Breaking News

Kurkukun Kaddara Book 2 Page 23

 _~*BossLadiesWriters*~_



           _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_




~Middle step~


          سجن القدر❤🤍❤



              _THE PRISONERS E23🔥💫_




*Daga alƙalamin Boss Bature*




Confusion of the heart💫




Sir mubarak ne zaune Cikin Motarshi, da su ka yi parking dinta a harabar ajiye motoci na asibitin Obinna,Tanƙameman asibiti ne Ya haɗu tamkar ba wurin Jinyar marasa lafiya ba, An zuba dukiya wurin gininsa, suna da ƙwararrun ma'aikata na gida Nigeria dana ƙasar waje.


  Su biyu ne acikin motar, Shi yana a back seat na motar Ya zauna a hakimce, A yayin da Driver-operator dake driving dinsa Yana zaune saman driver's seat kowan nan su na sanye ciki kakinsa na sojoji, sun yi shiru, Sanyin A.c din motar na ratsa fatar jikinsu, ga dukkan alamu wani muhimmin abu ne ya kawo su asibitin, akwai wanda suke Jira Ya ƙaraso, tsawon mintuna Biyar, wani kyakkyawan matashin likita Ya nufo motar da saurin shi kamar zai yi tuntu6e.


 A gaban motar su ya dakata da yin tafiyar, ya kai hannu yai knocking glass din motar, turo ƙofar da a kayi ne Yasa shi yin saurin gyara natsuwar shi, Sam hankalin shi ba a kwance ya ke ba, tun da sir mubarak ya kira shi awaya ya sanar da shi game da zuwan shi asibitin gaba ɗaya ya rasa natsuwar shi, saboda sanin matsayin shi a ƙasar.



 "Dr fawan, shigo ciki mana " muryar Sir mubarak ce ta fargar da shi, Jiki na rawa ya shiga motar, ya zauna yana faman zazzare idonshi yace"daddy, ina wuni Ya gida ya Iyali" sir mubarak yace"lafiya lou fawan, Ya aiki ya fama da marasa lafiya" tun da ya fara magana bai ɗago Ya daura idonshi akan fuskar fawan ba, Hankalin shi na akan Wayar hannun shi da yake daddanawa.


  Still muryarshi na rawa ya furta"Lafiya lou daddy, sai ga kiranka, Na ɗanyi mamaki" sai da ya ambaci hakan sir mubarak Ya ɗago da ido ya kalli fuskar fawan, duk da sanyin A c na motar, abun mamaki zufa ce ke tsastsafo mashi, kallon tuhuma sir mubarak yake jefa mashi, saboda zufar daya gani a saman goshin shi.


  "Ya akai naga kana zubar da gumi? Ko baka da lafiya ne"? Yawu fawan Ya haɗiya tare da cewa"babu komai, Lafiya ta ƙalau"



  Ta6e baki Sir mubarak Yai"Okey, Inaso ka kaini gidan kajin da kuke kiwo kai da Jazz," da alamun ruɗu akan fuskar dr Fawan yace"Gidan kaji? Daddy ban fahimci abunda kake nufi ba, waye ya buɗe gidan kaji" yanayin yadda ya furta maganar, babu alamun yasan da zancen.


  Fuskar sir mubarak a ɗaure tamau yace"You know who I am. I don't need to explain this to you, Don haka kada ka 6oye min gaskiya, wani gidan kaji ne kuka buɗe kai da jazz? Da kanshi ya faɗa mini cewa kun zuba jari don kuyi kiwon kaji, kusan kullum ne saina kama shi yana yin waya akan gidan kiwon kajin ku"


  Hankalin dr fawan ba ƙaramin tashi yai fa, Muyarshi na rawa ya furta"`wallahi thumma tallahi daddy bansan da zancen gidan kaji ba, sai dai ko ƙarya dr jazz yayi maka, ka ji na rantse maka da Allah..." Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, Sojan dake  zaune a driver seat Ya natsu Yana sauraron su, ta cikin ear-view mirror din motar Yake kallonsu. 


  "Fawan, Ka faɗamin gaskiya, ni nasan Jazz ba zai ta6a yi mini ƙarya ba, na lura gaba ɗaya baka acikin hayyacin ka, idan ma saboda ni ne to ka kwantar da hankalin ka, babu abun da zan yi maka, ni dai buri na shine ka kai ni gidan Kajin ku, inaso in gansu, nayi maka alƙawarin idan ka rakani na gansu zan ƙara maku jari"


  cikin ruɗu dr fawan ya girgiza kai yana fadin"bazan yi maka ƙarya ba daddy, ina ganin ka tamkar uba  agareni saboda ƙaunar dake a tsakanina da Jazz, wlh Daddy ni bamu ta6a yin maganar buɗe gidan kaji da dr jazz ba"

 

  Da kakkausar murya Sojan dake a gaban motar yace"Sir, this boy isn't telling us the truth. Why don't we take him to the headquarter? Maybe if we do, he'll tell us the truth."(yalla6ai Yaron nan bazai fada mana gaskiya ba, Me zai hana Mu shiga dashi headquarter Wata'ƙil idan mu ka je can Ya faɗa mana gaskiya)


Zaro ido waje dr fawan yai, jin ance za'aje dashi headquarter, sir mubarak yace"kada ka damu ai basai munje headquarter ba, akwai bindiga a ƙuguna, "yai maganar tare da sanya hannu ya zaro bindigar Ya ɗaurata saman laps dinshi, tsabar tashin hankali ne tsantsa akan fuskar fawan.


 Sir mubarak yace"idan na kashe ka na kashe banza, sai dai idan munje lahira ayi mana hisabi, don haka ka faɗa min gasiya, idan ba haka ba zan tarwatsa kanka da bindigar hannuna" bawan Allah dr fawan duk sun tsoratar dashi da barazanar su, ƴan hanjin cikin shi sun kaɗa.


  Hawaye tuni sun soma wanke fuskarshi, cikin sanyin murya yace"ko da zaka kashe ni daddy, bazan fasa faɗa maka gaskiyata ba, wlh rantsuwar ɗan musulmi bani da masaniya akan maganar gidan kaji, daddy banyi niyar fada maka ba, amma don in kare kaina zan sanar dakai wani abu da baka sani ba" Hankalinsu gaba ɗaya yana akan fuskarshi.


Numfasawa yayi kafin ya ɗaura da cewa "Daddy, jazz baya zuwa aiki, yau kusan wata ɗaya da sati, bansani ba ko kunsan da hakan, Ni kaina na damu da canzawarshi,". Zuciyar Sir mubarak a hautsine Ya furta"idan kuwa har hakane Dr fawan baka kyauta mini ba! Meyasa tuntuni baka kira awaya ka sanar dani cewa baya zuwa aiki ba? Kusan kullum sai na ganshi ya shirya zai je asibiti, hakan na nufin ba aiki yake zuwaba wani wurin daban ya ke tafiya? Ya jefa mashi tambayar yana mai jin ɗaci acikin zuciyarshi.


  "Ka yi hakuri daddy, Bana son in shiga tsakaninka da shi, sannan ni bansan baku da masaniya akan hakan ba"


  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!" Sir mubarak ne ya furta hakan, zuciyarshi tayi matuƙar karaya da jin cewa jazz baya zuwa aiki, Ya fara zargin shi akan ƙarairakin da ya ke yi mashi, bai ta6a tunanin Jazz zai yi mashi haka ba, duk da irin ƙaunar da yake nuna mashi.


   Idanuwan shi tuni sun kaɗa jawur, zuciyarshi ta motsa.


 "Bana so Jazz ya san cewa nazo asibitin nan! Ko nayi magana dakai! Kaja baki kayi shiru," dr fawan ya amsa mashi da toh daddy, in sha Allah bazan faɗa mashi ba.


     "Ka share hawayen ka," da sauri dr fawan ya zaro hanky ya soma goge fuskarshi.


  "Dr fawan, Na yarda da jazz sai dai a yanzu na fara zargin shi, wallahi If I find out that he's doing something wrong, sai ya ɗanɗani kuɗar shi," rai a6ace ya furta maganar, ya ƙara da cewa "dr fawan nagoda da bayanan da ka bani, zaka iya komawa bakin aikin ka" jiki na rawa dr fawan ya fito daga cikin motar, Bayan yayi masu sallama Ya nufi cikin asibitin yana faman sauke ajiyar zuciya.



    Shiru su ka yi babu wanda ya ƙara magana acikin motar, Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak Kai, Mamakin shi ƙaryar da jazz yai mashi na cewa Sun buɗe gidan kaji, da kuma zuwa aikin da yake yi ashe duk ƙarya ne.


  Driver-operator, Ya fahimci halin da sir mubarak ya shiga na damuwa, cikin kwantar da murya yace"Sir, pls kada hakan ya dame ka, nasan ba daɗi mutumin daka yarda dashi ya sa6aka, sai dai fa har yanzu bamu da tabbacin  abun da dr jazz ya ke yi, mu kyautata mashi zato, sannan shawarar da na ke so in baka yalla6ai, me zai hana mu fidda rana ɗaya, Mubi bayan shi ba tare da sanin shi ba, a lokacin da ya shirya zai tafi aiki,"


  Ta cikin mirror din motar Yake duban sir mubarak, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon drivern yace "Ka kawo shawara mai kyau, tabbas inason sanin me jazz yake aikatawa, nagode da shawararka, zamu Iya tafiya"


Cikin girmamawa Ya amsa mashi da toh, sannan ya tada motar Ya fito da ita daga cikin harabar ajiye motocin, atsanake ya ke yin driving har suka haura saman titi, sir mubarak bai dai na cizon yatsanshi ba, saboda Ya damu da jazz, Ƙaunar da ya ke yi ma mahaifiyar shi ce ta shafe shi, ko ƴa'ƴan shi da ya haifa bai jin su kamar yadda yake jin jazz, hankalin shi ba zai ta6a kwanciya ba idan har bai gano abun da ya ke aikatawa ba, ya jima yana danne zuciyarshi akan ƙin amincewa da zargin yaron da ta ke yi, abun da ya jawo shi ga bincikar shi a yanzu ya fahimci aduk lokacin daya kama jazz yanayin waya da zarar Yaganshi yake rasa natsuwarshi, Jikinshi ya hau kerma, shiyasa ya fara suspecting dinsa.

  

❤ANEELERH❤


Tun kafin ta sallame sallar azahar wayar ta dake ajiye saman drawer take ta buga ringing, da zarar kiran ya katse wani ke shigowa, sai da ta kammala sallar ta ɗaga hannu tayi addu'a ta shafa a fuska, kafin ta miƙe da sauri ta nufi drawer ta ɗauki wayar, murmushi ta saki ganin sunan surukar arziƙi ya bayyana akan screen din wayar, aranta ta ayyana halan baby junaid ne ya matsa a kirani awaya.


  Bayan ta ɗaga kiran ta manna wayar a kunnanta, kafin ta furta sallama muryar junaid ta katse mata hanzarin ta.


  "Mommy, baby junaid ne, ni ne na kira ki awayar granny," har sai da ta ji gabanta Ya ɗan faɗi, da mamaki tace"junaid da gaske kai ka kirani? Ina mommy adama? Ko dai itace ta baka wayar don ka yi mini magana"


muryarshi da shagwa6a yace"mommy ai bata nan, suna a falo, Ni kaɗai ne a ɗakin..." tun kan ya ƙarasa maganar tace"Junaid bana hana ka ɗaukarwa mutane waya ba? Faɗamin ya akai ka iya buɗe mata waya"?


    "Mommy wasa nake maki, itane ta bani wayar, ta fita falo, ni kaɗai ne a ɗakin"


 A faɗa ce tace"ƙarya ka ke yi mini junaid, ba ita bace ta baka wayar, kaine ka ɗauka ka kira ni, maza ka aje mata wayarta tun kan na 6ata maka rai," ta yi maganar tamkar ranta ya 6aci sai dai azahiri ta yarda bashi wayar akayi, kawai tana son ta hayaƙa shi ne.


Sautin kukan shi ne ya cika mata kunnuwanta.


"Mommy ba ki yi missing dina ba, shiyasa kike yi mini faɗa, Kin barni ni kaɗai agidan su, ni wlh gida zan dawo, ko dai kizo ki ɗauke ni ko kuma in gudu in 6ace kamar Angel" maganarshi tayi matuƙar bata dariya, cikin sigar lallashi tace"am sorry my baby boy, wlh nayi kewarka kamar zan zauce, yanzu dai ka yi haƙuri kadaina kuka, Mommyn ka bata son zubar hawayen ka"


   Cikin shessheƙar kuka yace"ni dai kizo ki ɗauke ni mommy, ko in gudu" hankalinta ya dan tashi, zuciya da saƙe saƙe saita dinga tunanin ko dai wani abu akayi mashi ne wanda ya 6ata mashi rai har yake neman dawowa gida.


   "Junaid, faɗamin meya faru? Basa baka abinci ne? Ko ba ayi maka wanka ne? Ko wani ya buge ka ne"! A jere ta furta hakan.


  "Ni ba su yi min komai, ina cin abinci kuma mommy adama tana min wanka har sau biyu safe da dare, ni kawai ke nakeso kizo ki dauke ni, ko in gudu" ajiyar zuciya ta sauke, hankalinta har ya ɗan kwanta.


  "My baby boy, ka kwantar da hankalin ka, zasu dawo mun da kai nan bada jimawa ba,'


  Rigima ya sanya mata"Allah in baki zo ba saina gudu" dariya ce ta kubce mata, jin sautin dariyarta ba ƙaramin 6ata mashi rai ba.


  "Mommy dariya kike mini ko! Shikenan zan kashe wayar" da sauri tace"sorry nadaina, pls kada ka kashe min waya, Ina jin daɗin yin magana dakai, Yanzu faɗa min a kwance kake ko a tsaye"


  "Saman gado" ya bata amsa atakaice, har ta buɗe baki zatayi magana ya katse ta da cewa"Mommy, na tuna sunan mutumin nan da ya kira ki a waya, ran nan, amma ba zan fada maki ba, In kina son ji kizo nan"


  "Am sorry my baby boy, yakamata ka fahimce ni, babu yadda za'ai inzo, Zasu yi tsammanin ban yarda ɗazu bane shiyasa na biyo ka, dan Allah ka faɗa min sunan shi, ka ji yaron kirki" 


cikin ƙagara da sonji tayi mashi maganar.

   "Toh mommy, zan faɗa maki amma bana so kowa yaji har zahra" muryarshi da shagwa6a yake magana.


  "Junaid, Ni kaɗaice a ɗakin, Zahra bata nan taje wurin aiki, Mahboob ma baya acikin gida, Abie da Uncle basu dawo gida ba, mami da ummi ne kuma  basa a ɗakin, suna a can palour suna fira" 


  "To zan faɗa maki, amma kada ki faɗa ma zahra da mahboob" ta rasa ya za ta yi da shi, Yaƙi faɗa mata sai jan maganar yake yi kamar baya son fadi.


   Kukan ƙarya ta soma yi mashi tana fadin"dan Allah baby junaid dina ka faɗamin, zuciyata zata iya bugawa idan ban ji ba" tuntsirewa yayi da dariya yana fadin"mommy wasa kike ba wani kuka ai na ganoki" gajiya tayi da tsayuwar, ta koma gefen gado ta zauna, tamkar tana agabanshi ta marairaice mashi fuska tana fadin"pls my baby boy, ka faɗa min, komi ka ke so zan yi maka"


  "Zoben Angel, da ki ka ce zaki siya mini in bata tun da na maida ba mahboob nashi"


     "Kada ka damu, kafin ka dawo gida zan siya maka zoben, Nayi maka alƙawari, Yanzu faɗa min toh"


  Sai da ya mula ya ishe iska tukunna Ya furta"wai ma...waima daddyn Unaisah, haka yace min fa" shiru tayi jimm tana tunanin sunan daya furta mata daddyn unaisa? Wanene daddyn unaisa? Ita kanta unaisan wacece ita!, sunan ya shige mata, jin tayi shiru yasa Baby junaid ambaton sunanta"mommy kin yi shiru baki ce komai ba"


  "Junaid, na ruɗe ne, na kasa gane wanene daddyn unaysa, amma shi mutumin Iya abun da ya faɗa maka kenan"?


   "Eh, bai faɗa min komai ba, Mommy ki kira shi ki ji toh wanene shi, ko daddyn Angel dina ne?"


lokaci ɗaya taji gabanta Ya faɗi Jin Ya ambaci ƙila daddyn Angel ne, nan take ƙwaƙwalwarta ta tunano mata sunan wacece Unaisa, a sukwane ta mike tsaye Tana faman zare idanuwanta, zurfi tunani ta shiga duk duniyar nan mutun ɗaya ta sani mai sunan daddyn unaisa, wato Tajuddeen, ta gaza yarda da abinda zuciyarta ke faɗa mata.


  La66anta na kerma ta furta"ka tabbata haka sunan yake? Ko dai abakina ka ta6a jin na ambaci sunan daddyn Unaisa?


  "Mommy wlh dagaske nike maki haka yace min wai in faɗa maki daddyn unaisa ne, mommy zan kashe wayar, ga mommy adama nan zata shigo dakin" kafin ta yi mashi magana yai rejecting kiran.


    Hakanan tadinga jin bugun zuciyarta na ƙaruwa, jiki asanyaye ta koma gefen gadon ta zauna, tsawon mintuna zuciyarta nayi mata kokwanton maganar da junaid Ya faɗa mata, har dai a ƙarshe ta yanke shawarar cire nombar daga black list, don ta kira ta ji wanene mutumin da junaid ya fada mata cewa daddyn Unaisa ne, fatanta Allah yasa Dagaske ne hasashenta. 


  Yatsun hannunta har kerma suke Yi wurin daddana wayar, bayan ta cire number daga black list, ta danna call cikin sa'a Kiran Ya shiga, wayar ta fara ringing, tsabar zumuɗi jikinta har kerma yake yi, Har kiran yayi rejecting ba'a ɗaga ba, Miƙewa tayi tsaye ta zame dogon hijabin jikinta ta jefar saman mattress, safa da marwa ta cigaba da yi a tsakar ɗakin, ta ruƙe wayarta a hannunta, a Ƙalla Ta Kira layin kusan sau biyar Yana ringing ba'a ɗaga ba, Hankalinta yaƙi kwanciya burinta taji wanene mutumin nan daya kira kanshi da sunan daddyn Unaisah.


Har ta fidda rai da za'a ɗaga Kiran, Unexpected A kira Na shida data yi mashi sai gashi Anyi picking call din.


  Cikin rashin natsuwa ta furta"Assalamu alaikuma" maimakon ta ji muryar Namiji sai taji muryar matashiyar mace tana yi mata magana da wani yare.


  "Baiwar Allah, bana jin harshen da kike yi mini magana dashi, Idan kina jin hausa mu yi magana da shi"


  Ko da Aneelerh ta ambaci hakan, matashiyar sai ta canza harshenta zuwa Yaren hausa ta ƴan koyo tace"wanene ke magana"? A ƙagare Aneelerh tace"sunana Aneelerh, dalilin dayasa na kira Layin, kwanakin baya ana yawan kirana dashi, Ina tunanin ko wani ne ke nema, pls ina neman me wayar" ta faɗi hakan ne don junaid ya fada mata cewa Namiji ne Ya daga kiran lokacin da aka kira.


  Matashiyar budurwar tace"Ni ce me wayar, wato irin kune ku ke bibiyar mazajen mu don ku ƙwace mana su ko"? Sakin baki Aneelerh tayi jin abun da matar tace.

  

  "Kiyi haƙuri, Nima matar aure ce kamar ke, kawai inason nasan ainihin wanene me wayar, ki taimaka min a ƙagare nake da son ji" da alama matashiyar Yarinyar Akwai ƙuruciya atattare da ita, tun daga kan kalamanta zaka shaida hakan.


  "Nace maki ni ce me wayar," atsawace ta furta hakan, Aneelerh tace"ba wayar ki bace, saboda ke da kanki ki ka ce irina ne masu bibiyar mazajan mutane don mu kwace masu miji, hakan na nufin ba wayarki bace wayar mijin ki ce" sautin dariyar matashiyar ne ya cika mata kunnuwanta, lamarin ya ɗaure ma Aneelerh kai, gashi duk ta ƙagara a matse take da son jin wanene.


  "Ke dai zan faɗa maki gaskiya, tun da kin gano ni, ba wayata bace, wayar mijina ce, kuma baya nan Ya fita ni ka ɗai ce agidan"


  "Okey, pls Ko zan Iya sanin sunan mijin naki"?

 

  "A'a gaskiya, salon ki je ki kai ma boka sunan shi ayi maki asiri ki mallake shi" duk yadda Aneelerh ta kai ga jurewa saida ta fashe da dariya jin abun da Yarinyar tace, daƙyar ta sassauta da yin dariyar tace"wlh ni bana bin boka, Ko hanyar zuwa wurin shi bansani ba, Yar uwata ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, ni bana ɗaya daga cikin matan dake zuwa wurin boka, saboda na dogara da Allah shi kadaine zai Iya biyamun buƙatuna"


  matashiyar tace"Ni ban yarda dake ba, mata dayawa suna son ƙwace mini mijina saboda kyakkyawa ne kuma yana da ƙarfi"


 Aneelerh tace"baiwar Allah na faɗa maki nima matar aurece, da mijina akan me zan nemi mijin ki"!


  "Oho nima bansani ba, idan kin gama magana zan kashe wayar" amsar data ba aneelerh kenan" Shiru aneelerh ta ɗanyi tana tunanin hanyar da zata 6ullo mata, ta fahimci Yarinyar bata da cikakken Ilmi da wayau sai a hankali. Dabara ce ta faɗo mata.


   Dariya ta fara saki, Matashiyar tace me kike yi ma dariya Aneeleh tace"Ai dole inyi dariya, ke yanzu baki gane muryata ba ne? Aneelerh fa ce matar abokin mijin ki Shu'aibu"


  Da buɗar bakin budurwar sai cewa tayi"ƙarya kike yi aini mijina basu nan shi shu'aib ba, TAJ ne sunan shi, Kina son ki yi mini wayau ne" 


Jin ta ambaci sunan Taj Yasa Aneelerh Tsayawa cak ta dakata da yin tafiya, yayin da bugun zuciyarta ya ƙaru, Muryarta na ɗan rawa ta furta"ƙarya kike yi, ba sunan mijin ki tajuddeen ba, so kike in yadda don kada ki faɗa min ainihin sunanshi, ai ni nasani Shu'aibu ne sunan shi"


  Matashiyar budurwar tace"To kada Allah yasa ki yadda ma, kuma wlh ma ƙarya kike yi mini cewa wai ke matar abokinsa ne baki da gaskiya," da alama ranta ya 6aci ta fara harzuƙa.


  Sassauta murya Aneelerh tayi"Ki yi haƙuri, ba yadda ki ke tsammani bane, Dan Allah ki faɗamin ina mijin naki yake inason yin magana dashi"


 Dogon tsoki matashiyar Taja, kafin ta furta"ba kin ce ke matar abokinsa bane? To ki ce ma shu'aibun Ya kawo ki gidan mu," kafin Aneelerh ta furta wani abu, Matashiyar ta katse kiran!"


 Hankalin ta Yaƙi kwanciya, Jiri ta soma gani acikin idanuwanta, a daddafe ta nufi gado, Ta haye ta kwanta, Yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling, zuciyarta ta shiga ruɗani, tun da Matashiyar ta ambaci sunan tajuddeen, natsuwarta tabar jikinta, taso ace tayi waya da shi don ta tabbatar da abun da take hasashe.


 Har ƙara jaraba kiran layin tayi amma matar taƙi ɗagawa.


  Dubara ce ta faɗo mata aranta, da sauri ta rubuta mashi saƙo cikin harshen turanci. 


  _Idan ka karanta saƙona, dan Allah ka kira ni, Inason Yin magana da kai, saƙo daga Aneelerh muhammad falgore_


 Ajiyar zuciya ta sauke Bayan ta kammala rubuta mashi sakon, Ta ɗaura wayar saman side drawer, A gogon ɗakin ta kalla ƙarfe Uku na rana, kwanciya tayi saman gadon tana jiran tsammanin Kiran me wayar.


  

   ❤ZEENATU❤



A 6angaren zeenatu kuwa tun da ta fito da gudu daga ɗakin Dr. Shureim ta koma ɗakinta, ta fada saman gado taci gaba dayin kuka tamkar ranta zai fita, cikin muryar kuka take fadin"yaya shureim ba sona yake yi ba, wata yake so daban, dama nasani babu namijin da zai yarda yaso ni saboda rashin natsuwata,"


  Idanuwanta sun kaɗa jawur, miƙewa tayi zaune ta soma cire lace jikinta a saman floor, ta watsar da kayan hada ribbon din da aka daure mata gashin kanta, iya undy ta bari a jikinta, ta jashi saman ƙirjinta, tana huci yayin hawaye ke cigaba da wanke mata fuskarta, saukowa tayi daga saman gadon ta nufi gaban dressing mirror dinta, cikin 6acin rai ta sanya hannu ta watsar da jerin turarurrukanta komai sai da ta wurgo shi ƙasa, bayan ta gama ta koma gaban wardrobe dinta, ɗaya bayan ɗaya sai da ta wurga da suturar saman floor, hankalinta bai kwanta ba har saida ta maida ɗakin kamar na mahaukata, tukunna ta koma saman gadon ta haye tare da jan bargo ta lullu6e zuciyarta na ta farfasa.


Bayan Dr. Shureim ya fito daga wankan, kimtsa kanshi yai ciki shiga ta larabawa Ya feshe jikinsa da turare, 

   Ya ruƙo wayar shi a hannun shi, tare da car key dinsa, walking quickly ya fito daga bedroom dinsa, Ya nufi ɗakin zeenatu, duk inda Ya gifta a paloun masu aiki ne suke Yin aikace aikacen su cikin girmamawa suke gaishe da shi.


    "Yalla6ai barka da fitowa" muryar Tani ce ta katse mashi hanzarinsa, dakatawa yai da yin tafiyar ya juya ya dubeta


   "Yawwa barkanki, Ya aiki" fuskarta da fara'a ta amsa mashi"Lafiyalou Alhamdulillah,"


    Har zai wuce ta Ya kuma tsayawa ya kalle ta"Ɗakin zeenatu nake nema" Da rawar Jiki ta ce"Yana a second floor, muje in nuna maka ɗakin" ta faɗa tare da yin gaba Yabi bayanta, Yayi matuƙar ƙagara da son ganinta, duk don Ya lallasheta akan laifin da yayi mata.


  Bayan sun hau elevator ta sauke su a second floor, Tani ta nuna mashi ƙofar ɗakinta.


 "ki shiga ki faɗa mata inason magana da ita"

    Tani ta amsa da toh, tana zura ƙafarta ɗakin zeenatu, gabanta Ya faɗi ganin irin 6arnar da tayi, hankalin ta ba ƙaramin tashi yai ba, jiki na rawa ta nufi gefen gadonta.


  "Zeenatu! Lafiya meke damunki ne? Meyasa kika hargitsa suturar ki"?


  Shiru zeenatu bata tanka mata ba, saima ƙara ƙudundune kanta da take yi cikin bargo.


  "Dan Allah zeenatu kiyi mini magana, nasan 6ata maki rai akayi ki fada mini wanene" 


 Jin tayi shiru ba ta yi mata magana ba yasa tace"ba zan takura maki ba, Yanzu ki tashi Yayan ki shureim Yana a ƙofar ɗakin ki, shine yace in yi maki magana yana son ganinki"


  Kamar jira ta ke yi Tani ta ambaci sunan shureim, Cikin shessheƙar kuka tace"Tani, I don't want to see him. Please tell him I won't come. Yaya Shureim doesn't love me wata yake so daban, tun jiya yayi min alƙawarin zamu fita yawo atare, yau kuma da kanshi yace min inje in shirya kafin in dawo zai yi wanka ya shirya, Tani da naje ɗakin shi babu abunda yayi, yana akwance saman gado yana kallon hoton girl friend dinsa a laptop...." daƙyar ta ƙare maganar.


  Jikin Tani yai sanyi, duk sai taji ba daɗi, sai yanzu ta gane dalilin dayasa ta shiga halin da take aciki.


   "Kiyi haƙuri zeenatu, ki tashi ki gyara jikinki, Yace yana son magana dake nasan yazo ne don ya baki haƙuri, kuma naga ya shirya hada key din mota a hannunshi...." Katse ta Zeenatu tayi"Na fasa zuwa ki faɗa mishi bazan je ba, tun da bayaso na"


 Cikin muryar raɗa Tani tace"yana fa jin ki, bai kamata kina ɗaga murya ba, sannan ke in banda abunki waya fada maki budurwashi ce yake kallo awayar? 


  "Ai naga hoton da yake kallo, Yana a kwance saman gado ya rungumeta a kirjinsa" ta fada tana jan numfashi taƙi fitowa daga bargon.


  "Zeenatu, kiyi mashi kyakkyawan zato, yaya shureim yana sonki fiye da yadda kike son shi, Ni shawarar da zan baki shine kada ki bari ya gane kina son shi, idan kika kwantar da hankalin ki da kan shi zai furta maki kalmar so"


   Sassauta muryarta tayi"Tani, zan iya jure wannan amma bazan Iya jure kallon hoton budurwarshi da Yake Yi ba,"


 Dafe kai Tani tayi da hannu ɗaya"zeenatu baki da tabbacin budurwashi ce, pls kibi komai a sannu zamu gano ainihin wacece Yake kallo awayarshi, Yanzu Ki tashi muje Yana awaje yana jiranki'


  "Tani ki daina wahalar da kanki, Nifa ba inda zanje, Ki fada mashi bana Jin daɗi bacci Nike Yi"


  Duk yadda Tani taso ta lallashe ta akan ta tashi ta je gare shi taƙiya, a dole ta ƙyaleta ta juya ta fuce daga ɗakin.


 A tsaye ta same shi Ya jingina bayanshi jikin bango.


  Harya fara Gajiya da tsayuwa

"Ka yi haƙuri, Zeenatu tayi fushi bansan meya haɗa ta dakai ba, nayi ƙoƙarin In lallasheta amma taƙi amincewa ta amsa kiran ka, ban ji daɗi ba shureim, duk da bansan meya haɗa ka da ita ba, amma bai kamata tun yanzu afara samun rashin jituwa a tsakaninka da ƙanwarka, zeenatu tana da haƙuri sai dai tana da zuciya idan aka 6ata mata rai'


     Tun da ta fara magana Ya natsu yana sauraronta, sai da ta kai karshen maganar tukunna yace"Inaso zan shiga ciki"


bai jira amsar da Tani zata bashi ba yai saurin haura ƙafarshi cikin ɗakin zeenatu.


   Dafe kai tayi da hannu ɗaya tunawa da 6arnar da zeenatu tayi a ɗakin, gashi kuma Ya shiga hake zai je ya same shi kamar bola, can kuma ta ayyana aranta cewa ɗan uwanta ne, daga haka ta ƙara gaba.


A tsanake Yake bin ko'ina na ɗakin da kallo, yayi mamakin ganin yadda ta hargitse komai, ta rikita mashi tunanin shi, Ya rasa gane fushin menene take yi da shi? Don shi a tunanin duk akan fitar da yace za su yi ne.


 Sam bai lura da lace din data cire ta jefar saman floor, idanuwanshi na akan gadonta, bargon da ta lullu6e dashi sai kerma yake kamar wadda sanyi ya kama.


   daddaɗan ƙamshin turarensa ne Ya daki hancinta, Nan take ta fahimci Ya shigo ɗakin nata.


  Gefen gadonta ya zauna Yana dubanta, calmly ya furta"Zeenat ina son yin magana dake

   Shiru tayi bata tanka mashi ba, tayi tunanin Tani ta fada mashi cewa bacci take yi kamar yadda tace ta gaya mashi.


   "Nasan Kina Jina zeenatu, Ki amsa mini, nazo ne don in baki haƙuri, nasan ban kyauta maki ba, Yanzu haka da nike yi maki magana na kammala shiryawa ke nake jira mu tafi"


     Cikin disasshiyar murya tace"yaya shureim bana jin daɗin jikina, bazan iya fita ba, sai dai zuwa gobe"


  "am sorry zeenatu, fushi kike yi da yayan naki? Ba za ki yi mini uziri ba? 


  "Yaya shureim ni ba fushi nike yi dakai ba, fitarce na fasa, Bana jin daɗi"


    Ya rasa ya zai yi ya shawo kanta don ta amince su fita.


     Yanke shawarar Yaye Bargon Jikinta yai don ya samu damar lallashinta dakyau.


  Tsautsayine Yakai hannun shi saman bargonta, Ya ruƙo shi tare da jan shi, Ras yaji gabanshi ya faɗi da sauri Ya maida mata bargon a jikinta, Yana faman jan numfashi da ƙarfi da ƙarfi, miƙewa yai da wani irin Yanayi ya nufi ƙofar fita daga ɗakin Yayin da la66ansa ke ambaton sunan Allah, Har ya kusa kaiwa ƙofar ɗakin Muryar zeenatu ta katse mashi hanzarin shi.


   "Yaya shureim kai da kanka ka faɗa mini cewa baka ta6a yin soyayya ba, amma meyasa kake kallon hoton wata awayarka" 


Ta gaza haƙura har saida ta amayar masa da abunda ke cikinta, shi kuwa Man din duk ya rasa natsuwarshi, tunda Yaja bargonta Yayi arba da undy din jikinta shara shara Hakan ba ƙaramin tada mashi hankalin shi yai ba, ga dukkan alamu ita batasan ma ya buɗe bargon ba saboda ta ƙudundune kanta, idanuwanta suna arufe.


  "Zeenatu, abun da na faɗa maki da gaske ne, banyi maki ƙarya ba, Ni ban ta6a yin soyayya ba"  A hankali Ya ɗan Juyo yana dubanta, a lokacin ta fiddo da kanta daga Cikin bargon, Yalwatacciyar sumar kanta, ta rufe mata gefen fuskarta, Jan bakin data shafa ya dame fuskar saboda kukan da tasha, har saman kumatunta jan bakin ne, duk da kwalliyar fuskarta ta 6aci ba ƙaramin kyau tayi mashi ba.


    Muryarta da shagwa6a tace"ka faɗamin wacece ka ke kallo awayarka? Idan ba budurwar ka bace.


   Ƙayataccen murmushine Ya bayyana akan fuskarshi, sai yanzu ya gane dalilin dayasa take haukan nan, wato kishin shi take Yi saboda yana kallon hoton wata wayarshi, aranshi ya ayyana da ace tasan hoton wacece yake kallo da batayi haukan nan ba.


   "Zeenatu, dama saboda hoton wayata kike kuka"? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh.

  "Okey, Ki kwantar da hankalin ki, ba budurwata ba ce," maƙe mashi kafaɗa tayi"ni ban yadda ba yaya shureim, idan har dagaske kake yi min ba budurwan ka bace to ka nuna min hoton in gani"


   Lumshe idonshi ya ɗanyi tare da waresu kan fuskarka, duk da tazarar dake a tsakanin su, ba ƙaramin Kyau take yi mashi ba musamman yanzu daya fahimci irin zazzafan son da take yi mashi.


  Ganin ya tsareta da ido, ba tare daya furta komai ba yasa tace"Yaya shureim  magana fa nake yi maka, kayi shiru baka ce komai ba, Ni dama nasani baza ka nuna min hoton in gani ba"


 Yadda take yin maganar tana jujjuya eyes balls dinta ne suka ƙara rikitar da shi.


  Gyaran murya ya ɗanyi kafin yace"Idan har Ki ka amince zaki shirya mu fita, Ni kuma zan nuna maki wacece nake kallo awayata," zum6ura mashi baki tayi"toh, amma ka fara yi min alƙawari,"


  "Nayi maki alƙawari" 


"Yanzu zan shirya yaya shureim," ganin tana ƙoƙarin miƙewa tsaye yai saurin fuce wa daga ɗakin gudun kada Ya ƙara ganin abunda zai hana shi Runtsawa.


Fitowa ya yi daga cikin gidan Ya nufi harabar ajiye motocin su, Wasu danƙara danƙaran motoci ne na Alhaji musa a killace a ƙalla sun haura goma shabiyar, kuma dukansu babu motar ƙasa da miliyan talatin, Manya manyan motocine tsadaddun gaske masu numfashi.


  Motarshi Ya buɗe Ya shige Ciki Ya zauna a driver seat haɗi da ɗaura kanshi jikin headrest, bakomai Yake tunawa ba face maganar da Alhaji musa ya faɗa mashi akan Aiki da kuma aure, A yanzu ya fara tunanin ta yadda zai 6ullo mashi da zancen auran zeenatu, yafi buƙatar auren akan komai, saboda yanason ya samu natsuwar cigaba da gudanar da rayuwarshi, zeenatu ta kwanta mashi aranshi ɗari bisa ɗari, kuma yana da tabbacin zeenatu zata maye mashi gurbin abunda ya rasa.


  Almost 15 mins, ƙamshin turarenta Ya doki hancinsa, Nan take ya fahimci ƙarasowarta, buɗe motar Tayi tare da samun wuri ta zauna gefenshi" ɗaura idonshi yayi akan face dinta, babu make up, zallar kyan da Allah yayi matane, ta canza kayan jikinta zuwa turkish gown launin black gray, Ta yafa mayafi akanta, Idanuwanta sun kumbura saboda kukan da tasha.


    Kallon Juna suka somayi kamar zasu haɗiye kawu nan su, Ko ƙyaftawa basa yi, kunyar shi ce ta kama ta, da sauri ta daura kanta saman laps dinta.


  "Zamu Iya tafiya" da shagwa6a tace"a'a yaya shureim, nafi so ka fara nuna mini hoton in gani"


  Zaro wayarshi yai daga cikin aljahu Ya daddanata, Kafin Ya miƙe mata wayar"kar6i ki ganta, Kyakkyawa ce tafi ki kyau, ita nike da burin aure"

 

Gabanta na faɗuwa ta ɗago, tare da sanya yatsun hannunta dake kerma ta kar6i wayar da ya miƙo mata, idanuwanta rufe tabarsu, Gudun kada taga abun da zai hanata kwanciyar hankali.


  Dr. Shureim dake kallonta, murmushine ɗauke akan fuskarshi


  "Meyasa ki ka rufe idonki"? Muryarta na rawa ta furta"bana son inga abunda zai hanani bacci" 


 "In sha Allah ba zai hanaki yin bacci ba, sai daima ya sanyaki yin bacci cikin kwanciyar hankali, now Open your eyes slowly and look at the picture," 


She took a deep breath and tried to slowly open her eyes kamar yadda ya bata umarnin ta bude su a hankali....."



(Kaɗan daga cikin na sati mai zuwa idan Allah yakaimu da rai da lafiya🤣 sai dai Allah yakaimu zamu gani, Very soon In sha Allah Zamu shiga Takun ƙarshe na labarin kurkukun ƙaddara)


 *Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya, Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*




First bank




3196407426, 




*Bature Hafsat Muhammad, za'a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*

No comments