata Duk randa ta zaɓi yin rayuwa domin kwato mutuncin kanta to shirya yin rayuwa mai daraja amma mai cikeda rauni da kunci.



Daga ta dayan bangaren kuwa halisar ce a mota suna kan hanyarsu na isa kamfanin Amina talba


Meenal na zaune a office tana waya da wasu business partners dinta duk hanklinta baiya jikinta sosai dan tafi minti talatin tana jiran shigowar halisa amma sai shiru basu shigo ba.


A hanya tasaka uztaz dan dole yakaita wani babban international shoping mall dan ta nemo kwalin tabar marlboro dan yana debe mata kewa dagayin tunani musmmn ma inta zauna shiru.


Dan daga tay shirun abu biyune suke fado mata..

Ko ta hau tunanin rayuwarta na baya ko ta soma nazari akan abunda jasmine ta gaya mata wanda dukkan su basonsu take aranta ba.


Da kyar uztaz ya amince ya je ya siyo mata kwalin tabar dan kwata kwata baisanta da shaye shayen taba ba, duk dama yasan halin datake cikine yake tunzirita tasha ynxu amma bai hanashi sauya yanayin fuskarsa ba.


Bata kulashi ba tana sha tana murmushi dan ji take kamar bazasu taba fahintar cewa dauriya kawai takeyi ayanzu ba.


Wajajen karfe goma da rabi na safe suka isa harabar kamfanin, uztaz yay sauri ya taho ya bude mata kofar mota ta sauko tacemai ya jirata anan snn ita ta nufi ciki itakadai.


Tafiya take tana busa tabarta ahankli, kusan idon kowa nakanta wanda ya dada sakawa taji kanta na juyawa dan sosai jikinta ya bata cewa kowa zancen rugujewar aurenta yakeyi kasa kasa.


Haka Taki sam ta dago kai sama bare ta kalle dumbin mutanen dake kallonta suna masu zancenta a sigar gulma 


Kafarta na harhadewa ta ciki amma haka nan ta daure tabita lifter yakaita sama izuwa office din meenal inda ko wani sallama batay ba ta turo kofar ta shigo ciki yanayinta adan dagule.


Cikin sauri meenal ta katse wayar datakeyi ta mike tsaye a mamaknce.

Ahankli tace Halisa ???


Waje halisan ta nema ta zauna tanamai kkrin kunna wani karar sigarin

Dake makale a bakinta


Meenal ta nade hannu tabita da kallon mamaki "what the fuck yau kuma da shan taɓa kika tashi?

I tot you quite smoking.


Hayakin na fita bakinta fuuu cikin nitsuwa ta dube meenal din tace 


"Forget it meenal"

Na dawo shan Abuna...


Meenal tay rau da ido tace what? You cant be serious, Keda kike neman saukin jikinki halisa mezaikaiki komawa ga shan taɓa gaskiya i wll not allow you to continue like this .

This is bad for ur health.


Hnnkli kwace kuma ahankli Halisa Tace haba meenal, just for a few more time ai zan dena nace miki ko.


Looking seriouly annoyed meenal ta zago izuwa gabanta ta zauna tare da harde hannayenta akan kirji tanata kallon yarda take busa hayakinta hanklinta akwance gashi ta mugun iya sha wanda hakan yasaka shan taɓar yake mata kyau sosai


Shiru ne ya dan gifta tsakaninsu halisa tanajin kamar tasoma yima meenal wasu yan tambayoyi amma kuma tanajin mugun nauyin hakan aranta shiyasa ma ta dada maida hanklinta akan busa hayakin tabar datakeyi dan ya dauke mata hanklinta daga tunani akan hakan.


Halisa ta dubeta ganin ta hade rai tana hararta tace.."Meenal Mummy fa? Ya jikinta, ko haryau bakuyi waya da ita bane.


Miƙewa meenal din tay sigar kame kame Duk ta rasa me zatacewa halisar atake kawai ta kirkiro karya tace yeah.. I think she is okay

Kinsan tun kafin bikin nan bamuy magana da ita ba, ai da munyi magama zata kiraki ta miki ya jiki da jaje.


Da mamaki Halisa tace

 Ohhh its been long...ta kyabe baki "der is no problm dama so nake naji ya nata jikin yake.


Yake meenal din tay cikin kaucar da maganan tace   halisa ina fatan kinsha maganinki? so how u feeling today..


Halisa tace "terible"

Inaga zan dena fita dan bazan iya zurar irin maganganun da mutane sukeyi akaina ba..

I dont think my mind is ready for this shhittt!!


Meenal tace To yau da safen ina kikaje dama?


Tace i was with jasmine


Jin sunan jasmine yasaka meenal ta yatsina fuska snn tace"Oh the model..No wnder..kice min dai kinje wajen lalattaciyar kawarki ta dauki taɓa ta jona ki dashi. Mtsww I just dont like dat girl, she is a bad influence amma sam kinki jina halisa..


Halisa ta dada busar hayakin tana cewa

"what ever meenal leave jasmine out of this


Ta kyabe baki to Zanyi magana da sauran babes   ai in bazaki jini ba zakiji nasu,mude wallh bazamu bari ki kara komawa wajenta ba if not next time kikaje saidai muga kinfara shan giya.


Ko amsata halisar batay ba wayar meenal ya fara ringing, da sauri ta dauka ganin lambar hajiya zee ne dama kuma ta nemeta kamar me amma bata dagawa.


Tana daukawa tace

"Hajiya ya da haka?

Inata kirarki tun safe amma sai shiru baki dauka ba.


Cikin gigin bacci hade da masifa tace Kai amina talba kefa akwai ki da nacin tsiya yo Inde akan yarinyar can ne toh ai tazo nan da sassafe ta bankadamin rashin kunya snn ta kwashe takardun duka zata kawo miki office dinki.


Meenal tace kikace ta bankada miki rashin kunya???


Hajya tace yess. Ai yar kutumar ubace bata da kunya Wallah zagewa tay ta zageni tass tacemin tsinanniya tsohuwar karuwa. Taci saa ina tare da baqine wallh da saina karya kafafunta amma i trust u to do the needful kici mun ubanta intazo.


Jikin meenal harna rawa tace karki damu hjya ai magana ya kare tunda kince tana zuwa yau kuwa zan mata hukuncin da bata taba gani arayuwarta ba.


Suna tsaka da wayar fadila ta iso harabar asibitin fuskarta a daure sosai dan duk wanda suke mata magana ma bata amsasu ba.


Direct tay sama izuwa offishin meenal dauke da takardun contracts din a hannunta duk anyi signing dinsu.


Meenal na kan bayanin irin hukuncin da zatay mata sai gata nan ta turo kofar..


suna haÉ—e ido meenal ta wani jaaa tukikin numfashi mai zafi kamar wacce taga mutum me siffar shaidan ya shigo.


Hajya kashe wayarki ga yar iskan nan ta dawo.


Daga tsaye fadila ta zuba mata jajeyen idanunta batace uffan ba bare tayi gaisuwa.


Sosai kan halisa ya daure ta tsaya tana satar kallon su ayayinda suke kallon junansu awani irin yanayi na hatsala da tsana.


Sai can snn fadila  ta karaso cikin offis din har gaban table din meenal snn ta aje files din tare da mata wani irin kallo mai wuyar fassara ta juya fuskrta a dore da niyyar zata fice taje ta rubuto resignation letter Meenal din ta wani cakumo ta baya a walakance tabita shakure mata wuyarta da karfi har dakyar take fidda numfashi..


A mugun tsawace tace mata Where did u thin ure going bitch, where have u been With my contrcts?


Da sauri halisa ta miƙe tsaye tayi kansu da zimman zata rabasu.


Fadila ta miƙa hannu tanai mata alaman karta matso kusa bare ta rabasu..


kafin ta hankara fadilar tay juyi ta waina meenal gefe ta hadata da jikin bango jiri ya debeta yuuu kamar zata fadi kasa haka tabita rike bango agigice.


Rai a bace fadila tace i was in hell cos dats where u sent me to be.


Muryan Meenal na wani irin shaking tsabar bacin rai atsawace tace how dare u pushed me. Zuwa tay da sauri tare da daga hannu zata wanka mata mari fadila tay saurim cafke hannunta ta watsar mata dashi acikin wata iriyar raini daya girgiza mata zuciya.


Nan da nan Halisa ta shigo tsakiyarsu da mamaki sosai ayanayinta tana kallonsu dukansu


Tace What are u guys doing Fadila kina da hankli kuwa,..ta juya ta kalli meenal babe wann ba girmanki bane.


Fadila batace komi ba sabida ganin girman halisan datakeyi.


Meenal tace Halisa stay out of this.


Yarinyar nan yar iska ce,.Nan ta soma masife fadilan ta inda take shiga batanan take fita ba.


Tanamai cewa Karuwar banza.. u think bansan agidan saurayinki kike ba..tafara mata gori tana cewa ai ubanki ma agindin matar makwbcin sa aka same gawarsa.


Sosai abun yay ma Halisa ciwo yadda meenal take zagin iyayen fadila amafi munin siga.


fadila na É“ari tana hawaye sosai daga ganinta kasan hakurinta ya riga ya kare.


Duk hnklin halisa saiya tashi tanata kkrin tarufe ma meenal baki amma tsabar masifa tabi ta ture halisar gefe tanata gaggasa ma fadila bakaken maganganu, yar iska kawai mun rufa miki asiri keda matsiyaciyar uwarki marokiya amma wai kinzo nan banda karuwanci babu abunda kika saka agaba? Am going to deal with u and U wil be fired.. ni ban yi gadon abun kunya kamar na ubanki ba, bazaki je garin iskanci kimutu ana cinki ba azo nima ashafama kamfanina gulman mummunan qaddararki irinta ubanki.

In iskanci zakiyi ki aje min aikina ki je bayan gari inda yan uwanki karuwai suke halama kici karo da kannenki awajen.


Abata hankara ba saiji tay an wanketa da maruka daya na bin daya har sau biyu.


Agigice tay kasa zata fadi kasa halisa ta rikota da sauri taki sam ta sake ta dan karda ta kirawa fadilar security.


Saida Meenal tay mintina uku ba'a hayyacinta ba jin saukar marin da tsananin fushi fadila ta watso matashi.


Kuka mai cin rai ya turnuke Fadila tace 

Wallahi kinci sa'ar kawarki dake nan wajen daban haka ba da yau sai na nunamiki cewa ni din kwarrriyar yar iska ce.

Amma kisani bashi kikaci,dani kuma kikeja yadda kika walakanta rayuwata kijira kema kiga naki karshen rayuwar duk wanda yaci tuwo dani miya yasha.. Am no longer ur slave, Dake da aikinki u can go to hell and burn to ashes ke baki isa ki rufamin asiri ba Allah ne yake rufamin asirina. 


Wani irin kokawa da kukan kura meenal ta somayi a hannun halisa tana firgici alaman tana son ta kufce ta kamo fadilar a hannunta kodama ta rama marinta dan shine yafi mata ciwo aranta, amma haka fir halisa taki ta saketa.


Sai ihu take tana cewa sai ta daureta..sai ta walakanta and she wll make sure babu kamfanin da zai sake daukarta a aiki a kasar nan.


Fadila nacewa inta isa ta Daure ta ita kuma sai ta mata abunda batayi tsammani ba.


Zazzafar cacar bakine ya kaure tsakaninsu.


Halisa ta kalle fadilar cikin mata fada tace 

"Its okay, fadila pls get out ure crossing the line.


Fadila na kuka bata kara cewa komi ba ta juya ta fita..wajen desk dinta direct ta wuce ta bude wani locker ta kwashe takardun dake ciki tasss sann ta bude computar ta ta dauko biro da paper tanata rubutu tare kofar wasu numbobi wanda Allah kadai yasan meta ke daukawa aciki.


Daga cikin office din kuwa kusan a fixge meenal ta iya kwace kanta daga hannun halisa. Hawayen tsananin bacin rai da takaici ya gama wanke mata fuska ta dakawa halisar tsawa "halisa akan me zaki rikeni kina kallon yarinya tanamin tsawa tana rainani, halisa why dont u call the police....what the hell cant u fucking react.


Cikin maida mata tsawar

Halisa tace mata 

"you want me to fucking React?....meenal ure insane.. ure wrong

..akanme xaki behaving da ita haka Kece kika jawo ta miki tsawa ta kuma rainaki


Muryanta kamr zai daga wajen da buhun masifa Tace "A'a kam halisa baki fahimce fadila bane Haka halinta yake yar iska ce wallhi.


Halisa tace Meenal is enough.  Banyi tsammanin wayann maganganun zasuna fitowa abakinki ba..kin shakure mata wuya and ure insulting her parents kuma kina tsammanin tay shiru ta kalleki while ure busy disrespecting her. Cmon dat was so extreme. Aiki take miki ko bauta?


Ranta bace tace bansani ba,..okay fine halisa just get out. Ure annoying me more!!!


Cikin kyabe baki halisar tace kanki akeji, ta jefa karar taɓarta abaki sanda ta buso mata hayaki sn tace 'am out!!.


Ta kama hanya zata wuce meenal din taja mata wani irin tsaki, har takai bakin kofa ta juyo ta kalle meenal din harta dauki waya jikinta na rawa zata kirawa fadila polisawa


Juyowa halisar tay bata hankaraba taji an karbe wayar anyi disconnecting

Tanamai kallon cikin idonta tace meenal please Dont call the police on her..for god sake owned up to ur own mistake meenal wallh kece bakiyi dede ba a matsayinki na babba.


Cikin katseta ahatsale tace wani mistake nayi kina gani yarinya tazo har ofice dina ta mareni snn ta zageni snn kicewai laifi nane? Halisa saiyau na tabbata cewa bakida hankli wallh a matsayinki na babban kawata memakon kitayani cin ubanta saiki rikeni.. tafadi hakan idonta na cikowa da ruwa tsabar bacin rai sai wani huci take saukewa azafafe .


Bama bajinta halisa take ba ahankli tace nide na gaya maki kibarta haka nan,Idan kuma kika yi taurin kai kika walakanta yarinyar nan i swear i will personally testify againts u banason shashanci.


Kamar ta shake halisar take ji taja ta yi shiru tanata kallonta harta fice a office din batace mata komi ba.


Halisa na ficewa ta hango motar fadilar acan lkcin har ta hau kan titi tanata kuka sosai dan batasan ina rayuwarta zai dosa ba, but all she knws is der is no going back, in sha Allah ta rabu da meenal talba kenan na har abada inma akwai wani abunda zai shige tsakaninsu sede na daukar fansa amma ba na mutunci ko yafiya ba.


Halisa dake cikin nata motar, a nitse take ta kallon bayan motar fadilan jikinta na bata cewa da akwai wani abu mummuna daya faru da yarinyar dan bata taÉ“a ganinta a wann yanayin ba..tabbas duk abunda zai saka tay ma meenal haka to abun mai girma ne, dan haka tay shiru cikin nazari. Sai can ta dube uztaz snn tacemai 


"Hey,..Follow that car" 


Bai yi wata wata ba ya juyo kan motar a ladabce yana me ce mata  

"yes maam..."


Daga Cikin offishin babu abunda meenal takeyi sai jeka ka dawo ranta yay mummann baci tana ziriya tana huci.


For the sake of halisa zata daure yau bazatay komi ba dan tasan halisa sarai ba kyaleta zatay ba, 


hakan yasaka bata iya daukar wayarta ta kirar wa fadila hukuma ba..ji take kamar kanta zai tarwatse da bomb tsabar bacin rai dan harga Allah niyyarta shine ta mata gundumammen sharrin da zai saka akaita gidan yari a kulleta na tsawon wasu shekaru. 


Ahakan ma bawai zata kyaleta bane,tsaye take cikin huci Tanakan sake saken wasu salon muguntan data mata aranta.


Can ta Wani irin Kyabe baki cikin kunci da tsananin bacin rai ta fito waje, direct gaban desk din fadilar ta nufa danta duba ko zata iya kwashe wasu delicate files na Abubuwan kamfaninta da suke hannunta, tana isa kan desk din iya farar takardan resignation na fadilar kawai ta gani a ajiye. Daukawa tay a fusace snn ta koma cikin ofishinta dashi tana zama ta dauki waya tare da dannawa mahaifiyarta kira.



08060712446

Surayyahms please ayi sharing

Post a Comment for "Cheaters Club 12"