Breaking News

Kurkukun Kaddara Book 2 Page 16

_~*BossLadiesWriters*~_



           _*KURKUKUN ƘADDARA*_




~Middle step~

          


              _The Prisoners E16🔥💫_




*Daga alƙalamin Boss Bature*





Kusan a tare Aneelerh da zahra su ka shigo palourn, a saman carpet kowan nan su yai zaman cin tuwo Junaid na azaune gefenta, tun da su ka zauna idanuwan su Mami da Abie na akan su, at same time suka haÉ—a baki wurin gaishe dasu cikin girmamawa, fuskokinsu Uncle abdallah da fara'a suka amsa masu.

  

Bayan kowan nan su Ya natsu, Hajiya adama ta soma magana cikin nutsastsiyar murya

 "Dama jiyane Aneelerh ta ke faÉ—amin dangane da tada zancen 6acewarsu tajuddeen da za'ayi, a gaskiya naji daÉ—in jin hakan sosai, Kuma na yabama zahra da ta kawo wannan shawarar ta yi tunani mai kyau" Tun da ta fara magana sun natsu suna sauraronta, Zahra sai faman washe baki take yi jin anyabi shawararta, tana matuÆ™ar son taga An yabeta.


  Bayan Hajiya adama ta Æ™are magana Uncle abdallah Ya É—aura da cewa"yanzu haka abun da mu ke tattaunawa akai kenan, Ni kaina Naji daÉ—in tunanin nan da akayi abune mai kyau da buÆ™atar atada zancen 6acewar su ya dawo sabo, wata'Æ™il ta silar hakan Allah ya agaza mana Muji É—uriyarsu duk da bamu da tabbacin ko suna araye don ni har yau bana ji araina cewa babu su a doron duniyar nan!" 


Numfasawa Abie Yai Kafin ya É—aura da nashi jawabin"In sha Allahu muna sa ran wannan Karan zamuci nasara, dama dalilin taruwar mu anan don kowa Ya bada tashi shawarar" Bayan Kammala Maganar abie, Uncle É—an Iya Ya soma magana


  "Na riga nayi magana da Ziyad babban É—an jarida ne, Tun ranar da muka Yi magana da Aneelerh, ta turo min hotunansu already na tura mashi su, da duk wasu bayanai da za'a buÆ™ata, Ya ce min in sha Allah cikin weekend da zamu shiga komai za'a fara yaÉ—a labarinsu"  Murmushine Ya bayyana akan fuskokinsu da alama sun ji daÉ—in Jin hakan

  Uncle abdalla yace"Wai kana Nufin Ziyad É—an Gidan senate Lateef"?


 Jinjina kai Uncle É—an Iya yayi"Æ™warai kuwa, Ziyad yanzu ae shi ke jan Ragamar Companynsu Na jarida mai suna Obinna News Network (ONT) Yaron Akwai hazaÆ™a Kullum ne saina bibiyi Labaransu a shafinsu, Æ™wararrune a 6angaren Aikin Jarida, duk wani labari da zaiyi trending a social media Sune na farko da zasu fara buga shi a shafinsu"


  Uncle abdalla Yace"Allah sarki, Uzair Da tajuddeen Sunci burin yin Aiki a companynsu, suna son Yin aiki tare da Ziyad Allah bai nufa ba" cikin karyayyiyar Murya Uncle abdallah ya Æ™arasa maganar, jikin kowan nan su Yai sanyi


  "Nima a bakin uzair na ta6a jin labarin Ziyad É—in nan shahararran É—an Jarida, " Acewar Hajiya adama


  Uncle É—an Iya na murmushi yace"Allah sarki, ae muna mutunci da Iyayensu, lokacin da ace nasan suna da burin yin aiki da shi ai dana haÉ—asu, Yadda Taj da uzair suke da hazaÆ™a a 6angaren Jarida tabbas da suna atare ba Æ™aramin Cigaba za'a samu a Æ™asar nan ba, don shima Ziyad É—in Akwai Æ™walwa Bashi da tsoro gaskiya tsirararta yake faÉ—in ta" murmushi kowannan su Ya saki.


  "Yakamata ka gayyato mana shi agidan nan, tunda kowa nasan ganin shi, Ko da ya ke nasan zaiyi wuya ya iya samun lokacin zuwa sai dai mu muje inda Yake" Abie ne yai maganar


  "In dai ziyad ne baku da matsala, mutunne mai sauÆ™in kai, zan Gayyace zuwa gidan nan"


  Tun da suka fara magana sai Yanzu ummi tasa baki"kaga daga nan Idan Yazo sai mu bashi auran zahra...." tunkan ta Æ™arasa magana zahra dake chatting da wayarta A sukwane ta É—ago Girarta a haÉ—e tana kallon fuskar mami.


  Hakan da ta yi ba Æ™aramin dariya ya basu ba, Uncle É—an Iya yace"kin kawo shawara mai kyau, Ni kaina nayi tunanin hakan don yaron akwai farin Jinin Æ´an mata ita kanta zahra nasan zata Æ™yasa" Kifa kai zahra tayi saman cinyoyinta, takaicin Duniya ya isheta, ita da ta ke da burin mallakar Uban gayyar family É—in su kuma suna yi mata zancen Ziyad.


 "Akwai Kyauta ta musamman da zan ba Aneelerh, nasan Itama zata taimaka mana sosai"  Hajiya adama ce ta yi maganar idonta Akan uncle abdallah.


  "Na baro ta a mota, jiya na manta ban shigo da ita gidan ba, Bari naje na É—auko" yai maganar yana yunÆ™urin  miÆ™ewa Sai ga Mahboob Kamar an wurgoshi Rai a6ace yake Tafiya Fuskar shi a haÉ—e babu mutunci.


  "Ka koma ka zauna Ga mahboob nan, ka bashi key É—in motar ya É—auko maka" Karaf acikin kunnanshi Maganar ta sauka, Har Æ™ara sauri yake yi don yabar falon

  ÆŠaga murya Uncle É—an Iya yai"Kai Mahboob zonan" Cak Ya tsaya da yin tafiyar fuskarshi A murtuke ya Juyo Ya nufi inda suke zazzaune saman sofa.


  ZuÆ™unnawa Yai Æ™asa Ya É—ago da fuska Yana kallon Abie É—in nasu


  Rai a6ace yace dashi"Mahboob ba ka ga munyi baÆ™i bane a gidan namu"?


Hannu yasa ya ɗan sosa ƙeyarshi Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta


"Bana Jin É—aÉ—i jiya shiyasa ban samu damar zuwa ganin su ba," 


Wani kallo Da Ummi ke wurga mashi daga inda take zaune saman Sofa kamar zata kifa masa mari, Hakan yasa shi yin sauri kallon Uncle Abdallah Ya furta"sannunku da zuwa, ya gajiyar tafiya, ya kuma aka baro mutanan can"


 fuskar uncle abdalla asake ya amsa mashi"lafiyalou Mahboob, ya school ko an kammala" fuskar shi ba yabo ba fallasa ya ce"diploma ce na kammala"


 Ganin yanayin fuskarshi babu walwala Uncle abdalla yace  "Ko dai har yanzu ba lafiyane? Naga kamar baka acikin natsuwarka" 


  Sai lokacin Ya É—an sakin murmushin yaÆ™e "Bakomai, ai naji sauÆ™i" Iya abunda ya furta kenan, Baby Junaid  ya tsareshi da ido, Dariya ce Æ™umshe a cikin bakinshi don ya fahimci damuwar rashin zoban shi ce ta sanya shi shiga wannan halin, Cikin kunne yai ma Aneelerh raÉ—a"Mommy zoben yake nema, kalli idonshi ki gani sunyi jawur, Allah bani bashi mommy sai ya zubar da hawayensa"


 Æ˜iris ya rage Aneelerh ta saki dariya yayin da take sauraron muryar junaid, ita kanta ta lura da 6acin ran da ke akan fuskar Mahboob.


  "zai baka Key É—in mota, saÆ™o zaka É—auko mashi" Fuska a É—aure uncle É—an Iya yai mashi maganar, tare da kallon uncle Abdalla


"Bashi key ɗin motar," acewar ɗan Iya, ciro key ɗin uncle abdallah yayi kafin ya miƙa ma Mahboob, Ya sanya hannu biyu ya kar6a.


Yunƙurawa yai ya miƙe ya fuce daga ɗakin yana ƙunƙuni.


Kafin dawowar Mahboob Junaid Ya miƙe da sauri Ya nufi ɗakin Mommyn shi don Ya duba zoben da su ka 6oye.


Yana shiga É—akin Ringing wayar Aneelerh Ya daki dodon kunnan shi, Da sauri ya nufi wayar dake Ajiye saman pillow Ya haye gadon ya janyo ta.

 Jikinshi har kerma yake yi wurin yin Picking call É—in ya kara wayar a kunnanshi.


  Da Æ™arfi Ya furta"Wanene"? Shiru ba"a tanka masa ba.


Hakan baisa ya fasa yin maganar shi ba


"Mommy bata nan tana a palour suna magana da su Abie, I'm the only one in the room." still ba'a tanka mashi ba, Surutu Yaci gaba da Yi


"Angel ce ke kira"? Shiru ba amsa"Sister Angel, say something! It's your brother, Baby Junaid. I miss you so much"


Da shagwa6a ya yi maganar, Sai lokacin Muryar mutumin da ya kira a wayar ta bayyana da sauti mai matuƙar Ratsa zuciya.


  "Where is the owner of the phone?"  ta6e baki Junaid yai"ai na faÉ—a maka tana a palour"

  "Okey ina son yin magana da ita, ko zaka Iya kai mata wayar" Tuntsirewa Junaid Yai da dariya yana faÉ—in"a'a Sai dai ka yi magana dani, sai in faÉ—a mata"

  "Pls ka kai mata wayar, " maÆ™e kafaÉ—a Junaid Yai kamar yana agabanshi"ni dai a'a, Ka faÉ—amin sai in faÉ—a mata saÆ™on" 


  "Shekarunka nawa"? Ga dukkan alamu wanda ya kira wayar ya fahimci Æ™aramin yaron ne ya É—aga tun daga kan voice É—insa.


 "HuÉ—u Biyar shidda" Sautin dariyar mutumince ta ratsa kunnan junaid.


  "No wonder ashe babban mutun ne kai, zamu iya zama abokai" maÆ™e kafaÉ—a junaid yai"to aini yarone kai kuma babba".

  "Okey yanzu faÉ—amin Ina yayarka Angel"? Kwa6e fuska junaid yai cikin muryar shagwa6a yace"ta 6ace 6era ya cinyeta ita da daddynta da daddyna sun mutu nima mommyna ta faÉ—a min" sosai mutumin Ya fashe da dariya, jin wautar Junaid


  "Ka hana Ni Yin magana da mommynka, gashi kanata cinye min kati"

  "Ae nace ka faÉ—amin saÆ™on sai In gaya mata" mutumin yace"Okey, ka faÉ—a mata DADDYN UNAISAH NE ya Kira"! 


   "To zan faÉ—a mata Sai anjima" Yana kai Æ™arshen magana Yai rejecting call É—in tunkafin mutumin yai mashi sallama, Pillow Ya janyo ya zuge zip É—in Ya curo ring box É—in Yana Kallon zoben

  "Na Angel ne wannan, Bazan bashi ba Allah tun da ya cinye min chocolate É—ina" Yana magana yana ta6e la66ansa.


Shigowa Mahboob Yai cikin palourn Hannun shi ruƙe da Kyautar wani abu Mai faɗi an rufe shi da wrap sheet mai Ƙyalƙyali, Karasowa Yai agaban sofas din da Uncle Abdallah Yake zaune Ya sauke gift ɗin kafin ya miƙa mashi key ɗin motar, Kar6a Uncle Abdalla yai"nagode sannu da ƙoƙari" muryarshi ƙasa ƙasa Ya amsa da"yawwa" Juyawa yai da sauri Ya nufi Sashen kitchen ganin Ana na zarya kai abinci a dining.



 Tunkafin a buÉ—e Kyautar kowa Ya Æ™agara da son ganinta, musamman zahra ta Æ™ura idanuwanta kamar na mazuru.

  Ummi na murmushi tace"masha Allah wannan kyauta tunkafin abuÉ—e mun fara zumuÉ—in ganinta" Mami tace"ni kaina a Æ™agare nake Allah"

  A hankali Uncle Abdallah Yake warware wrapping sheet É—in, slowly Kyawawan idanuwanta dara dara suka Fara Bayyana, da mamaki su ke Kallon juna cikin rashin fahimtar wacece wannan Kyakkyawar Matashiyar.


  Lokacin da ya warwaro wrapping sheet É—in dai dai Saitin hancinta ya Æ™arasa 6an6are ledar gaba É—ayanta, adai dai time É—in Mahboob da Ana sun fito daga kitchen Hannun shi ruÆ™e da glass Na lemu Karaf Idanuwanshi suka sauka akan Hoton zanan fuskar Angel, Nan take ya saki glass É—in hannunshi gaba É—aya ya tarwatse ruwan lemun dake acikinsa ya tsiyaye saman tiles.


  Tsabar Al'ajabi da mamakine Yasa Aneelerh da mami YunÆ™urawa a sukwane suka miÆ™e tsaye Suna Æ™are ma Zanan Kallo Yasha fenti kamar horonta aka É—auka.


  Gaba É—aya sun Rasa bakin magana, zanan yayi bala'en Yin kyau, fuskar Angel ta fito raÉ—au Kyakkyawar matashiyar balarabiya bugu da Æ™ari buzuwa a 6angaren Mahaifinta" Zahra Ko sai faman Yarfa hannu take yi tana ambaton Wow wow Tabarakallahu ahsanul khalikin! Gaskiya koma wanene portrait artist É—in da ya zana hoton nan ba Æ™aramin Æ™wararre bane ya baje basira"


  Ummi tace"Masha Allah, Yarinyar ba Æ™aramar kyakkyawa bace, kamar tajuddeen Ya yi kakinta, Kamanninta sak Kalar nashi, Hasken fatarne  ta É—auko Na mahaifiyarta benazir"


  Lamarin ya É—aurewa Ana kai Ganin yadda Mahboob Ya fasa glass cup ko ajikin shi, Hankalin sam baya atare dashi, Zanan Fuskar Angel Ya tafi da Imaninsa, dama can tun fil azal Mahboob Mayen mata ne.


  "Mahboob Meke damunka ne? Baka ga 6arnar da ka yi ba ne'?


Ba tare da ya kalli fuskar Ana ba Ya furta"dama akwai matan Hurul aini A duniya"?


 Girgiza kai Ana ta yi Fuskarta É—auke da murmushi ta nufi dinning, don ta jera kayan tray din hannunta.


   Farin Ciki Ya hana Aneeleeh furta kalma, agaban zanan da ke a jingine jikin hannun sofa, ta zuÆ™unna saman gwiwowinta, yatsun hannayenta na kerma ta É—aura su saman fuskar Angel, Lokaci É—aya ta fashe da matsanancin kuka ta kifa kanta saman zanan


 "Haba Aneelerh menene abun kuka? Ke da za ki yi farin Ciki"? Mami ce tayi maganar


 Hajiya adama ta miÆ™e ta nufi Aneelerh ta É—an ranÆ™wafa ta É—aura hannunta saman kafaÉ—arta.


  "Share hawayen ki Aneelerh, banaso pls, Ni ban Kawo maki zanan nan don ki yi kuka ba, saboda farin Cikin ki yasa Nasa aka yi min shi, nasan zaki ji daÉ—i sosai" Abie yace"in dai ko bazaki daina kukan nan ba, zansa su koma da zanan" sai lokacin ta É—ago da rinannun idanuwanta da suka kaÉ—a jawur ta kalli fuskokinsu cikin shessheÆ™ar kuka tace"Nadaina, wlh kukan farin cikine Ya kubce min, Inason Angel sosai, na kasa jurewa ne, da na ga zanan nan sai naji na Æ™ara Æ™agara da son ganinta a shekarunta Na yanzu" Mayar da idanuwanta ta yi a kan hoton


"Allah sarki my Angel, ɗiyata ƙanwata kuma ƙawata abokiyar firana, Na yi missing ɗinki sosai bazan ta6a mantawa dake ba har abada" Kifa kanta tayi saman hoton Hawaye suka cigaba da wanke fuskarta, ta yi matuƙar karya masu zuciya.



*Middle step A gidan Alhaji ubaid*



Tun lokacin da Dr. shureim Ya kammala kimtsawa ya zauna gefen gadon shi ya natsu yana kallon hotunan abar ƙaunarsa, Ƙarfe Goma sha Biyu Na bugawa, Kiran Alhaji musa Ya shigo wayarsa.


 Da sauri Yai picking call É—in Ya kara a kunnanshi


  "Shureim Ina Jiran ka a palour!"


 Abun da Ya furta mashi kenan, Ajiyar zuciya ya sauke Tare da miÆ™ewa Ya fito daga Bedroom É—insa, Yana mai jin kewar É—akin nashi, tafiya yake yi tamkar bayason Taka Æ™asa, Ji yake kamar In yabar gidan zai Æ™ara nisanta kanshi da ita ne, duk irin yadda yake zumuÉ—in barin gidan hakan bai hana wani sashe na zuciyarshi Æ™in amince masa ba, Saboda acikin gidan ne, abar Æ™aunarsa ta kafa tarihi acikin zuciyarshi.


Lokacin da ya ƙaraso palourn, A zaune ya samu Alhaji musa da Uncle ubaid, Sai Mahaifiyarshi laila Da Mai aikin gidansu zainab, Hannunta ruƙe da shopping bag.


  Yanayin fuskokin su Ya nuna alamun rashin jin daÉ—in tafiyar shi, musamman mai aikin gidansu zainab da kuma Mahaifiyarshi Layla, tana a tsaye ta ruÆ™e qugu fuskarta babu annuri ko misÆ™ala zarratin zallar 6acin raine.


 Shi ko Alhaji ubaid sai faman sakin fara'a ya ke yi babu alamun zaiyi kewar É—an nashi idan ya tafi. 


  Idanuwan dr. Shureim akan na mahaifiyarsa, da sauri ya nufi inda take atsaye, hannu biyu ta sanya ta rungumo shi a Æ™irjinta, hakan da tayi mashine yasa shi jin hawaye sun cicciko idanuwanshi.


  Bubbuga bayanshi take yi a hankali tana faÉ—in"Shureim É—ina, zanyi missing É—inka sosai, naji takaicin tafiyar nan duk da ba wani wuri zakaje me nisa ba, sai dai sam hankalina bai kwanta da tafiyarka ba, Naci burin In gatantaka In baka kulawa ta musamman tuntuni, sai dai rashin zamanka agida da kuma gudunmu da ka ke yi, shi yasa ban samu damar yin hakan ba, Yanzu kuma na samu na shawo kanka, an nuna anfini iko da kai za'a rabani da kai,' tun da ta fara magana Alhaji musa Ya haÉ—e rai fuskarshi a tamke ba annuri, don yasan dashi take magana.


  "Mommy ki samin albarka ita nake buÆ™ata daga gare ki, Sannan ki kwantar da hankalinki, Ni musulmine kuma nayi imani da Allah dashi na dogara, aduk inda zan kasance Allah yana atare dani, ballanta kuma agidan Uncle É—ina ne ba nisa zanyi ba, nasan za ku dinga zuwa akai akai kuna ganina, Nima kuma zan dinga zuwa gida" Maganar Dr. shureim ta yi matuÆ™ar karya mata zuciya, Allah na gani tana son É—anta sosai, Muryar Alhaji musa ce ta katse su"shureim bamu da isashen lokaci, ka wuce mu tafi"


  ÆŠagowa Yai daga jikin mahaifiyarshi ido cikin ido suke kallon Juna, Canza harshe ta yi zuwa larabci kafin taci gaba da magana


 "Shurem hankalina bai kwanta da kawunka ba, Ni ban yarda dashi ba, Bai ta6a nuna damuwa akanka ba, tun lokacin da Æ™addarar nan ta risÆ™e ka har ka fara shaye shaye a Æ™arshe ma kabar Æ™asar gaba É—aya, musa bai ta6a bibiyar rayuwarka ba, babu ruwanshi dakai Ƴa'Æ´anshi kaÉ—ai Ya sani, Ta ya ya hankalina zai kwanta da zuwan ka gidan shi? Allah kaÉ—ai yasan mugun nufin shi akan ka" Tana magana tana shafa sumar kanshi da ta sauko saman wuyanshi, babu wanda Yasan me ta ke cewa, dama da biyu ta yi mashi maganar da larabci don saboda tasan basa Jin Yaren, mai aikinsu kaÉ—aice ta ke ji saboda itama balarabiyace, jikin zainab duk yai sanyi da jin maganar Hajiya layla, baiwar Allah duk ta damu da Shureim gani ta ke yi kamar idan ya tafi wani abu zai faru dashi.


  Muryarshi araunace Ya soma magana da harshen larabci"Mommy kidaina wannan tunanin dan Allah bana so, ki kwantar da hankalin ki, Uncle musa bazai Ta6a cutar dani ba, duk da bai damu dani ba a lokacin baya, yanzu ya nuna yana Æ™aunata zai Iya yiwuwa ko dan saboda tausayin halin da nake aciki ne, Nafi so ki yi mashi kyakkyawan zato mommy"

 

 GyaÉ—a kai ta yi "Shikenan shureim zan cigaba da yi maka addu'a akan Allah ya kare mun kai ya tsaremun kai daga sharrin duk wani abun cutarwa" Cikin harshen labaraci ta dinga jero addu'o'i tana tottafa masa Yana amsawa da ameen.


  Bayan ta kammala ya É—ago da ido Ya kalli zainab, idanuwanta sun cicciko tab da kwalla.


  Matsawa ya yi kusa da ita, fuskarshi É—auke da murmushi yace"auntyna zan tafi asanyamin albarka" yai maganar tare da duÆ™ar da kanshi, Hakan ba Æ™aramin daÉ—i yayi mata ba, Ƴan hawayen da ta ke matsewa tuni sun soma shararowa saman kuncinta.

 

Tafin hannunta ta ɗaura saman arab turban ɗin dake naɗe akanshi, a tsanake take jero addu'o'i tana tottofa masa a ƙarshe ta ƙara da cewa"Allah yasa Silar komawarka can ka samu farin Ciki na har abada" Ya amsa mata da ameen ameen"Allah ya saukeku lafiya shureim" ya ƙara amsa mata da ameen


 Daga Haka Ya juya ya nufi Mahaifinshi Alhaji Ubaid.


  Fuskarshi É—auke da murmushi yake duban shureim"daddyna, asanya min albarka"


 Da buÉ—ar bakin Alhaji ubaid sai cewa yai "Shureim sai ka ce zaka Bar Æ™asar, irin wannan bankwana haka! Na lura Jikinka duk Yai sanyi, Ko kamanta Abuja ne zaka je gidan Æ™anina"? Harara Hajiya layla ta jefa ma Alhaji ubaid a fakaice.


  "Lokacin da ka ke Æ´an guje gujenka ba tare da sanin kowa ba, Ka ke barin Æ™asar nan sai yau don zaka tafi gidan uncle É—inka kake Neman albarkarmu"?


Da mamaki akan fuskar Dr Shureim ya ke kallon Alhaji ubaid, Ran Hajiya layla ya 6aci A harzuÆ™e tace"Dan Allah Ya isa haka! Me yakawo wannan  maganar? Saboda kawai yace ka sanya mashi albarka? Idan baza ka sanya mashi ba sai ka Æ™yale shi Ya tafi, dama albarkar uwa aka fi buÆ™ata, bata uba ba"

 

  Runtse ido shureim Yai, Maganar daddynsa ta ta6a mashi zuciyarshi tuni Æ™walla sun Ciko idonshi, Hatta zainab ta ji É—acin maganar Alhaji ubaid ji take kamar ta kikkifa mashi maruka a kuncinsa.


   Still da murmushi akan fuskar Alhaji ubaid ya ke dubanta, kafin ya maida dubanshi ga shureim.


  "Ka ji abunda Mommynka tace, babu buÆ™atar albarka ta, Don haka zaka Iya tafiya" cikin jin Æ™unar rai Yace"daddy na roÆ™e ka, Ka sanya min albarka ina buÆ™atar taka"! hawaye tuni sun wanke fuskarshi, Jinjina kai Alhaji Ubaid Yai, Kafin Ya janyo Dr shureim Ya rungume shi, Yana tofa mashi albarka, Hankalin shi ba Æ™aramin kwanciya ya yi ba.


Miƙewa Alhaji musa yai daga saman sofa ɗin da ya ke azaune, ko kallo basu ishe shi ba, Cikin takun nan nashi na izza, ya juya ya fuce daga falon don shi arayuwarshi Ya tsani 6ata lokaci.


  Tsoki Hajiya layla taja aranta tace"abanza, Uban Ji da kai, ai ni da za ka burgeni, ka kama Hanya ka yi tafiyarka, kabarmin É—ana"


   RuÆ™o Hannun dr shureim Alhaji ubaid Yai, Yaja shi suka nufi Hanyar fita falon, Da sauri Zainab Tabi su Hajiya layla kam zama tayi dirshan saman sofa tana faman cije le6e.


  Abakin Engry hall na gidan, Zungureriyar motar da zata É—auki Alhaji musa zuwa airport tayi parking, HamshaÆ™iyar gaske Ƴar ubansu mota mai numfashi.


  Yana daga kishingiÉ—e a É—aya daga cikin back seat na motar, tamkar yana acikin bedroon É—insa saboda tsabar haÉ—uwarta, slowly murfin motar ke zugewa Dr shureim na Æ™oÆ™arin shiga ciki, Muryar Zainab ta katse masa hanzarinsa.


"Namanta da wannan, kai na haɗamawa" juyowa yai tare da kallonta, Ledar hannunta ta miƙa masa, fuskar shi ɗauke da murmushi ya kar6a Yana yi mata godiya, kafin daga bisani yayi masu sallama, yasa kai cikin motar, daddaɗan Sanyin a.c ya ra6i sassan jikinsa shi kanshi Ya yi al'ajabin haɗuwar motar.


Mutun Biyune agaban motar, Driver ɗinsa da kuma p.a ɗinsa wani gabjejen mutun mai ƙirar Ƙarfi daga gani yana gym saboda ko'ina na jikinsa a murɗe Yake, wankan suit ne a jikinsa Baƙi wulik baida fara'a a fuska.


Kaitsaye Airport Suka nufa, already An shirya mashi privet jet dinsa, Bayan shigarsu cikin jirgin wanda Tsayawa zayyana HaÉ—uwarshi 6ata lokaci ne, abune da hankali bazai É—auka ba, saboda an kashe dukiya kamar ba asan zafin nemanta ba, Kai kace saman bishiya ake tsinko kuÉ—in ana amfani da su.  (😂)


 Dr. shureim Yaga aljannar duniya, Bayan tashin jirgin Cikin mintuna da basu wuci arba'in ba Suka Æ™araso Airport É—in Abuja, Tun kafin jet É—insa ya Æ™araso airport É—in tuni Escords É—insa sun hallara abakin motocin su cikin shiga ta baÆ™aÆ™en suits domin tarbarsu da kuma basu tsaro.


*EX-PRISONERS❤*



Tun Bayan da suka kammala Cin abinci kowan nan su yai kulu wash rabu hani'an, Nurse ta shigo É—akin ta kwashe kayan abincin da suka ci ta fuce da su waje.


  Gaba É—ayansu suna A saman gadon zazzaune Sai Yanzu su ka samu damar Æ™arewa É—akin kallo.


  "Angel menene wancan"? Parveen ce ta yi maganar tana nuna mata plasma tv dake manne a jikin bango.


  "Tv ce da ita ake yin kallo" 

"To ki kunna mana mu gani mu ma" girgiza kai Angel ta yi"a'a Parveen ku bari sai munje gidan daddyna tukunna"


ta faɗi hakanne don tasan muddin ta kunna masu kallo zasu birkice mata ne, a ƙarshe ay abun kunya, tun da basu ta6a gani ba.


  Tambayoyi suka dinga jera mata kamar Æ´an jarida, komai na É—akin sai sun tambayeta menene shi ya akeyin amfani da shi, ita kanta ba komai ta sani ba saboda ba kalar É—akinsu na gida bane, Iya abunda ta sani take amsa masu.


   "Zan shigo toilet" Batul ce ta yi maganar, saukowa ta yi daga saman gadon ta nufi Æ™ofar da take tunanin ta toilet ce ta tura da hannu ta shiga, tun da ta shiga take bin ko'ina da kallo sauÆ™in ma toilet É—in su na prison na zamani ne, da ko anga Æ™auyanci sai dai da banbanci sosai, don wannan akwai sink da bathtub hada shower ga mirror da sauran Kayan amfani.


Agaban madubi Batul ta tsaya tana kallon fuskarta, bata ta6a ganin Kyanta irin na yau ba yatsun hannunta ta tura cikin Curly hair É—inta tana cakuÉ—a shi.


  Acan bedroom É—in Bayan shigarta toilet, zuciya da saÆ™e saÆ™e Angel sai ta dinga ayyanawa aranta ga Batul can ta kunna Ruwan zafi amaimakon na sanyi" Jiki Na rawa ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet É—in, ko neman excuse babu ta shigo toilet din kamar an jeho ta.


Jin motsin shigowar mutun yasa Batul Juyowa a firgice don ganin wanene. Kusan atare suka sauke Ajiyar zuciya


  "Dama ba wani abu za ki yi a toilet É—in ba"?

  Murmushi Batul ta sakar mata"Inaso ne in Æ™are ma ko'ina kallo,"


  "In dai wannan ne kada ki damu zan yi maku bayanin komai, amma Yanzu ki fito mu koma É—aki" Amsa mata ta yi da toh ta juya ta nufi Angel ta ruÆ™o hannunta suka fito, shugowarsu É—akin ke da Wuya Aka buÉ—e Æ™ofar, Dr Daniel brown ne tare da Nurse rebecca.


 Fuskokinsu É—auke da murmushi, cikin harshen turanci ya soma yi mata magana.


  'Masoyiya Angel da Æ´a'Æ´anta, fatan na same ku Lafiya" Amsa mashi sukayi da lafiyalou

  "Ya jikin naku? Ko akwai inda ke yi maku ciwo "? Atare suka girgiza mashi kai


  "Okey, Starting tomorrow, you'll be receiving injections for three days, and you'll also be taking regular medication to improve your health." cikin kulawa dr brown ke yi masu magana idonshi akan fuskar Angel.


  Murmushi ta sakar mashi"mun gode  sosai da kulawarku agare mu, Allah ne kaÉ—ai zai Iya biyanku"  


  "Kada ki damu, aikin mu ne, Ko akwai wani abu da kuke buÆ™ata"? 


  Cikin raÉ—a Batul ta yi ma Angel magana a kunne"muna son ganin Haris da Danish" 


   "Doctor, can we see our brothers?" kamar mai jin shakkar shi ta yi maganar.


Jinjina mata kai Yai alamar eh, Kafin ya É—aura idonsa akan Nurse rebecca" Ki kai su É—akin Ƴan uwansu" 

 "Okey sir" Mayar da idonshi yai kan Angel" pls muna so ki samu natsuwa sosai, ki kwantar da hankalinki dana Æ´an uwanki, akwai magana da zamuyi dake tare da sojojin da suke ceci Rayuwarku, sunce da zarar kin farka a sanar da su, Ni kuma na bari sai zuwa gobe idan kin Æ™ara wartsake wa duk da naga jikin naki da Æ™wari"


   shiru Angel ta yi tana faman zazzare mashi gray eyes É—inta aranta ta ayyana komai suke son sani? fatanta Allah ya bata ikon amsa masu tambayoyin da zasu Yi mata


  "HaÉ—in kanki mu ke buÆ™ata Masoyiya Angel" murmushin yaÆ™e ta sakar mashi wanda bai kai zuci ba.


  Bayan fitar shi daga É—akin, Nurse ta kalli faces É—insu"zamu Iya tafiya" A hanzarce suka sassauko daga saman gadon suka bi bayanta, tun da suka fito daga É—akin gabansu ke faÉ—uwa ganin haÉ—aÉ—É—en wurin da suka tsinci kansu a cikinsa, Asibitin Har ya gaji da haÉ—uwa, babu tazara a tsakanin É—akunansu da inda aka kwantar da su Haris duk acikin amenity ward ne.


  Abakin Æ™ofar É—akin da aka kwantar da Haris suka tsaya, sai da nurse É—in ta fara tura Æ™ofar ta shiga tukunna ÆŠaya bayan É—aya su ka soma shiga cikin É—akin cike da zumuÉ—in son ganin É—an uwansu, tun kan su Æ™arasa suka hango Haris kwance magashiyan saman medical bed an sanya mashi robar oxygen a hancin sa.


  Da sauri suka Æ™arasa gaban gadonshi, gida biyu suka raba kansu, gefen dama Gabriel ne da Javed sai Naufal da Parveen ta 6angaren hagu Angel ce da Batul, Jamimah da azeeza sai Hannah, tsananin tausayin Haris ne Ya kamasu, tuni idanuwansu sun cicciko tab da Æ™walla.


  Cikin shessheÆ™ar kuka Angel ta ambaci sunansa"Haris!" har cikin dodon kunnanshi Kiran Ya isar mashi, sambatu ya soma yi masu Yana ambaton sunan Deeja yana faÉ—in"mu koma ku É—auko ta, Deeja na tana araye suna can suna azabtar min da ita, dan Allah ku taimakamin ku cece rayuwata ku É—auko min deeja na" tuni Hawaye  sun wanke fuskokinsu, Hatta nurse rebecce Dake atsaye jikinta yai sanyi ganin hawayen su, Duk da bata iya jin abunda É—an uwan nasu ke cewa


"Haris"! Muryar Angel ce ta ƙara ratsa kunnan su, A hankali Ya soma ƙoƙarin buɗe idanuwansa da suka kumbura jawur ya ɗaura su akan fuskarta, Ware su yai sosai, Ganin Yana ƙoƙarin miƙewa yasa Nurse ɗin Yin saurin matsawa bakin gadon ta rankwafa ta zame mashi roban oxygen din daga hancinsa, ta taimaka mashi Ya miƙe zaune Bayan ta sanya mashi pillow a tsakankanin bayan shi da headboard na gadon.


  Sun natsu suna kallon shi, azabar ciwo tasa shi canza kamanni, fatarshi ta yi haske Ya rame sosai, hakan ba Æ™aramin Kyau ya fiddo mashi ba, sumar kan shi a cukurkuÉ—e kamar mahaukaci sabon kamu, É—aya bayan É—aya ya ke binsu da kallo Yana ambaton sunansu da raunatacciyar muryarsa

 "Angel, Batul, Azeeza, Jamimah, Hannah, Javed, Naufal, Gabriel.." Numfashi Yaja Kafin ya furta sunan Deeja"Ya akai banganta ba? Ina aka kaimin deejana? Baku zo da ita ba"? Idanuwanshi acike tab da hawaye yai masu maganar


  Cikin sanyin murya Angel tace"Haris pls ka daina sanya damuwa aranka, dubi kaga yadda ka rame, tamkar ba Haris É—in mu ba, duk kabi ka zauce, Why pls? Bama Jin daÉ—in canzawar da ka yi, gashi baka da Æ™oshin lafiya"


daƙyar sautin muryarshi ke fita"Bazan Iya jurewa bane Angel, inason deejana ina jin tsoron ace narasa ta, donni inaji araina tana araye tun da har su azeeza basu mutu ba, Itama sumane tayi"


  "Haris idan har baka kwantar da hankalin ba, Ta ya ya zamu Iya samun Æ™warin gwiwar fallasa asirin masu kurkukun Æ™addarar har muci nasarar  É—auko sauran Æ´an uwanmu da suke acan idan basu mutu ba? Dole fa sai ka bamu haÉ—in kai ka danne damuwar dake aranka tukunna zamu Iya Cin galaba akan su"! Angel ce ke yi mashi magana cikin kwantar da murya


  Gabriel ya É—aura da cewa"Kin faÉ—i gaskiya Angel, Haris pls ka taimaka ma kanka muma kuma ka taimake mu sannan ka taimaki rayuwar su Deeja Rashin lafiyarka shi zai tarwatsa mana shirin mu, Nurse ta faÉ—amin abunda ke damun ka, Ciwon zuciyane Haris kuma nasan bakomai ne ya jawo hakan ba face Deeja!! kaga yanzu mun ku6uta daga Daji muna acikin mutanan duniya, Nan inda muke asibiti ne Inda ake duba marasa Lafiya sune suka bincika lafiyarka kuma suka tabbatar mana da cewa damuwace ta silar wani abu daka Æ™wallafa rai akan son shi, pls Haris Ka taimaka mana! Idan har ba ka ji sauÆ™i ba Likitocin nan bazasu ta6a bari mu koma Nigeria ba gidan daddyn Angel" tunda Gabriel Ya fara magana Haris Yake bin É—akin da suke da kallo, sai lokacin Ya gane ba adaji suke ba, shifa gaba É—aya baya acikin hayyacinsa baisan ma a ina yake ba, idanuwanshi sun makance.


  Azeeza sarkin tausayi tun da ta tsareshi da ido, Hawaye ke bin fuskarta.

  Cikin shessheÆ™ar kuka tace"Dan Allah haris ka yi haÆ™uri, In sha Allah deejan mu bata mutu ba da sauran Æ´an uwanmu Zamuje mu É—auko su"


  Batul tace"kwanciyar hankalinka kawai muke buÆ™ata Haris, idan ba haka ba kaga zaka mutune kafin muyi nasarar dawo da su deeja, me kake tsammani idan Ka mutu muka gano deeja araye ya za ta ji? Ka mutu saboda ita? Kaima ka sani yadda take Æ™aunarka itama mutuwa zatayi tabi ka"


lumshe idanuwanshi yai, ƴan uwanshi ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya suke yi ba, sai kwantar mashi da hankali suke yi duk don su samu ya wartsake


  "Ina É—an uwana"? yai tambayar yana kallom faces dinsu

  "Danish bai farka ba Haris Har yanzu, bacci yake yi, " Angel ce ta bashi amsa,  damuwace Æ™arara akan fuskarshi

  "Angel wani irin bacci ne wannan Har yanzu bai farka ba? Ina jin tsoro wani abu yasame shi" girgiza kai Angel tayi"a'a Hairs ba abunda zai same shi, Ni inaji araina Lafiyar danish qalou, Bacci ne kawai ya ke yi kasan ya É—auki tsawon lokaci bai runtsa ba shiyasa bai farka ba"

 

GyaÉ—a kai yai"Allah yasa hakane,"

. "Haris ka ci abinci ko kana jin yunwa"? Kallon parveen yai"bana Jin yunwa parveen, Naji daɗin kulawarku agare ni, sannan Ina tayamu murnar barin kurkukun ƙaddara" murmushi kowan nan su Ya saki, shima ya ƙalalo murmushi akan fuskarshi


  Muryar Jemimah da shagwa6a tace"Idan ka ji sauÆ™i, zamu ga deeja ma har kuci abinci atare da ita, kana bata abaki itama tana baka abaki, agidan daddyn genie É—ita" gaba É—ayansu suka sanya dariya, Nurse rebecca dake tsaye tuni ta zauna saman chair tana dubansu sam bata gajiya da kallon Yaran burgeta suke Yi kamar ta sace su take ji.


  Haris Ya ji daÉ—in maganar Jemimah har saida yaÉ—an murmusa

  "Sannan Haris zai dinga wanke ma deeja gashin kanta yana sharce mata shi," Batul ce tayi maganar, tsabar daÉ—in maganarta har saida fararen haÆ™oransa suka bayyana.


  "Bayan haka zai dinga goyata a saman bayanshi Suna yawo" acewar Hannah sosai Haris ya fashe da dariya yayin da hawaye ke cigaba da yin sintiri akan fuskarsa, Lamarin ya É—aurewa rebecca kai, mamakinta yadda yaran suke matuÆ™ar Æ™aunar junansu, wani abu da ya Æ™ara burgeta yadda suke ta sanya shi dariya tabbas su ka É—ai suke Iya sarrafa junansu.


  "In sha Allah Haris our dream will come true"  lumshe idanuwanshi yai tare da buÉ—e su akan fuskokinsu sai ya dinga ganin tamkar Deejar sa ce zaune a tsakiyar gadon tana sakar mashi murmushi, hakan yasashi sakin murmushi kamar wani zautacce


  "Haris ka kwanta ka huta, kada mu cika ka da surutu, zamuje É—akin Danish mu duba shi" 


  "Nima inaso naganshi Angel, muje atare" 


  Kallon Nurse É—in tayi"pls sister zamu Iya tafiya da shi É—akin É—an uwanmu"?

  Smilling gently, nurse rebecca tace"badamuwa, zamu Iya tafiya da shi" ta yi maganar tare da miÆ™ewa Ta nufi gaban gadon, da taimakonta Haris ya sauko daga saman gadon tace mashi ya dafa shoulder É—inta don ya samu damar yin tafiya, RurruÆ™eta yai da hannayenshi a haka suke Yin tafiyar, Su Angel suna abayansu har suka Æ™araso É—akin da aka kwantar da garkuwa, Jikin Angel har 6ari yake yi saboda tsabar zumuÉ—i, tun kafin su Æ™arasa shiga É—akin suka hango Danish Baje saman gadon, kamar matacce, lallausar sumar kanshi ta tarwatse saman mattress É—in gadon, da sauri Angel ta nufi gadon Ta haye daga gefe Idonta akan Kyakkyawar fuskarshi, Har kullum kamar ana Æ™ara ninka mashi kyawunshi, fatarshi tayi smooth fara sol Ko tabo babu, Sun canza mashi uniform É—inshi wanda ke a jikin sa Yanzu kalar nasu ne Riga da wando light blue, rigar tayi tighting É—insa, gajeran hannu ne da ita Hakan ya bayyana Æ™aƙƙarfan Damtsen hannun shi, Likitoci sun sha wahala wurin canza mashi kayan Jikinshi saida suka haÉ—a Æ™arfi tukunna su ka samu damar raba shi da su.


    A hankali take bin Shi da kallon so da Æ™auna tun daga saman sumar kanshi har i zuwa kan Long eye lashes É—insa, dogon hancin nan nashi yayi sam6al babu lanÆ™wasa, full lips É—insa sun ciza launinsu, slowly ta sauke idonta akan Zanan tattoo dake a gefen dogon wuyanshi Yayi bala'in yi mashi kyau

 A gefe da gefen gadonshi kowannansu Ya samu wuri ya zauna hada haris da nurse ta zaunar dashi, natsuwa su ka yi a yayin da su ke kallon É—an uwansu, daÉ—i kamar zai kashe su

  Angel ta shagala da kallonsa ji ta ke kamar ta faÉ—a saman chest É—insa ta Æ™anÆ™ame shi ko ta samu sassaucin kewarsa da ta ke yi, Muryar Haris ce ta fargar da ita.


  "Angel zuciyarshi tana bugawa"?


A hanzarce ta kwantar da kunnanta saman chest É—insa saitin heart É—insa nan take taji bugun zuciyarshi na harbawa a tsanake

 ÆŠagowa tayi fuskarta É—auke da murmushi tace dasu"zuciyarshi tana bugawa, bacci ne yake yi" 


  Jin haka yasa Kowan nan su Ya matsa kusa da shi, É—aya bayan É—aya suke É—aura kunnuwansu saitin zuciyarshi, nurse rebecca dake a tsaye murmushine É—auke akan fuskarta


 hankalinsu ba Æ™aramin kwanciya yai ba, jin zuciyarshi na bugawa


  "Sai yaushe zai farka? Baccin yayi yawa" Javed ne yai maganar, Naufal yace"may be saiya É—auki adadin kwanakin da yayi bai runtsa ba tukunna zai farka" zaro ido Angel tayi haÉ—i da girgiza kanta"in sha Allah  ba zai kai wannan lokacin ba zai farka.


 Ta Æ™are maganar tare da ruÆ™o zira ziran yatsun hannun Danish na dama acikin nata, sosai ta runtse su (nima kuma na runtse alÆ™alamina)



  

  *Boss Bature✍️ Mu haÉ—u gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun Æ™addara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuÉ—in*




First bank




3196407426, 




*Bature Hafsat Muhammad, za'a tura evidence of payment ta phone number É—ina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*

No comments