Breaking News

Mai Daki Complete Hausa Novel

 SADAUKARWA

Sadaukarwar littafin ta Iyayena ce,

Alhaji Chindo Muhammad Sodangi da

Hajiya Fatima Musa Sodangi, Ubangiji

ya saka muku da alheri ya kuma kara

muku lafiya amin.



TUKUICI

Tukuicin littafin naki ne;

Khadija Chindo Sodangi (Mrs Nasiru

Idiris)


JINJINA

Jinjinar littafin taki ce Amarya ba kya

laifi (Maman Umar) Zuhuriyya Ibrahim

(Mrs Lawal Chindo Sodangi), Ubangiji

ya raya Umar da Imani


FATAN ALHERI GARE KU

Fatima Abdulkadir Kazaure

Hafsat Iliyasu Unguwar Rimi



Khadija Usman Nasarawa

Nafisatu Ibrahim Muhammad

Fatima Ahmad Shehu Kaduna

Maryam Muhammad Gusau, Zamfara

Umaima Abubakar Umar

Maijidda Uba Magaji

Na gode, Ubangiji ya saka da alheri

amin.


KUNA RAINA

Hajiya Maryam (Mami) Dan Hassan

Hajiya Jamila Ibrahim Na-Bature

Hajiya A'isha Balarabe (Jazan)

Ubangiji ya bar zumunci amin.


4


Littattafan SODANGI:

Uwar Mijii

Naga Ta Kaina

Rabon Kwado..

Cikar Alkawari

Wayyo Duniya

Yi wa Wani..

Abu Naka...

Mata Ma su Duniya

Nufin Allah

Kifi Na Ganinka...

Daga Kin Gaskiya...

Da Kamar Wuya..

Mai Uwa...

Duk Daya..

Mata Da Kicin Dinsu

Wacece Ni? 

Wata Fuskar...

Mijin Ta ce

Garin Banza..

Ga ni Gare ka


5


Biyan Bukatar Rai

Shamaki

Hattara

Mata Masu Duniya

Kyautata

Ayi Dai Mu Gani...

Tabbataccen Alamari

In Kunne Yaji..

Halin Rayuwa

Mai Daki.


Littattafan ba sa nufin yi da wani ko

habaici ga kowa sai dai an rubuta su ne

don fadakarwa da nishadantarwa, ana

neman afuwa ga duk wanda yaga wani abu

yayi kamar abinda ya shafe shi, ba da shi

ake ba dace ne kawai.


6


MAI DAKI.3

Bin ta da kallo suka yi cikin

mamakin irin yadda ta dangwarar

da kula,  wannan kuma wacece? 

Ina dan murmushin da ban san na meye ba

na ce, yarshi ce.

Fu Suka hada baki Yarshi? Na ce, Eh, ita

ce ta biyun tana da wa yana Makaranta

Dankaci ke ki ce akwai babbar magana

haka suke sakaka babu tarbiyya.

Ban sake cemusu komai ba mikewa

nayi na shiga kicin na debo plates da

cokala na dawo sai ga Larai ta shigo dauke

da wata kular da kato kular ruwa mai

famfo alamar abin sha ne a ciki. 

Ta gaisa da su Baba Ladi sannan ta juya

ta tafi. Na bude kular miya da taji naman

kaji ta ukun kuwa kunun aya ne mai kauri.

Na zuba musu na mika musu sannan

nima na zuba naci sosai saboda yunwar da

ke damuna.


7


Sai da muka gama cin abincin ne Baba

Iya ta ce "To kai mu wurin uwar mijin taki

mu gaisa ko 'yannan."

Na mike suka bi ni. A bakin kofar

dakin muka yi sallama ban shiga ba sai da

ta ce a shiga.

Karba sosai tayi musu sannan suka fara

tattaunawa a kan al'amuran aure da

halayya na ya'yan zamani na rashin

kunya da fitsara har suka kawo kan danta

tana basu labarin rasuwar da mahaifinshi

yayi ya bar mata su tun bata fi shekaru

talatin ba a duniya.

Ya barta da Ahmad da Yayarshi Kausar

da a yanzu take aure a Kano wurin dangin

Babanta, da aure-auren da ya yi guda hudu

mata biyu suka haifan mishi 'ya'yanshi

Zaidu da Zainaba.

Sai kuma wata ta haifi Ziradat da

Zinatu, sai wasu biyu da ba su haihu ba.


8


A raina na ce, "Dankari! To me yasa

bai taba gaya mun cewa ni ce matarshi ta

biyar ba?"

Na kawar da wannan tunanin daga

cikin raina, ko bai gaya mun yawan matan

da ya aura ba ai ya gaya mun yana da

'ya'ya hudu.

Shi kenan magana ta kare.

Hira sosai suka y1 sannan suka taso

muka dawo sashena. Hajiya ce tasa aka

mayar da su Baba Ladi gida bayan nayi

musu kyaututtuka daga cikin kayan

aurena.

Kwalliya sosai na sake tsalawa da

yamma shadda danya da aka yi wa wani

irin dinki na Senegal ruwan kofi na saka,

na saka dan kunne fashion ruwan zaren

jikin shadar.

Na feshe jikina da turaruka sannan na

kunna bumer na saka na daki yabi gidan gaba

daya. Karfe shida daidai naji tsayuwar mota a

Wurina.


9


Na leka, Ahmad ne. Na dawo na zauna ina

jiran naga shigowarshi ban ji ba, har aka yi

magriba aka yi Isha'i sannan ya shigo dakin.

Yana kallona ya ce "Wow! Allah na gode

maka da kayi mun baiwa da samun Hauwa' u

a matsayin mata ka bani zaman lafiya da ita

ka albarkace mu da albarka da ka ke yi wa

Ma'aurata.

Murmushi na rinka yi har ya iso in da

nake ya jani zuwa jikinshi ya rungume

ni yana rada mun a kunnena ke baki iya

yiwa mijinki oyoyo ba ne?

Rike hannuna yayi ya jani zuwa wani

wuri da ban kula da shi ba a gidan. Kofa

ce ya budeta muka shiga.

Babban wuri ne, don falon yafi nawa.

Duk wani abu da ke falon faci ne tas tun

daga kujeru har zuwa labule.

Falon ya matukar kawatuwa ba

kadan ba, bai bar ni a nan ba cikin

dakinshi ya wuce da ni.

Wanka za ki taya ni nayi."


10


Na gwalo ido ina kallonshi, ya ce

"Ko ba za ki iya ba?

Nayi shiru, murmushi yayi ya soma

cire kayan jikinshi na kawar da kaina

zuwa kallon wani wawakeken hoton da

ke manne jikin bangon gadon shi na

wani irin ruwa da ke zubowa daga wani

tsauni zuwa wani dan koramai masu

tsuntsaye.

Kafin na juyo har ya shiga bayan

gidan dakin. Mintuna kadan ya sake

fitowa da tawul daure a kugunshi yana

goge jikinshi da wani.

Dauko mun kaya a cikin wardrop

din gabanki. Na bude ina dubawa.

An kakkasa kayan kashi-kashi, under

wears, kayan barci, jallabiya da tract

suit alama na babu kayan fita a wurin na

ce wacce zan dauko maka?

Ya zubo hannayenshi ta kwibina tare

da dora kanshi a kan kafadata har ina


11


shakan kamshin man wankan da yayi

amfani da shi da ke jikinshi.

Ya ce, "Kamshin turarenki mai dadi

Hauwa'u. Ban iya ce mishi komai ba

don ban saba irin wannan mu'amallar

ba.

"Idan ba ki san wacce za ki ba ni ba,

to bar shi haka mana kawai ba shi kenan

ba, dama ai ba fita zan sake yi ba."

Na jawo wata rigar barci da ke can

sama saboda ya sassauta rikon da yayi

mun, na ce "To ga wannan. Ya ce, "To

juyo ki saka mun. 

"To ai saika sake ni tukuna

zan iya saka makan.". Na juyo ina saka

mishi rigar tun daga hannu har na daure

mishi belt dinta.

Yayi murmushi ya ce, "Hauwana

kenan." A falon shi muka zauna yana

kallonlabarai yana yi mun yan

12


hirarraki ya ce, "So nake na dan takura

miki kadan."

Na ce,"Wacce irin takura kuma?" Ya

ce, To ban sani ba ko ba za ki ji dadin

ta ba, so nake daga gobe na fara cin

abinciki. Idan ki ka yi mun haka zan ji

dadi."

Nayi murmushi "Nima hakan yafi

mun ai, kamar na gaya mishi haka sai

na fasa. Ya ce, "Ba ki ce komai ba."

Na ce,Yadda duk ka ke so haka zan

yi." Ya ce, "To na gode."

Washegari daga fitan shi sai ga

cefane rigigif babu abinda babu, kaji,

kifi, nama, tumatir, komai dai na

bukatar gida.

Wayata na dauka na kira shi na ce,

"Za a yi na rana ne da za a kawò

maka?'


13


Ya ce, "A'a Hauwa'u wannan Haj1ya

tana sawa a kawo na dare kawai za ki

yi."

Na ce, "To me za ka ci da daddaren?

Yayi shiru zuwa can ya ce, Na baki

zabin yau dai kam ko meye ki ka yi zan

ci."

Tsayuwa nayi ina kallon cefanen da

aka yi, na rasa yadda zan yi na fara

tamfar wacce bata taba girki ba.

Karaf na tuno da littafin Momin

Hindu, shi na dauko na bude ina

dubawa amma na kasa zaben abinda zan

yi. 

Da kyar na iya zaben wani da na

gani ina dubawa meat 'tagine' sunan

ne ya yi mun dadi, har nake dubawa

ganshi ba mai wahala sosai ba. 


14


Sannan akwai kayan hadin gaba

daya, yanayin yadda naga girkin a

hoto.

Na fara hada kayan amfanin nama,

mangyada, yaji, tattasai, attarugu,

albasa, tafarnuwa, gishiri, maggi,

karas, citta, bawon lemon tsami,

tumatirin gongoni da ruwa.

Nan da nan na hada abubuwan na

rangada miyata mai wani irin kyau da

sha'awa. Na daukó ledar cous-cous

na dafa saboda ganin da nayi da shi

zai dace.

Na kira Momin Hindu ina bata

labarin abincin da nayi. Tayi

murmushi ta ce, "To saura abin sha."

Na ce, To ai ban san me zan yi na

sha ba. A gajarce ta gaya mun.

Ina gamawa na shiga bayan gida

nayi wanka.


15


Yau ma kwalliya nayi ta materia

ya kuma yi mun kyau sosai. Na yane

jikina da babban gyale na dauki

babban food flask din da na zubawa

Hajiya abinci a ciki na dauka nayi

sallama a bakin dakin na shiga, bayan

an ba ni 1zinin shiga.

Na ajiye abincin a gefe na zauna.

Ta kalli food flask din ta ce "Ai ba sai

kin rinka sako abinci ba don ba ci

suke yi ba, sannan ga Larai nan idan

muna bukatar abu zata rinka girkawa,

mijinki kawai ban da mu."

Na kai kamar mintina goma na

tashi na dawo wajena, na kalli agogo

har yanzu karfe shida bata yi ba.

Na gyara kwanciyata a kan

doguwar kujera na kunna TV ina

kallon CCTV Documentry da ake yi

akan wani kabarin tsohon Sarkin


16


Kasar Sin da ya mutu shekaru dari

biyar da suka wuce.

Yau ma Ahmad bai shigo ba sai

bayan sallar Isha'i. A dakin shi na

ajiye mishi abincin saboda wankan da

yake yi.

Ya fito yana goge jikinshi da tawul,

ya samu na ciro mishi riga da wando

na hutawa masu sauki.

Ya dan yi murmushi yana kallona

tare da amsa gaisuwar da nake yi

mishi.

Yasa hannu ya dauki kayan da na

ajiye ishi akan gadon yana sakawa, ya

gama ya riko hannuna.

"Muje ki bani abinci." A kasa ya

zauna a kan kafet yana duba wani

sako da ya shigo wayarshi, ni kuma

ina zuba mishi abinci a plate.


17


Na gama na tsiyaya mishi coconut

juice din da nayi mishi na fara mika

mishi.

Ya karba ya dan yi murmushi ya

ce, "Bismillah zan fara cin abincin

amarya. Nayi murmushin jin abin da

ya ce. Ya kai juice din bakinshi ya

kwankwade ya ajiye kofin a kasa.

Ya kalle ni na dauka madara ce, na

ce a'a ba madara ba ce, ya ce To

menene'? Na ce Juice din kwakwa

ne."

Ya sa cokali ya fara cin abincin

gaba daya muka yi shiru sai da ya

cinye abincin tas sannan ya ce, "To

masallah Allahu, na gode Hauwa u.

Allah ya yi miki albarka, ya kuma

ba mu zaman lafiyamai dorewa.

Abinci yayi kyau."


18


Nasa hannu na kwashe kwanukan

na fitar na kai kicin, sannan na dawo

na zauna. Ya fara magana, "Tunda ki

ka zo ban samu wani lokaci na zaunar

da ke don nayi miki magana dangane

da al'amuran gidana ba.

Amma duk da hakan dai nasan kin

ga abinda ki ka gani na zahiri. Akwai

mahaifiyata wacce idan kin lura za ki

gane ba ni da wanda nake girmamawa

nake kuma so fiye da ita.

A rayuwata ita kadai ce na mallaka

ina nufin mallakar da ban taba wayar

gari na gane na rasata ba.

Ina yi mata soyayyar da bana yiwa

kowa shi a duniya Hauwa'u, don

kuwa nasan itama tana yi mun fiye daa

hakan.

Babana ya rasu ne ya bar ni ban fi

shckaru biyar ba a duniya, amma


19


kuruciyarta bai sa ta barni zuwa wani

mijin ba.

Sai ta zauna da ni da Yata don ta

tarbiyyantar da mu, ta ilimantar da mu

ta hakura ta sadaukar da jin dadin

rayuwarta.

Don haka duk wani abu da ki ka ga

nayi a yau ko na zama a yau din nan

to da bazarta ne. Ina rokonki daki

taimake ni ki zauna lafiya da ita.

Zan iya yin hakuri idan ki ka saba

mun, amma ina da gajen hakuri ta

fannin sabawa mahaifiyata.

Sai abu na biyu, nasan kin ga yara

to ina so ki san ko ni da nake ubansuu

Hajiya bata yardar mun ta bani

yancin shiga harkarsu ba.

ldan kin ga wani abu da suka yi

miki da bai yi miki dadi ba, to na

roke ki da kiyi hakuri, idan kuma kin


20


ga ba za ki iya ba to ki jira ni na dawo

ko menene a lokacin sai ki fada mun.

Ina yi miki wannan maganar ne

saboda ni nasan kan gidana, na kuma

san matsalar da ke cikin shi. Ina so ki

taimake ni na samu nutsuwar da nake

bukata a cikin gidana."

Na yarda da duk abubuwan da

mijina ya gaya mun da kanshi ya

kuma roke ni a kai ina kuma iyakacin

kokarina wajen ganin na biya mishi

bukatunshi.

Gara nake shirya mishi kullum mai

dadi, daga cikin littafin girkina a

kullum kuma bai gajiya wajen yaba

mun.

Haka nan baya gajiya da yabon

kwalliyata, don kuwa kullum a cikinta

nake safe da yamma, matukar yana

gidan.


21


lna son mijina ina kuma son zama

da shi. Zama nake yi na yanci da

walwala. A yanzu ne kuma na gane

me ake nufi da zaman aure.

Zama na hakika ba mai cike da

kunci ba. Zama na sanin hakki da

yancin dan Adam.

A yanzu ne nasan so nasan abinda

kalmar take nufi don abinda nake ji a

game da Ahmad. 

Shima burinshi a kullum bai wuce

na ganin ya faranta mun ba. Da

matukar wuya ya dawo gida ba tare

da ya riko mun wani abu ba, wanda

zan yi amfani da shi don kaina ba don

shi ko wani ba.

Iyayena kuwa yana mutunta su

tamfar nashi. To abinda nake so

kenan na kuma samu, zan kuma

jurewa zama da ya' yanshi da


22


mahaifiyarshi kamar yadda ya ce, don

na tabbatar mishi matsayin shi a

wurina.

Watana biyu cif, Ahmad ya ce na

shirya a kai ni gida wuni. Cikin doki

ranar na kama shiri. Tsaraba sosai

yayi mun wanda zan tafi dashi tamfar

wacce take nesa.

Nayi sallama a kofar dakin Hajiya

na shiga a gefe na durkusa na gaya

mata zuwana gida.

Ta ce, Eh mijin naki yazo ya gaya

mun. Allah ya kiyaye hanya, ki gaida

manyan naki. Na fito na shiga mota.

Bala direba ya tuka muka tafi.

Babu wanda bai yi murna da ganina

ba.

Umma ta ce, "Haka fa Allah ke

lamarinsa, ki duba ki gani wannan

auren naki nutsuwarshi ma daban. "


23

Wajen karfe uku Ahmad ya kira ni

a waya. Na dauka "Yaushe ki ke

shirin zuwa gida ne?

Na ce, "Ina ce wai ko za ka bari ne

na yi sallar Magriba tukuna daidai

lokacin dawowarka kenan."

Ya ce, "To abincina fa? Ko zan

zauna da yunwa ne yau tunda nayi

karambanin yi miki gwaninta?

Nayi maza na ce, "A'a yallabai

mu tafi." Ban iya tsayawa jiran

Babana ba na kama shiri.

Tasi'u ne yake ta magana yana

cewa, Zai bini yaje yaga gidana,

Umma ta ce, Aa a wane dalili ka

bari dai a kai ku wani lokacin." Ba

tare da wata fargaba ba na ce a hada

musukayansu shi da Sabi'u.

Wurin Hajiya muka fara shiga, na

gaisheta. Su Tasi'u ma haka, na mike


24


zan fito ta ce mun, "Zo mana. Na

dawo na sake tsugunnawa ta ce, Su

waye wadannan?

Tana nuna su da baki, na ce

Kannena ne. ziradat ta leko daga cikin

dakinsu ta kalli su Tasi'u ta ce, Wai!

Sannan ta kwashe da dariya.

Ta ce, Lallai kuwa. Na tashi bayan

ta bani umarnin tafiya, na dawo

sashena amma ina jin wani abu a

raina maras dadi.

Muka shigo falona sannan na kara

bin yaran da kallo wadanda tuni suka

bi lafiyar kujera suka zauna. Ni nasan

mu ba masu kudi ba ne.

Amma daidai gwargwado Umma

tana iyakacin tawajen ganin ta

tsaftace danta babu kazanta a tare da

shi.


25


Tsarguwar da nayi ita ce tasa na

leka na kira Bala direba na ba shi

kudi na ce ya sayo mun kaya daidai

nasu Tasi'u set bibbiyu wadanda zan

yi musu amfani da shi.

Aikina na fara yi gadan-gadan

saboda kada na makara. Abinci mai

kyau sosai nayi mishi. Sai da na gama

sannan nayi wa su Tasi'u wanka na

saka musu sababbin kayansu nima

nayi wankan nayi alwala, sannan nayi

kwalliyata.

 Ka'idar Ahmad shi ne, yana

dawowa zai shiga wurin

Mahaifiyarshi, idan aka yi sallar

Magriba ya dawo zai shiga suyi hira.

Daga sallar Isha'i ne zai shigo

wajena, don haka yau ma hakan ya yi.

Yana ganin su Tasi'u ya sai

murmushi.


26


"A'a'a, ke ki ce yau muna da

manyan baki a gidan nan, amma ba ki

sanar dani ba, ai da na shigo da kayan

tsaraba. To yanzu me ki ka ba su na

saukan baki?"

Na bude baki zan yi magana ya ce,

"A'a bar su kawai su bani amsa.

Suka fara lissafa mishi abubuwan da

suka ci tun da suka zo.

Sai da suka gama ya ce, "Ba ta ba

ku sweet ba, ba ta ba ku Ice Cream ba

kenan kun ga bata iya karbar baki

ba."

Ya jawo wayarshi daga aljihu ya

kira Bala direba ya ba shi kudi ya ce

yaje ya siyo mishi Ice Cream da

candy. 

Sannan ya kalleni, "To baiwar

Allah ya ya ki ka samu gida? Nayi

murmushi har cikin zuciyata na ce


27


"Lafiya lau yallabai, kowa yana

gaisheka tare da godiya mai yawa, sai

dai ban ga Baba ba saboda gudun

kadana makara."

Ya mike ya nufi hanyar sashen shi

ina bin shi har muka shiga. Ya tsaya a

bedroom din shi yana tube kayanshi,

ni kuma na wuce bayangida ina hada

mishi ruwan wanka a kwarmi.

Ya ce, Ki koma wurinki kawai

saboda yaran nan na ce to. Ban dawo

ba sai da na ajiye mishi dukkan abin

da zai bukata idan ya fito daga

wankan.

Na dawo dakin inda na bar su

Tasi'u suna nan inda suke, kallon

cartoon din da na saka musuna

Kiddies world suke yi har yanzu.


28


Ban dade da dawowa ba Bala ya

shigo da aiken da aka yi mishi babbar

leda cike da kayan kwalama.

Ya ajiye ya juya na kira shi na debi

mai yawa na ba shi saboda sanin da

nayi yana da yaya suna kuma zaune

ne a boys Quarters din gidan.

Godiya sosai yayi ya juya. Na bai

wa su Tasi'u wanda za su iya ci na kai

saura fridge na ajiye saboda Ice

Cream din kada ya narke.

Ganin da nayi hankalinsu ya yi nisa

yasa na koma wurin Ahmad ya gama

shirinshi har ya fito falon yana

kokarin fitowa na ce, "Ai abincinka

nazo na baka ya ce mu koma wurinki

na ci a can, na ce to."

A falona yaci abincin shi muka ci

gaba da hirar mu, su Tasi'u ma suna

harkokinsu har suka yi barci. Na


29


dauke su naje daya dakin nawa na

kwantar da su na dawo in da Ahmad

yake.

Ya jawo ni jikinshi ya kwantar da

ni a kan kafafunshi yana shafa gashin

kaina.

"Tun da ki ka zo gidan nan ina

kallon ki ba ki taba yin kitso ba." Na

ce, Ai ban san inda za a yi mun

kitson ba ne a unguwar nan."

Ya ce, "Eh mai yi ma su Zainab

tazo tayi miki gobe. Na ce, "To."

A dakinamuka kwana ya ce

saboda su Tasi'u kada a bar su su

kadai. Sammako sOsai yanzun nake yi

saboda karyawar Ahmad tunda na

lura ba son shayi da biredi yake yi ba.

Pizza na mishi na hada mishi da

ruwan lipton saboda complain din da


30 


yake yi akan tebar shi da take kara

habaka.

Duk da na gaya mishi ni bana

ganinta. Sai da na sallame shi ya tafi

sannan na dawo na shirya su Tasi'u

cikin sababbin kayansu muka karya

muna 'yar hirarmu cikin raha da ban

dariya suna bani labarai.

Su na tambaya abinda zan girka

musu suka fadaa na shiga nayi musu

muka ci tare sannan na dauko Ice

Cream din su na jiya na ba su suka

sha suka ce mun za su je wasa a waje.

Kamar na hana su sai dai naga kada

na takura su tunda yara ne.

Tashi nayi na nuna musu wurin da

yara suke wasa sannan na dawo

dakina na hau gado na kwanta.

Ban dadc sosai da kwanciya ba sai

ga dan aika daga kasuwa Ahmad ya


31


aiko shi da sakon su Tasi'u. Na karba

ina dubawa.

Kaya ne masu asalin kyau yan

kanti set uku-uku, sai takalma sandals

na asali.

Na ajiye kayan na leka don na kira

su daga nesa na hango su a kan lilo,

don haka na dawo na bar su suka ci

gaba da wasan su.

Ni kuma na shiga kicin don fara

shirin abincin dare. Ihun da nake

jiyowa ne yasa ni saurin fitowa, don

kuwa ya yi mun kama da na Tasi'u.

Sai dai kafin na fita waje har sun

shigo dakin cikin tsananin rudewa na

kwallara kara tare da fadin "Inna

lillahi wa inna ilaihi raj1'una."

Jini ne kawai har ya rine rigarshi

gaba daya. Waje nayi da gudu saboda

rudewa.


32


Daga nesa Bala direba ya hango ni

ya taho cikin sauri "Lafiya, lafiya? 99

Na ce, Zo ka gani. Na taho dakin

har ya zauna a kasa cikin saurin shi

ya sunkunci Tasi'u nima na bishi a

mota ya saka shi zuwa asibiti.

Ban jira dawowansu ba bin su nayi.

Ba karamin jin ciwo Tasi'u ya yi

ba, don kuwa sai da aka yi mishi

dinki a keyarshi a ka yi dressing din

wurin aka yi mishi allurai sannan

muka dawo gida wajen karfe shida da

rabi na yamma.

Har dakina Bala direba ya kawo shi

kan kujera ya ajiye shi. Muryar shi

har ta dishe saboda kuka. Na tsaya a

kanshi ina kallon shi saboda tausayin

da ya bani.

Na koma bandakina na dauko

sandar goge-goge na goge duk jinin


33

da ya mannu a tayels din na saka

dettol na sake gogewa sannan na

shiga kicin cikin sauri don na dan yi

wa Ahmad abincin da zai ci.

Sai dai ko dorawa ban yi ba sai ga

motarshi ta shigo gidan, duk da haka

ban fasa ba saboda nasan ba wurina

zai wuto ba.

Cikin kankanin lokaci na yi mishi

fried rice da coleslaw salad, sannan na

dawona dauki Tasi'u da barci ya riga

ya dauke.

Naje nayi mishi wanka da ruwa

mai zafi saboda ya ji dadin jikinshi,

na hada mishi tea na ba shi sannan na

ba shi magungunan da Likita ya ba

shi.

Naje na kwantar da su ban wani bar

su suka tsaya kallo ba.


34


Ahmad ya shigo lokacin ne nake

wanka amma kafin na fito ya tafi

dakinshi, don haka sai kawai na bi shi

can.

Shi ma wankan na samu yake yi

don kuwa dabi'arshi ce vin wanka, da

zarar ya idar da sallar Isha'i yana cin

abincin shi yana dan kallona.

Zuwa can dai ya kasa yin shiru ya

ce, "Menene ya faru ne amarya?

Na ce "Me ka gani? Ya ce, "Ba

haka na saba ganinki ba. Kamar nayi

shiru don kuwa abin da zuciyata take

ta gaya mun kenan sai dai na kasa.

Abin kawai da na sani shi ne,

Sabi'u ba zai yi mun karya ba, don

kuwa yana wurin da abin ya faru ya

kuma tabbatar mun da Ziradat ce ta

wurgar da Tasi'u akan liie ya ji

wannan ciwon.


35


Na share hawayena da na gama yi

mishi bayani, ya ce "Yanzu yana

ina? Na ce, Ya yi barci. Mikewa

yayi ya taho dakin da nake kwantar

da su har yanzu wata irin ajiyar

zuciya yake yi.

Duk da nisan da barcin shi ya yi ya

zuba mishi ido yana kallon lafcecen

bandejin da aka toshe ciwon da shi,

ya juya ya fita.

Shiru naji bai dawo ba, na mike

zan fita sai na hango shi yana tahowa

daga sashen Hajiya, duk da ban san

me ya faru ba gabana ne ya fadi da na

kalli fuskarshi.

Na kauce na ba shi hanya ya shige

daki ya kwanta, ni ma kwanciyar nayi

ban ce mishi komai ba, tunda shi ma

bai ce mun ba.


36


Washegari sai da ya gama shiri zai

fita ne ya kalle ni.

"Kiyi hakuri Hauwa'u, zan so ki

dauke shi a matsayin tsautsayi duk da

dai nasan ganganci ne kawai irin na

yara."

Na ce, "Babu komai." Ya fita, Na

shirya kamar kullum na shiga sashen

Hajiya don na gaisheta.

Kallon kawai da ta yi mun ne ya y1

matukar sanyaya mun jikina.

Na gaisheta ta amsa sannan ta ce,

Ko da wasa kada ki kuskura ki kara

kai karar yaran nan wurin Babansu na

gaya miki kada ki kara.

Ba a yi mun haka, kada ki shiga

gonata saboda bana son abinda zai sa

na saba miki. Tashi ki bani wuri."

37


Dawowa dakina nayi, nayi

sumukwi nayi tsit saboda sanyin da

jikina ya yi.

Ban yarda na mayar da su Tasi'u

gida ba kamar yadda naso nayi sai da

ya ji sauki sosai har aka cire mishi

bandejin.

Ahmad kuwa siyayya ya yi musu

mai ban sha'awa har da Kekuna ya ba

su, sannan yasa Bala ya mayar da su

gida.

Na riga na saba duk ranar Litinin

da Alhamis Hajiya tana Azumin

nafila, tunda nazo kuma duk da cewar

da tayi na daina saka mata abinci idan

nayi bai sa na fasa yi mata girkin

abincin buda baki a wadannan

ranakun ba.

Tun tana hanawa har tayi shiru,

kasancewar yau Alhamis sai na shirya


38


mata farfesun danyen kifi mai hadi

sannan nayi mata lafiyayyen alcle na

ganye da kunun gyada na danyar

shinkafa. 

Na hada wuri daya ina nufin dauka

na kai sai ga wayar Ahmad ya aiko

dan aike na ba shi takardar da ya bari

a kan bed side din shi da ke cikin

dakinshin.

Hakan ne yasa nayi waya sashen su

don Larai tazo ta dauki abincin, sai

aka ce bata nan, don haka na ce

Zainab tazo ta dauka.

Na shiga na dauko wa dan aiken

sakon shi na ba shi, sannan na dawo

na ci gaba da harkokin abincina.

Sai da na kammala komai nayi

wanka nayi kwalliya tare da sallar

Magriba sannan na fito wurin Hajiya

don nayi mata sannu da shan ruwa.


39


Ina shiga Ahmad yana fita saboda

sallamar da aka yi da shi a waje.

Na durkusa gefe na gaisheta tana

amsawa kamar kullum yanayinta ta

kuma yi mun sannu. Na mike zan fito

sai naji an kira sunana.

Na waiwayo da sauri don ganin

mai maganar. Tun da nazo gidan yau

ne naji Zainab tayi magana da ni.

Tana rike da kofar dakinsu da

hannu daya yayin da dayan kuma

take nuno ni da shi.

"Kada ki kuskura ki sake yin waya

ki ce a turo ni ki aike ni kin ji na gaya

miki. Ba na daukan raini idan kin lura

za ki gane tunda ki ka zo gidan nan

ban taba shiga harkarki ba.

Idan me aika ki ke so, to gayawa

wanda ya ajiye ki ya nemo miki." Ta

juya ta koma dakin da ta fito.


40


Ina tsaye a bakin kofar dakin ko

ina a jikina sai tsatsafo da gumi yake

yi.

Murmushi Hajiya tayi ta ce "Kai

Zainab kenan, ina dai yi miki addu'a

Allah ya shirye ki. Je ki abin ki

Hauwa'u rabu da ita."

 Na juyo na dawo daki raina a

cushe. Har lokacin da Ahmad ya

shigo na rasa yadda zan yi na saki

raina.

Duk wani abinda na saba yi mishi

na mishi sai dai da muka kwanta

Juyawata nayi na rabu da shi, don

kuwa abin har yanzu yana cina.

Yayi tambayar har ya gaji wai na

gaya mishi abinda ke damuna na ce

babu komai. Ya ce, haka kawai ki ke

mun irin wannan abin.


41


Nayi shiru naga zai ja mun wata

matsala na ce mishi ba ni da lafiya, ya

ce Idan ba ki da lafiya ba za ki yi

magana ba sai kawai ki juya mun

keya?

Juyowa nayi na ba shi hakuri,

sannan aka zauna lafiya.

Duk wani kokari da nake yi na gani

ban shiga sabga r 'ya'yan Ahmad ba

nayi shi, amma hakan bai sa sun bar

ni ba tare da su suna shiga tawa

harkar ba.

Babu ma dai shaidaniya irin

Ziradat, haka kawai yarinyar bata

kwanta mun ba. Gara Zainab bata

kallon inda nake bata yi mun magana

amma ita ko baki nayi to sai tasan

yadda tayi ta yi musu abinda ransu ya

6aci.


42


Duk wanda tayi wa rashin

mutuncinta hakuri nake ba shi tunda

ko a gaban Hajiya ne hakurin zataa

bayar sai ko bin su da take yi da

addu'ar shiriya.

Ba ni da wata matsala daga wurin

mijina, muhimmmin abu kenan a

wajena.

Wata irin iska mai karfin gaske aka

yi da daddare, wacce ta bugo satelite

dish din sashen su ya fado kasa.

A lokacin nan Ahmad baya nan,

don haka ba a gyara ba. Tun da abin

nan ya lalace sai suka dawo kallon su

Wurina.

Ziradat da Zinatu safe, rana da dare

a dakina suke wuni, ba na sawa ba na

hanawa.

Sannan ga su da ciye-ciye duk

abinda suka ci kuma to a wurin za su


43


yar da bawon shi ko kuma su bar

kwanon a wurin ko da wacce irin

shara ko gyara na yi wa gun.

Ban taba daga ido na kalli abin da

suke yi ko na gaji nayi musu magana

ba.

Abin dai da na sani shi ne, ya kusa

wucewa tunda maigidan ya dawo a

jiya da daddare bayan tafiyar da yayi

ta wajen sati biyu.

Na gama aikina tas da yamma na

gyara dakina da na Ahmad na duba

babu wani abin da zan yi.

Don haka nayi wanka na gyara

kaina, nayi kwalliya ta burgewa

sannan na dawo falona da yake ta

kanshi na zauna ina kallon

programme din (Ask Huda) da ake yi

a Huda TV.


44


Kan wata tambaya dangane da jinin

Haila da ake amsa ta wacce ta dade

tana daure mun kai.

Sai kawai Zinatu ta shigo dakin

nan da sauri ta dauki remote ta canza

zuwa kidsco wai zata ga cartoon.

Wani gululun takaici ya taso min,

ban san yadda aka yi na daka mata

tsawa ba.

Na ce, "Meye haka? Dalla can

mayar mun inda ki ka same shi."

Iyakacin abinda na ce kenan yarinyar

nan ta tayi jifa da remote dinnan ya

daki bango ya wargaje.

Sannan ta falla a guje tana kurma

wani irin ihu, sai ka ce wacce ya

yanke wa wata gaba a jikinta.

Wani sabon takaicin ya sake kama

ni, ganin remote din ya ki aiki na

tattara shi na aj1ye.


45

Na shiga dakina na bi lafiyar gado

ina 'yan sake-sakena.

Larai ce tayi sallama ta shigo, wai

in je Hajiya tana kirana. Na fito bayan

na lullube jikina da gyale.

"Me ya hada ki da Zinatu ki ka

bugeta?" Na kalli yarinyar yadda ta

takure a jikin kujera har yanzu kuka

take yi. 

Na ce, "Hajiya ban bugeta ba." Na

fara kokarin yi mata bayanin abin da

ya faru.

Ta ce, "Dakata! Kin ga yadda muka

fara zama cikin fahimtar juna? To ba

na so wani abu ya shigo daga baya,

don idan nayi niyyar daukan mataki

akan mutum abin ba ya yi mishi kyau.

Kada na sake jin an ce ko kallon

banza kin yi wa wani da a cikin gidan


46 

nan, ballantana har ta kai ga kin saka

hannu a jikinsu.

Ki zauna a matsayinki su zauna a

matsayinsu. Ni bana dukan yarana

tunda ubansu ma a haka na

tarbiyantar da abina.

Duk wanda ya ce ba zai yi hakuri

da su a haka har kafin su fahimci kan

al'amarin duniya ba, to sai yasan

nayi.

Ba na so, kada kuma na sake jin

don sun je wurinki sai kiyi mata haka

har tana sulewa saboda razana? Ai

nan gidan ubanta ne tana da ikon

shiga duk inda take so ta wala."

Na dawo dakina nayi alwala nayi

sallar magriba har aka yi Isha'i ban

tashi daga wurin ba.

Don haka na mike nayi sallar Isha'i

tare da shafa'i da wutiri. Motsin


47

Ahmad naji a wurin shi ne na dauki

abincin shi na kai mishi.

Ina ajiyewa ya ce, "Me ya hada ki

da Zinatu ki ka yi mata irin wannan

dukan? Wato kin gane ko? Ni da ki ke

gani ina matukar tsoron tashin

hankali.

A waje ban huta ba, babu abin da

nake bukata irin na shigo gida dan

hutun da zan yi da iyalina na yishi

cikin kwanciyar hankali da farin ciki

ba. 

Menene haka? Tun farko na gaya

miki kiyi kokarin zama ba tare da

wani abu ya hada ki da wani yaro ba,

saboda nima hakuri nake yi da su.

Hajiya kuma ina matukar kokarin

ganin bacin rai, bai same ta ba

ballantana a ce sanadina ne,"


48

Naga fadan nashi zai yi yawa

saboda wani abu bai taba hada ni da

shi makamancin haka ba, a tsawon

zaman da nayi a gidan na watanni

shida.

Na ce, Ban fa bugeta ba." Ya

watso mun ido "Ba ki bugeta ba? Na

ce "Na rantse maka ban bugeta ba."

"Me ki ke nufi kenan? Kina so ki

ce mun Mahaifiyata tayi miki karya?"

Nan da nan na fara kuka saboda jin

inda ya mayar da abin.

Nan take kuma fadan yafi na dah

wai na karyata mishi uwa. Ga gaskiya

nan kiri-kiri jikin yarinya ya rure har

zazzabi ya rufeta amma kina karyata

mahaifiyata.

Mara kunyar yarinya, tashi ki ba ni

wuri."


49

Na tashi na dawo dakina nayi kuka

har na gaji, idanuna suka yi luhu-luhu

saboda rashin barcin da ban yi ba.

Na gama abin karyawa kamar ba

zan shiga sashen nashi ba, tunda

korata ya yi jiya sai naga kada na

karawa kaina matsala.

 Na dauka na kai mishi na ajiye na

juyo abina, tunda a da wannan damar

tayin gaba da wani ina dai bin doka

ne kawai. To da haka wanna ya wuce.

Ba karamin taka tsantsan nake yi

da yaran Ahmad da mahaifiyarshi ba,

saboda ina son aurena.

Gashi kuma cikin kankanin lokaci

sai na mallaki abubuwan kadara irin

Su,gold da zinari saboda yawan

tafiyar da yake yi.

Kuma shi mai sakin hannu ne.

matsalata a kullum ba daga shi ba ne


50


sannan babu fashi sai dai idan bai yi

tafiya ya dawo ba sai an ce nayi kaza

nayi kaza.

Ita kuma Hajiya ta ce aja mun

kunne, to garin aja kunnen sai ya

zama tashin hankali, ina batawa

mahaifiyarshi rai.

Sannan babu damar nayi musun

ban yi ba sai laifin nawa yayi yawa,

na karyata mahaifiyarshi, don haka

kullum a haka muke.

A daidai wannan lokacin ne ta

bayyana ina dauke da juna biyu har

na shiga wàta na uku.

Hakan ne ya matukar takura ni naa

kasa yin Azumin watan Ramadana,

saboda tsananin laulayin da nake yi.

Ba Ahmad ba ma har Hajiya a

wannan lokacin ta sassauta mun, don


51


haka babbar matsala a yanzu

laulayina ne da kuma yaran.

Tunda yanzu ba barina suka yi da

karata wurin Babansu duk da laulayin

da nake yi bai hana ni kiba na murje

ba.

Shirin sallah sosai ake yi don kuwa

gidan ma a cike yake da mutane 'yan

uwan su da suka zo daga kauye da

kuma babban dan Ahmad Zubair.

Wanda yanzu ne muka san juna da,

shi.

Shi kam babu laifi yana da hankali

don Aunty ma yake kirana. Haka nan

nima duk da sanin da nayi suna buda

baki a wurin Hajiya hada mishi nake

yi da Babanshi.

Sannan ganin shi yasa hatta Zainab

ta saurara da wasu abubuwan

ballantana su Ziradat.


52


Zama yazo yayi yana gaya mun

abubuwan da yake so nayi mishi, na

sallah saboda bakin abokanshi da za

su kawo mishi ziyara.

Na ce, To ka bari mana idan nayi

na Babanku sai na diban maka a ciki.

Yayi godiya sosai, take kuma farin

cikinshi ya bayyana, ya tashi ya tafi.

Bai dade da fita ba na fita don

zuwa sashen Hajiya kai mata farfesun

kodar da Ahmad ya aiko ya ce nayi

mata da hannuna.

Na isa bakin kofar tun kafin nayi

sallama naji Ziradat tana cewa, "Ai

munafuka ce tunda gashi har Hajiya

ma yanzu ba ta yarda idan mun ce

mata tayı mana wani abu.

Ni a matan da Babanmu ya aura

duk ita nafi tsana. Hajiya ta ce,


53


"Um'um Ziradat na fa kwabe ki da

irin wannan maganganun."

Shi kuma Zubair cewa ya yi "Ni

banä son irin wadannan maganganun

ban san abinda yasa Baba yake biye

muku ba.

Menene laifin wannan matar? Ko

harkar mutum bata shiga ba za ku

taba barin Baba ya zauna lafiya da

mata ba. Shi kuma ku ke sakawa a

matsala."

Sallama nayi na ajiye mata na fito

na dawo wurina, a raina na ce kwaji

da shi, ni kam nawa auren daram in

Allah ya yarda.

Shiri sosai nayi na sallah mutanen

gidan kaf na basu abinci da abinsha

da su kek din da nayi ba tare da nayi

la'akari da Hajiya tayi ba.


54


Makwabta baki daya sai da na

zagaya su da abinci. Ahmad ne kuma

ya taso keyar su Zainab suka kai mun

rabon.

Gidanmu ma duk da ya aike musu

da nama cikin babban baho saboda

yankan da yayi da kuma shinkafa da

tumatur kwando.

Bai hana ni kai musu abincin sallah

ba wannan kuwa Bala direba na aika.

Da yamma ne baki abokan harkar

Ahmad suka zo gidan hakan ne yasa

sashenshi ya cika dankam ba kadan

ba.

Nima gagarumar liyafa na shirya

musu sinasir da farfesun kafar saniya

sai dambun nama da kek da manyan

donghnut na asali mai ridi.

Sai kwalayen juice wanda na hada

musu duka a cikin wani madaidaicin


55

 

kwando na Rafia da nayi rafin

dinshi da wata 'yar leda da aka rubuta

iyalan gidan Alhaji Ahmad Rufa'i

suna muku barka da Edil Fitr.

Kuma gaba dayansu ya wadace su.

Shima abin yayi mishi dadi ba kadan

ba.

Ya shigo dakina lokacin da nake

shirin shiga wanka har yanzu

fuskarshi a washe take ya sa hannu ya

dauke ni yana cewa bari nima na taya

ki wankan irin wannan gajiya da ki ka

yi haka.

Duk da dai ni da yunwa ki ka bar ni

na ce, "Haba yallabai na dauka ai

yau ba za ka ji yunwa ba."

Dariya yayi ya fita bayan ya gaya

mun yana jirana idan na gama shiri.

Doguwar riga na saka mai gyale na

dauko abincin a babban tire na nufi


56

falon shi na waje don a nan na jiyo shi

alamar ya sake yin wasu bakin.

Ni kuma ba zan iya jiran tafiyar su

ba tunda na gane yana 1in yunwa.

Wani irin santsi ne ya debe ni gaba

daya na zame na kife a kasa tire yayi

nesa ya kife abubuwan ciki suka

tarwatse.

Karar fashewar abu da salatin da

nayi ne yasa Ahmad tahowa wurin

cikin sauri har ya karaso inda nake.

Ba iya motsawa ba sa hannu yayi

ya dauke ni zuwa cikin dakinshi

tunda daga inda nake nan dinne ya fa

kusa.

"Sannu Hauwa'u."

Sai dai ko amsawa na kasa yi

saboda wani irin gigitaccen ciwo da

nake jiwowa daga gadon bayana yana

hadowa har gabana zuwa marata.

57


Ya juya yana kiran Larai don tazo

ta kwashe barin da aka yi yana kumna

gayawa Hajiya.

Durkusawa nayi saboda murdawan

da yake yi mun da irin azabar da na

ke sha.

Ahmad yana shigowa tare da

Hajiya daidai lokacin dá naji kamar

fitsari yana zubo mun.

Hajiya ce ta fara salati tana karawa,

wannan wane irin mummunan

faduwa ki ka yi 'yannan. Ai jini nake

gani."

*Jini Hajiya?" Ahmad ya fadi

daidai ya kara matsowa inda nake

cikin sauri ya dauke ni zuwa mota

muka tafi asibiti.

Jinin da ya zuban ya yi yawa, don

haka cikin ya lalace wankin ciki aka

yi mun aka sallamo ni da magunguna


58


muka dawo gida wajen karfe sha

biyun dare saboda cewar da Ahmad

yayi a sallamo ni mu dawo gida.

Cikin dan kankanin lokacin da abin

ya faru nayi wani irin ramewa saboda

bakar azabar da na sha.

A daren Hajiya tazo duba ni ta

kuma hado mun da abincin da ta girka

mun, tuwo miyar kuka ta ce na ci na

sha maganina.

Ba karamin jjjaga Ahmad ya yi da

barin da nayi ba, don kuwa shi mutum

ne mai son haihuwa.

A yanzu kuma Zinatu ita ce

karamar 'yarshi, wacce a bana ya ce

mun shekarunta takwas.

Hakanne yasa ni daurewa nayi

niyyar wartsakewa duk kuwa da abin

da ke damuna a zuciyata.


59


Da safe ma Hajiya ta shigo ta

gaishe ni, haka Larai da Bala direba

de matarshi sai Zubairu.

Wajen karfe tara ne Ahmad ya sake

shigowa ya kalle ni, ganin ina zaune a

kan gadon "Har kina iya tashi?

Na dan yi murmushi na ce, "Ai naji

sauki. Ya zuba mun ido tare da

kamo hannayena duka biyu ya rike a

nashi hannuwan yana dan matsawa.

Yace, Kin dai daure Hauwa'u ba

kin ji sauki ba, ki taya ni addu'a

Ubangiji ya ba mu. wasu masu

albarka." Na ce, "To amin."

Yayi shiru zuwa wani lokaci ya ce

"Ina son zama da ke Hauwa'u. Ina

rokonki ki kara hakuri da duk wata

matsala da ki ke fuskanta a tare da ni

ko wai nawa."


60


Ban fahimci inda maganar tashi ta

dosa ba, amma sai na dan yi

murmushi kawai.

Duk kokarina bai wuce na ganin na

nunawa Ahmad cewa naji sauki ba.

Na dan daure na yi kwalliya na sanya

doguwar riga na fito ina lallabawa

zan shiga dakin, shi ne naji maganar

Zubair.

Kamewa nayi na kasa shiga.

"Na rantse Baba naga lokacin da

Ziradat ta saka ai ba zan yi maka

karya ba, amma ina gaya maka ne

don kada wata rana suyi abinda yafi

haka."

Ahmad ya ce "To kai Zubairu me

yasa da ka ganta ba ka ce komai ba?"

Ya ce, "Ai ni ban san da wata

manufa tayi ba. Na juyo. na dawo

dakina saboda na fahimci wani

61


muhimmin abu ne duk da dai ban san

ko menene ba.

Wajen La'asar na rinka jiwo ihun

yaran, sai dai n1 kam ban je ba, don

ban san abinda yake faruwa ba kumna

babu ruwana ko ma menene.

A dakina yau ma na kwana sai dai

tare da Ahmad.

Washegari matar Bala direba ta

dawo gaishe ni tana zaune a kan

kujera muna yar hira saboda

mutuntani da matar take yi da kuma

kokarin shiga sabgata yasa nake dan

hira da ita.

Don ba za ta wuce sa'ata ba.

"Oh ni 'yasu, wadannan yara kuma

ashe sune."

Na ce,  Su ne kamar ya ya?

Wadanne yara? "  Nayi mata

tambayoyin a tare kuma lokaci daya.


62 


"Au, jiya ba ki jiyo ihunsu ba? Ai

Baban ne ya yi musu duka ba na wasa

ba, don wansu yaje ya gaya mishi

cewa ita wannan shu'umar ita ce ta

saka miki abu ki ka fadi."

Nayi shiru ina kallonta saboda jin

abin da take fada, abin dai ya yi

matukar bani mamaki, sai dai duk da

haka ban tanka ba don tsoron halin

mutane.

Shiru nayi a kwance ina tunani me

nayi wa wadannan mutane haka?

Ahmad ya shigo ya nemi wuri kusa da

ni ya zauna.

"Ya ya Amarya me ke faruwa ne?"

Ban ce mishi komai ba sai zuba

mishi ido da nayi. Ya jawo ni jikinshi

yana cewa.


63


"Kin san fa tunda wannan ya fita to

aiki ya koma baya, sabon zubi kumna

zamu yi yanzu."

Daurewa nayi na ce mishi "To,

amma dai ai ba yanzu ba ko?" Ya ce,

"Eh to, ko gobe tunda Likita ya ce

bari ba a wuce kwana uku, ko ba haka

ba?"

Wartsakewa nayi saboda

farantawa maigidan rai na nuna mishi

naji sauki don hankalinshi ya kwanta.

Haka nan kuma abubuwa sun

matukar yi mun sauki ba kadan ba,

tunda dai yanzu zan iya ganin Ziradat

a hanya ba tare da ta ja mun tsaki ba.

Abin har mamaki nake yi, wai 'yar

karamar yarinya mai shekaru goma

sha uku ce ta ke irin wannan abin.


64


Lokacin komawan Zubair

Makaranta ya yi, don dama hutun

nasu ba mai yawa ba ne.

Tambayar shi nayi abinda yake so

nayi mishi na tafiya. Ya yi shiru yana

'yan tunane-tunane.

Ya ce, Ai ba na so ne Baba ya ji

zai ce na cika fitina, tun da ana siya

mun komai."

Na ce, "To fada mun ba zan bari ya

ji ba." Ya ce, "To ina son kek irin

wanda ki ka yi da sallah."

Na ce, "Sai me?" Ya ce, "Ko shi

kadai aka yi mun Aunty na gode. Na

ce, "To shi kenan.

Cefane sosai nasa aka yi na kira

Larai muka yi aikin tare. Cincin nayi

mishi mai yawa, nayi mishi kek na

sassaka su a leda daidai saboda kada

su bushe tunda Makaranta ce.


65


Sai dambun naman da nayi mishi

cikin babbar roba fara.

Ana gobe zai tafi na ba shi tsalle ya

rinka yi kamarzai yi ya ya don murna.

Sallamaa muka yi mai dadi ya kumaa

roke ni idan Babanshi zai je mishi

visiting na raka shi muje tare, na ce

to. 

Da yamma ne Ahmad ya shigoo

bayan ya kai shi Makaranta ya dawo

na kawo mishi ruwa mai sanyi yasha

sannan ya yi hamdala ya ce "Zubairu

ya ce na sake yi miki godiya."

Ban saurare shi ba kicin na koma

na hado mishi fruit salad na kawvo

mishi, ya karba yana sha ya ce "To ni

ina nawa dambun naman?"

Na kalle shi na gane da gaske yake

yi na ce "Ban ajiye maka ba saboda

ya ce ba ya so ka sani."


66


Ya dan yi murmushi ya ce, "Haka

ya gaya mun, to amma kuma sai ya

kasa yin shirun ya fada mun da

kanshi.

Kin san alheri komai kankantarshi

yawa ne da shi, to ballantana irin

wannan."

Na ce, "Kai dai don Allah bari zuga

ni, ai ba da kudina nayi ba a cikin

cefanen gida na saka."

Ya ce, "Ko ma dai ya ya ne ai

cefanen gida idan wata ce ba za ta yi

ba, ina so kuma na gaya miki cewa ba

Zubairu ki ka yi ma ba ni ki ka yi ma,

zan kuma tabbatar. ban mance

alherinki ba."

Komawar Zubairu Makaranta sai

abubuwwa suka sake rincabewa. Ashe

dama sun bari ne don sun gane yana

kai kararsu wurin Babansu.


67 


To yanzu ba ya nan sun ci gaba

daga inda suka tsaya. Sai dai Ziradat

ta riga ta tsorata saboda dukan da

Baban ya yi mata a kaina.

Zainab ce take nuna mun salo iri-iri

na rashin kunya da kuma nuna 1sa,

amma na danne zuciyata ko kallon

iya-shegenta bana yi.

A daidai nan ne kuma wani sabon

laulayin ya kama ni, watanni uku

bayan barin da nayi.

Amma a hakan na tsaya tsayin daka

wajen ganin na gamsar da mijina duk

wata lalura tashi.

Kullum nayi mishi maganar zuwa

gida sai ya yi mirsisi ya hana ni, ya ce

ba na yi mishi adalci da yana gari

amma sai na tsallake hidimominshi na

tafi gidanmu.


68 

Na ce, To ai kai da rana kana

kasuwa, da daddare ne ka ke dawowa

gida ka bar ni mana naje da rana na

dawo kafin lokacin dawowarka gida?

Sai ya ce, Wai a'a yafi son idan ya

tuna ni a lokacin da yake kasuwa ya

rinka tuna ni a cikin gidan shi ina

harkokina.

Kallon Ahmad kawai nayi nayi

murmushin takaici, amma a raina

tunda ba ni da abin yi a kai, ba na

musu dashi koda kuwa hukuncin da

ya yanke bai yi mun dadi ba.

Hakanne yasa da yazo tafiya Kano

gaida kanin Babanshi da ya yi rashin

lafiya, tafiyar kwana daya sai na tuna

mishi da zuwana gida.

Ya ce, Ba ki fa da lafiya Hauwa'u.

Na dakatar da hada mishi kayan da


69

nake y1, na ce "Haba yallabai, ba

haka muka yi da kai ba fa."

Ya ce, "Eh na sani, amma ai

wannan karon tafiyar tawa ba mai

jimawa ba ce, kwana daya zan yi."

Na ce, To ni ai tawa tafiyar wuni

ce. Shiru yayi sai da ya fita wurin

Hajiya ya dawo sannan ya ce naje

gidan yau Bala zai kai ni."

Nayi tsalle don murna ya ce, "To

kin gani ba. Nayi-nayi da ke ki rinka

kula da irin wadannan abubuwan kin

ki kanmar kin mance da abinda ya

same ki wancan karon."

Ahmad yana tafiya nayi shirina tsaf

na rufe sashena na fito na shiga wurin

Hajiya don nayi mata sallama.

Sannan na fito harabar gidan na

samu Bala har ya yi warming din

mota ni yake jira.


70 

Sai kawai ga Zainab da Ziradat sun

fito su ma za su je unguwa. Kai tsaye

suka nufi motar za su shiga.

Bala ya ce, "A'a Zainab kada ki

shiga motar nan, Hajiya zan kai

unguwa a ciki."

Tayi mishi wani wawan kallo.

Akwai wata HHajiya nc a gidan nan

baya ga wacce dama can na sani? Ina

tsaye a gefe ina kallonsu ban tanka

ba. 

Ita dai Ziradat ta dan nutsu duk da

dai nasan ba wani hankali ta kara ba.

Zainab ce da Bala dircba suke ta

jayayya ya shiga mota ya tuka ya ki,

ita kuma ta fita a motar ta ki.

Ziradat fita kije ki kira mun

Hajiya. Ba a wani jima ba sai ga

Hajiya ta iso wurin cikin hijabinta.


71 

"Lafiya?" Ta kalli Bala dircba. Nan

da nan ya fara yi mata bayanin abinda

ke faruwa.

Hajiya ta kalli Zainab ta ce, "To ke

Zainaba ku shiga mana idan aka

sauke ta a gidansu sai a kai ku taku

unguwar ba shi kenan ba."

Nan take ta fashe da kuka ita

gaskiya ba za ta shiga mota da ni ba,

bayan ba sonsu nake yi ba.

Na kalli Bala na ce, "Bala idan ka

kai su ka dawo kayi mun magana.

Ya ce,"To Hajiya. Na dawo na shiga

dakina na zauna.

Ban san yadda zan yi da yarannan

ba, abinda na sani shi ne bana kin su.

Na zauna kato-kato ina jiran Bala ya

dawo da su Zainab mu tafi bai dawo

gidan ba sai wajen karfe hudu da rabi. 

72


Har sashena ya iso yayi sallama, na

ce "Kun dawo Bala? Ya ce, "Eh

Hajiya kiyi hakuri zai fara yi mun

bayani na ce a'a Bala babu komai je

ka kawai."

Ya tsaya zai ci gaba da ba ni

hakuri, na ce ba fushi nayi ba Bala,

amma kaga gidanmu zan je yanzu

kuma yamma ta riga tayı, ya ce to

Hajiya na gode.

Washegari ba ni da halin fita tunda

Ahmad zai dawo gida a ranar, don

haka tashi nayi don nayi mishi shiri.

Da aikin wurinshi na fara. Na

wanke bayan-gida, nayi shara ko ina

fes sannan na canza labilayen dakin

gaba daya na zuba wasu na kira mai

wanki na ba shi.

Na sake shimfida ko ina ya yi kal,

sai kamshi kawai. Na dawo sashena


73

 

na shirya mishi abinci na yi mishi

fruit salad sannan na shiga bandaki

nayi wanka nayi kintsi na sosai.

Nayi kwalliya mai kyau ta riga da

siket, ina gamawa ko sai ga isowar

motarshi cikin gidan.

Sai da ya shiga wurin Hajiya kamar

yadda ka'idar shi yake, sannan ya

shigo wurina da gudu na isa inda yake

na rungume shi ina mishi oyoyo.

Yana dariya ya ce, Anya Hauwa'u

ce kuwa ba canje aka yi mun ba da ba

na nan?

Na ce, Canje kuma 'Yallabai? Ya

ce, Eh mana naga ne sai wani

danyacewa ki ke yi kina dawowa 'yar

karamar yarinya.

Sashen shi muka shiga don ya yi

wanka, yana ganin irin gyaran da na

yi wa wurin ya ce,  "Wow! Ke da


74

 

waye ku ka yi wannan aikin

Hauwa'u?

Na ce, "Da waye ka ke tsammanin

zan yi?" Ya dan yi shiru zuwa can ya

dan kada kai ya ce, "Ke kadai ko?"

Na ce, Yauwa ashe ka gane kenan?

Ya ce, To Allah yayi miki albarka. Na

wuce shi na shiga bandakin shi ina

hada mishi ruwa da turarukan wanka.

Ya shiga ni kuma na fito na ciro

mishi jallabiya ruwan kasa saboda

sanin da nayi zai fita zuwa Masallaci

idan anyi magriba.

Yana cin abinci ina zuba mishi

yana ba ni labarin garinsu da mutanen

garin. 

Ya ce, "Sai kin haihu zamu je su

ganki suga abin da muka samu. Ya ce

kin ga ma na manta jiya da muka yi

waya ban tambaye ki su Umma ba.


75

 

Na ce, Ai ma ban je ba. Ya kalle ni

ya ce, Ba ki je ba kuma? Na ce, Eh. to

saboda me? Nayi shiru ban ce mishi

komai ba.

Ya ce, Ke dinnan fitanarki yawa ne

da ita, da ban bar ki ba da har yanzu

kina yi mun mitar na hana ki zuwa

gida.

Ya fita sallar Magriba ya wuce

wurin Hajiya, bai dawo ba sai da aka

yi sallar Isha'i sannan ya shigo.

Tashi ki shirya muje gidan tare.

Sannan ya wuce sashenshi. Ya dawo

sanye da jamfa da wando na yadin

material din maza yana rike da

mukulln mota a hannunshi.

Ni ma yadin material na saka mai

hadari ya kuma yi mun kyau sosai.

Muka fito tare muka shiga wurin

Hajiya don yi mata sallama.


76

 

Ta ce, lna zuwa haka a daren nan?

Ya ce, "Yar wata unguwa zata raka

ni. Ta ce, To a dawo lafiya. Muka

fito.

A wani babban shago ya tsaya ya yii

siyayya mai yawa, sannan muka wuce

gida.

Hira muke yi sosai da Umma shi

kuwa yana wurin Babana ba mu dawo

ba sai wajen karfe goma na dare.

Tashi nayi naga jini kadan-kadan

yana fitar mun, sai dai ban kula na

gani ba sai bayan da Ahmad ya tafi

kasuwa.

Bana son daga mishi hankali, don

haka nayi nufin bari sai ya dawo naayi

mishi bayani.

Nayi ta aikace-aikacena ba tare da

wani abu a raina ba, tunanina dai bai

wuce laulayi irin na ciki ba.


77 

Sai da na gama ayyukana na shiga

bayan gida da nufin yin wanka, sai

kawai na ganni kace-kace cikin jini.

Sauri nayi na fito na dauki waya na

sanarwa Ahmad cewa ina son Zuwa

asibiti, ya ce lafiya? Na ce ch, ba na

dai jin dadi ne kawai, ya ce to Allah

ya sauwake.

Bala ya kai ni asibiti sai dai tun

kafin nan a takure nake cikin sauri

aka kai ni dakin Likita sai dai gwajin

farko ya tabbatar mana cikin ya

lalace, ya fita daga mahaifa dole a

cire.

Duk da halin da nake ciki a haka na

daure na kira Ahmad.

Cikin kankanin lokaci ya iso

asibitin, sai dai duk da saurin da ya yi

har an shigar da ni don wanke mun

mahaifa.


78 


Duk da kokarin da nayi tayi na

hana kaina kuka kasa daurewa nayi da

Ahmad ya iso kaina.

Wannan karon ma bari nayi na ciki

wata hudu har da sati biyu, kamar dai

wancan kenan.

Kwana nayi a asibitin kowa kuma

yazo duba ni har daga gidanmu.

Likita ya shigo saboda sallama ta da

za a yi Ahmad yana yi mishi wasu

yan tambayoyi.

Ya ce, To dai a fayil dinta na ga ta

samu matsala makamanciyar wannan

shima a watanni hudu, don haka

tunda ga abinda ka fada zamu sake yi

mata scarming don mu gani ko da

matsala.

Likitan ya jawo wata 'yar takarda

yayi rubutu ya bamu. Ahmad ne da

kanshi ya kai ni wurin scarning din


79

 

muka dawo Likita ya duba ya ce, "To

a gaskiya ta samu matsala ne a

mahaifa saboda jijigar farat-daya da

mahaifarta tayi a wancan karon.

Saboda irin faduwar da tayi, hakan

ne yasa mahaifarta ba za ta iya rikke

wani ciki da zai yi fiye da watanni

hudu a mahaifarta ba.

Saboda bakin mahaifarta da ya riga

ya bude. Kuma shawarar da zan ba ku

a yanzu shi ne, kafin a san matakin da

za a dauka a kan matsalar, ta dan yi

hutu.

Don kuwa idan tayi wani cikin ma

a yanzu abinda zai faru kenan.

Dawowa gida muka yi jikinmu a

sanyaye, ni kam Ciwo ne ya rufe ni

jinya sosai Ahmad kwata-kwata ranar

bai fita kasuwa ba.

80 


Bai kuma fadawa kowa abinda

Likita ya ce ba. Kwana biyu ko

abincin da zan ci daga wurin Hajiya

ake kawo mun.

Kullum kuma Ahmad zai ba ni

hakuri saboda lurar da yayi na dan

saka damuwa a raina.

Duk kokarin da nayi kada ya

fahimci wani abu kasawa nayi. Yau

ma yana zama zai fara mun magana

kuka na kama yi.

Sai da nayi ya ishe ni sannan na

share hawayena, babu abinda ke tsaya

mun a rai naji zuciyata ta baci irin na

tuna 'ya' yan Ahmad ne suka yi mun

wannan sanadin.

To tambayar ita ce, shin idan da ni

ce nayi wa wani a cikin su haka anya

zan zauna lafiya kuwa?

81 


Amma gashi nan ni sun yi mun sun

zauna lafiya, sun ma mancc in ban da

shi Ahmad da yake ba ni hakuri. 

Duk da warkewan da nayi a duk

lokacin da na tuna ina jin wani iri na

kuma kasa sakewa nayi harkokina

kamar da.

Ko shi Ahmad din ya lura ya gane

hakan, don yau ma muna zaune a

falonshi muna kallon labarai ya Juyo

yana kallona.

Hauwa'u magana nake so nayi

miki. Na lura duk tsawon lokacin nan

har yanzu ba ki saki jikinki ba. 

Na kuma tambaycki shekaran iya

ko wani abu na damunki ne kin ce

a'a, lafiyarki kalau.

Ina so ki san wannan abun ba ke

kadai ya samu ba har da ni, amma


82 

kuma kin takura ni na rasa walwalar

da a da nake farin cikin samu.

Idan ni ne nayi miki wani abu ki

gaya mun na gyara, idan kuma a kan

matsalar nan ne ina so kiyi hakuri.

Ina kokarin a wannan watan da zai

kama idan zan yi tafiya mu tafi tare

saboda wannan matsalar, sai ki ga

Likita a Dubai."

Ban ce mishi komai ba, amma nayi

kokari wajen ganin na rage takura ko

don saboda Ahmad.

Sai dai har karshen wata yazo ya

wuce Ahmad bai yi tafiyar ba, bai

kuma ce mun komai ba.

Muna kwance a dakinshi da

daddare a daren da ya dawo daga

Legos dauko wasu kayan shi da suka

shigo.


83 

Nayi mishi maganar tafiyar da ya

ce zamu yi don ganin Likita. Ya ce,

"Kiyi hakuri Hauwa'u, ina nan ina

wasu shirye-shirye ne kawai."

Sai dai ba a wani jima ba ya shirya

ya tafi Dubai ya dawo ba tare da ya ce

mun komai ba.

Na shiga dakinshi na same shi

zaune ya baje takardu, lissafi yake yi.

Na zauna a gefe ina jiranshi ya gama

shiru bai gama ba har na gaji' na mike

na kwanta nayi barci.

Washegari tun da Asuba yayi shirin

shi gaba daya alamar daga wurin

Hajiya zai wuce.

Haka ina ji ina ganin babu yadda

zan yi ya fita. Da daddare kuwa da ya

dawo sai da na gama mishi komai

sannan na kwashe kwanukan.


84 

Wai kafin naje na dawo nayi mishi

maganar da ke Cina a zuciyata nan ma

dawowa nayi na samu wai Hajiya ta

ira shi.

Zama nayi daram a kan kujera ina

jiran shigowarshi, bai shigo ba sai

wajen karfe goma da kwata.

Har yanzu ba ki yi bacci ba?" Na

ce, "Eh kai nake jira." Ya ce, "Akwai

magana kenan? Na ce, "Eh."

Ya gyara ya kwanta ya ce, "To ki

barta gobe kafin na fita kasuwa sai

muyi."

Na ce, Idan kuma a wurina tana da

muhimmanci fa? Ya ce, "Komai

muhimmancinta ki barta sai gobe, don

a yanzu na gaji."

Wani irin gululun bakin ciki ne ya

tokare mun makogorona. Da kyar

nake iya numfashi.


85 

Tashi nayi na dawo dakina na hau

gadona na kwanta. Sai dai ban iya yin

barcin ba.

Ji nake yi kamar na koma na samu

Ahmad muyi duk wacce zamu yi da

shi daren nan amma ba zan iya ba.

Ko wani sauraron shi ban yi ba da

safe haka nan shi ma bai bukaci ya ji

maganar da nake son yi da shi ba.

Da dai ya gama shirinshi ne zai fita

ya leko dakin.

"Hauwa'u ina son burabusko da

miyar bindi".   Na ce, To babu tsakin

shinkafa." Ya ce, "Ki karba a wurin

su Hajiya." Ya tafi.

Babu abinda na tsana yanzu a

rayuwata irin zuwa wajen su Hajiya.

Tun da dai gaisheta ya zama mun

dole, to kullum da safe ina zuwa


86 


amma baya ga haka bana komawa sai

wata safiyar.

Sai da aka yi sallar Azahar sannan

na dauki roba na shiga wurin Hajiyan

na gaya mata ina son tsakin shinkafa.

Ta kalli Zainab ta ce, "Zainaba

tashi ki debowa Mamanku tsakin

shinkafa."

Ta dago ido ta kalle ni, sannan ta

ce, "Maman wasu dai Hajiya, ammna

ban da mu."

Ta ce, "To naji bana dai son rashin

kunya, karbi ki debo mata. Kin dai

kusa tafiya Makaranta a huta."

Ta ce, "Ai idan na ganc tafiyata zai

sa wasu murna ma sai na cc na fasa."

Ta dawo da tsakin a hannunta ta

dangwarar a kasa.

Ban tsaya sauråronta ba, dauka

nayi na yi tafiyata.

87 


Zainab a yanzu ta rubuta

jarrabawarta na gama makaranta

sceondary, Jami'a ake neman mata

har ma an samu.

Dawowa wajena nayi na shiga

kokarin ganin na kammala cikin

lokaci, kuma nayi sa'a yayi kyau ya

yi dadi.

Ga kamshi ko ina a cikin gidan. Ina

gamawa na shiga bandaki nayi wanka

na fito kenan naj1 motsi a falona.

Don haka na fito falon bayan na

sanya zulumbun hijabina don ganin

ko waye.

Zainab ce rike da tircn abincin

Babansu, gabaki dayan shi zata fita.

Sa hannu nayi na rike na ce "Yau

kam a'a, abin ya ishe ni haka ba zai

yiwu ba.


88 

A duk ranar da ki ka ga kina da

bukatar cin abincina to rinka gaya

mun sai na rinka saka sanwa da ke.

Ba haka kawai idan na gama girki

ki saka hannu ki sunkuci na mijina

kiyi gaba ki bar ni da dora sabo ba."

Ta zuba mun ido tana kallona, nimna

ita nake kallo, don na lura su gaba ki

dayansu ba su san zuru ba.

Kuma a gaban kowa sai Zainab ta

caccaba mun magana ba za a ce

komai ba.

Ba tun yau ba lokuta da dama sai

na gama abinci sai tazo ta sunkuta

gaba daya ta tafi da shi wurinsu ta ci

1ya cinta ta rabar da saura.

Wani lokacin ma ko rabi ba a ci sai

ta bar shi haka ya lalace, sannan ba za

ta dauko kwanukan ta dawo da shi ba

sai dai ni nabi bayan su.


89

Sau daya Hajiya bata taba yin

magana a kan hakan da take yi ba,

duk da tasan abincin danta Zainab

take dauka.

Kallon da take yi mun ne ya ishe ni

nayi nufin karbe tiren, sai kawai

yarinyar nan ta kabar da tiren gaba

daya abubuwan ciki suka watse.

Abincin ya zube a kasa, sannan tayi

murmushi ta raba ta gefena ta wuce.

Zubawa abincin da ya tarwatse din

ido nayi ba na ko kyaftawa.

Ban taba ganin danyen rashin

mutunci irin wannan ba.

Cikin dakina na koma na sanya

doguwar riga na futo zuwa wurin

Hajiya don na gaya mata abinda ke

faruwa.

Na shigo na zauna a kasa zan fara

magana sai ta ce "Dakata! Yau kuma


90


abin naki har ya kai ma ki hana

Zainaba abinci?

Ta dauko kuma kin biyo ta kin

kifar. Me ki ke nufi da abinda ki ka

yin?

Kin taba siyo abinci kin shigo da

shi gidan nan ne da ki ka samu damar

hana wani?"

Na ce, "Hajiya..".  "Bana son jin

komai daga bakinki, nasha gaya miki

ba sau daya ba ba sau biyu ba cewa

duk abinda za ki yi a gidan nan to ya

tsaya tsakaninki da wasu amma kada

ki tsallako hurumina, don ba za ki ji

da dadi ba.

Ya ya za ki hanata cin abincin da

ubanta ya kawo ya ajiye takamar kina

matarshi?"

91


Tun ina daurewa bacin raina har

ban san sanda na fara zazzago

maganganu ba.

"Ai tun farko da nazo gidannan na

fara kawo abinci sashen nan aka ce na

daina don kuwa akwai mai girki.

Me yasa tunda haka ne idan tana

son abincina ba za ta fada mun tun da

wuri ba sai na girka da ita, sai ta bari

na gama tazo ta dauke gaba daya

haka ake yi?

Duk hakurin da nake yi da yarann

nan bai isa ba kullum kokarinsu bai

wuce na ganin sun kure ni ba.

Menene na yi musu?

Tunda na fara magana har na gama

Hajiya bata sake cewa komai ba, sai

kallona kawai da take yi.

Zuwa can ta ce, Lallai kin isa, ni

ki ke gayawa irin wadannan


92

 

maganganun? Dama ai biri ya yi

kama da mutumn.

Tun kwanakin baya na gane ya ba

ki isasshen damar da ta wadace ki. To

amma ba laifinki ba ne.

Tashi ki ba ni wuri, bari yazo ya

same ni mu san wacce muke ciki da

nida shi."

Mikewa nayi na dawo dakina na

kara tsallake abincin a wurin na shiga

uwar dakina na zauna.

Ni kaina na gane nayi kuskure

amsawa Hajiya da nayi, to amma ya

ya zan yi da raina?

Rashin 'yancin yayi yawa, ace wai

har a kan budurwar yarinya mai

shekara goma sha shidda kamar

Zainab za a zaunar da ni a titsiye ni

wai nayi laifi!


93 

Kawai takamar ina auren ubanta

bayan da za a bi Silsilar abin za a iya

fahimtar ba ni ba ce mai laifin.

To amma saboda daurin gindi da

Son kai sai ya zama komai suka yi

daidai ne.

A madadin abubuwa su gyaru

kullum kara cabewa suke yi?

Kamar yadda ya saba dawowa haka

ya dawo yau ma. Ko inda yake ban je

ba ballantana na ba shi wani abu.

Don kuwa babu, na kuma san an

gaya mishi komai da ya faru.

Karfe tara har ta wuce ina zaune a

kan sallayata da nayi sallar Isha'i a

kai ban tashi ba.

Jiran kawai abinda zai biyo baya

nake yi. Bai shigo dakin ba sai wajen

karfe goma na dare.

94 


Yadda nayi zaton zai shigo ba haka

ya shigo mun ba. Ya karewa abincin

da har yanzu yake shimfide a kasan

falon da food flask din da kuma

fasassun plates din kallo.

Ya sunkuya ya kwashe plates din

da kofunan da suka faffashe ya zubar

a abin zuba shara na nan kicin.

Sannan ya fito ya dawo da abin

kwashe shara da tsintsiya yasa ya

kwashe ya gyara wurin tsaf, sannan

ya wanke hannunshi ya zo ya zauna a

inda nake muna fuskantar juna.

"Ba kya jin maganata Hauwa'u, ko

nayi miki magana ba kya ji. me ya

hada ki da Zainab?"

Nan take na fahse da kuka saboda

karayar da nayi. Nayi kukana sai da

na gaji nayi shiru, sannan nayi mishi

bayanin komai.

95


 Tun daga lokacin da Zainab ta tsiro

da abubuwanta har zuwa yau abinda

ya faru.

Ya yi shiru zuwa can ya ce, "Me

yasa ba ki taba gaya mun ba? Na

kalle shi.

"Na gaya maka fa ka ce? Idan na

gaya maka me za ka yi? Na taba gaya

maka wani abu da aka yi mun ka

dauki mataki?

Sannan ko karata aka kawo

wurinka ko ni ce da gaskiya ko ba ni

ba ce ba ka taba saurarona ka ji ta

bangarena ba.

Ni dai a kullum ni ce maras

gaskiya,  'ya'yanka kuma masu

gaskiya. A ina ne aka ce a yi haka don

daidaita zaman lafiya?


96 

 

Ni kenan kullum ina da matsala da

'ya'yan miji, to menenhe aibuna? Me

nayi musu?"

"Za ki iya zama a Kano?"

Tambayar ta yi mun kwatsam! Na bar

kukan da nake yi a take na kalle shi.

"Ina da gida a Kano, idan kin yarda

za ki zauna a can sai na mayar da ke

can tunda ina shirye-shiryen bude

wata harkar a Kano kwanannan.

Ina son zama da ke Hauwa'u. Ni

kaina nasan ina da matsala a cikin

gidan nan. Kiyi hakuri a yanzu ko

meye Zainab zata yi miki ki daure ki

jure saboda ni da ke mu samu biyan

bukatarmu."

Hankalina ya dan kwanta, ya ce

"Ina neman alfarma idan ba zan

takura miki ba?"


97 

Na ce, "Ta meye?" Ya ce, "Abinci

nake so ki samar mun wanda zan ci,

yunwa ta dame ni."

Tashi nayi a daren nayi wa Ahmad

dan girki mai sauri yaci sannan muka

kwanta.

Tun daga nan na samu sassaucin

damuwa, sai dai Hajiya ta daina amsa

gaisuwata, duk da haka kuma ban

daina zuwa gaisheta ba.

Zan zauna na kai mintina goma

bata saurare ni ba. Shi ma na lura

yana da 'yar matsala amma tunda dai

bai bude bakinshi ya fada mun ba sai

ban tambayar shi ba.

Na dai tsaya tsayin daka wajen

ganin bai kuntata da yawa ba, don

nasan matsalar ba ta wuce ta Hajiya

ba.


98 

Ba a fi wata daya zuwa kwanaki

arba'in ba sai shirin Ahmad ya

kammala na bude babbar harkarshi ta

kasuwanci a Kano.

Har yaje ya yi sati daya a can don

ya tabbatar komai ya daidaita, sannan

ya dawo.

Muna kwance a dakinshi yana bani

labarin yadda abin yazo cikin

gagarumar nasara, ni kuma dokina sai

karuwa yake yi zai bar zama da su

Hajiya da 'yan fitinannun jikokinta,

zan koma Kano tare da mijina.

Ina ta ayyano irin tattalinshi da zaan

kara yi da irin abubuwan da zan yi na

ci gaba don kaina.

Don kuwa nima yanayin

kasuwancin Ahmad yana ba ni

sha'awa, har nima na kan yi tunanin a


99 


matsayina na mace idan zan gwada

babu mamaki nayi nasara.

Na ce, Kaga idan muka koma ni ma

sai na gwada kasuwancin mata na

cikin gida.

Kallona ya yi cikin mamaki.

"Kasuwanci kuma Hauwa'u?

Na ce, "Eh mana, na zannuwa da

gwala-gwalai irin naku ba."

Shiru yayi yana kallona, ya ce

"Ashe kina sha'awar kasuwanci?"

Na ce, "Eh, zama da kai ne yasa

hakan, da can ba na yi."

Ya ce, To bari kayan da nayi oda

wannan watan su zo sai na diban miki

a ciki ki gwada muga irin taki nasarar.

Kin san mata da yawa suna karban

kaya a hannuna kuma suna samun

riba ba kadan ba.


100 


Amma abin da na lura da shi shi ne,

sai wacce ta iya rikici saboda siyan

kayan gida yawanci bashi ne.

Ke kuma ban ga wannan a tare da

ke ba."

Ba mu yi bacci ba sai karfe daya

saboda 'yan hirarrakin da muke yi.

Washegari bai kintsa da wuri ba

saboda bakin da yayi abokan

kasuwancinsa.

Sai kusan sha daya na rana. Ya

shigo dakina rike da mukullin

motarshi yana ba ni sakon da zan bai

wa Bala direba idan yazo, saboda

haihuwar da matarshi tayi.

Sannan ya shiga wurin Hajiya.

Kwanciya nayi don na dan yi barci

kafin Azahar tayi. Sai dai ban ko yi

nisa ba naji sallamar Larai.


101


Daga cikin dakin na daga murya

ina tambayarta ko lafiya? Ta ce,

Lafiya kalau Hajiye ce take kiranki.

Gabana ne ya fadi, to menene

kuma? Ba dai naje na gaisheta ba.

Nayi sallama a kofar dakin na shiga.

Har yanzu Ahmad yana nan bai fita

ba, yana zaune can gefe a asa,

kanshi kamar zai dunguri kasa saboda

irin sunkuyon da ya yi.

Jikina a sanyaye na zauna a gefe

nesa da inda yake.

"Ina ce dai ita ce wannan?"

Hajiya ta fara magana.

"Yarinyar da ko darajar sauran

matanka bata kai ba. A kanta ne kuma

nake baka umurni ka ke kin bi.

Abinda ban taba zaton zaka iya yi

ba shi ne take umurnina. Na kyale ku


102


na zuba muku ido amma gaba

dayanku ba ku fahimci hakan ba.

Nan wurin nan kazo mun da

maganar za ka kaita Hajji a bana na

ce a'a banyarda ba, don ina ta binka

ka biya wa Lado dan kanina har

yanzu ba ka biya ba kana daga

tafiyar. 

Sai ka dawo min da maganaar

zuwan ku Dubai wanda wannan ma

duk wani salo ne na kin bin umurnin

da na bayar din.

Ka dai nuna mun a yanzu kai ma ka

girma. Ba a wani dauki lokaci mai

tsawo ba yarinyar nan ta zo har dakin

nan ta zage ni.

Na gaya maka ban ji ka dauki

matakin komai a kai ba. A jiya kuma

abinda ka zo da shi shi ne za ka daukec

ta ku koma Kano da zama ko Amadu?


103


To bari ka ji wata magana, idan ba

mantawa nay1 ba, ko a ranar da na

haife ka, nayi nakudar ka ne ni kadai

a dakina na haife ka na yanke maka

cibi da kaina.

Sannan ne nayi maka wanka kafin

wasu ma daga gidan suka san na

haihu, kenan ka gani babu wanda ya

taya ni.

Don haka ba zan haifi da nayi

tarbiyyarshi da irin abubuwan dadi da

wahala da dawainiyar da nasha wata

tazo ta kwace mun shi rana tsaka ina

kallo ba, babu ita.

Zagina da tayi ba ka ce komai ba

saboda ka daina gudun bacin raina sai

nata, to na yafe maka amma ko don

na yi wa tufka hanci ya zama hakan

bai sake faruwa ba.

104


Ga takarda da biro nan na baka

rubuta takardar sakin aurenta

yanzunnan ka bata, auren nata ya ishe

ni haka."

"Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un."

A bayyane na furta saboda firgitan da

nayi. Saki kuma? Wannan wacce irin

musiba ce?

Na kalli Ahmad wanda har yanzu

yake a yadda na same shi, sannan na

kalli Hajiya.

Kamar kullum tana zaune ne a kan

dardumarta ta sallah, sanye da

zurmemen hijabinta.

Zan iya cewa a tsawon zaman da

nayi a gidan na watanni ashirin ban

taba ganin ranar da na ganta babu

hijabinta ba.

Sai nayi sha'awar ace ita din mata

ce mai sassauci da rangwame a kan


105 


al'amuranta, tunda kowa ya shaideta

mace ce mai yawan Ibada.

To me yasa ita din halinta ya zama

haka. Danta da yake matukar

kokarinsa wajen ganin yayi mata

biyayya ya kaucewa bacin ranta ya

batawa wanda ya bata mata.

Danta da a kullum yake fadin irin

alherinta da dawainiyar da tayi da shi

wajen ganin bai yi maraicin uba ba.

Danta da a kullum yake fadin cewa

ita ce abinda ya fi so da girmamawa a

duniya shi ta ke yi wa irin wannan

kuntatawar da kuma rashin sassauci?

Lallai halinta sai ita.

Take na fara kokarin rarrashin

zuciyata don ta samu sassaucin

tsananin da zata fuskanta a gaba.


106


Na rinka tunanin abubuwan da zan

yi wadanda za su taimaka mun a

rayuwata da zan shiga nan ba da

dadewa ba.

Tunda nasan babu makawa Ahmad

zai aikata abinda Hajiya ta umurce shi

tunda da bakinshi ya tabbatar mun

cewa ita din bata taba bashi wani

umurni da ya ketare ba, face ya

aiwatar da shi komai tsananin shi.


**   **   **

Ina kwance a kan shimfidaddiyar

katifata da ta sha lallausan shimfidan

zanin gado na yadin (American bed

sheet) dan asali da bargonshi.

Na kai hannu na shafa yadin zanin

gadon tare da tuna ranar da na fara

shimfida shi a kan gadona, lokacin da


107 

nake ganiyar cin amarcina a gidan

Ahmad.

Na runtse idanuwana da karfi

saboda wasu tunane-tunane da suke ta

kawowa zuciyata ziyara.

Tunanin abubuwan da suka zo suka

kuma wuce tamfar a mafarki tamfar

dai ace wani barci kawai nayi mai

dadi na kuma farka.

A da can, ban taba tunanin haka 

al'amurana za su kasance ba. A

matsayin shekaruna a yanzu ashirin

da uku kacal a duniya.

Amma har an fara kirga mun

aurena. Yanmata da yawa sa'o'ina ba

su ma yi auren ba, ballantana har ace

ya kare.

Take kuma nayi hanzarin yin

Istigfari da na tuna akwai wasu mata

kuma da suke zuwa duniya su gama


108 

rayuwarsu a cikinta su koma ga

mahaliccinsu ba tare da sun yi auren

ba.

Don haka ba zai yiwu nayi wa

Ubangijina butulci ba, a kullum zan

kasance mai yawan godiya a gare shi

bisa irin yawa-yawan n imomin da

ya yi mun a rayuwata.

Ban kuma dauka wannan

mummunan jarrabawa ba ce sai na

dauka cewa ni kuma tawa kaddarar

kenan ba kuma zai yiwu na tsallake

wata kaddara tawa ba face kawai na

roki Ubangijina da kowacce ta tashi

zuwa mun, to ta zamto mai sauki.

Ya kuma ba ni ikon dauka don

Imanina ya zamto cikakke tun da aan

gaya mana cewa Imaninmu ba zai

cika ba sai mun yarda da kaddararmu

ta alkairi ko wanin alkairi.


109 

Bai kuma jarraba ni da ciwo ba ko

wanina ko kuma ya jarrabe ni da rashi

na wata gaba a jikina ba.

Sannan da aurena ya mutu a farko

sai ya bani wanda ya fi mun na

farkon, to ina rokon shi a yanzu ma

ya bani wanda ya fi mun na biyun.

Sai dai tunanina yana kawowa

daidai nan sai naji gabana ya yanke ya

fadi ras!

Kenan na rabu da Ahmad ba zan

sake komawa gidanshi ba? Ina son

mijina shima kuma yana sona.

Mahaifiyarshi ce matsalarmu, don

kuwa idan ba don shigarta cikin

lamarin ba to don ta ya'yanshi zan

iya zama da su a yadda suke, tunda

ina son ubansu.

Sabanin matsalata da Ishak wanda

a lokacin da aka yi aurena da shi


110 

shekaruna goma sha bakwai ne a

duniya.

Ba komai yasa a ka yi auren ba

face rashi da mahaifina yake ciki ga

kuma kwadayinshi a kaina na ganin

ni din nayi karatu.

Ya dauke ni ya ba shi ni ba tare da

wani dogon nema ko bincike ba,

saboda jin irin alkawuran da yayi a

kaina.

Alkawuran da suka zamo shi ne

sanadin faruwar auren da kuma

rugujewarshi.

Idan kuma da ace zaman da yayi da

ni akwai adalci a ciki ko kuma

sassauci ko tausayawa wadanda

wadannan abubuwa sune suka hadu

suka zamo soyayya da kauna to duk

da da sauki.


111 

Idan har akwai abinda nake tunawa

da Ishak da ke sake sani kin shi to bai

wuce dukan rashin tausayi da yake yi

mun ba.

To sai na auri Ahmad, mutumin da

ya an yanci na walwala. Nayi

rayuwar aure irin wacce ban taba

mafarkin ana yin irinta ba a gidan

aure.

Saboda irin sona da tattalina da

mijina yake yi. Ya nuna mun cewa ni

din ina da matukar muhimmanci a

wurinshi.

Ya kuma so ni so na hakika, ya

mutunta iyayena da yan uwana, ya

guje mun bacin raina, ya tattali farin

cikina.

Amma sai gashi 'ya'yanshi da

mahaifiyarshi sun ki yarda su bar ni


112 

na zauna da shi duk da hakuri da

halinsu da nake yi.

Idan har ina da laifi ko kuma wani

ganganci da na aikata a lokacin da

aurena na fari ya mutu, to a wannan

karon kam nasan ba ni da wani laifi.

Sai dai na kasa hakura, fatana bai

wuce da ni da shi mu samu maslaha

kan al'amarin aurenmu ba.

Tunda dai an yi sa'a saki daya ne a

tsakaninmu.

An kwaso kayana tas daga gidan

Ahmad, ba wai don na hakura da

zama da shi ba.

Sai dai kawai don jiran shawarar da

shi da kanshi zai zartar a kan maganr.

Sakon da ya turo mun kenan a waya

daren da na dawo gida.


113 

Cewa na saurare shi kan shawarar

da zai yanke na neman mana mafita

nan da kwanaki uku.

Sai kuma kudi da suka shigo

account dina masu auki.

Ta bangaren Babana dai abin ba a

cewa komai, don kuwa bakin cikinshi

ba ya' misaltuwa.

Umma kam har a wannan karon ba

ta ce komai ba, harkokinta take yi.

Nayi matukar kokarin ganin ban

takura kaina da tunane-tunane ba, ta

hanyar shiga duk wani hidima na gida

da ake yi.

Har girki na karba ni nake yi da

sassafe kan bakwai zuwa bakwai da

rabi na kammala abin karyawa.

Idan na gama kumana zauna taya

Umma saye da sayarwanta, muna

kulla na kullawa.


114 

Babbar matsalata ba ta wuce na

rashin barciba. Sai nayi matukar sa'a

ne kwarai nake samu na dan runtsa.

Al'amurana ne kawai za su yi ta

dawo mun rayuwar da nayi da Ahmad

mu'amallarshi da kuma yadda yake

harkokinshi a cikin gidanshi.

Daga manya zuwa yara da kuma

masu yi mishi hidima bisa sassauci da

ganin mutuncin kowa.

Ranar shi da farin cikinshi dakuma

fushin shi da kuma wasu abubuwa

masu dama. 

Me yasa mutane ba su da tausayi

ne, babu sassauci a cikin al'amura

amma kuma mu sai muce muna

neman sassauci a wurin Ubangijinmu.

Bayan mun san shi ne ya yi umurni

da mu yi wa na kasa damu sassauci da

adalci.


115 

Duk da abin da Hajiya tasa danta

ya yi mun zama dashi bai fita a kaina

ba, har yanzu kuma jiran shi nake yi

naji abinda zai ce.

Satina uku cif a gida Ahmad yazo

sai da ya gaisa da Babana da Umma

sannan na same shi a zauren gidanmu,

bayan Babana ya aiko Tasi'u cewa

naje na same shi.

Cikin kyakkyawar shiga na dogon

hijabi da na dora akan kayan dake

jikina dinkin atamfa riga da zani na

same shi.

Nayi matukar kokarin daurewa ta

ganin bai fahimci wani abu game da

halin da na shiga ba.

Kaina na sunkuye na gaishe shi

bayan na zauna akan shimfidar

tabarmar da aka yi mishi.


116 

Ya amsa cikin yanayin shi kadaran

kadahan. Ban kalle shi ba na ce, "Ya

su Hajiya?"

Ya dan yi jim bai amsa ba kafin ya

ce, "Suna nan kalau." Abinda a sani

kuma shi ne kallona yake yi duk da

kin yarda mu hada ido da nayi ta

hanyar kallon 'yan yatsun hannuna da

na yi wa lalle a safiyar yau.

"Nayi tafiya ne Hauwa'u, shi ne

abinda yasa ba ki ganni ba, tafiyar ta

dauke ni tsawon kwanaki goma sha

takwas, sai a daren jiya na dawo. Don

haka kiyi hakuri."

Shi dai mai yawan bada hakuri ne,

abinda zuciyata ta ke fada mun kenan.

To amma hakurin da ya bani a yanzu

menene ma'anarshi?


117 

Nayi hakuri ne a kan sakin da ya ya

mun, ba zai iya sake zama da ni ba ko

kuwa nayi hakuri ne na koma dakina?

A yanzu ne nasan na daga kaina na

kalle shi muka hada ido alamar ya

dade yana kallona hakan bai sa na

daina kallon shi ba babu abinda ya

canza a tare da shi.

Komai nashi yadda yake illa

idanunshi da launin su ya dan surka.

"Kiyi hakuri Hauwa'u." Abinda ya

sake fada kenan a lokacin da na

sunkuyar da kaina na hadiye wani abu

mai tsanani da ya rike mun wuya.

"Ina so ki san kowa da irin

jarrabawarshi a rayuwa ni tawa

jarrabawar kenan.

A tafiyar da nayi nasa mutane

daban-daban sun je don su taushi

zuciyarta har sau úku.


118 

A tunanina idan na dawo zan samu

wani dan sauyi daga gareta a game da

maganarmu wanda har da hakan ne

yasa na kara jan kwanakina na

dawowa.

Amma da na iso gida sai ban ga

hakan ba, don haka ne nayi

sammakon zuwa Kano a yau na gana

da kanin Mahaifina da a gobe nake sa

ran zai zo don ya samu Hajiyan."

Wani irin tunani ne ya yi gaggawan

shiga zuciyata da kwakwalwata, duk

da irin kwabata da zuciyata take yi sai

da bakina ya furta na ce.

"Idan a kaina ne ka ke tura mutane

wajen Hajiya to na roke ka ka daina

saboda kai da kanka ka gaya mun

cewa baka taba saba mata ba.


119 

Kenan kana so ka tilastata ta

hakura ta barka ka zauna da ni ba bisa

son ranta ba.

Wanda hakan ba zai sa ta yi

sassauci a kan kiyayyar da take yi

mun ba."

"Ba a kanki nake turawa ba, a

kaina ne saboda halin da na shiga,

barin ki gidan da kuma dawowan da

nayi ba kya cikin shi.

Gaskiya ki ka fada, ban taba yin

makamancin hakan ba sai a yanzu

wanda nasan ko ta sassauto ta hakura

to akwai wani tsanani da za ki iya

fuskanta.

Amma ina so nayi miki alkawarin

ba zai yiwu na barki haka ba.

Har a yanzu ina da niyyar dauke ki

a gidan zuwa Kano. A karo na biyu na


120 

dago kai na kalli Ahmad da har yanzu

yake kallona.

"Ba zan jagoranci batawarka da

Mahaifiyarka ba. Burina bai wuce

naga mun daidaita matsalolinmu sun

kare mun maida aurenmu ba.

Amma sai dai dama matsalar ba

tamu ba ce a inda matsalar take kuma

banga alamar wani sauki ba.

Ina rokonka kada ka tilasta

Mahaifiyarka zama da ni, don Allah.

Yadda a yanzu zuciyata ta hakura

ina rokonka kaima ka sakawa taka

Zuciyar sassauci.

Ina kaiwa nan na mike na shiga

gida, na fada kan katifata, kuka nake

yi irin wanda na dade ban yi ba.

Duk yadda na kai da son zama da

Ahmad abin ba zai yiwu ba.


121 

Ya zama dole na taushi zuciyata na

danganaa na fawwalawa Ubangiji

lamarinshi, don ya isar mun ya bani

abin yi.

Kwana nayi cikin wani yanayi da

ba zan iya kwatantawa ba, don saukin

abin ma nayi alwala nayi ta nafilfili

ina rokon Ubangiji sauki, da

kyakkyawan zabi.

A cikin satin ne aka kai sadakin

Yaya Auwalu abin da muka dauka shi

ne za su saka ranar auren da nisa.

Sai kawai muka ji sun saka sati

hudu kacal.

Muna zaune da Umma a tsakar

gida muna kullin kukar da Baba Ladi

ta aikowa Umma na siyarwa.

Na ce, "Amma Umma gaskiya

auren nan da suka saka ya yi kusa da

yawa."


122 

Ta ce, ""To ai na Allah ne, sannan

shi Babanku jiya ya same shi yayi

mishi bayanin komai.

Ya ce, Babu damuwa, don yana da

dan abin da ya dade yana tanadawa

don shirin auren.

Na ce "To ai shi kenan."

Umma ta ce, "To sannan kin san

shi hidima irin wannan ba ka shirya

mata nemi taimako kawai a wurin

Ubangiji idan tazo maka."

Na ce Haka ne, Allah yasa mu

gani lafiya." Ta ce, To amin.

Ke kuma Ubangiji ya baki mafita

kan wannan matsala da ta same ki na

mutuwar aure, ya ba ki miji nagari da

zai zauna da ke bisa adalci da

kyautatawa.

Ya kuma zaunar da ke a dakinki ba

tare da kin sake fitowa ba."


123 

Ban iya amsawa Umma ba, don

kuwa babu abin da nake so naji irina

ce Allah ya sassauta zuciyar Hajiya ta

bar ni na koma dakina.

Gidan Alhaji Ahmad Rufa'i, don

kuwa har a yanzu dinnan burina

kenan ko zuciyata tayi kamar ta

hakura sai kuma ta kara harzukowva.

Idan na tuna da irin rayuwar da

nayi tare da shi, daurewa kawai nake

yi nake rokon zabin alkairi a wurin

Ubangiji a lokacin da nayi sallah.

Amma idan da da hali to da rokon

komawa kawai na rinka yi ko da

hakan yana nufin batawar Ahmad da

Mahaifiyarshi.

To amma abinda na sani shi ne,

idan nayi haka ban yi mishi adalci ba,

don kuwa da kanshi ya gaya mun


124 

cewar ta sadaukar da farin cikin

rayuwarta domin shi.

Da kuma Yarshi da har a yau din

nan ban ma santa ba.

Sannan shi din ko ba don haka ba

mahaifiyarshi ce da Aljannarshi take

karkashinta.

Hakan da na sani shi ne yasa na

danne zuciyata na kara ba shi

shawarar cewa mu hakura har a jiya

da ya kira ni.

Don na tabbatar da ban zalunce shi

ba. Idan yaso ni kuma Allah sai yayi

mun kyakkyawan sakamako.

Shiri sosai muke yina shirin bukin

Yaya Auwalu. Ya hada lefenshi rigijif

gwanin sha'awa.

Samun Umma nayi na ce mata ina

so na kwashe kayan dakinta na zuba

mata nawa na gidan Ahmad.


125 


Ta kalle ni ta ce, To a wane dalili?

Ki zuba mun kayanki ke kuma idan ki

ka tashi yin wani auren ko kuma ki ka

koma dakinki fa?

Tunda ai ba gama iddah ki ka yi

ba. Na dan yi murmushi na ce,

"Umma ai komawata gidan Ahmad

abu ne mai wuya.

Tunda ba matsala ce a tsakanina da

shi ba, matsalar Mahaifiyarshi ce ba

ta kuma da niyyar yin sassauci a kai."

Ta ce, "Eh dai duk da haka ki bar

Umma ba sai kiyi mun addu'a ba

su ba ni da bukata." Na ce, "To ba

kawai idan na tashi yin wani auren

Allah ya bani wadanda suka fi

wadannan ba."

Ta ce, "To amin, amma dai duk da

haka ba zan saka kayan dakinki a


126 

nawa dakin ba, haba abin ma ai bai yi

tsari ba."

Da safe na shirya na gama aikina

da wurwuri na samu Babana na roke

shi ya bani izinin fita don ina da

uzuri.

Yayi shiru zuwa can ya ce, "To kin

dai san mutane ba a iya musu, ni fa

ina gudun magana.

Amma idan kin ga a matse ki ke shi

kenan kije amma kada ki dade."

Babban shagon da muka yi

siyayyan kayan aurena naje, mutumin

kuma ya gane ni.

Nayi mishi bayanin bukatata na son

canza kayan tare da neman sanin

cikon da zan yi mishi.

Cikin sauki da mutunci muka

daidaita na zabi wasu masukyau nayi


127 

mishi ciko na dawo gida da motar

kaya.

Su kuma suka saka nawa da damna

suke jingine a dakin su Tasi'u suka

tafi da su.

Sai da nasa a ka yi wa Umma

fentin dakinta tsaf sannan a ka zuba

mata sabbin kayanta a ciki.

Abin sai wanda ya gani, duk da irin

fadan da Babana yayi mun wanda bil

hakki abin ya ba shi haushi.

Ni a raina dadi naji don kuwa

nasan shima Babana idan ya hau

gadon zai huce.

Tun ana saura kwanakki ake ta

isowa yan biki kowa da shirin shi,

yan uwan Umma daga Gamawa da

na Babanmu daga birnin Kudu.

Su Inna Hadiza suka tasa ni a gaba

kowa da abinda yake fada.


128 

Ba ni da abinda zan ce musu don

na riga na gaji da bayani.

Da daddare Baba Ladi ta kira ni

dakin da aka sauketa da yake na Yaya

Auwalu ne tana yi mun magana ne ita

ma kamar kowa a kan rabuwata da

Ahmad.

Ban ce matakomai ba ta yi ta

maganganunta ina jinta. Ta ce, "Wato

ina miki magana kin yi shiru ko?

Na dan yi murmushi daidai wayata

tayi kara na dauka Ahmad ne.

Gabana ya fadi kamar kowanne

lokaci idan ya kira abinda ban san

dalilin faruwar hakan ba.

Nayi mishi sallama ya amsa.

"Ya ya shirin biki?

Na ce, "Mun gode Allah."

Ya ce, Wato sai a yanzu nasan

rashin kirkinki."


129 

Na ce, Da na yi me kuma

'Yallabai?"

Ya dan yi murmushin da na jiyo

sautinshi har a cikin wayar. Ya ce, "Ba

kya kirana Hauwa'u, ba ki damu da ni

ba a yanzu.

Yau kwana goma sha hudu ban kira

ki mun gaisa ba, hakan bai sa kin yi

tunanin ke ki neme ni ba.

Sannan sai aka saka auren Yaya

Auwalu ba ki saka ni cikin wadanda za

ki gayyata ba."

Na ce, "To kayi hakuri.

Ya ce, "An ya zan iya kuwa? Ina dai

so a duk lokacin da ki ka tunani ki rinka

yi mun adalci."

Na ce, "To."

Ban san adalcin me Ahmad yake

sonayi mishi ba. Sannan a tsakaninmu

wanene ya kamata ya yi wa wani

adalci?


130 

Ni ce zan yi mishi adalci ko shi ne zai

yi mun'? Wayar da na tsirawa ido ita ce

ta sa Baba Ladi fara sabuwar magana ta

bar wacce da take yi.

"Kina yi mishi irin wannan so me ya

fito da ke? A hankali na kalleta na ce

mata, "Mahaifiyarshi."

Da yamma kawai sai mota ta tsaya

aka fara sauke kaya, buhun shinkafa

biyar, sugar, filawa, wake, gero,

mangyada, manja, maggi, tumatir da su

albasa kwando-kwando. 

Sai cinyoyin bayana Saniya guda

biyu, sakon Ahmad ne. sai yadin

material 'yan asalin Dubai guda biyu,

boyil biyu.

Sai atamfa Erclusive guda biyu duka

a dinke. Takalma set kafa biyu da za su

iya shiga da kayan.


131

Sai gyale biyu, kayan duk a dinke

suke. Na zuba musu ido ina kallo. Wani

sanyi ya rinka kwarara a cikin zuciyata.

Shi ma har a yanzu da alama bai

fidda rai ba. Text nayi mishi na godiya,

duk da korafin da ya yi na ba na

kiranshi.

Don kuwa ban ga dalilin yin hakan

ba. Text din yana shiga sai ya kira, na

ce "Mun ga sako mun gode."

To fa! Lallai kam da gaske Ahmad

yake ba zai iya hakura da Hauwa'u ba.

To idan kuma Ishak ya ji labarin

abinda ya faru shi ma zai dawo?



Bari in dan huta a nan kafin na dora

daga baya, don haka sai mu tara a littafi

na (4) kuma na karshe insha Allahu.

Taku;

Haj. Hafsat C. Sodangi

(Mrs Yunus Abdullahi Dabai)

08025078968, 07035586299

132

No comments